Categories
L. MAH

L. MAH 20

Yaƙi da Mutanen Biliyaminu

1 Dukan jama’ar Isra’ila fa suka fito tun daga Dan a arewa har zuwa Biyer-sheba a kudu da kuma Gileyad daga gabas. Suka hallara gaba ɗaya a gaban Ubangiji a Mizfa.

2 Dukan shugabannin kabilar Isra’ila suna cikin wannan taron jama’ar Allah. Sojojin ƙafa yawansu ya kai dubu ɗari huɗu (400,000).

3 Mutanen Biliyaminu kuwa sun ji labari sauran Isra’ilawa sun haura zuwa Mizfa. Isra’ilawa suka tambayi Balawen suka ce, “Ka faɗa mana yadda wannan mugun abu ya auku.”

4 Balawe, mai ƙwarƙwarar da ka kashe, ya amsa ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata muna biyo Gibeya ta Biliyaminu mu kwana.

5 Sai mutanen Gibeya suka kewaye gidan da nake da dare, suna neman kashe ni, da ba su same ni ba, sai suka yi wa ƙwarƙwarata faɗe har ya kai ta ga mutuwa.

6 Ni kuwa na ɗauki gawarta na yanyanka gunduwa gunduwa na aika cikin ƙasar gādon Isra’ila duka, gama waɗannan mutane sun aikata abin ƙyama da abin kunya ga dukan Isra’ila.

7 Dukanku nan Isra’ilawa ne, me za mu yi a kan wannan al’amari?”

8 Dukan jama’a kuwa suka tashi gaba ɗaya, suna cewa, “Daga cikinmu ba wanda zai koma alfarwarsa ko kuwa gidansa.

9 Wannan shi ne abin da za mu yi wa Gibeya, mu zaɓi waɗansunmu su fāɗa mata da yaƙi.

10 Kashi ɗaya daga goma na Isra’ilawa su ba da abinci ga sojoji. Sauran jama’a kuwa su je su hukunta Gibeya saboda muguntar da ta aikata cikin Isra’ila.”

11 Saboda haka dukan mutanen Isra’ila suka taru niyya ɗaya domin su fāɗa wa garin da yaƙi.

12 Kabilar Isra’ila kuwa suka aiki manzanni ga kabilar Biliyaminu suka ce, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?

13 Yanzu sai ku ba da mutanen nan ‘yan iska da take cikin Gibeya don mu kashe su, mu kawar da mugunta daga cikin Isra’ila.” Amma mutanen Biliyaminu ba su kula da maganar ‘yan’uwansu, Isra’ilawa ba.

14 Mutanen Biliyaminu kuwa suka fita daga Gibeya gaba ɗaya domin su yi yaƙi da jama’ar Isra’ila.

15 A ran nan mutanen Biliyaminu suka tattaru daga garuruwansu, mutum dubu ashirin da shida (26,000). Banda waɗannan, sai da mazaunan Gibeya suka tara zaɓaɓɓun mutane ɗari bakwai.

16 Daga cikin waɗannan duka akwai zaɓaɓɓun mutane bakwai, bahagwai. Kowannensu yana iya ya baraci gashi guda da majajjawa ba kuskure.

17 Isra’ilawa kuwa banda kabilar Biliyaminu, suka tara mayaƙa dubu ɗari huɗu (400,000) horarru.

Yaƙi da Mutanen Biliyaminu

18 Isra’ilawa suka tashi suka tafi Betel. A can suka yi tambaya ga Allah suka ce, “Wace kabila ce daga cikinmu za ta fara faɗa wa kabilar Biliyaminu?”

Ubangiji ya ce, “Kabilar Yahuza ce za ta fara.”

19 Sa’an nan Isra’ilawa suka tashi da safe suka kafa sansani kusa da Gibeya.

20 Suka kuwa fita su yi yaƙi da mutanen Biliyaminu, suka jā dāgar yaƙi suna fuskantar Gibeya.

21 Mutanen Biliyaminu kuwa suka fito daga birnin suka hallakar da mutum dubu ashirin da biyu (22,000), daga cikin mutanen Isra’ila a ranar.

