Categories
A.M.

A.M. 23

1 Sai Bulus ya zuba wa majalisar ido ya ce, “Ya ku ‘yan’uwa, bautar Allah nake yi da lamiri mai kyau har ya zuwa yau.”

2 Sai Hananiya babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa.

3 Sai Bulus ya ce masa, “Kai munafiƙi, kai ma Allah zai buge ka! Ashe, wato kana zaune kana hukunta ni bisa ga Shari’a ne, ga shi kuwa kana yin umarni a doke ni, a saɓanin Shari’a?”

4 Sai waɗanda suke tsaye a wurin suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?”

5 Sai Bulus ya ce, “Ai, ban sani shi ne babban firist ba, ‘yan’uwa, don a rubuce yake cewa, ‘Kada ka munana shugaban jama’a.’ ”

6 Amma da Bulus ya ga sashe ɗaya Sadukiyawa ne, ɗayan kuma Farisiyawa, ya ɗaga murya a majalisar ya ce, “Ya ‘yan’uwa, ni ma Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ga shi kuwa, saboda na sa zuciya ga tashin matattu ne ake yi mini shari’a.”

7 Da ya faɗi haka sai gardama ta tashi a tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, har taron ya rabu biyu.

8 Sadukiyawa sun ce, wai ba tashin matattu, ba kuma mala’iku, ko ruhu. Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai.

9 Sai ƙasaitacciyar hargowa ta tashi, waɗansu malamai kuma na ɗariƙar Farisiyawa suka miƙe a tsaye, suka yi ta yin matsananciyar jayayya, suna cewa, “Mu ba mu ga laifin mutumin nan ba. In wani ruhu ne ko mala’ika ya yi masa magana fa?”

10 Da gardamar ta yi tsanani, don gudun kada su yi kaca-kaca da Bulus, shugaban ya umarci sojan su sauka su ƙwato shi daga wurinsu ƙarfi da yaji, su kawo shi a kagarar soja.

11 Da daddare sai Ubangiji ya tsaya a kusa da Bulus, ya ce, “Ka yi ƙarfin hali, don kamar yadda ka shaide ni a Urushalima, haka kuma lalle ne ka shaide ni a Roma.”

Ƙulla Shawara a Kashe Bulus

12 Da gari ya waye, Yahudawa suka gama baki suka yi rantsuwa, cewa ba za su ci ba, ba za su sha ba, sai sun kashe Bulus.

13 Waɗanda suka ƙulla wannan makirci kuwa sun fi mutum arba’in.

14 Sai suka je wurin manyan firistoci da shugabanni, suka ce, “Mun yi wata babbar rantsuwa, cewa za mu zauna ba ci ba sha sai mun kashe Bulus.

15 Saboda haka, yanzu ku da majalisa ku shaida wa shugaban soja ya kawo muku shi, kamar kuna so ne ku ƙara bincika maganarsa sosai, mu kuwa a shirye muke mu kashe shi kafin ya iso.”

16 To, ɗan ‘yar’uwar Bulus ya ji labarin farkon da za su yi, ya kuma je ya shiga kagarar soja ya gaya wa Bulus.

17 Bulus kuwa ya kira wani jarumi ya ce, “Ka kai saurayin nan wurin shugaba, yana da wata magana da zai faɗa masa.”

18 Sai jarumin ya ɗauki saurayin ya kai shi gun shugaba, ya ce, “Ɗan sarƙan nan, Bulus, ya kira ni, ya roƙe ni in kawo saurayin nan a wurinka, don yana da wata maganar da zai gaya maka.”

19 Sai shugaban ya kama hannun saurayin, ya ja shi a waje ɗaya, ya tambaye shi a keɓance, “Wace magana za ka gaya mini?”

20 Yaron ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kai musu Bulus majalisa gobe, kamar suna so su ƙara bincika maganarsa sosai.

21 Amma kada ka yardar musu, don fiye da mutum arba’in daga cikinsu suna fakonsa, sun kuma yi rantsuwa a kan ba za su ci ba, ba za su sha ba, sai sun kashe shi. Yanzu kuwa a shirye suke, yardarka kawai suka jira.”

22 Sai shugaban ya sallami saurayin ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka sanar da ni maganar nan.”

An Aika da Bulus zuwa ga Mai Mulki Filikus

23 Sa’an nan ya kira jarumi biyu ya ce, “Ku shirya soja metan, da barade saba’in, da ‘yan māsu metan, su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.”

24 Ya kuma yi umarni su shirya wa Bulus dabbobin da zai hau, don su kai shi wurin mai mulki Filikus lafiya.

25 Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka:

26 “Daga Kalaudiyas Lisiyas zuwa ga mafifici mai mulki Filikus. Gaisuwa mai yawa.

27 Bayan haka mutumin nan, Yahudawa sun kama shi, suna kuma gab da kashe shi, sai na yi farat na je da soja na ƙwato shi, saboda na ji cewa shi Barome ne.

28 Da ina so jin laifin da suke zarginsa a kai, sai na kai shi majalisarsu.

29 Na kuwa tarar suna zarginsa a kan maganar Shari’arsu, amma laifin da suka ɗora masa bai kai ga kisa ko ɗauri ba.

30 Da aka buɗa mini cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, nan da nan na aika da shi a gare ka, na kuma umarci masu ƙararsa su faɗi ƙararsu a gabanka. Wassalam.”

31 Saboda haka, sojan suka ɗauki Bulus, kamar yadda aka umarce su, suka kai shi Antibatiris da daddare.

32 Kashegari kuma suka bar barade su ci gaba da shi, su kuwa suka koma kagarar soja.

33 Da baraden suka isa Kaisariya, suka ba mai mulkin wasiƙar, suka kai Bulus a gabansa.

34 Da ya karanta wasiƙar, ya tambayi Bulus ko shi mutumin wane lardi ne? Da ya ji daga Kilikiya yake,

35 ya ce, “Zan saurari maganarka duka, in masu ƙararka sun zo.” Sai kuma ya yi umarni a tsare shi a fadar Hirudus.

Categories
A.M.

A.M. 24

An Kai Ƙarar Bulus

1 Bayan kwana biyar sai babban firist, Hananiya, ya zo tare da waɗansu shugabanni, da kuma wani lauya, mai suna Tartulus, suka yi ƙarar Bulus a gaban mai mulki.

2 Da aka kirawo Tartulus, ya shiga kai ƙarar Bulus, ya ce, “Ya mafifici Filikus, tun da yake ta gare ka ne muke zaman lafiya ƙwarai, ta tsinkayarka ne kuma ake kyautata zaman jama’armu,

3 kullum muna yarda da haka ƙwarai a ko’ina, tare da godiya ba iyaka.

4 Amma don kada in gajiyad da kai, ina roƙonka a cikin nasiharka, ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu.

5 Mun tarar da mutumin nan fitinanne ne, yana ta da hargitsi tsakanin Yahudawa ko’ina a duniya, shi kuma ne turun ɗariƙar Nazarawa.

