Categories
M. SH

M. SH 28

Albarkun Biyayya

1 “Idan kun yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, kuna aikata dukan umarnansa waɗanda nake umartarku da su yau, to, Ubangiji Allahnku zai fifita ku fiye da dukan sauran al’umma.

2 Idan kun yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, dukan albarkun nan za su sauko muku, su zama naku.

3 “Za ku zama masu albarka, ko kuna cikin gari, ko kuna cikin karkara.

4 “’Ya’yanku za su zama masu albarka, haka nan kuma amfanin gonakinku, da ‘ya’yan dabbobinku, da ‘ya’yan shanunku, da ‘ya’yan tumakinku da awakinku.

5 “Kwandunanku da makwaɓan za su yalwata ƙullunku.

6 “Da albarka za ku shiga, da albarka kuma za ku fita.

7 “Ubangiji zai sa ku fatattaki abokan gābanku a gabanku waɗanda suke tasar muku. Ta hanya guda za su auka muku, amma ta hanyoyi bakwai za su gudu daga gabanku.

8 “Ubangiji zai sa wa abin da yake cikin rumbunanku albarka da dukan aikin hannuwanku. Zai sa muku albarka a ƙasar da yake ba ku.

9 “Ubangiji zai sa ku zama tsattsarkar jama’arsa kamar yadda ya rantse muku, idan za ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin tafarkunsa.

10 Dukan mutanen duniya za su gane ku na Ubangiji ne, za su ji tsoronku.

11 Ubangiji zai arzuta ku ƙwarai da ‘ya’ya, da ‘ya’yan dabbobi, da amfanin gona, a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba ku.

12 Ubangiji zai buɗe muku taskarsa ta sammai, don ya ba ƙasarku ruwa a kan kari, zai kuma sa albarka a kan dukan aikin hannuwanku. Al’ummai da yawa za su karɓi rance a wurinku, amma ku, ba za ku karɓi rance ba.

13 Ubangiji zai sa ku zama kai, ba wutsiya ba. Kullum ci gaba za ku yi, ba baya ba, idan kuka yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku waɗanda nake umartarku da su yau, in kun lura, kun yi aiki da su,

14 idan kuma ba ku kauce zuwa dama ko hagu daga maganar da na umarce ku da ita yau ba, wato don ku bi waɗansu gumaka, ku bauta musu.”

Sakamakon Rashin Biyayya

15 “Amma idan ba za ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku ba, ko kuwa ba ku lura kuka aikata umarnansa da dokokinsa waɗanda nake umartar da su yau ba, to, dukan waɗannan la’ana za su auko muku, su same ku.

16 “La’anannu za ku zama a gari da karkara.

17 “La’anannu ne kwandunanku da makwaɓan ƙullunku.

18 “La’anannu ne ‘ya’yanku, da amfanin gonakinku, da ‘ya’yan shanunku, da ‘ya’yan tumakinku da na awakinku.

19 “Da la’ana za ku shiga, da la’ana kuma za ku fita.

20 “Ubangiji zai aiko muku da la’ana, da ruɗewa, da damuwa cikin dukan abin da za ku yi, har ya hallaka ku, ku lalace da sauri saboda mugayen ayyukanku, domin kuma kuka rabu da ni.

21 Ubangiji zai aiko muku da annoba wadda za ta manne muku, ta cinye ku cikin ƙasar da za ku shiga, ku mallake ta.

22 Ubangiji zai buge ku da ciwon fuka, da zazzaɓi, da ciwon kumburi, da zafi mai tsanani, da fari, da burtuntuna, da fumfuna. Waɗannan za su yi ta damunku har ku lalace.

23 Samaniya da take bisa kanku za ta zama tagulla, ƙasar kuma da kuke a bisa kanta ta zama baƙin ƙarfe.

24 Ubangiji zai mai da ruwan sama na ƙasarku gāri da ƙura, zai zubo muku da shi daga sama har ku hallaka.

25 “Ubangiji zai sa abokan gabanku su rinjaye ku cikin yaƙi. Ta hanya guda za ku auka musu, amma ta hanyoyi bakwai za ku gudu daga gabansu. Za ku zama abin ƙi ga dukan mulkokin duniya.

26 Gawawwakinku za su zama abinci ga dukan tsuntsayen sama, da namomin duniya. Ba wanda zai kore su.

27 Ubangiji zai buge ku da marurai irin na Masar, da basur, da ƙazwa, da ƙaiƙayi waɗanda ba za su warke ba.

28 Ubangiji kuma zai buge ku da ciwon hauka, da makanta, da rikicewar hankali.

29 Da tsakar rana za ku riƙa lalubawa kamar makaho, ba za ku yi arziki cikin ayyukanku ba. Za a riƙa zaluntarku, ana yi muku ƙwace kullum, ba wanda zai cece ku.

30 “Za ku yi tashin yarinya, wani ne zai kwana da ita. Za ku gina gida, wani ne zai zauna a ciki. Za ku dasa inabinku, wani ne zai girbe amfanin.

31 Za a yanka sanku a idonku, amma ba za ku ci ba. Za a ƙwace jakinku ƙiri ƙiri a idonku, ba za a mayar muku da shi ba. Za a ba magabtanku tumakinku, ba wanda zai cece ku.

32 A idonku za a ba da ‘ya’yanku mata da maza ga wata al’umma dabam, za ku yi ta jin kewarsu, amma a banza, gama ba ku da ikon yin kome.

33 Mutanen da ba ku sani ba, su za su ci amfanin gonakinku da dukan amfanin wahalarku. Za a zalunce ku, a murƙushe ku kullum.

34 Abubuwan da idanunku za su gani za su sa ku zama mahaukata.

35 Ubangiji zai bugi gwiwoyinku da ƙafafunku da marurai tun daga tafin ƙafarku har zuwa ƙoƙwan kanku.

36 “Ubangiji zai bashe ku, ku da sarkin da kuka naɗa wa kanku ga wata al’ummar da ku da kakanninku ba ku sani ba. Can za ku bauta wa gumakan itace da na duwatsu.

37 Za ku zama abin ƙi, da abin karin magana, da abin habaici a cikin dukan mutane inda Ubangiji zai kora ku.

38 “Za ku shuka iri da yawa a gonakinku, amma kaɗan za ku girbe gama fara za su cinye.

39 Za ku dasa gonakin inabi, ku nome su, amma ba za ku sha ruwan inabin, ko ku tsinke ‘ya’yan inabin ba, gama tsutsa za ta cinye shi.

40 Za ku sami itatuwan zaitun ko’ina cikin ƙasarku, amma ba za ku sami man da za ku shafa ba, gama ‘ya’yan za su kakkaɓe.

41 Za ku haifi ‘ya’ya mata da maza, amma ba za su zama naku ba, gama za a kai su bauta.

42 Ƙwari za su cinye dukan itatuwanku da dukan amfanin ƙasarku.

43 “Baƙin da suke tare da ku za su yi ta ƙaruwa, ku kuwa za ku yi ta komawa baya baya.