22-23 Mutanen Isra’ila suka tafi inda ake sujada suka yi makoki a gaban Ubangiji har zuwa dare. Suka tambaye shi suka ce, “Mu sāke zuwa domin mu yi yaƙi da ‘yan’uwanmu mutanen Biliyaminu?”

Ubangiji ya ce musu, “I, ku tafi.”

Saboda haka sai sojojin Isra’ilawa suka ƙarfafa, suka sāke jān dāga a inda suka jā ta dā.

24 Sai mutanen Isra’ila suka tafi su kara da mutanen Biliyaminu a rana ta biyu.

25 Mutanen Biliyaminu kuwa suka fito daga birnin suka hallakar da mutum dubu goma sha takwas (18,000) daga cikin Isra’ilawa. Dukan waɗannan da aka hallaka horarru ne.

26 Dukan rundunan Isra’ilawa suka haura zuwa Betel, suka yi makoki, suka zauna a gaban Ubangiji suka yi azumi har maraice. Sa’an nan suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da na salama.

27-28 Suka sāke yin tambaya ga Ubangiji suka ce, “Mu sāke tafiya mu yi yaƙi da ‘yan’uwanmu, mutanen Biliyaminu, ko kuwa mu bari?”

Ubangiji kuwa ya ce musu, “Ku je, gama gobe zan ba da su gare ku.” A lokacin nan akwatin alkawari na Ubangiji yana nan. Finehas ɗan Ele’azara, ɗan Haruna, shi ne mai aiki a gabansa.

29 Isra’ilawa kuwa suka sa ‘yan kwanto kewaye da Gibeya.

30 Sa’an nan suka tafi su kara da mutanen Biliyaminu a rana ta uku. Suka jā dāgar yaƙi gaba da Gibeya kamar dā.

31 Mutanen Biliyaminu kuma suka fito, suka tasar musu. Aka jawo su nesa da birnin. Suka fara kashe Isra’ilawa kamar yadda suka yi a dā, suka kashe wajen mutum talatin a kan karauka wadda ta nufi Betel da wadda ta nufi Gibeya, da filaye.

32 Sai mutanen Biliyaminu suka ce, “Mun fatattake su kamar dā.”

Amma Isra’ilawa suka ce, “Mu gudu don mu jawo su nesa da birnin zuwa karauka.”

33 Isra’ilawa duka suka tashi daga wurin da suke, suka jā dāga a Ba’altamar. Mutanensu da suke kwanto a yammacin Gibeya suka fito.

34 Horarrun sojojin Isra’ila, su dubu goma (10,000), suka faɗa wa Gibeya. Yaƙi kuwa ya yi zafi, amma mutanen Biliyaminu ba su san masifa tana gab da su ba.

35 Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Biliyaminu a gaban Isra’ilawa. Isra’ilawa kuwa suka hallaka mutanen Biliyaminu dubu ashirin da biyar da ɗari ɗaya (25,100) a wannan rana, waɗannan duka kuwa mayaƙa ne.

36 Mutanen Biliyaminu kuwa suka gane an ci su da yaƙi.

Mutanen Isra’ila kuwa suka yi ta ja da baya daga mutanen Biliyaminu domin sun dogara ga mutanensu da suka yi wa Gibeya kwanto.

37 Sai ‘yan kwanto suka gaggauta suka faɗa wa Gibeya, suka kutsa suka kashe dukan waɗanda suke a birnin.

38 Alamar da mayaƙan Isra’ila da na ‘yan kwantonsu suka daidaita a tsakaninsu, ita ce murtukewar hayaƙi a cikin birnin.

39 Idan mutanen Isra’ila sun hangi hayaƙin, sai su juya su fāɗa wa mutanen Biliyaminu da yaƙi. Kafin alamar hayaƙin sai mutanen Biliyaminu suka fara kashe wa Isra’ilawa wajen mutum talatin. Suka ce, “Ai, suna shan ɗibga a hannunmu kamar yadda suka sha da fari.”

40 Amma sa’ad da alamar hayaƙin ta fara murtukewa a cikin birnin, sai mutanen Biliyaminu suka juya, suka duba, suka ga hayaƙi ya murtuke cikin birnin, ya yi sama.