6 Har ma yana nema ya tozarta Haikali, amma muka kama shi. [Niyyarmu ce mu hukunta shi bisa ga shari’armu.

7 Amma shugaba Lisiyas ya zo ya ƙwace shi daga hannunmu ƙarfi da yaji,

8 ya yi umarni masu ƙararsa su zo a gabanka.] In kuwa ka tuhume shi da kanka, za ka iya tabbatarwa daga bakinsa duk ƙarar da muke tāsarwa.”

9 Yahudawa ma suka goyi bayan haka, suna tabbatarwa haka abin yake.

Hanzarin Bulus a gaban Filikus

10 Da mai mulki ya alamta wa Bulus ya yi magana, sai ya amsa ya ce, “Tun da na sani ka yi shekaru da yawa kana yi wa jama’ar nan shari’a, da farin ciki zan kawo hanzarina.

11 Ai, ka iya tabbatarwa, bai fi kwana goma sha biyu ba tun da na tafi Urushalima yin sujada.

12 Ba su kuwa taɓa samuna ina muhawwara da kowa ba, ko kuwa ta da husuma har mutane su taru a Haikali, ko a majami’u, ko kuwa a cikin birni.

13 Ba kuma za su iya tabbatar maka abin da yanzu suke ƙarata a kai ba.

14 Amma na yarda cewa, bisa ga hanyar nan da suke kira ‘Ɗariƙa’ nake bauta wa Allahn kakanninmu, nake kuma gaskata duk abin da yake a rubuce a cikin Attaura da kuma littattafan annabawa.

15 Ina sa zuciya ga Allah, yadda su waɗannan ma suke sawa, wato za a ta da matattu, masu adalci da marasa adalci duka.

16 Saboda haka, a kullum nake himma in kasance da lamiri marar abin zargi a wurin Allah da wurin mutane.

17 To, bayan ‘yan shekaru sai na je domin in kai gudunmawa ga jama’armu, in kuma yi sadaka.

18 Ina cikin yin haka sai suka same ni a tsarkake a Haikali, ba kuwa da wani taro ba, balle hargowa. Amma akwai waɗansu Yahudawa daga ƙasar Asiya–

19 su ne kuwa ya kamata su zo nan a gabanka su yi ƙarata, in suna da wata magana a game da ni.

20 Ko kuwa waɗannan mutane kansu su faɗi laifina da suka samu, sa’ad da na tsaya a gaban majalisa,

21 sai ko maganar nan ɗaya tak, da na ɗaga murya na faɗa, sa’ad da nake a tsaye a cikinsu, cewa, ‘Game da maganar tashin matattu ake yi mini shari’a a gabanku yau.’ ”

An Tsare Bulus

22 Filikus kuwa da yake yana da sahihin ilimi a game da wannan hanya ya dakatar da su, ya ce, “In shugaba Lisiyas ya iso, zan yanke muku shari’a.”

23 Ya kuma ba jarumi umarni ya tsare Bulus, amma ya sassauta masa, kada kuwa ya hana mutanensa zuwa wurinsa su kula da shi.

24 Bayan ‘yan kwanaki Filikus ya zo tare da matarsa, Durusila, wata Bayahudiya. Sai ya aika a zo da Bulus, ya kuwa saurare shi a kan maganar gaskatawa da Almasihu Yesu.

25 Bulus yana ba da bayani a kan adalci, da kamunkai, da kuma hukuncin nan mai zuwa, Filikus ya kaɗu, ya kāda baki ya ce, “Yanzu kam, sai ka koma. In na sami zarafi nā kira ka.”

26 Don yana sa rai Bulus zai ba shi kuɗi, shi ya sa ya yi ta kiransa a kai a kai, yana zance da shi.

27 Amma bayan shekara biyu sai Borkiyas Festas ya gāji Filikus. Filikus kuwa don neman farin jini a wurin Yahudawa, ya bar Bulus a ɗaure.

Categories
A.M.

A.M. 25

Bulus Ya Ɗaukaka Ƙara zuwa ga Kaisar

1 To, da Festas ya iso lardinsa, bayan kwana uku sai ya tashi daga Kaisariya ya tafi Urushalima.

2 Sai manyan firistoci da manyan Yahudawa suka kai ƙarar Bulus gunsa, suka roƙe shi

3 ya kyauta musu, ya aika a zo da shi Urushalima, alhali kuwa sun shirya ‘yan kwanto su kashe shi a hanya.

4 Amma Festas ya amsa ya ce, “Bulus yana a tsare a Kaisariya, ni ma kuwa da kaina ina niyyar zuwa can kwanan nan.”

5 Ya kuma ce, “Saboda haka, sai waɗansu manya a cikinku su taho tare da ni, in kuwa mutumin nan na da wani laifi, su yi ƙararsa.”

6 Bai fi kwana takwas ko goma a wurinsu ba, sai ya tafi Kaisariya. Kashegari kuma ya zauna a kan gadon shari’a, ya yi umarni a zo da Bulus.

7 Da ya zo, Yahudawan da suka zo daga Urushalima suka kewaye shi a tsaitsaye, suna ta kawo ƙararraki masu yawa masu tsanani a game da shi, waɗanda ma suka kasa tabbatarwa.

8 Amma Bulus ya kawo hanzarinsa ya ce, “Ni ban yi wani laifi game da shari’ar Yahudawa, ko Haikali, ko a game da Kaisar ba, ko kaɗan.”

9 Festas kuwa don neman farin jini wurin Yahudawa, ya amsa ya ce wa Bulus, “Ka yarda ka je Urushalima a yi maka shari’a a can a kan waɗannan abubuwa a gabana?”

10 Amma Bulus ya ce, “Ai, a tsaye nake a majalisar Kaisar, a inda ya kamata a yi mini shari’a. Ban yi wa Yahudawa wani laifi ba, kai kanka kuwa ka san da haka sarai.

11 To, in ni mai laifi ne, har na aikata abin da ya isa kisa, ai, ba zan guji a kashe ni ba, amma in ba wata gaskiya a cikin ƙarata da suke yi, to, ba mai iya bashe ni gare su don a faranta musu rai. Na nema a ɗaukaka ƙarata gaban Kaisar.”

12 Bayan da Festas ya yi shawara da majalisa, sai ya amsa ya ce, “To, ka nema a ɗaukaka ƙararka gaban Kaisar! Gun Kaisar kuwa za ka tafi.”

Bulus a gaban Agaribas da Barniki

13 Bayan ‘yan kwanaki sai sarki Agaribas da Barniki, suka zo Kaisariya don su yi wa Festas maraba.

14 Da yake kuma sun yi kwanaki da dama a can, sai Festas ya rattaba wa sarki labarin Bulus, ya ce, “Akwai wani mutumin da Filikus ya bari a ɗaure,

15 wanda sa’ad da nake Urushalima manyan firistoci da shugabannin Yahudawa suka kawo mini ƙararsa, suka roƙe ni in yi masa hukunci.

16 Ni kuwa na amsa musu na ce, ba al’adar Romawa ba ce a yi wa wani hukunci, don faranta wa wani rai, ba tare da masu ƙarar, da wanda aka kai ƙara, sun kwanta a gaban shari’a ba, ya kuma sami damar kawo hanzarinsa game da ƙarar da aka tāsar.