44 Za ku karɓi rance a wurinsu, su ba za su karɓi rance a wurinku ba. Su za su zama kai, ku kuwa za ku zama wutsiya.

45 “Dukan waɗannan la’anoni za su auko muku, su bi ku, su same ku, har ku hallaka, domin ba ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku ba, ba ku kiyaye umarnai da dokoki da ya umarce ku da su ba.

46 Za su zama alama da abin mamaki a kanku da zuriyarku har abada.

47 Ba ku bauta wa Ubangiji Allahnku da murna da farin ciki ba, saboda dukan abin da ya ba ku a yalwace,

48 domin haka za ku bauta wa magabtanku waɗanda Ubangiji zai turo muku. Za ku bauta musu da yunwa, da ƙishirwa, da tsiraici, da talauci. Za su sa karkiyar ƙarfe a wuyanka har su hallaka ku.

49 Ubangiji zai kawo wata al’umma daga nesa, wato daga bangon duniya, mai kai sura kamar gaggafa, wadda za ta yi gāba da ku. Al’ummar da ba ku san harshenta ba,

50 al’umma mai zafin hali, wadda ba ta kula da tsofaffi, ba ta kuma jin tausayin yara.

51 Za ta ci shanunku da amfanin ƙasarku har ku hallaka. Ba za ta bar muku hatsi ko ruwan inabi, ko mai, ko ‘ya’yan shanunku, ko na tumaki da na awakinku ba, har ta lalatar da ku.

52 Za su kewaye garuruwanku da yaƙi, har dogayen garukanku, da kagaranku waɗanda kuke dogara gare su, su rurrushe. Za su kewaye garuruwan ƙasarku da yaƙi a ƙasar da Ubangiji Allahnku ya ba ku.

53 Za ku ci naman ‘ya’yanku, mata da maza, waɗanda Ubangiji Allahnku ya ba ku, saboda irin tsananin kewayewar da magabtanku suka yi muku da yaƙi.

54 Nagarin mutum mai taushin zuciya wanda yake tare da ku, zai ƙi ɗan’uwansa, da matarsa, da ‘ya’yansa da suka ragu,

55 domin kada ya ba wani daga cikinsu naman ‘ya’yansa wanda yake ci, gama ba abin da ya rage masa saboda irin tsananin kewayewar garuruwanku da yaƙi wanda abokan gabanku suka kawo muku.

56 Matar kirki mai taushin zuciya wadda take tare da ku wadda ba za ta sa tafin ƙafarta a ƙasa ba saboda taushin zuciyarta da kyakkyawan halinta, za ta ƙi ƙaunataccen mijinta, da ɗanta, da ‘yarta.

57 A ɓoye za ta ci mahaifar da take biyo bayan ta haihu, da ‘ya’yan da za ta haifa, saboda ba ta da wani abinci lokacin da magabtanku za su kewaye garuruwanku da yaƙi mai tsanani.

58 “Idan ba ku lura, ku aikata dukan maganar dokokin nan da aka rubuta a wannan littafi ba, domin ku ji tsoron sunan nan mai ɗaukaka, mai kwarjini, wato sunan Ubangiji Allahnku,

59 to, Ubangiji zai aukar muku, ku da zuriyarku, da munanan masifu waɗanda ba su kawuwa, da mugayen cuce-cuce marasa warkewa.

60 Sai ya sāke kawo muku cuce-cuce irin na Masar, waɗanda kuka ji tsoronsu, za su kuwa manne muku.

61 Har yanzu kuma Ubangiji zai kawo muku kowace irin cuta, da kowace irin annoba, waɗanda ba a ambace su a littafin dokokin nan ba, har ku hallaka.

62 Ko da yake kuna da yawa kamar taurarin sama, za ku zama ‘yan kaɗan, domin ba ku yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku ba.

63 Kamar yadda Ubangiji ya ji daɗi ya arzuta ku, ya riɓaɓɓanya ku, haka nan kuma zai ji daɗi ya lalatar da ku, ya hallaka ku. Za a fitar da ku daga ƙasar da za ku shiga, ku mallaka.

64 “Ubangiji zai warwatsa ku cikin dukan al’ummai daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Can za ku bauta wa gumakan itace da na dutse waɗanda ku da kakanninku ba ku san su ba.

65 Ba za ku sami zaman lafiya wurin waɗannan al’ummai ba, ko tafin ƙafarku ma ba zai sami wurin hutawa ba. Ubangiji kuma zai sa fargaba a zuciyarku, ya sa idanunku su lalace, ranku zai yi suwu.

66 Kullum ranku zai kasance da damuwa, za ku zauna da tsoro dare da rana, kuna tsoron abin da zai sami ranku.

67 Da safe za ku ce, ‘Da ma maraice ne.’ Da maraice kuma za ku ce, ‘Da ma safiya ce,’ saboda tsoron da yake a zuciyarku, da abubuwan da idanunku suke gani.

68 Ubangiji zai komar da ku Masar cikin jiragen ruwa, ko da yake na ce ba za ku ƙara tafiya can ba. Can za ku sayar da kanku bayi mata da maza, amma ba wanda zai saye ku.”

Categories
M. SH

M. SH 29

Alkawarin Ubangiji da Isra’ilawa a Ƙasar Mowab

1 Waɗannan ne zantuttukan alkawari da Ubangiji ya umarci Musa ya faɗa wa Isra’ilawa a ƙasar Mowab, wato banda alkawarin da ya yi da su a bisa Dutsen Horeb.

2 Sai Musa ya kira dukan Isra’ilawa ya ce musu, “Ai, kun ga dukan abin da Ubangiji ya yi wa Fir’auna da barorinsa a dukan ƙasar Masar.

3 Idanunku sun ga manyan wahalai, da alamu, da mu’ujizai masu girma.

4 Duk da haka har wa yau Ubangiji bai ba ku zuciyar ganewa, ko idanun gani, ko kunnuwan ji ba.

5 Shekara arba’in na bi da ku cikin jeji. Rigunanku da takalmanku ba su tsufa ba.

6 Ba ku ci hatsi ba, ba ku kuma sha ruwan inabi ba, ko barasa, don ku sani shi ne Ubangiji Allahnku.

7 Sa’ad da kuka isa wannan wuri, sai Sihon Sarkin Heshbon, da Og, Sarkin Bashan, suka fito su yi yaƙi da mu, amma muka ci su.

8 Muku ƙwace ƙasarsu, muka ba Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa, su gāda.

9 Saboda haka sai ku kiyaye, ku aikata dukan zantuttukan wannan alkawari don ku arzuta a cikin dukan abin da za ku yi.

10 “Yau, ga ku nan tsaye, dukanku a gaban Ubangiji Allahnku, shugabannin kabilanku, da dattawanku, da shugabannin sojojinku, da dukan mazajen Isra’ila,

11 da ‘ya’yanku, da matanku, da baƙin da suke a zangonku, da mai yi muku faskare ko mai ɗebo muku ruwa.

12 Don ku ƙulla alkawari da Ubangiji Allahnku, alkawarin da Ubangiji Allahnku yake yi da ku yau.

13 Don ya mai da ku jama’arsa yau, shi kuma ya zama Allahnku kamar yadda ya yi muku magana, da yadda kuma ya rantse wa kakanninku, wato Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.