41 Da mutanen Isra’ila suka juyo kansu, sai mutanen Biliyaminu suka tsorata, gama sun ga masifa ta auko musu.

42 Don haka suka juya suka kama gudu suka nufi hamada, amma ba su tsira ba. Aka datse su tsakanin ‘yan kwanto da sauran sojojin Isra’ilawa.

43 Suka yi wa mutanen Biliyaminu tarko, suka runtume su ba tsayawa tun daga Menuha har zuwa daura da Gibeya daga gabas.

44 Aka kashe jarumawan mutanen Biliyaminu mutum dubu goma sha takwas (18,000).

45 Sauran suka juya, suka gudu, suka nufi wajen hamada zuwa Dutsen Rimmon. A kan hanyoyi, aka kashe musu mutum dubu biyar. Aka kuma runtumi sauran da suka ragu har zuwa Gidom inda suka kashe mutum dubu biyu.

46 Mutanen Biliyaminu da aka kashe a ran nan dubu ashirin da biyar (25,000) ne. Dukansu kuwa jarumawa ne.

47 Amma mutum ɗari shida suka juya, suka gudu suka nufi hamada zuwa Dutsen Rimmon inda suka zauna har wata hu:du.

48 Mutanen Isra’ila kuma suka komo, suka fāɗa wa sauran mutanen Biliyaminu. Suka karkashe su, mutane, da dabbobi, da dukan abin da suka iske. Suka ƙone garuruwan wannan yankin ƙasa.

Categories
L. MAH

L. MAH 21

Mata domin Mutanen Biliyaminu

1 Mutanen Isra’ila kuwa suka yi wa Ubangiji ƙaƙƙarfan alkawari a Mizfa cewa, “Ba wani daga cikinmu da zai ba da ‘yarsa aure ga mutumin Biliyaminu.”

2 Sai mutanen Isra’ila suka zo Betel, suka zauna a nan a gaban Allah har maraice. Suka yi makoki mai zafi.

3 Suka ce, “Ya Ubangiji Allah na Isra’ila, me ya sa wannan abu ya faru a cikin Isra’ila, har da za a rasa kabila guda ta Isra’ila?”

4 Kashegari mutanen suka tashi da safe, suka gina bagade a can. Suka miƙa hadayun ƙonawa da na salama.

5 Suka kuma ce, “Daga cikin kabilar Isra’ila, wace ce ba ta halarci wannan taro na gaban Ubangiji ba?” Gama sun riga sun yi ƙaƙƙarfan alkawari cewa, “Duk wanda bai hauro zuwa wurin Ubangiji a Mizfa ba, za a kashe shi.”

6 Jama’ar Isra’ila kuwa suka yi juyayin ‘yan’uwansu, mutanen Biliyaminu, suka ce, “Yau an hallaka kabila guda daga cikin Isra’ila.

7 Ƙaƙa za mu yi don mutanen da suka ragu su sami mata. Ga shi, mum riga mu rantse da Ubangiji ba za mu ba su ‘ya’yanmu mata su aura ba?”

8 Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce daga cikin kabilar Isra’ila ba ta hauro zuwa wurin Ubangiji a Mizfa ba?.. Sai suka ga, ashe, ba wani daga Yabesh-gileyad da ya halarci taron.

9 Gama sa’ad da aka tattara mutanen, aka ga ba wani daga cikin mazaunan Yabesh-gileyad a wurin.

10 Taron jama’a kuma suka aiki jarumawansu mutum dubu goma sha biyu (12,000) zuwa Yabesh-gileyad. Suka umarce su cewa, “Ku je ku karkashe mazaunan Yabesh duka har da mata da yara.

11 Abin da za ku yi ke nan, ku je ku kashe dukan maza, da kowace mace wadda ba budurwa ba ce.”

12 Suka sami budurwai ɗari huɗu daga mutanen Yabesh-gileyad, sai suka kawo su zango a Shilo, wadda take a ƙasar Kan’ana.

13 Sa’an nan taron jama’a suka aika wa mutanen Biliyaminu da suke a Dutsen Rimmon, cewa, yaƙi ya ƙare, sai salama.

14 Mutanen Biliyaminu kuwa suka komo, aka ba su budurwan nan da aka bar su da rai aka kawo su Yabesh-gileyad, amma budurwan ba su ishe su ba.