17 Saboda haka, da suka zo nan tare, ban yi wani jinkiri ba, sai kawai na hau gadon shari’a kashegari, na kuma yi umarni a kawo mutumin.

18 Da masu ƙarar suka tashi tsaye, ba su kawo wata mummunar ƙara yadda na zata a game da shi ba,

19 sai dai waɗansu maganganu da suka ɗora masa a game da addininsu, da kuma wani, wai shi Yesu, wanda ya mutu, amma Bulus ya tsaya a kan, wai yana da rai.

20 Ni kuwa da na rasa yadda zan bincika waɗannan abubuwa, sai na tambayi Bulus ko ya yarda ya je Urushalima a yi masa shari’a a can a kan waɗannan abubuwa.

21 Amma da Bulus ya nema a dakatar da maganarsa sai Augustas ya duba ta, sai na yi umarni a tsare shi har kafin in aika da shi zuwa gun Kaisar.”

22 Sai Agaribas ya ce wa Festas, “Ni ma dai na so in saurari mutumin nan da kaina.” Festas ya ce, “Kā kuwa ji shi gobe.”

23 To, kashegari sai Agaribas da Barniki suka zo a cikin alfarma, suka shiga ɗakin majalisa tare da shugabannin yaƙi da kuma jigajigan garin. Sai aka shigo da Bulus da umarnin Festas.

24 Sai Festas ya ce, “Ya sarki Agaribas, da dukan mutanen da suke tare da mu, kun ga mutumin nan da duk jama’ar Yahudawa suka kawo mini ƙararsa a Urushalima, da kuma nan, suna ihu, bai kamata a bar shi da rai ba.

25 Amma ni ban ga abin da ya yi wanda ya isa kisa ba. Tun da kuma shi kansa ya nema a mai da shari’arsa a gaban Augustas, ƙudura in aika da shi zuwa wurinsa.

26 Amma ba ni da wata tabbatacciyar magana da zan rubuta wa ubangijina game da shi. Saboda haka na kawo shi a gabanku, musamman kuwa a gabanka, ya sarki Agaribas, don bayan an yi bincike, ko na abin da zan rubuta.

27 Don ni, a ganina, wauta ce a aika da ɗan sarƙa, ba tare da an nuna laifofin da ya yi ba.”

Categories
A.M.

A.M. 26

Hanzarin Bulus a gaban Agaribas

1 Daga nan, sai Agaribas ya ce wa Bulus, “An ba ka izinin yin magana.”

Sa’an nan fa Bulus ya ɗaga hannu, ya fara kawo hanzarinsa ya ce,

2 “Lalle na yi arziki, ya sarki Agaribas, da yake a gabanka ne zan kawo hanzarina yau a game da duk ƙarata da Yahudawa suka yi,

3 musamman da yake gwani ne kai ga sanin al’adun Yahudawa da maganganunsu. saboda haka, ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.

4 “Irin zaman da na yi tun daga ƙuruciyata, wato tun da farko, a cikin jama’armu da kuma a Urushalima har ya zuwa yau, sananne ne ga dukan Yahudawa.

5 Sun sani tun ainihi, in dai za su yarda su yi shaida, cewa lalle ni Bafarisiye ne bisa ga ɗariƙar nan da ta fi tsanani cikin addinin nan namu.

6 Ai, saboda na sa zuciya ga cikar alkawarin nan ne da Allah ya yi wa kakanninmu nake nan a tsaye a yi mini shari’a.

7 Alkwarin nan kuwa, shi ne wanda kabilanmu goma sha biyu suke himmantuwa ga bauta wa Allah dare da rana, suna sa zuciya su ga cikarsa. Saboda sa zuciyar nan kuma fa Yahudawa suke ƙarata, ya sarki!

8 Yaya cewa Allah yana ta da matattu sa’an nan, ya ƙi gaskatuwa a gare ku?

9 “To, ni kaina ma a dā na ga kamar wajibi ne in yi abubuwa da yawa, na gāba da sunan Yesu Banazare.

10 Na kuwa yi haka a Urushalima, har na sami izini daga manyan firstoci, na kulle tsarkaka da yawa a kurkuku. Har ma a lokacin da ake kashe su ina goyon bayan yin haka.

11 Na kuma sha gwada musu azaba a dukan majami’u, ina ƙoƙarin sa su yin saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.”

Labarin Juyowar Bulus

12 “Cikin halin haka ne, ina tafiya Dimashƙu da izinin manyan firistoci da kuma saƙonsu,

13 da rana a tsaka a hanya, ya sarki, na ga wani haske ya bayyano daga sama, fiye da hasken rana, duk ya haskaka kewaye da ni da abokan tafiyata.

14 Da duk muka fāɗi, sai na ji wata murya tana ce mini da yahudanci, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Da wuya a gare ka ka yi ta shuri bisa a kan tsini.’

15 Ni kuwa sai na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ Sai Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.

16 Amma tashi ka miƙe tsaye, gama na bayyana a gare ka ne da wannan maƙasudi, wato in sa ka mai hidima, mashaidi kuma na abubuwan da ka gani a game da ni, da kuma abubuwa waɗanda zan bayyana maka a nan gaba.

17 Zan tsirar da kai daga jama’ar nan da kuma al’ummai, waɗanda zan aike ka a gare su,

18 domin ka buɗe musu ido, su juyo daga duhu zuwa haske, daga kuma mulkin Shaiɗan zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai, da kuma gādo tare da dukan tsarkaka saboda sun gaskata da ni.’ ”

Shaidar Bulus a Gaban Yahudawa da Al’ummai

19 “Saboda haka, ya sarki Agaribas, ban ƙi biyayya ga wahayin nan da ya zo mini daga Sama ba.

20 Da fari, na yi wa mutanen Dimashƙu wa’azi, sa’an nan na yi a Urushalima da dukan kewayen ƙasar Yahudiya, sa’an nan kuma na yi wa al’ummai, cewa su tuba su juyo ga Allah, su kuma yi aikin da zai nuna tubarsu.

21 Saboda wannan dalili ne Yahudawa suka kama ni a Haikali, har suna neman kashe ni.

22 Da na sami taimakon Allah kuwa, ga ni a nan har yanzu, ina shaida wa babba da yaro, ba na faɗar kome sai abin da annabawa da Musa suka ce zai auku,

23 cewa dai lalle ne Almasihu yă sha wuya, shi ne kuma zai fara tashi daga matattu, ya sanar da jama’ar nan da al’ummai haske.”

Bulus Yana Fata Agaribas Ya Gaskata

24 Bulus na cikin kawo hanzarinsa, sai Festas ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Bulus, kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”

25 Amma Bulus ya ce, “Ya mafifici Festas, ai, ban ruɗe ba, gaskiya nake faɗa, cikin natsuwa kuwa.

26 Ai, al’amarin nan sananne ne ga sarki, ina kuma masa magana gabagaɗi ne, gama na tabbata ba abin da ya kuɓuce wa hankalinsa cikin al’amarin nan, don wannan abu ba a ɓoye aka yi shi ba.