14 Ba da ku kaɗai nake yin wannan alkawari ba,

15 amma da wanda ba ya nan tare da mu yau, da shi wanda yake tare da mu a nan yau, a gaban Ubangiji Allahnmu.

16 “Kun sani dai yadda muka zauna a ƙasar Masar, da yadda muka yi ta ratsawa ta tsakiyar al’ummai muka wuce.

17 Kun ga abubuwan da suke da su masu banƙyama, wato gumakansu na itace, da na dutse, da na azurfa, da na zinariya.

18 Kada zuciyar wani mutum, ko ta wata mata ko na wani iyali, ko wata kabila cikinku yau, ta bar bin Ubangiji Allahnku, ta koma ga bauta wa gumakan al’umman nan. Kada a iske wani tushe a cikinku mai ba da ‘ya’ya masu dafi, masu ɗaci.

19 Idan wani mutum ya ji zantuttukan la’anan nan sa’an nan ya sa wa kansa albarka a zuciyarsa, yana cewa, ‘Ba abin da zai same ni ko na bi taurin zuciyata,’ wannan zai haddasa lalacewar ɗanye da busasshe gaba ɗaya.

20 Ubangiji ba zai gafarce shi ba, amma fushin Ubangiji da kishinsa za su auko a kan wannan mutum, dukan la’anar kuma da aka rubuta a littafin nan za ta bi ta kansa, Ubangiji kuma zai shafe sunansa daga duniya.

21 Ubangiji zai ware mutumin nan daga dukan kabilan Isra’ila, don ya hukunta shi bisa ga dukan la’anar da aka rubuta a wannan littafin dokoki.

22 “Tsararraki masu zuwa nan gaba, wato ‘ya’yan da za su gaje ku, da baƙon da ya zo daga ƙasa mai nisa, za su ga annobar ƙasar, da cuce-cucen da Ubangiji zai ɗora mata.

23 Dukan ƙasa za ta zama kibritu da gishiri, ba shuka, ba amfani, ciyawa kuma ba ta tsirowa, kamar yadda Ubangiji ya kabantar da Saduma da Gwamrata, da Adam da Zeboyim, da zafin fushinsa.

24 Dukan al’ummai za su ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan ƙasa? Me ya sa ya yi fushi mai tsanani haka?’

25 Sa’an nan jama’a za su ce, ‘Saboda sun yi watsi da alkawarin Ubangiji Allah na kakanninsu, wato alkawarin da ya yi da su sa’ad da ya fisshe su daga ƙasar Masar.

26 Suka tafi suka bauta wa gumaka, suka yi musu sujada, gumakan da ba su san su ba, ba Ubangiji ne ya ba su ba.

27 Saboda haka Ubangiji ya husata da wannan ƙasa, ya kawo mata kowace irin la’anar da aka rubuta a wannan littafin.

28 Ubangiji ya tumɓuke su da zafin fushinsa, da babbar hasala, daga ƙasarsu, ya watsa su cikin wata ƙasa dabam kamar yadda suke a yau.’

29 “Sanin gaibu na Ubangiji Allahnmu ne, amma abubuwan da aka bayyana namu ne, mu da ‘ya’yanmu har abada, don mu kiyaye dukan maganar dokokin nan.”

Categories
M. SH

M. SH 30

Sharuɗan Komar da Mutane, da kuma Sa musu Albarka

1 “Sa’ad da duk waɗannan abubuwa suka same ku, wato albarka da la’ana waɗanda na sa a gabanku, in kun tuna da su a zuciyarku a duk inda kuke cikin al’ummai inda Ubangiji Allahnku ya kora ku,

2 kuka sāke komowa wurin Ubangiji Allahnku, ku da ‘ya’yanku kuka yi biyayya da maganarsa da zuciya ɗaya, da dukan ranku, bisa ga yadda na umarce ku yau,

3 sa’an nan Ubangiji Allahnku zai komo da ku daga bauta, ya yi muku jinƙai. Zai tattaro ku daga cikin al’ummai inda ya warwatsa ku.

4 Idan korarrunku suna can ƙurewar duniya, Ubangiji Allahnku zai tattaro ku daga can, ya dawo da ku.

5 Ubangiji Allahnku kuma zai komo da ku cikin ƙasar da kakanninku suka mallaka, za ku mallake ta. Ubangiji zai arzuta ku, ya riɓaɓɓanya ku fiye da kakanninku.

6 Ubangiji Allahnku kuma zai tausasa zuciyarku da ta ‘ya’yanku domin ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da zuciya ɗaya da dukan ranku, domin ku rayu.

7 Ubangiji Allahnku kuwa zai ɗora wa magabtanku da maƙiyanku waɗanda suka tsananta muku waɗannan la’ana.

8 Sa’an nan za ku yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, ku kiyaye dukan umarnan nan waɗanda na umarce ku da su yau.

9 Ubangiji Allahnku zai arzuta dukan aikin hannuwanku ƙwarai, ya kuma arzutar da ‘ya’yanku da ‘ya’yan shanu, da amfanin gona, gama Ubangiji zai ji daɗi ya arzuta ku kuma yadda ya ji daɗin kakanninku,

10 idan za ku yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, ku kiyaye umarnansa da dokokinsa waɗanda suke rubuce a littafin dokokin nan, idan kuma kun juyo wurin Ubangiji Allahnku da zuciya ɗaya da dukan ranku.

11 “Gama wannan umarni da na yi muku yau, bai fi ƙarfinku ba, bai kuma yi nisa da ku ba.

12 Ba cikin Sama yake ba, balle ku ce, ‘Wa zai hau zuwa sama, ya sauko mana da shi don mu ji, mu kiyaye?’

13 Ba kuma a hayin teku yake ba, balle ku ce, ‘Wa zai haye mana wannan teku don ya kawo mana shi don mu ji, mu kiyaye?’

14 Amma umarnin yana kurkusa da ku, yana cikin bakinku da zuciyarku don ku kiyaye shi.

15 “Ga shi yau, na sa rai da nagarta a gabanku, da mutuwa da mugunta.

16 Idan kuka kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku waɗanda nake umartarku da su yau, idan kuma kun ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna yin tafiya cikin tafarkunsa, kuna kiyaye umarnansa, da dokokinsa, da farillansa, to, za ku rayu, ku riɓaɓɓanya, Ubangiji Allahnku kuwa zai sa muku albarka cikin ƙasar da za ku shiga, ku mallake ta.

17 Amma idan zuciyarku ta kangare kun ƙi ku saurara, amma zuciyarku ta janye ku kun yi wa gumaka sujada, kuka bauta musu,

18 to, ina faɗa muku yau, lalle za ku hallaka. Ba za ku yi tsawon rai a ƙasar da za ku haye Urdun ku shiga ciki don ku mallake ta ba.

19 Ina kiran sama da duniya su zama shaidu a kanku yau, cewa na sa rai da mutuwa a gabanku, da albarka da la’ana. Ku zaɓi rai fa, don ku rayu, ku da zuriyarku.