15 Sai mutanen suka yi juyayin mutanen Biliyaminu domin Ubangiji ya naƙasa kabila daga kabilar Isra’ila.

16 Saboda haka dattawan taron jama’a suka ce, “Ƙaƙa za mu yi da waɗanda suka ragu da ba su sami mata ba, da yake an hallaka matan kabilar Biliyaminu?”

17 Sai suka ce, “Tilas, waɗanda suka ragu daga mutanen Biliyaminu su sami gādo domin kada a shafe kabila daga cikin Isra’ila,

18 amma fa ba za mu iya aurar musu da ‘ya’yanmu mata ba.” Sun faɗi haka ne kuwa, domin sun riga sun rantse cewa, “Duk wanda ya aurar da ‘yarsa ga mutumin Biliyaminu la’ananne ne.”

19 Suka kuma ce, “Ga shi, idin Ubangiji na shekara shekara a Shilo ya kusa.” (Shilo tana arewacin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.)

20 Suka umarci mutanen Biliyaminu suka ce, “Ku tafi ku yi kwanto a gonakin inabi,

21 ku lura, idan ‘yan matan Shilo sun fito domin su yi rawa, sai ku fito daga cikin gonakin inabi, kowa ya kama daga cikin ‘yan matan da ƙarfi, ya sami mata ke nan, ya tafi da ita a ƙasar Biliyaminu.

22 Sa’ad da iyayensu ko ‘yan’uwansu sun kawo ƙara gare mu, za mu ce musu, ‘Ku bar mana su, muna roƙonku, domin ba daga wurin yaƙi muka kamo su domin su zama matanmu ba. Amma tun da ba ku ba mu su ba, ba ku da laifin ta da alkawari.’ ”

23 Haka kuwa mutanen Biliyaminu suka yi. Suka kama budurwai gwargwadon yawansu daga cikin masu rawa. Sa’an nan suka koma zuwa yaƙin ƙasarsu ta gādo. Suka sāke gina garuruwansu, suka zauna.

24 Haka nan kuma sauran mutanen Isra’ila suka tashi daga can. Kowa ya tafi wurin kabilarsa, da iyalinsa, da abin da ya mallaka.

25 A lokacin ba sarki a Isra’ila, sai kowa ya yi ta yin abin da ya ga dama.

Categories
RUT

RUT 1

Elimelek da Iyalinsa a Mowab

1 A zamanin da mahukunta suke mulkin Isra’ila, aka yi yunwa a ƙasar. Sai wani mutumin Baitalami a Yahudiya ya yi ƙaura zuwa ƙasar Mowab, shi da matarsa, da ‘ya’yansa maza biyu.

2 Sunan mutumin, Elimelek, matarsa kuwa Na’omi, ‘ya’yanta maza kuma Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Baitalami ta Yahudiya. Suka tafi Mowab suka zauna a can.

3 Elimelek, mijin Na’omi, ya rasu, aka bar Na’omi da ‘ya’yansu maza biyu.

4 Sai suka auri ‘yan matan Mowab, Orfa da Rut. Bayan da suka yi wajen shekara goma a can,

5 sai kuma Malon da Kiliyon suka rasu, Na’omi kuwa ta rasa mijinta da kuma ‘ya’yanta maza biyu.

Na’omi da Rut sun Komo Baitalami

6 Daga can Mowab, Na’omi ta ji cewa, Ubangiji ya taimaki mutanensa, ya ba su abinci, sai ta tashi daga ƙasar Mowab tare da surukanta.

7 Suka kama hanya zuwa ƙasar Yahudiya.

8 Amma a hanya, sai Na’omi ta ce wa surukanta, “Bari ko waccenku ta koma gidan iyayenta. Ubangiji ya yi muku alheri kamar yadda kuka yi mini alheri, ni da marigayan.

9 Ya sa kuma ko waccenku ta yi aure, ta sami hutawa a gidan miji.” Sa’an nan ta yi bankwana da su ta sumbace su.

Sai suka fashe da kuka,

10 suka ce mata, “A’a, mā tafi tare da ke wurin mutanenki.”