27 Ya sarki Agaribas, ka gaskata annabawa? Na dai sani ka gaskata.”

28 Sai Agaribas ya ce wa Bulus, “Wato a ɗan wannan taƙaitaccen lokaci kake nufin mai da ni Kirista?”

29 Bulus kuwa ya ce, “Ko a ɗan wannan, ko a mai yawa, ina fata ga Allah, ba kai kaɗai ba, har ma duk waɗanda suke saurarona a yau, su zama kamar yadda nake, sai dai banda sarƙar nan.”

30 Sai sarki ya tashi, haka kuma mai mulki da Barniki, da waɗanda suke a zaune tare da su.

31 Bayan sun keɓe waje ɗaya, suka yi shawara, suka ce, “Ai, mutumin nan bai yi wani abin da ya isa kisa ko ɗauri ba.”

32 Agaribas kuma ya ce wa Festas, “Ba don dai mutumin nan ya riga ya nemi ɗaukaka ƙararsa a gaban Kaisar ba, da sai a sake shi.”

Categories
A.M.

A.M. 27

Bulus Ya Shiga Jirgi zuwa Roma

1 Da aka shirya mu tashin jirgin ruwa zuwa ƙasar Italiya, sai suka danƙa Bulus da waɗansu ‘yan sarƙa a hannun wani jarumi, mai suna Yuliyas, na ƙungiyar Augustas.

2 Da muka shiga wani jirgi na Adaramitiya, mai shirin tashi zuwa waɗansu garuruwan da suke gaɓar Asiya, muka fara tafiya. Aristarkus kuwa, wani mutumin Tasalonika ta ƙasar Makidoniya, na tare da mu.

3 Kashegari ga mu a Sidon. Yuliyas kuwa ya yi wa Bulus alheri, ya ba shi izini ya je ya gano abokansa, su yi masa taimako.

4 Da muka tashi daga nan a jirgin ruwa sai muka zaga ta bayan tsibirin Kubrus, saboda iska tana gāba da mu.

5 Bayan da muka haye bahar ɗin da yake kusa da kasar Kilikiya da ta Bamfiliya, muka isa Mira ta ƙasar Likiya.

6 A nan jarumin ya sami wani jirgin Iskandariya mai zuwa ƙasar Italiya, ya sa mu a ciki.

7 Muka yi kwana da kwanaki muna tafiya kaɗan kaɗan, har da ƙyar muka kai kusa da Kinidas. Da dai iska ta hana mu ci gaba, muka zaga ta bayan tsibirin Karita kusa da Salmoni.

8 Muna bin gefen gaɓarsa da ƙyar, har muka isa wani wuri mai suna Amintacciyar Mafaka, wadda take kusa da birnin Lasiya.

9 Da yake an ɓata lokaci mai yawa, tafiyar ma ta riga ta zama mai hatsari, lokacin azumi kuwa ya wuce, sai Bulus ya gargaɗe su,

10 ya ce musu, “Ya ku jama’a, na dai ga tafiyar nan za ta zamanto da masifa da hasara mai yawa, ba wai ta kaya da jirgi kawai ba, har ma ta rayukanmu.”

11 Amma jarumin soja, ya fi mai da hankali ga maganar mai tuƙin jirgin da kuma ta mai jirgin, a kan abin da Bulus ya faɗa.

12 Da yake mafakar nan ba ta kamaci jirage su ci damuna a ciki ba, sai yawanci suka kawo shawara a tashi daga nan, ko ta ƙaƙa su iya kaiwa Finikiya, wata mafakar tsibirin Karita, mai duban gabas maso arewa da kuma gabas maso kudu, su ci damuna a can.

Hadiri a Teku

13 Da iska ta buso daga kudu sannu sannu, a tsammaninsu muradinsu ya biya ke nan, sai suka janye anka suka bi ta gefen tsibirin Karita gab da gaci.

14 Ba da jimawa ba kuwa sai ga wata gawurtacciyar iska da ake kira Yurokilidon ta bugo daga tsibirin.

15 Da iskar ta bugo jirgin, har ya kasa fuskantarta, sai muka sallama mata, ta yi ta kora mu.

16 Da muka bi ta jikin wani ɗan tsibiri wai shi Kauda muka samu muka yi iko da ƙaramin jirginmu da ƙyar.

17 Bayan suka jawo ƙaramin jirgi ɗin a cikin babban jirgi, sai suka yi dabara suka ɗaɗɗaura igiyoyi ta gindin babban jirgin, suka rage shi. Don kuma gudun kada a fyaɗa su a yashin nan na Sirtis mai haɗiye kome, suka sauke filafilai, aka kora jirgin haka.

18 Saboda hadiri yana sa mu tangaɗi ƙwarai da gaske, kashegari sai suka fara watsar da kayan da jirgin ya ɗauko, a ruwa.

19 A rana ta uku kuma, su da kansu suka jefar da kayan aikin jirgin.

20 Da dai muka yi kwana da kwanaki ba mu ga rana ko taurari ba, gawurtacciyar iskar hadiri kuma ta yi ta bugunmu, sai muka fid da zuciya da tsira.

21 Da yake an daɗe ba cin abinci, sai Bulus ya miƙe a tsaye a tsakiyarsu, ya ce, “Ya ku jama’a, da kun ji maganata, da ba ku taso daga tsibirin Karita kun fāɗa wannan masifa da hasara ba.

22 To, a yanzu, ina yi muku gargaɗi ku yi ƙarfin hali, don ba wanda zai yi hasarar ransa a cikinku, sai dai a yi hasarar jirgin.

23 Don a daren jiya wani mala’ikan Allah wanda ni nasa ne, nake kuma bauta masa, ya tsaya kusa da ni,

24 ya ce, ‘Kada ka ji tsoro Bulus, lalle za ka tsaya a gaban Kaisar, ga shi kuma, Allah ya amsa ya yardar maka duk abokan tafiyarka su tsira.’

25 Saboda haka, sai ku yi ƙarfin hali, ya ku jama’a, domin na gaskata Allah a kan cewa, yadda aka faɗa mini ɗin nan, haka za a yi.

26 Amma fa lalle ne a fyaɗa mu a wani tsibirin.”

27 A dare na goma sha huɗu, ana ta kora mu sakaka a bahar Adariya, wajen tsakar dare sai masu tuƙi suka zaci mun yi kusa da ƙasa.

28 Sai suka gwada zurfin ruwan, suka sami gaba ashirin, da muka ci gaba kaɗan, sai suka sāke gwadawa, suka sami gaba goma sha biyar.

29 Don gudun kada a fyaɗa mu a kan duwatsu, sai suka saki anka guda huɗu na bayan jirgin, suka ƙagauta gari ya waye.

30 Masu tuƙi suna neman gudu daga jirgin ke nan, har sun zura ƙaramin jirgi a cikin ruwa, wai don a ga kamar za su ja su anka ɗin ne daga goshin jirgin su sake su,

31 sai Bulus ya ce da jarumin yaki da kuma sojan. “In mutanen nan ba su tsaya a cikin jirgin nan ba, ba yadda za a yi ku tsira.”