20 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi biyayya da maganarsa, ku manne masa, gama wannan shi ne ranku da tsawon kwanakinku, don ku zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku ya rantse zai ba kakanninku, wato Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.”

Categories
M. SH

M. SH 31

Joshuwa zai Gāji Musa

1 Sai Musa ya ci gaba da yi wa dukan Isra’ilawa magana.

2 Ya ce, “Yau shekarata ɗari da ashirin ne, ba na iya kaiwa da komowa. Ubangiji kuwa ya ce mini, ‘Ba za ka haye wannan Urdun ba.’

3 Ubangiji Allahnku shi ne zai yi gaba ya haye, ya hallaka al’umman da take gabanku don ku ci su. Joshuwa ne zai shugabance ku, ya haye kamar yadda Ubangiji ya faɗa.

4 Ubangiji zai yi musu kamar yadda ya yi wa Sihon da Og, sarakunan Amoriyawa, da ƙasarsu, sa’ad da ya hallaka su.

5 Ubangiji zai bashe su a gare ku. Za ku yi musu kamar yadda dā na umarce ku.

6 Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro, ko ku firgita saboda su, gama Ubangiji Allahnku yana tare da ku. Ba zai kunyatar da ku ba, ba kuwa zai yashe ku ba.”

7 Sai Musa ya kira Joshuwa, ya yi masa magana a gaban dukan jama’ar Isra’ila, ya ce, “Ka ƙarfafa, ka yi ƙarfin hali, gama kai ne za ka kai wannan jama’a cikin ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba kakanninsu. Kai ne za ka ba su ita gādo.

8 Ubangiji kansa zai bi da kai, ba zai kunyatar da kai ba, ba kuwa zai yashe ka ba. Kada ka ji tsoro, kada kuma ka karai.”

A Karanta Dokokin Kowace Shekara ta Bakwai

9 Sai Musa ya rubuta waɗannan dokoki, ya ba firistoci, ‘ya’yan Lawiyawa, waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawari na Ubangiji, da dukan dattawan Isra’ila.

10 Sai Musa ya umarce su, ya ce, “A ƙarshen kowace shekara bakwai, a lokacin da aka ƙayyade na shekarar yafewa, a lokacin Idin Bukkoki,

11 sa’ad da dukan Isra’ilawa za su hallara a gaban Ubangiji Allahnku a inda zai zaɓa, to, sai ku karanta musu waɗannan dokoki su ji da kunnuwansu.

12 Ku tara dukan jama’a wuri ɗaya, mata da maza, da yara, da baƙin da suke zaune tare da ku a garuruwanku domin su ji, su koyi tsoron Ubangiji Allahnku, su kuma lura su aikata dukan dokokin nan,

13 domin ‘ya’yansu, waɗanda ba su sani ba, su ji, su koyi tsoron Ubangiji Allahnku dukan kwanakinku cikin ƙasar da za ku haye Urdun, ku mallaka.”

Umarnin Ƙarshe da Ubangiji Ya Yi wa Musa

14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Lokacin rasuwarka ya yi, sai ka kira Joshuwa, ku shigo alfarwa ta sujada, don in ba shi ragamar mulki.” Sai Musa da Joshuwa suka tafi, suka shiga alfarwa ta sujada.

15 Ubangiji kuwa ya bayyana a cikin alfarwar a al’amudin girgije. Al’amudin girgijen kuwa ya tsaya a ƙofar alfarwar.

16 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ga shi, za ka rasu ka tarar da kakanninka. Wannan jama’a kuwa za ta fara kaucewa daga hanya, su bi gumakan ƙasar da za su shiga, su zauna. Za su rabu da ni, su ta da alkawarina wanda na yi da su.

17 A wannan rana zan husata da su ƙwarai, in rabu da su, in ɓoye musu fuskata, za a cinye su. Masifu da wahalai za su same su. Za su kuwa ce a ranar, ‘Masifun nan sun same mu domin Allahnmu ba ya tare da mu.’

18 Hakika kuwa, zan ɓoye musu fuskata sabili da muguntar da suka aikata, suka kuma bi gumaka.

19 “Don haka, sai ka rubuta wannan waƙa, ka koya wa Isra’ilawa. Ka sa ta a bakinsu don waƙan nan ta zama shaida a gare ni game da Isra’ilawa.

20 Sa’ad da na kawo su a ƙasar da take da yalwar abinci, wadda na rantse zan ba kakanninsu, har suka ci, suka ƙoshi, suka yi ƙiba, za su juya, su bi gumaka, su bauta musu. Za su raina ni, su tā da alkawarina.

21 Sa’ad da yawan masifun nan da wahalan nan suka same su, to, waƙar nan za ta ba da shaida a kansu, gama zuriyarsu ba za ta manta da wannan waƙa ba, gama na san ƙudurin da suke yi kafin in kawo su ƙasar da na rantse zan bayar.”

22 Saboda wannan sai Musa ya rubuta wannan waƙa a ranar, ya koya wa jama’ar Isra’ila.

23 Sai Ubangiji ya umarci Joshuwa ɗan Nun ya ce, “Ka ƙarfafa, ka yi ƙarfin hali, gama kai ne za ka kai jama’ar Isra’ila a ƙasar da na rantse zan ba su, ni kuma da kaina zan tafi tare da kai.”

24 Sa’ad da Musa ya gama rubuta maganar dokokin nan sarai a littafin,

25 sai ya umarci Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, ya ce,

26 “Ku ɗauki littafin dokokin nan, ku ajiye shi tare da akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku domin ya zama shaida a kanku,

27 gama na san tayarwarku da taurinkanku. Tun ma ina da rai ke nan tare da ku kuka tayar wa Ubangiji, balle bayan rasuwata.

28 Ku tattaro mini dattawan kabilanku da manyanku don in faɗa musu wannan magana a kunnensu, in kuma kira sama da duniya su zama shaida a kansu.

29 Gama na sani bayan rasuwata za ku aikata mugunta, ku kauce daga hanyar da na umarce ku. Masifa za ta auko muku a kwanaki masu zuwa saboda za ku aikata mugunta a gaban Ubangiji, za ku tsokani fushinsa da aikin hannuwanku.”

Waƙar Musa

30 Sa’an nan Musa ya hurta kalmomin wannan waƙa a kunnen dukan taron jama’ar Isra’ila har ƙarshensu.

Categories
M. SH

M. SH 32

1 “Ku saurara, ya ku sammai, gama zan yi magana,

Bari duniya ta ji maganar bakina.

2 Bari koyarwata ta zubo kamar ruwan sama,

Maganata ta faɗo kamar raɓa,

Kamar yayyafi a bisa ɗanyar ciyawa,

Kamar ɗiɗɗigar ruwa a bisa ganyaye.

3 Gama zan yi shelar sunan Ubangiji,

In yabi girman Allahnmu!

4 “Shi Dutse ne, aikinsa kuma cikakke ne,

Gama dukan hanyoyinsa masu adalci ne.

Allah mai aminci ne, babu rashin gaskiya a gare shi,

Shi mai adalci ne, nagari ne kuma.