11 Amma Na’omi ta ce musu, “Ku koma, ‘ya’yana, don me za ku tafi tare da ni? Ina da sauran ‘ya’ya maza a cikina ne da za su zama mazajenku?

12 Sai ku koma, ‘ya’yana, gama na tsufa da yawa, ba kuma zan sami miji ba. Ko da a ce ina fata in yi aure, a ce ma zan yi aure a daren nan, in haifi ‘ya’ya maza,

13 za ku yi ta jira har su yi girma? Ai, ba zai yiwu ba, ‘ya’yana. Ina baƙin ciki ƙwarai saboda abin da ya same ku, da yadda Ubangiji ya yi gāba da ni.”

14 Suka sāke fashewa da kuka. Sai Orfa ta yi wa surukarta, sumba, ta yi bankwana da ita, amma Rut ta manne mata.

15 Na’omi ta ce wa Rut, “Kin ga, ‘yar’uwarki ta koma wurin mutanenta da wurin gumakanta, sai ki koma, ki bi ‘yar’uwarki.”

16 Amma Rut ta ce, “Kada ki yi ta roƙona in rabu da ke, ko in bar binki, gama inda za ki tafi, ni ma can zan tafi, inda kuma za ki zauna, ni ma can zan zauna. Mutanenki za su zama mutanena, Allahnki kuma zai zama Allahna.

17 Inda za ki rasu, ni ma can zan rasu, a binne ni. Idan na bar wani abu ya raba ni da ke, in dai ba mutuwa ba, to, Ubangiji ya yi mini hukunci mai zafi!”

18 Da Na’omi ta ga Rut ta ƙudura ta tafi tare da ita, sai ta ƙyale ta.

19 Su biyu kuwa suka kama hanya har suka isa Baitalami. Da suka isa Baitalami, sai dukan garin ya ruɗe saboda su. Mata suka ce, “Na’omi ce wannan?”

20 Ita kuwa ta ce musu, “Kada ku kira ni Na’omi, wato mai farin ciki, sai dai Mara, wato mai baƙin ciki, gama Mai Iko Dukka ya wahalshe ni ƙwarai.

21 Na tafi a wadace, ga shi, Ubangiji ya komo da ni hannu wofi. Don me kuke kirana mai farin ciki da yake Ubangiji Mai Iko Dukka ya wahalshe ni, ya kuma aukar mini da masifa?”

22 Haka Na’omi ta koma daga ƙasar Mowab tare da surukarta Rut, mutuniyar Mowab. Suka isa Baitalami a farkon kakar sha’ir.

Categories
RUT

RUT 2

Rut a Gonar Bo’aza

1 Na’omi tana da wani dangin mijinta, Elimelek, sunansa Bo’aza, shi kuwa attajiri ne.

2 Sai Rut, mutuniyar Mowab, ta ce wa Na’omi, “Bari in tafi, in yi kalan hatsi a gonar wanda ya yarda in yi.”

Na’omi ta ce mata, “Ki tafi, ‘yata.”

3 Rut ta tafi wata gona, tana bin bayan masu girbi, tana kala. Ta yi sa’a kuwa ta fāɗa a gonar Bo’aza, dangin Elimelek.

4 Sai ga Bo’aza ya zo daga Baitalami, ya ce wa masu girbi, “Salamu alaikun.”

Suka amsa, “Alaika salamu.”

5 Sa’an nan Bo’aza ya tambayi baransa da yake shugaban masu girbin, ya ce, “’Yar wace ce wannan?”

6 Baran ya ce, “Ita ‘yar Mowab ce wadda ta zo tare da Na’omi daga ƙasar Mowab.

7 Ita ce ta ce mana, ‘In kun yarda, ku bar ni in bi bayan masu girbin, ina kala.’ Haka ta yi ta kala tun da sassafe har yanzu ba hutu, sai dai ‘yar shaƙatawar da ta yi kaɗan.”

8 Sa’an nan sai Bo’aza ya ce wa Rut, “Kin ji, ‘yata, kada ki bar wannan gona ki tafi wata gona domin kala, amma ki riƙa bin ‘yan matan gidana.