32 Sai sojan suka yayyanke igiyoyin ƙaramin jirgin, suka bar shi ya bi ruwa.

33 Da gari ya yi kusan wayewa sai Bulus ya roƙe su su taɓa ɗan abinci, ya ce, “Yau fa kwana goma sha huɗu ke nan kuke zaman jira, ba wani abin da kuka ci.

34 Saboda haka, ina roƙonku ku ci abinci, don lafiyarku, tun da yake ba wanda ko gashin kansa zai yi ciwo a cikinku.”

35 Da ya faɗi haka, ya ɗauki curin gurasa, ya yi godiya ga Allah a gabansu duka, sa’an nan ya gutsuttsura ya fara ci.

36 Sai duk suka farfado, su ma kansu suka ci abinci.

37 Mu duka a cikin jirgin kuwa mutum metan da saba’in da shida ne.

38 Da suka ci suka ƙoshi, sai suka riƙa rage wa jirgin nauyi, suka yi ta zub da alkama a cikin ruwa.

Ragargajewar Jirgi

39 Da gari ya waye ba su shaida ƙasar ba, amma dai sun lura da wani lungu da gaci mai yashi, sai kuma suka yi shawara cewa in mai yiwuwa ne su kai jirgin kan yashin.

40 Sai suka daddatse su anka duka, suka bar su a ruwa, suna kuma ɓalle maɗaurin abin juyar da jirgin a lokacin, sa’an nan kuma suka ta da filafilan goshin jirgin daidai iska, suka doshi gaci.

41 Amma da muka isa wata mahaɗar ruwa, sai suka tura jirgin ya dunguri yashi, har goshinsa ya cije ya kasa motsi, ƙarshensa kuma ya fara ragargejewa saboda haukan raƙuman ruwa.

42 Sai sojan suka yi niyya su kashe ‘yan sarka, don kada wani ya yi ninƙaya ya tsira.

43 Amma jarumin da ya so ya ceci Bulus, ya hana i da nufinsu, ya kuma yi umarni duk waɗanda suka iya ruwa su fara fāɗawa zuwa gaci,

44 sauran kuwa waɗansu suka hau katako, waɗansu kuma suka hau tarkacen jirgin. Da haka duk suka kai gaci lafiya.

Categories
A.M.

A.M. 28

Bulus a Tsibirin Malita

1 Bayan da muka tsira, sai muka ji, ashe, sunan tsibirin nan Malita ne.

2 Mutanen garin kuwa sun yi mana alheri matuƙar alheri, don sun hura wuta sun karɓe mu, mu duka, saboda ana ruwa, ga kuma sanyi.

3 Sa’ad da Bulus ya tattaro waɗansu ƙirare rungume guda ya sa a wutar, sai ga wani maciji ya bullo saboda zafi, ya ɗafe masa a hannu.

4 Da mutanen garin suka ga mugun ƙwaron nan a makale a hannun Bulus, suka ce wa juna, “Lalle mutumin nan mai kisankai ne, kun ga ko da yake ya tsira daga bahar, duk da haka alhaki yana binsa sai ya mutu.”

5 Bulus kuwa ya karkaɗe ƙwaron a cikin wutar, bai kuwa ji wani ciwo ba.

6 Su kuwa suna zaton wurin zai kumbura, ko kuwa farat ɗaya ya fāɗi matacce. Amma da aka daɗe suka ga ba abin da ya same shi, suka sāke magana suka ce lalle shi wani Allah ne.

7 A nan kusa kuwa akwai wani fili, mallakar shugaban tsibirin nan, mai suna Babiliyas. Shi ne ya karɓe mu, ya sauke mu a cikin martaba har kwana uku.

8 Ashe, uban Babiliyas yana a kwance, yana fama da zazzaɓi da atuni. Sai Bulus ya shiga wurinsa ya yi addu’a, ya ɗora masa hannu ya warkar da shi.

9 Da aka yi haka sai duk sauran marasa lafiya a tsibirin suka riƙa zuwa ana warkar da su.

10 Suka yi mana kyauta mai yawa, da za mu tashi a jirgin ruwa kuma, suka yi ta tara mana duk irin abubuwan da muke bukata.

Bulus Ya Isa Roma

11 Bayan wata uku muka tashi a cikin wani jirgin Iskandariya, wanda ya ci damuna a nan tsibirin. An kuwa yi masa alama da surar Tagwaye Maza.

12 Da muka zo Sirakusa muka kwana uku a nan.

13 Daga nan kuma muka zaga sai ga mu a Rigiyum. Da muka kwana, iska ta taso daga kudu, kashegari kuma muka kai Butiyoli.

14 A nan muka tarar da waɗansu ‘yan’uwa, suka roƙe mu mu kwana bakwai tare da su. Da haka dai har muka isa Roma.

15 Da ‘yan’uwa na can suka ji labarinmu, sai da suka zo don su tarye mu har Kasuwar Abiyus, da kuma wurin nan da ake kira Maciya Uku. Da kuwa Bulus ya sadu da su, ya yi godiya ga Allah, jikinsa kuma ya yi ƙarfi.

16 Da muka shiga Roma aka yardar wa Bulus ya je ya sauka abinsa tare da sojan da yake tsaronsa.

Wa’azin Bulus a Roma

17 Bayan kwana uku ya kira manyan Yahudawan birnin. Da suka taru sai ya ce musu, “Ya ku ‘yan’uwa, ko da yake ban yi wa jama’armu wani laifi ba, ko laifi a game da al’adun kakanninmu, duk da haka an bashe ni ɗaurarre ga Romawa tun daga Urushalima.

18 Su kuwa da suka tuhume ni, suna so su sake ni, don ban yi wani laifi da ya isa kisa ba.

19 Amma da Yahudawa suka ƙi yarda, sai ya zamar mini dole in nema a ɗaukaka ƙarata gaban Kaisar, ba don ina ƙarar jama’armu ba ne.

20 Shi ya sa na nema in gana da ku, tun da yake dai saboda sa zuciyar nan da Isra’ila take yi ne nake ɗaure da sarƙan nan.”

21 Sai suka ce masa, “Mu kam, ba mu sami wata wasiƙa daga Yahudiya game da kai ba, ba kuwa wani ɗan’uwanmu da ya zo nan ya kawo labarinka, ko yă faɗi wata mummunar magana game da kai.

22 Amma muna so mu ji daga bakinka abin da yake ra’ayinka, don in dai ta ɗariƙar nan ne, mun sani ko’ina ana kushenta.”

23 Da suka sa masa rana, sai suka zo masaukinsa, su da yawa. Sa’an nan ya yi ta yi musu bayani, yana ta shaidar musu Mulkin Allah, tun daga safe har magariba, yana ƙoƙarin rinjayarsu a kan Yesu, ta hanyar Attaurar Musa da littattafan annabawa.