5 Sun aikata mugunta a gabansa,

Su ba ‘ya’yansa ba ne saboda lalacewarsu,

Su muguwar tsara ce, karkatacciya,

6 Haka za ku sāka wa Ubangiji,

Ya ku wawaye, mutane marasa hikima?

Ba shi ne Ubanku, Mahaliccinku ba,

Wanda ya yi ku, ya kuma kafa ku?

7 “Ku fa tuna da kwanakin dā,

Ku yi tunani a kan shekarun tsararraki,

Ku tambayi mahaifanku, su za su faɗa muku,

Ku tambayi dattawanku, su kuma za su faɗa muku,

8 Sa’ad da Maɗaukaki ya ba al’ummai gādonsu,

Sa’ad da ya raba ‘yan adam,

Ya yanka wa mutane wurin zama bisa ga yawan Isra’ilawa.

9 Gama rabon Ubangiji shi ne jama’arsa,

Yakubu shi ne rabon gādonsa.

10 “Ya same shi daga cikin hamada,

A jeji marar amfani, inda namomi suke kuka.

Ya kewaye shi, ya lura da shi,

Ya kiyaye shi kamar ƙwayar idonsa.

11 Kamar gaggafar da take kaɗa fikafikanta a kan sheƙarta,

Tana rufe da ‘yan tsakinta,

Ta buɗe fikafikanta, ta kama su,

Ta ɗauke su a bisa kafaɗunta.

12 Ubangiji ne kaɗai ya bishe shi,

Ba wani baƙon allah tare da shi.

13 “Ya sa shi ya hau kan tuddai,

Ya ci amfanin ƙasa,

Ya sa shi ya sha zuma daga dutse,

Ya ba shi mai daga dutsen ƙanƙara.

14 Ya sami kindirmo daga shanu,

Da madara daga garken tumaki da na awaki,

Da kitse daga ‘yan raguna, da raguna,

Da bijimai, da bunsurai daga Bashan,

Da alkama mafi kyau.

Ka sha ruwan inabi jaja wur, mai kyau.

15 “Yeshurun ya yi ƙiba, yana harbin iska,

Ka yi ƙiba, ka yi kauri, ka yi sumul.

Ya rabu da Allahn da ya yi shi,

Ya raina Dutsen Cetonsa.

16 Suka sa shi kishi, saboda gumaka,

Suka tsokani fushinsa da abubuwan banƙyama.

17 Suka miƙa hadayu ga aljannun da ba Allah ba,

Ga gumakan da ba su sani ba,

Sababbin allolin da aka shigo da su daga baya,

Waɗanda kakanninku ba su ji tsoronsu ba.

18 Kun ƙi kula da Dutsen da ya haife ku,

Kun manta da Allahn da ya ba ku rai.

19 “Ubangiji ya gani, ya raina su,

Saboda tsokanar da ‘ya’yansa mata da maza suka yi masa.

20 Ya ce, ‘Zan ɓoye musu fuskata,

Zan ga yadda ƙarshensu zai zama.

Gama su muguwar tsara ce,

‘Ya’ya ne marasa aminci.

21 Suka sa ni kishi da abin da ba Allah ba,

Suka tsokani fushina da gumakansu,

Ni kuma zan sa su su yi kishi da waɗanda suke ba mutane ba.

Zan tsokane su da wawanyar al’umma.

22 Gama fushina ya kama wuta,

Tana ci har ƙurewar zurfin lahira.

Za ta cinye duniya da dukan amfaninta,

Za ta kama tussan duwatsu.

23 “ ‘Zan tula musu masifu,

Zan ƙare kibauna a kansu,

24 Za su lalace saboda yunwa,

Zazzaɓi mai zafi, da muguwar annoba za su cinye su.

Zan aika da haƙoran namomi a kansu,

Da dafin abubuwa masu jan ciki.

25 Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su,

A cikin ɗakuna kuma tsoro,

Zai hallaka saurayi da budurwa,

Da mai shan mama da mai furfura.

26 Na ce, “Zan watsar da su,

In sa a manta da su cikin mutane.”

27 Amma saboda gudun tsokanar maƙiyi,

Kada abokan gābansu su zaci su ne suka ci nasara.

Ai, ni ne na yi wannan.’

28 “Gama su al’umma ce wadda ba ta yin shawara,

Ba su da ganewa.

29 Da suna da hikima, da sun gane wannan,

Da za su gane da yadda ƙarshensu zai zama!

30 Ƙaƙa mutum ɗaya zai runtumi dubu,

Mutum biyu kuma su kori zambar goma,

Sai dai Dutsensu ya sayar da su,

Ubangiji kuma ya bashe su?

31 Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne,

Ko abokan gabanmu ma sun san haka.

32 Kurangar inabinsu daga kurangar inabin Saduma ne

Da gonakin Gwamrata.

‘Ya’yan inabinsu dafi ne,

Nonnansu masu ɗaci ne.

33 Ruwan inabinsu dafin macizai ne.

Da mugun dafin kumurci.

34 “ ‘Wannan ba a jibge suke a rumbunana ba,

A ƙulle kuma a taskokina?

35 Sakayya da ɗaukar fansa nawa ne,

A lokacin ƙafarsu za ta zame,

Gama ranar masifarsu ta kusa,

Hallakarsu za ta zo da sauri.’

36 Ubangiji zai ɗauka wa jama’arsa fansa,

Zai ji ƙan bayinsa,

Sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya kāsa,

Ba kuma wanda ya ragu, bawa ko ɗa.

37 Sa’an nan zai ce, ‘Ina gumakansu,

Dutse wanda suka nemi mafaka gare shi,

38 Waɗanda suka ci kitsen hadayunsu,

Suka sha ruwan inabin hadayarsu ta sha?

Bari su tashi su taimake ku,

Bari su zama mafaka!

39 “ ‘Ku duba fa, ni ne shi,

Ba wani Allah, banda ni,

Nakan kashe, in rayar,

Nakan sa rauni, nakan kuma warkar,

Ba wanda zai cece su daga hannuna.

40 Na ɗaga hannuna sama,

Na rantse da madawwamin raina,

41 Sa’ad da na wasa takobina mai walƙiya,

Na riƙe shi da hannuna don yin hukunci,

Zan ɗauki fansa a kan magabtana

Zan sāka wa maƙiyana.

42 Zan sa kibauna su bugu da jini,

Takobina zai ci nama,

Da jinin kisassu da na kamammu,

Da ƙoƙon kan shugabannin maƙiya.’

43 “Ya ku al’ummai, ku yabi jama’arsa,

Gama zai rama wa bayinsa saboda jininsu,

Zai ɗauki fansa a kan magabtansa,

Zai tsarkake ƙasar jama’arsa.”

Gargaɗin Musa na Ƙarshe

44 Sai Musa da Joshuwa ɗan Nun suka zo, suka hurta dukan kalmomin wannan waƙa a kunnen jama’a.

45 Sa’ad da Musa ya gama hurta waɗannan kalmomi ga Isra’ila,

46 ya ce musu, “Ku riƙe dukan waɗannan kalmomi a zuciyarku, waɗanda nake yi muku kashedi da su a yau don ku umarci ‘ya’yanku su kiyaye dukan maganar dokokin nan sosai.