9 Ki kula da gonar da suke girbi, ki bi su. Ga shi, na riga na umarci barorina kada su dame ki. Sa’ad da kika ji ƙishirwa, sai ki tafi ki sha ruwa a tuluna, wanda barorin suka ɗebo.”

10 Sai Rut ta rusuna har ƙasa, ta ce masa, “Me ya sa na sami tagomashi a gare ka, har da za ka kula da ni, ni da nake baƙuwa?”

11 Amma Bo’aza ya ce mata, “An faɗa mini dukan abin da kika yi wa surukarki tun lokacin da mijinki ya rasu, da yadda kika bar iyayenki da ƙasarku, kika zo wurin mutanen da ba ki taɓa saninsu ba a dā.

12 Ubangiji Allah na Isra’ila, wanda kika zo neman mafaka gare shi, ya sāka miki da cikakken lada saboda abin da kika yi.”

13 Rut ta ce, “Shugaba, kā yi mini alheri ƙwarai, gama kā ta’azantar da ni, kā yi wa baiwarka maganar alheri, ko da yake ni ba ɗaya daga cikin barorinka ba ce.”

14 Da lokacin cin abinci ya yi, sai Bo’aza ya kira Rut, ya ce, “Zo nan ki ci abinci, ki riƙa tsoma lomarki a ruwan inabin da aka surka.” Sai ta zo, ta zauna kusa da masu girbin. Shi kuwa ya ba ta tumun hatsi. Ta ci, ta ƙoshi har ta bar saura.

15 Sa’ad da ta tashi, za ta yi kala, sai Bo’aza ya umarci barorinsa, ya ce, “Ku bar ta, ta yi kala a tsakanin tarin dammunan, kada ku hana ta.

16 Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.”

17 Ta yi ta kala a gonar har yamma. Ta sussuka abin da ta kalata, ta sami tsaba wajen garwa biyu.

18 Ta ɗauka, ta koma gari, ta nuna wa surukarta abin da ta kalato. Ta kuma kawo mata sauran abincin da ta ci ta ƙoshi har ta rage.

19 Surukarta kuma ta ce mata, “A ina kika yi kala yau? A gonar wa kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga wannan mutum wanda ya kula da ke.”

Sai ta faɗa mata sunan mutumin da ta yi kala a gonarsa, ta ce, “Sunan mutumin da na yi kala a gonarsa yau, Bo’aza.”

20 Na’omi ta ce wa Rut, “Ubangiji wanda bai daina nuna alheri ga masu rai da marigayan ba, ya sa masa albarka.” Ta ƙara da cewa, “Ai, mutumin, shi danginmu ne na kusa.”

21 Rut kuma, mutuniyar Mowab, ta ce, “Banda wannan ma, ya ce mini, ‘Ki riƙa bin barorina, har lokacin da suka gama mini girbin.’ ”

22 Sa’an nan Na’omi ta ce wa Rut, “Madalla, ‘yata, ki riƙa bin ‘yan matan gidansa, kada ki tafi wata gona dabam.”

23 Sai ta riƙa bin ‘yan matan gidan Bo’aza. Ta yi ta kala har aka gama girbin sha’ir da na alkama, tana zaune tare da surukarta, wato Na’omi.

Categories
RUT

RUT 3

Bo’aza da Rut a Masussuka

1 Wata rana, Na’omi ta ce wa Rut, “’Yata, ya kamata in nemar miki miji don ki sami gida inda za ki huta, ki ji daɗi.

2 Bo’aza wanda kika yi aiki da barorinsa danginmu ne. Ga shi, zai tafi sussukar sha’ir a masussuka da maraice.

3 Sai ki yi wanka, ki shafa man ƙanshi, ki yafa tufafinki na ado, ki tafi masussukar, amma kada ki bari ya san zuwanki, sai bayan da ya riga ya ci ya sha.

4 Sa’ad da ya kwanta, sai ki lura da inda ya kwanta, sa’an nan ki tafi, ki buɗe mayafinsa a wajen ƙafafunsa, ki kwanta a ciki. Zai kuwa faɗa miki abin da za ki yi.”