24 Waɗansu sun rinjayu da maganarsa, amma waɗansu sun ƙi gaskatawa.

25 Da suka kasa yarda a junansu, kafin su watse sai Bulus ya yi musu magana ɗaya ya ce, “Ashe kuwa, Ruhu Mai Tsarki daidai ya faɗa, da ya yi wa kakanninku magana ta bakin Annabi Ishaya cewa,

26 ‘Je ka wurin jama’ar nan, ka ce,

Za ku ji kam, amma ba za ku fahimta ba faufau,

Za ku gani kuma, amma ba za ku gane ba faufau.

27 Don zuciyar jama’ar nan ta yi kanta,

Sun toshe kunnuwansu,

Sun kuma runtse idanunsu,

Wai don kada su gani da idanunsu,

Su kuma ji da kunnuwansu,

Su kuma fahimta a zuciyarsu,

Har su juyo gare ni in warkar da su.’

28 To, sai ku sani, wannan ceto na Allah, an aiko da shi har ga al’ummai, su kam za su saurara.”

29 (Da ya faɗi haka, sai Yahudawa suka tashi suna ta muhawwara da juna.)

30 Sai Bulus ya zauna a nan a gidan da yake haya, har shekara biyu cikakku, yana maraba da duk wanda ya je wurinsa,

31 yana ta wa’azin Mulkin Allah, da koyar da al’amarin Ubangiji Yesu Almasihu gabagaɗi, ba tare da wani hani ba.

Categories
ROM

ROM 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, bawan Yesu Almasihu, manzo kirayayye, keɓaɓɓe domin yin bisharar Allah,

2 wadda Allah ya yi alkawari tun dā, ta bakin annabawansa a cikin Littattafai masu tsarki.

3 Bishara ɗin nan a kan Ɗansa ce, Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ga jiki shi zuriyar Dawuda ne,

4 amma ga tsarkinsa na ruhu shi Ɗan Allah ne, da iko aka ayyana shi haka ta wurin tashinsa daga matattu.

5 Ta wurinsa ne muka sami alheri da kuma manzanci, saboda sunansa dukan al’ummai su gaskata su yi biyayya,

6 a cikinsu kuma har da ku da kuke kirayayyun Yesu Almasihu.

7 Daga Bulus zuwa ga dukan ƙaunatattun Allah da kuke a Roma, tsarkaka kirayayyu.

Alheri da salama na Allah Ubanmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu su tabbata a gare ku.

Nufin Bulus Ya Ziyarci Roma

8 Da farko dai ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Almasihu saboda ku duka, domin ana baza labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.

9 Domin kuwa Allah, wanda nake bauta wa a ruhuna ta yin bisharar Ɗansa, shi ne mashaidina a kan yadda kullum ba na fasa ambatonku a cikin addu’ata,

10 ina addu’a, ko ta ƙaƙa, da yardar Allah, a yanzu kam, in sami arzikin zuwa wurinku.

11 Domin ina ɗokin ganinku, in ni’imta ku da wata baiwa ta ruhu, domin ku ƙarfafa.

12 Wato ni da ku, mu ƙarfafa juna ta bangaskiyarmu, tawa da taku.

13 Ina so ku sani ‘yan’uwa, na sha ɗaura niyyar zuwa wurinku, ko da yake har yanzu ba a yardar mini ba, domin ku ma in sami amfani a gare ku, kamar yadda na samu a cikin al’ummai.

14 Akwai hakkin Helenawa, da na bare, da na masu ilimi, da na jahilai duka a kaina.

15 Saboda haka a gwargwadon iyawata, ina da himma ku ma in yi muku bisharar, ku da kuke a Roma.

Ikon Bishara

16 Gama ba na jin kunyar bishara, domin ita ce ikon Allah mai kai kowane mai ba da gaskiya ga samun ceto, Yahudawa da fari, sa’an nan kuma al’ummai.

17 Gama bishara ɗin ta bayyana wata hanyar samun adalci a gaban Allah, hanyar nan kuwa ta bangaskiya ce, tun daga farko har zuwa ƙarshe, yadda yake a rubuce cewa, “Wanda yake da adalci ta wurin bangaskiya zai rayu.”

Laifin ‘Yan Adam

18 Gama ana bayyana fushin Allah daga Sama, a kan dukan rashin bin Allah, da aikin mugunta na mutanen da suke danne gaskiya, ta aikin muguntarsu,

19 Domin abin da za a iya sani a game da Allah a bayyane yake a gare su, gama Allah ne ya bayyana musu shi.

20 Gama tun daga halittar duniya al’amuran Allah marasa gănuwa, wato ikonsa madawwami, da allahntakarsa, sun fahimtu sarai, ta hanyar abubuwan da aka halitta kuma ake gane su. Saboda haka mutane sun rasa hanzari.

21 Domin kuwa ko da yake sun san da Allah, duk da haka ba su ɗaukaka shi a kan shi Allah ne ba, ba su kuma gode masa ba. Sai tunaninsu ya wofince, zuciyarsu marar fahimta kuma ta duhunta.

22 Suna da’awa cewa, su masu hikima ne, sai suka zama wawaye.

23 Sun sauya ɗaukakar Allah marar mutuwa da misalin siffar mutum mai mutuwa, da ta tsuntsaye, da ta dabbobi, da kuma ta masu jan ciki.

24 Saboda haka Allah ya sallama su ga rashin tsarkaka ta mugayen sha’awace-sha’awacensu, har su wulakanta jikinsu a junansu,

25 saboda sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, har yi wa halitta ibada, sun kuma bauta mata, sun ƙi su yi wa Mahalicci, shi wanda yabo ya tabbata a gare shi har abada. Amin.

26 Don haka Allah ya sallama su ga mugayen sha’awace-sha’awace masu banƙyama, har matansu suka sauya ɗabi’arsu ta halal, da wadda take ta haram.

27 Haka kuma maza suka bar ma’amalarsu ta halal da mata, jarabar juna ta ɗebe su, maza da maza suna aikata rashin kunya, suna jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.

28 Tun da yake sun ƙi su yarda su san Allah, Allah ya sallama su ga halin banza, su aikata abin kunya.

29 Su masu aikata rashin adalci ne ƙwarai, da mugunta, da kwaɗayi, da ƙeta. Masu hassada ne, da kisankai, da jayayya, da ha’inci, da kuma nukura gaya matuƙa. Macizan ƙaiƙayi ne,

30 da masu yanke, da maƙiyan Allah, da masu cin mutunci, da masu girmankai, da masu ruba, da masu haddasa mugunta, da marasa bin iyaye,

31 da marasa fahimta, da masu ta da alkawari, da marasa ƙauna, da marasa tausayi.

32 Waɗannan kuwa ko da yake sun san shari’ar Allah cewa masu yin irin waɗannan abubuwa, sun cancanci mutuwa, duk da haka, ba aikata su kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon masu yinsu.

Categories
ROM

ROM 2

Hukuncin Allah Daidai Ne

1 Saboda haka ba ka da wata hujja, kai mutum, ko kai wane ne da kake ganin laifin wani. A yayin da kake ganin laifin wani, ai, kanka kake hukunta wa, don ga shi, kai mai ganin laifin wani, kai ma haka kake yi.