47 Wannan ba magana kurum ba ce, amma ranku ne. Ta wurin wannan magana ce za ku yi tsawon rai a ƙasar da za ku haye Urdun zuwa ciki don ku mallake ta.”

An Yarda wa Musa Ya Hangi Ƙasar Kan’ana

48 A wannan rana ce Ubangiji ya ce wa Musa,

49 “Ka hau duwatsun Abarim, wato Dutsen Nebo wanda yake a ƙasar Mowab, daura da Yariko, ka duba ƙasar Kan’ana wadda zan ba Isra’ilawa su mallaka.

50 Za ka rasu a kan dutsen da za ka hau, za a kai ka wurin mutanen da suka riga ka gidan gaskiya, kamar yadda ɗan’uwanka, Haruna, ya rasu a Dutsen Hor, aka kai shi wurin mutanensa waɗanda suka riga shi gidan gaskiya.

51 Gama ba ku amince da ni ba a gaban mutanen Isra’ila a wurin ruwan Meriba ta Kadesh a jejin Zin a wannan lokaci, domin ba ku nuna tsarkina a gaban jama’ar Isra’ila ba.

52 Za ka ga ƙasar da nake ba jama’ar Isra’ila, amma ba za ka shiga cikinta ba.”

Categories
M. SH

M. SH 33

Musa Ya Sa wa Kabilan Isra’ila Albarka

1 Wannan ita ce albarkar da Musa, mutumin Allah, ya sa wa Isra’ilawa kafin ya rasu.

2 Ya ce,

“Ubangiji ya taho daga Sina’i,

Daga Dutsen Faran kuma ya haskaka,

Ya taho tare da dubban tsarkakansa,

Da harshen wuta a damansa.

3 Hakika, yana ƙaunar jama’arsa,

Dukan tsarkaka suna a ikonka,

Suna biye da kai,

Suna karɓar umarninka.

4 Musa ya ba mu dokoki,

Abin gādo ga taron jama’ar Yakubu.

5 Ubangiji shi ne sarki a Yeshurun,

Sa’ad da shugabanni suka taru,

Dukan kabilan Isra’ila suka taru.

6 “Allah ya sa Ra’ubainu ya rayu, kada ya mutu,

Kada mutanensa su zama kaɗan.”

7 A kan Yahuza ya ce,

“Ka ji muryar Yahuza, ya Ubangiji,

Ka kawo shi wurin jama’arsa.

Ka yi yaƙi da ikonka dominsu,

Ka taimake shi a kan maƙiyansa.”

8 A kan Lawi ya ce,

“Ka ba Mai Tsarki Tumminka da Urim naka,

Shi wanda ka jarraba a Masaha,

Wanda ka yi jayayya da shi a ruwan Meriba,

9 Wanda ya ce wa mahaifinsa da mahaifiyarsa,

‘Ban kula da ku ba.’

Ya ce wa ‘yan’uwansa su ba nasa ba ne.

Ya kuma ƙyale ‘ya’yansa,

Domin sun kiyaye maganarka,

Sun riƙe alkawarinka.

10 Suna koya wa Yakubu farillanka,

Suna koya wa Isra’ila dokokinka.

Suna ƙona turare a gabanka,

Suna ƙona hadaya ta ƙonawa a bagadenka.

11 Ya Ubangiji ka inganta jaruntakarsu,

Ka karɓi aikin hannuwansu,

Ka murƙushe ƙarfin abokan gābansu,

Da waɗanda suke ƙinsu don kada su ƙara tashi.”

12 A kan Biliyaminu, ya ce,

“Shi ƙaunatacce na Ubangiji ne,

Yana zaune lafiya kusa da shi,

Ubangiji yana yi masa garkuwa dukan yini,

Yana zaune a kan kafaɗunsa.”

13 A kan Yusufu, ya ce,

“Ubangiji ya sa wa ƙasarsa albarka,

Da kyawawan kyautai daga sama, da raɓa,

Da ruwan da yake a ƙasa,

14 Da kyawawan kyautan da rana take bayarwa,

Da kyawawan kyautan da watanni suke bayarwa,

15 Da abubuwa mafi kyau na duwatsun dā,

Da kyawawan kyautai na madawwaman tuddai.

16 Da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta,

Da alherin wanda yake zaune a jeji.

Bari waɗannan kyautai su sauka a kan Yusufu,

A kan wanda yake keɓaɓɓe daga cikin ‘yan’uwansa.

17 Darajarsa kamar ta ɗan farin bijimi take,

Ƙahoninsa kamar na ɓauna suke,

Da su yake tunkwiyin mutane,

Zai tura su zuwa ƙurewar duniya,

Haka fa rundunan Ifraimu za su zama,

Haka kuma dubban Manassa za su zama.”

18 A kan Zabaluna ya ce,

“Ka yi murna da tafiye-tafiyenka, ya Zabaluna,

Kai kuma Issaka, cikin alfarwanka.

19 Za su kira mutane zuwa dutse,

Can za su miƙa hadayu masu dacewa,

Gama za su ɗebo wadatar tekuna,

Da ɓoyayyun dukiyar yashi.”

20 A kan Gad, ya ce,

“Mai albarka ne wanda ya fāɗaɗa Gad,

Gad yana sanɗa kamar zaki,

Yana yayyage hannu da ƙoƙon kai.

21 Zai zaɓar wa kansa wuri mai kyau,

Gama wurin ne aka keɓe wa shugaba.

Ya zo wurin shugabannin mutane,

Tare da Isra’ila, ya aikata adalcin Ubangiji,

Ya kiyaye farillansa.”

22 A kan Dan, ya ce,

“Dan ɗan zaki ne,

Mai tsalle daga Bashan.”

23 A kan Naftali, ya ce,

“Ya Naftali, ƙosasshe kake da alheri,

Cike kake da albarkar Ubangiji.

Sai ka mallaki tafki da wajen kudu.”

24 A kan Ashiru, ya ce,

“Ashiru mai albarka ne fiye da sauran ‘yan’uwansa,

Bari ya zama abin ƙauna ga ‘yan’uwansa,

Ya kuma tsoma ƙafarsa cikin mai.

25 Kurfanka na baƙin ƙarfe ne da tagulla,

Ƙarfinka ba zai rabu da kai ba muddin ranka.”

26 “Babu wani kamar Allahn Yeshurun,

Wanda yakan sauko daga Sama don ya cece ka,

Wanda ya sauko daga bisa da ɗaukakarsa.

27 Allah Madawwami, shi ne wurin zamanka,

Madawwaman damatsansa suna tallafarka,

Yana kore maka maƙiyanka,

Ya ce, ‘Ka hallaka su!’

28 Da haka Isra’ila yana zaune lafiya,

Zuriyar Yakubu tana zaune ita kaɗai

A ƙasa mai hatsi da ruwan inabi,

Wurin da raɓa take zubowa daga sama.

29 Mai farin ciki ne kai, ya Isra’ila!

Wane ne kamarku, mutanen da Ubangiji ya ceta?