5 Rut ta amsa, “Zan yi dukan abin da kika faɗa.”

6 Rut kuwa ta gangara zuwa masussukar, ta yi yadda surukarta ta faɗa mata.

7 Sa’ad da Bo’aza ya ci ya sha yana cikin jin daɗi, sai ya je ya kwanta kusa da tsibin tsabar sha’ir. Sa’an nan Rut ta tafi a hankali, ta buɗe mayafin da ya rufa da shi wajen ƙafafunsa, ta kwanta a ciki.

8 Da tsakar dare, sai mutumin ya farka a firgice, ya juya, sai ga mace kwance a wajen ƙafafunsa.

9 Ya ce, “Wace ce?”

Sai ta amsa, “Ni ce Rut, baranyarka, sai ka rufe ni da mayafinka, gama kai dangi ne na kusa.”

10 Sa’an nan ya ce, “Ubangiji ya sa miki albarka ‘yata, yanzu kin nuna alheri mafi girma fiye da na dā da yake ba ki nemi saurayi, matalauci ko attajiri ba.

11 Yanzu dai, ‘yata, kada ki damu, zan yi miki dukan abin da kika roƙa, gama dukan mutanen garin sun sani ke macen kirki ce.

12 Gaskiya ce, ni dangi na kusa ne, amma akwai wanda yake dangi na kusa fiye da ni.

13 Ki dakata nan sai gobe, da safe za mu gani, idan shi zai cika wajibin dangi na kusa a gare ki. Idan ya cika, to, da kyau, amma idan bai cika ba, na rantse da Allah mai rai, zan cika wajibin dangi na kusa a gare ki. Ki kwanta sai da safe.”

14 Sai ta kwanta a wajen ƙafafunsa har safiya. Sa’an nan ta tashi tun da jijjifi kafin a iya gane fuskar mutum, gama ba ya so a sani mace ta zo masussukar.

15 Bo’aza ya ce mata, “Kawo mayafinki, ki shimfiɗa shi.” Sai ta shimfiɗa mayafin, ya zuba mata sha’ir ya kusa garwa huɗu ya aza mata a kā. Sa’an nan ta koma gari.

16 Lokacin da ta zo wurin surukarta, sai surukarta ta ce mata, “’Yata, ina labari?”

Sai ta faɗa mata dukan abin da mutumin ya faɗa mata.

17 Ta kuma ce, “Ga sha’ir da ya ba ni, gama ya ce, ‘Ba za ki koma wurin surukarki hannu wofi ba.’ ”

18 Sai surukarta ta ce, “Ki jira dai, ‘yata, har ki ga yadda al’amarin zai zama, gama mutumin ba zai huta ba, sai ya daidaita al’amarin a yau.”

Categories
RUT

RUT 4

Bo’aza ya Auri Rut

1 Bo’aza fa ya tafi, ya zauna a dandalin ƙofar gari. Sai ga wani daga cikin waɗanda hakkinsu ne su ɗauki Rut, shi ne kuwa wanda Bo’aza ya ambata, ya iso. Bo’aza kuwa ya ce masa, “Ratso nan, wāne, ka zauna.” Sai ya ratsa, ya zauna.

2 Bo’aza ya kuma kirawo goma daga cikin dattawan gari, ya ce musu, “Ku zauna nan.” Suka kuwa zauna.

3 Sa’an nan ya ce wa dangin nan nasa na kusa, “Ga Na’omi wadda ta komo daga ƙasar Mowab, tana so ta sayar da gonar Elimelek danginmu.

4 Don haka na ga ya kamata in sanar da kai cewa, ka saye ta a gaban waɗanda suke zaune a nan, da a gaban dattawan jama’a. Idan za ka fanshi gonar sai ka fanshe ta, idan kuwa ba za ka fansa ba, ka faɗa mini don in sani, gama daga kai sai ni muke da izinin fansar gonar.”

Sai mutumin ya ce, “Zan fanshe ta.”

5 Sa’an nan Bo’aza ya ce, “A ranar da ka sayi gonar daga hannun Na’omi, sai kuma ka ɗauki Rut, mutuniyar Mowab, matar marigayin, domin ka ta da zuriyar da za ta gaji marigayin.”