2 Mun dai san hukuncin Allah a kan masu yin haka daidai ne.

3 Ya kai mutum, kai da kake ganin laifin masu yin haka, alhali kuwa kai kanka, kana yinsu, kana tsammani za ka tsere wa hukuncin Allah ne?

4 Ko kuwa kana raina yalwar alherinsa, da jimirinsa, da kuma haƙurinsa ne? Ashe, ba ka sani ba alherin Allah yana jawo ka zuwa ga tuba?

5 Amma ga shi, saboda ƙeƙasasshiyar zuciyarka marar tuba, kana nema wa kanka fushin Allah a ranar fushi, sa’ad da za a bayyana hukuncin Allah macancani.

6 Allah ne zai saka wa kowa gwargwadon aikinsa.

7 Waɗanda suke neman daraja da ɗaukaka da kuma dawwama ta wurin naciyarsu ga aikata nagarta, zai saka musu da rai madawwami.

8 Waɗanda suke masu sonkai, da waɗanda suke ƙin bin gaskiya, da masu bin rashin adalci, zai saka musu da fushi da hasala.

9 Duk waɗanda suke aikata mugunta za su sha wahala da masifa, da fari Yahudawa, sa’an nan kuma al’ummai.

10 Amma Allah zai ba da daraja, da ɗaukaka, da salama ga dukan waɗanda suke aikata nagarta, da fari ga Yahudawa, sa’an nan ga al’ummai.

11 Domin kuwa, Allah ba ya nuna tara.

12 Ɗaukacin waɗanda suka yi zunubi a rashin sanin Shari’a, za su hallaka ne ba tare da Shari’a ba. Ɗaukacin waɗanda suka yi zunubi a ƙarƙashin Shari’a kuwa, za a hukunta su ta hanyar Shari’a.

13 Don ba ta jin shari’ar kawai mutum yake samun kuɓuta ga Allah ba, sai dai masu aikata ta, su ne za su kuɓuta.

14 In al’ummai, su da ba su da Shari’a, jikinsu ya ba su suka bi umarnin Shari’a, ko da yake ba su da Shari’ar, ashe kuwa, suna da shari’a ke nan.

15 Ayyukansu sun nuna, cewa abin da Shari’a ta umarta a rubuce yake a cikin zukatansu, lamirinsu kuwa yana shaidawa, tunaninsu kuwa yana zarginsu, ko kuma yana kāre su.

16 A wannan rana Allah zai yi wa ‘yan adam shari’a a kan asiransu, ta wurin Yesu Almasihu, bisa ga bishara da nake wa’azinta.

Yahudawa da Shari’a

17 To, in ka ce kai Bayahude ne, cewa ka dogara da Shari’a, har kana taƙama da Allah,

18 ka san abin da yake so, da yake kuma ka karantu da Shari’a, ka iya bambancewa da abubuwa mafifita,

19 har ka amince kai kanka jagoran makafi ne, haske ga waɗanda suke a cikin duhu,

20 mai horon marasa azanci, mai koya wa sababbin shiga, don a cikin Shari’ar kana da ainihin sani da ainihin gaskiya,

21 to, kai mai koya wa wani, ba ka koya wa kanka? Kai mai wa’azin kada a yi sata, shin, kai ba ka yi ne?

22 Kai mai cewa kada a yi zina, kai ba ka yi ne? Kai mai ƙyamar gumaka, ba ka sata a ɗakin gunki ne?

23 Kai mai taƙama da Shari’a, ashe, ba wulakanta Allah kake yi ba ta keta Shari’ar?

24 Yadda yake a rubuce cewa, “A sanadinku ne al’ummai suke saɓon sunan Allah.”

25 Lalle yin kaciya yana da amfani, in dai kana bin Shari’ar. Amma in kai mai keta shari’ar ne, kaciyarka ba a bakin kome take ba.

26 In kuwa marar kaciya yana kiyaye farillan Shari’a, ashe, ba sai a lasafta rashin kaciyarsa a kan kaciya ba?

27 Ashe, wanda rashin kaciya al’adarsa ce, ga shi kuwa, yana bin Shari’ar daidai, ba sai yă kāshe ka ba, kai da kake da Shari’a a rubuce da kuma kaciya, amma kana keta Shari’ar?

28 Gama Bayahude na ainihi ba mutum ne wanda yake Bayahude bisa siffar jikinsa na fili ba, kaciya ta ainihi kuwa ba kaciya ce ta fili ta fatar jiki ba.

29 Wanda yake Bayahude a zuci, ai, shi ne Bayahude. Kaciyar ainihi kuwa a zuci take, wato ta ruhu, ba ta zahiri ba. Irin wannan mutum, Allah ne yake yaba masa, ba ɗan adam ba.

Categories
ROM

ROM 3

1 To, ina fifikon Bayahude? Ko kuma ina fa’idar kaciya?

2 Ai kuwa, akwai ƙwarai, ta kowace hanya. Da farko dai, Yahudawa su ne aka amince wa a game da zantuttukan Allah.

3 To, ƙaƙa ke nan in waɗansu sun ci amanar nan? Sai cin amanarsu ya shafe cikar alkawarin Allah?

4 A’a, ko kusa! A dai tabbata Allah mai gaskiya ne, ko da yake kowane mutum maƙaryaci ne, yadda yake a rubuce cewa,

“Don maganarka tă tabbatar da adalcinka,

Ka kuma yi rinjaye in an binciki al’amarinka.”

5 In kuwa rashin adalcinmu shi ne yake nuna adalcin Allah a fili, me za mu ce? in Allah ya hore mu, ya yi rashin adalci ke nan? (Misali nake yi kawai.)

6 A’a, ko kusa! To, in da haka ne, ta ƙaƙa Allah zai yi wa duniya shari’a?

7 In kuwa, a dalilin ƙaryata, gaskiyar Allah ta ƙara bayyana, har aka kara ɗaukaka shi, to, don me har yanzu ake hukunta ni a kan ni mai zunubi ne?

8 In haka ne, ba sai mu yi ta yin mugun aiki don ya zama sanadin nagarta ba? Kamar yadda dai waɗansu suke mana yanke, cewa haka muke faɗa. Hukuncin da za a yi wa irin waɗannan kuwa daidai ne.

Babu Mai Adalci

9 To, ƙaƙa? Mu Yahudawa mun fi sauran ne? A’a, ko kaɗan! Don dā ma mun ɗora wa Yahudawa da al’ummai laifi, cewa dukkansu zunubi yana iko da su.

10 Kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Babu wani mai adalci, babu, ko ɗaya,

11 Babu wani mai fahimta, babu wani mai neman Allah.

12 Duk sun bauɗe, sun zama marasa amfani baki ɗaya,

Babu wani mai aiki nagari, babu kam, ko da guda ɗaya.”

13 “Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗen kabari ne,

Maganarsu ta yaudara ce.”

“Masu ciwon baki ne.”

14 “Yawan zage-zage da ɗacin baki gare su.”