Ubangiji ne garkuwarku,

Shi ne kuma takobinku mai daraja.

Magabtanku za su yi muku fādanci,

Amma ku za ku tattake masujadansu.”

Categories
M. SH

M. SH 34

Rasuwar Musa

1 Sai Musa ya tashi daga filayen Mowab zuwa Dutsen Nebo, a ƙwanƙolin Fisga wanda yake daura da Yariko. Sai Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, tun daga Gileyad har zuwa Dan,

2 da dukan Naftali, da ƙasar Ifraimu, da ta Manassa, da dukan ƙasar Yahuza har zuwa Bahar Rum,

3 da Negeb, da filin kwarin Yariko, birnin itatuwan giginya, har zuwa Zowar.

4 Ubangiji ya ce masa, “Wannan ita ce ƙasar da na rantse wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, zan ba da ita ga zuriyarsu. Na bar ka ka gan ta da idanunka, amma ba za ka haye, ka shiga ba.”

5 Nan fa, a ƙasar Mowab, Musa bawan Ubangiji, ya rasu kamar yadda Ubangiji ya faɗa.

6 Aka binne shi cikin kwarin ƙasar Mowab, kusa da Betfeyor, amma ba wanda ya san inda aka binne shi har yau.

7 Musa ya yi shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya rasu. Idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuma bai ragu ba.

8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab har kwana talatin. Sa’an nan kwanakin kuka da makoki domin Musa suka ƙare.

9 Joshuwa ɗan Nun yana cike da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya masa hannuwansa. Isra’ilawa suka yi masa biyayya, suka aikata bisa ga yadda Ubangiji ya umarci Musa.

10 Tun daga lokacin nan, ba a taɓa yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska.

11 Ubangiji ya aike shi ya aikata alamu da mu’ujizai a ƙasar Masar a gaban Fir’auna da dukan barorinsa, da dukan ƙasarsa.

12 Ya kuma aikata ayyuka masu iko, masu bantsoro a gaban dukan Isra’ilawa.

Categories
JOSH

JOSH 1

Shirin da Aka Yi don Cin Ƙasar Kan’ana

1 Bayan rasuwar Musa, bawan Ubangiji, Ubangiji ya ce wa Joshuwa ɗan Nun, wanda ya yi wa Musa aiki,

2 “Bawana Musa ya rasu, sai ka tashi ka haye Kogin Urdun, kai da dukan jama’an nan, zuwa cikin ƙasar da nake ba Isra’ilawa.

3 Duk inda tafin sawunku ya taka na riga na ba ku, kamar yadda na alkawarta wa Musa.

4 Tun daga jejin, da Lebanon, har zuwa babban kogin, wato Kogin Yufiretis, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum wajen yamma, za ta zama ƙasarku.

5 Ba mutumin da zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Kamar yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai, ba zan kunyatar da kai ba, ba kuwa zan yashe ka ba.

6 Ka dāge, ka yi ƙarfin hali, gama kai ne za ka yi jagorar wannan jama’a su mallaki ƙasa wadda na rantse zan ba kakanninsu.

7 Ka dai dāge, ka yi ƙarfin hali ƙwarai, kana kiyaye dukan dokokin da bawana Musa ya umarce ka da su. Kada ka kauce musu dama ko hagu, gama da haka nan za ka arzuta cikin dukan harkokinka.

8 Kada wannan littafin dokoki ya rabu da bakinka, amma zai zama abin da za ka yi ta tunani a kansa dare da rana domin ka kiyaye, ka kuma aikata bisa ga dukan abin da aka rubuta a ciki, gama ta haka za ka yi albarka cikin hanyarka, ta haka kuma za ka yi nasara.

9 Ashe, ban umarce ka ba? Ka dāge ka yi ƙarfin hali, kada ka firgita ko ka tsorata, gama Ubangiji Allahnka yana tare da kai duk inda za ka.”

10 Sai Joshuwa ya umarci shugabannin jama’a, ya ce,

11 “Ku shiga zango, ku umarci jama’a, ku ce, ‘Ku shirya wa kanku guzuri, gama nan gaba da kwana uku za ku haye Kogin Urdun don ku mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.’ ”

12 Joshuwa kuma ya ce wa Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa,

13 “Ku tuna da maganar da Musa, bawan Ubangiji, ya umarce ku da ita, ya ce, ‘Ubangiji Allahnku zai hutar da ku, zai kuma ba ku wannan ƙasa.’

14 Da matanku, da ‘yan ƙanananku, da dabbobinku, za su zauna a ƙasar da Musa ya ba ku a wannan hayin Urdun, amma jarumawanku su haye tare da ‘yan’uwanku da shirin yaƙi domin su taimake su,

15 har lokacin da Ubangiji ya hutar da ‘yan’uwanku kamarku, su kuma su mallaki ƙasa wadda Ubangiji Allahnku yake ba su, a sa’an nan za ku koma zuwa ƙasar da take mulkinku, ku mallake ta, wato ƙasar da Musa, bawan Ubangiji, ya ba ku a hayin Urdun wajen gabas.”

16 Su kuwa suka amsa wa Joshuwa, suka ce, “Iyakar abin da ka umarce mu za mu yi, duk inda ka aike mu kuma za mu tafi.

17 Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya a kowane abu haka nan za mu yi maka biyayya, Ubangiji Allahnka dai ya kasance tare da kai kamar yadda ya kasance tare da Musa.

18 Duk wanda ya ƙi bin umarninka, bai kuwa yi biyayya da maganarka da dukan irin abin da ka umarce shi ba, za a kashe shi. Kai dai ka dāge, ka yi ƙarfin hali.”

Categories
JOSH

JOSH 2

Joshuwa Ya Aiki ‘Yan Leken Asirin Ƙasa zuwa Yariko

1 Sai Joshuwa ɗan Nun ya aiki mutum biyu ‘yan leƙen asirin ƙasa daga Shittim a asirce, ya ce musu, “Tafi, ku leƙo asirin ƙasar, musamman Yariko.” Suka tafi, suka shiga gidan wata mace, karuwa, sunanta Rahab, a nan suka sauka.

2 Sai aka faɗa wa Sarkin Yariko, aka ce, “Ga waɗansu mutane sun shigo nan da daddare domin su bincike ƙasar.”

3 Sarkin Yariko kuwa ya aika wurin Rahab ya ce, “Fito da mutanen da suka zo wurinki, waɗanda suka shiga gidanki, gama sun zo ne domin su leƙi asirin ƙasar duka.”

4 Amma macen ta riga ta ɓoye mutanen nan biyu, sai ta ce, “Gaskiya ce, mutanen sun zo wurina, amma ban san ko daga ina suka zo ba,

5 da maraice kuma, sa’ad da za a rufe ƙofar garin, sai mutanen suka fita, inda suka tafi kuwa ban sani ba, ku bi su da sauri, gama za ku ci musu.”