15 “Masu hanzarin zub da jini ne,

16 Ta ko’ina suka bi sai hallaka da baƙin ciki,

17 Ba su kuma san hanyar salama ba.”

18 “Babu tsoron Allah a cikin sha’aninsu sam.”

19 To, mun sani duk abin da Shari’a ta ce, ya shafi waɗanda suke ƙarƙashinta ne, don a tuƙe hanzarin kowa, duk duniya kuma tă sani ƙarƙashin hukuncin Allah take.

20 Ai, ba wani ɗan adam da zai sami kuɓuta ga Allah ta kiyaye ayyukan Shari’a, tun da yake ta Shari’a ne mutum yake ganin laifinsa.

Adalci ta Wurin Bangaskiya

21 A yanzu, ba kuwa a game da shari’a ba, an bayyana wata hanyar samun adalcin Allah, wadda ma Attaura da littattafan annabawa suke yi wa shaida.

22 Adalcin nan na Allah, wanda yake samuwa ta wurin bangaskiya ga Yesu Almasihu, na masu ba da gaskiya ne dukka, ba kuwa wani bambamci,

23 gama ‘yan adam duka sun yi zunubi, sun kasa kuma ga ɗaukakar Allah.

24 Amma ta wurin alherin da Allah ya yi musu kyauta, sun sami kuɓuta ta wurin fansar da Almasihu Yesu ya yi.

25 Allah kuwa ya ayyana Yesu Almasihu ya zama hadayar sulhu, ta wurin ba da gaskiya ga jininsa. Allah kuwa ya yi haka domin yă nuna adalcinsa ne, domin dā saboda haƙurinsa ya jingine zunuban da aka gabatar,

26 domin a nuna adalcinsa a wannan zamani, wato a bayyana shi kansa mai adalci ne, mai kuɓutar da duk mai gaskatawa da Yesu kuma.

27 To, ina kuma fariyarmu ta shiga? Ina kuwa! Ta wace hanya aka kawar da ita? Ta aikin lada? A’a, sai dai ta hanyar bangaskiya.

28 Domin mun amince, cewa ta bangaskiya ne mutum yake kuɓuta, ba ta kiyaye ayyukan Shari’a ba.

29 Wato Allah, Allahn Yahudawa ne kurum? Ashe, ba na al’ummai ba ne kuma? Hakika na al’ummai ne ma,

30 tun da yake Allah ɗaya ne, zai kuwa kuɓutar da masu kaciya ta wurin bangaskiya, marasa kaciya ma ta wannan bangaskiya.

31 Wato mun soke Shari’a ke nan ta bangaskiyar nan? A’a, ko kusa! Sai tabbatar da ita muka yi.

Categories
ROM

ROM 4

Misali na Ibrahim

1 To, me ke nan za mu ce a game da Ibrahim, kakan kakanninmu?

2 Gama in da Ibrahim ya sami kuɓuta ta aikinsa na lada, ashe kuwa, yana da abin yin taƙama ke nan, amma fa ba a gaban Allah ba.

3 To, me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, bangaskiyar nan tasa kuma aka lasafta ta adalci ce a gare shi.”

4 Wanda yake aikin lada, ladarsa ba kyauta ba ce, sakamakon aikinsa ce.

5 Wanda ba ya aikin lada, amma yana dogararsa ga Allah, wanda yake kuɓutar da masu laifi, akan lasafta bangaskiyar nan tasa adalci ce.

6 Haka kuma Dawuda ya yi maganar albarkar da aka yi wa mutumin da Allah yake lasafta adalci a gare shi, ba don ya yi aikin lada ba,

7 da ya ce,

“Albarka tā tabbata ga waɗanda aka yafe wa laifofinsu,

Waɗanda kuma aka shafe zunubansu,

8 Albarka tā tabbata ga wanda faufau Ubangiji ba zai lasafta zunubansa ba.”

9 To, wannan albarka, masu kaciya ne kawai ake yi wa, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Gama abin da muke cewa shi ne, “Aka lasafta bangaskiyar Ibrahim adalci ce a gare shi.”

10 To, a cikin wane hali aka lasafta masa ita? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa tun ba a yi ba? Ai, tun ba a yi ba ne, ba bayan da aka yi ba.

11 Kaciyar da aka yi masa alama ce, wato tabbatacciyar shaida ce ta samun adalci, albarkacin bangaskiyar da yake da ita tun ba a yi masa kaciya ba. Wannan kuwa, domin yă zama uban dukkan masu ba da gaskiya ne, domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba,

12 haka kuma yă zama uban masu kaciya, waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba, har ma suna bin hanyar bangaskiyar nan ta kakanmu Ibrahim, wadda shi ma ya bi, tun ba a yi masa kaciya ba.

Tabbatar da Alkawari ta Wurin Bangaskiya

13 Alkawarin nan da aka yi wa Ibrahim da zuriyarsa, cewa zai zama magājin duniya, ba ta Shari’a aka yi masa ba, amma domin ya ba da gaskiya ne, shi ya sa Allah ya karɓe shi mai adalci ne.

14 In dai masu bin Shari’a su ne magāda, ashe, bangaskiya ta zama banza ke nan, alkawarin nan kuma ya wofinta,

15 don Shari’a tana jawo fushin Allah. A inda ba Shari’a kuwa, ba keta umarni ke nan.

16 Saboda haka al’amarin ya dogara ga bangaskiya, domin yă zama bisa ga alheri, don kuma a tabbatar da alkawarin nan ga dukkan zuriyar Ibrahim, ba ga masu bin Shari’a kaɗai a cikinsu ba, har ma ga waɗanda suke da bangaskiya irin Ibrahim, shi da yake ubanmu duka.

17 kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na sa ka uban al’ummai da yawa.” Shi ne kuwa ubanmu a gaban Allah, wannan da ya gaskata, wato mai raya matattu, shi ne kuma mai kiran marasa kasancewa kamar sun kasance.

18 Ibrahim kuwa ko da yake ba halin sa zuciya a gare shi, sai ya yi ta sawa, ya gaskata zai zama uban al’ummai da yawa, kamar yadda aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za ta yawaita.”

19 Bangaskiyarsa kuwa ba ta raunana ba, bai dubi gajiyawar jikinsa ba, don yana da shekara wajen ɗari a lokacin, ko kuma cewa Saratu ta wuce haihuwa.

20 Ba kuwa wata rashin bangaskiyar da ta sa shi shakkar cikar alkawarin Allah, sai ma ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa ya yi, yana ɗaukaka Allah,

21 yana haƙƙaƙewa, cewa Allah na da ikon yin abin da ya yi alkawari.

22 Shi ya sa aka lasafta bangaskiyarsa adalci ce a gare shi.

23 To, “lasafta masa” ɗin nan da aka rubuta kuwa, ba saboda Ibrahim kaɗai aka rubuta ba,

24 har saboda mu ma, za a lasafta mana, wato mu da muke gaskatawa da wannan da ya ta da Yesu Ubangijinmu daga matattu,

25 wanda aka bayar a kashe saboda laifofinmu, aka kuma tashe shi, domin mu sami kuɓuta ga Allah.