6 Gama ta riga ta kai su bisa rufin ɗaki, ta rufe su da ƙasheshen rama waɗanda ta shimfiɗa a bisa rufin.

7 Mutanen kuwa suka tafi don su bi bayansu a hanyar Urdun har zuwa mashigai. Da fitar masu bin sawun, sai aka rufe ƙofar garin.

8 Amma kafin ‘yan leƙen asirin ƙasar su kwanta, sai ta tafi wurinsu a bisa rufin ɗakin,

9 ta ce musu, “Na sani Ubangiji ya ba ku ƙasar, tsoronku kuma ya kama mu har zukatan mazaunan ƙasar duka sun narke saboda ku.

10 Gama mun ji yadda Ubangiji ya sa ruwan Bahar Maliya ya ƙafe a gabanku a sa’ad da kuka fito daga Masar, da irin abin da kuka yi wa sarakunan nan biyu na Amoriyawa waɗanda suke a hayin Urdun, wato Sihon da Og, waɗanda kuka hallakar da su sarai.

11 Da muka ji, sai zukatanmu suka narke, har ba sauran ƙarfin hali da ya ragu a kowane mutum saboda ku. Gama Ubangiji Allahnku shi ne Allahn da yake a Sama daga bisa, da duniya a ƙasa.

12 Yanzu fa, ku rantse mini da Ubangiji, kamar yadda na yi muku alheri, haka ku kuma za ku yi wa gidan mahaifina, ku ba ni tabbatacciyar alama.

13 Ku ceci mahaifina, da mahaifiyata, da ‘yan’uwana mata da maza, da dukan abin da yake nasu, ku ceci rayukanmu daga mutuwa.”

14 Mutanen kuwa suka ce mata, “Ranmu a bakin naki, idan ba ki tone al’amarinmu ba, za mu yi miki alheri da aminci sa’ad da Ubangiji ya ba mu ƙasar.”

15 Sa’an nan ta zurarar da su da igiya ta taga, gama gidanta yana haɗe da garun birnin ne.

16 Sai ta ce musu, “Tafi cikin tsaunuka domin kada masu bin sawun su same ku, ku ɓuya a wurin kwana uku, har masu bin sawun su komo, sa’an nan ku kama hanyarku.”

17 Mutanen suka ce mata, “Za mu kuɓuta daga rantsuwarki wadda kika rantsar da mu.

18 A lokacin da za mu shigo ƙasar, sai ki ɗaura wannan jan kirtani a tagar da kika zurarar da mu, ki kuma kawo mahaifinki, da mahaifiyarki, da ‘yan’uwanki, da dukan iyalin gidan mahaifinki a gidanki.

19 Idan waninku ya fita daga ƙofar gidanki zuwa kan titi, to, alhakin jininsa yana bisa kansa, mu kuwa sai mu kuɓuta. Amma idan aka sa wa wani hannu wanda yake cikin gida tare da ke, alhakin jininsa yana kanmu.

20 Amma idan kika tone al’amarin nan namu, to za mu kuɓuta daga rantsuwar da kika rantsar da mu.”

21 Sai ta ce, “Bisa ga maganarku ya zama haka.” Sa’an nan ta sallame su, suka tafi. Ta kuwa ɗaura jan kirtanin a tagar.

22 Sai suka tafi, suka shiga tsaunuka, suka yi zamansu a can kwana uku har masu bin sawun suka koma, gama masu bin sawun suka yi ta nema ko’ina a hanyar, amma ba su sami kowa ba.

23 Mutanen nan biyu suka sauko daga tsaunuka, suka haye zuwa wurin Joshuwa ɗan Nun, suka faɗa masa dukan abin da ya same su.

24 Suka kuma ce masa, “Hakika, Ubangiji ya ba da ƙasar duka a hannunmu, banda wannan kuma mazaunan ƙasar duka sun firgita saboda mu.”

Categories
JOSH

JOSH 3

Isra’ilawa Sun Haye Urdun

1 Joshuwa kuwa ya tashi da sassafe, da shi da dukan jama’ar Isra’ila, suka kama hanya daga Shittim zuwa Urdun, inda suka sauka kafin su haye.

2 Bayan kwana uku sai shugabannin jama’a suka bibiya zango,

3 suna umartar jama’ar suna cewa, “Sa’ad da kuka ga akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku, sai ku tashi daga inda kuke, ku bi shi,

4 domin ku san hanyar da za ku bi, gama ba ku taɓa bin hanyar ba. Sai dai tsakaninku da shi za ku bar rata misalin nisan kamu dubu biyu, kada ku kusace shi.”

5 Sai Joshuwa ya ce wa jama’a, “Ku tsarkake kanku, gama gobe Ubangiji zai aikata abin al’ajabi a tsakiyarku.”

6 Ya kuma ce wa firistocin, “Ku ɗauki akwatin alkawari ku wuce gaban jama’ar.” Sai suka ɗauki akwatin alkawari suka wuce gaban jama’a.

7 Ubangiji kuwa ya ce wa Joshuwa, “A yau ɗin nan zan fara ɗaukaka ka a gaban dukan Isra’ilawa domin su sani, kamar yadda na kasance tare da Musa, haka kuwa zan kasance tare da kai.

8 Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari cewa, ‘Sa’ad da kuka shiga gefen ruwan Urdun, sai ku tsaya cik a wurin.’ ”

9 Joshuwa kuma ya ce wa Isra’ilawa, “Ku kusato ku ji zantuttukan Ubangiji Allahnku.”

10 Joshuwa kuma ya ƙara da cewa, “Ta haka za ku sani Allah mai rai yana tsakiyarku, ba makawa kuwa zai kori Kan’aniyawa, da Hittiyawa, da Hiwiyawa, da Ferizziyawa, da Girgashiyawa, da Amoriyawa, da Yebusiyawa a gabanku.

11 Ga shi, akwatin alkawari na Ubangijin dukkan duniya yana wucewa a gabanku zuwa cikin Urdun.

12 Yanzu fa, ku ɗauki mutum goma sha biyu daga kabilanku, wato mutum ɗaya daga kowace kabila.

13 A sa’ad da firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji, Ubangijin dukkan duniya, suka tsoma tafin sawunsu cikin ruwan Urdun, ruwan Urdun zai yanke, ruwan da yake gangarowa zai tsaya tsibi guda.”

14-15 (Da kaka Urdun yakan yi cikowa makil.) Jama’a fa, suka tashi daga alfarwansu don su haye Urdun. Firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari suna gaba. Da firistocin suka tsoma ƙafafunsu cikin ruwa daga gefe,

16 sai ruwan da yake gangarowa ya tsaya, ya tattaru wuri ɗaya, ya yi soro daga nesa kusa da Adam, birnin da yake kusa da Zaretan. Ruwan kuma da yake gangarowa zuwa Tekun Araba, wato Tekun Gishiri, aka yanke shi ɗungum. Jama’a kuwa suka haye daura da Yariko.

17 A sa’ad da Isra’ilawa duka suna tafiya a kan sandararriyar ƙasa a cikin Urdun, firistoci kuwa waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari na Ubangiji suka yi ta tsayawa a bisa sandararriyar ƙasa a tsakiyar Urdun har al’ummar ta gama hayewa.