6 Sai dangin nan mafi kusa ya ce, “Ba zan iya ɗaukar Rut ba, domin kada in ɓata nawa gādo. Na bar maka ka ɗauke ta gama ni ba zan iya ba.”

7 Wannan ita ce al’adar Isra’ilawa a dā a kan sha’anin fansa ko musaya, don tabbatar da al’amarin. Sai mai sayarwar ya tuɓe takalminsa ya ba mai sayen. Wannan ita ce hanyar tabbatarwa a cikin Isra’ila.

8 Saboda haka a sa’ad da dangin nan mafi kusa ya ce wa Bo’aza, “Sai ka saye ta,” sai ya tuɓe takalminsa ya ba Bo’aza.

9 Sa’an nan Bo’aza ya ce wa dattawan da dukan jama’ar da suke wurin, “Yau ku ne shaidu, cewa, na sayi dukan abin da yake na Elimelek, da na Kiliyon, da na Malon daga hannun Na’omi.

10 Game da wannan kuma Rut, mutuniyar Mowab, matar marigayi Malon, ta zama matata domin in wanzar da sunan marigayin cikin gādonsa, don kada sunansa ya mutu daga na ‘yan’uwansa, da kuma a garinsu. Ku ne fa shaidu a yau.”

11 Dukan jama’a suka ce, “Mu ne shaidu, Ubangiji yă sa matar da za ta zo gidanka ta zama kamar Rahila da Lai’atu waɗanda suka gina gidan Isra’ila. Allah ya arzuta ka cikin Efrata, yă sa ka yi suna a cikin Baitalami,

12 gidanku kuma ya zama kamar gidan Feresa, wanda Tamar ta haifa wa Yahuza, saboda ‘ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace.”

13 Bo’aza kuwa ya auri Rut, ta zama matarsa. Ya kuma shiga wurinta, Ubangiji kuwa ya sa ta yi ciki, ta haifa masa ɗa.

14 Sai mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, da bai bar ki bā dangi na kusa ba, Allah ya sa ɗan ya yi suna a cikin Isra’ila.

15 Ya zama mai sanyaya miki rai, mai goyon tsufanki, gama surukarki wadda take ƙaunarki, wadda ta fiye miki ‘ya’ya maza bakwai, ita ta haife shi.”

16 Sa’an nan Na’omi ta ɗauki yaron ta rungume shi a ƙirjinta, ta zama mai renonsa.

17 Mata, maƙwabta kuwa suka ce, “An haifa wa Na’omi ɗa!” Suka raɗa masa suna Obida, shi ne mahaifin Yesse, uban Dawuda.

Asalin Zuriyar Dawuda

18-22 Wannan shi ne asalin zuriyar Dawuda. Aka fara daga Feresa zuwa Dawuda. Feresa ne mahaifin Hesruna, Hesruna kuma ya haifi Arama, Arama ya haifi Amminadab, Amminadab kuma ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon, Salmon kuma ya haifi Bo’aza, Bo’aza ya haifi Obida, Obida kuma ya haifi Yesse, sa’an nan Yesse ya haifi Dawuda.

Categories
1 SAM

1 SAM 1

Haihuwar Sama’ila

1 Akwai wani mutum daga kabilar Ifraimu sunansa Elkana, yana zaune a Rama, a ƙasar tudu ta Ifraimu. Shi ɗan Yeroham ne, jika ga Eliyab, na iyalin Nahat, daga zuriyar Zuf.

2 Yana da mata biyu, sunayensu Hannatu da Feninna. Feninna tana da ‘ya’ya, amma Hannatu ba ta haihuwa.

3 A kowace shekara Elkana yakan haura daga garinsu zuwa Shilo domin ya miƙa wa Ubangiji Mai Runduna hadaya, ya kuma yi masa sujada. ‘Ya’yan Eli, maza biyu, Hofni da Finehas, su ne firistoci na Ubangiji a can.

4 Duk lokacin da Elkana ya miƙa hadayarsa, sai ya ba Feninna da ‘ya’yanta mata da maza nasu rabo.

5 Amma Hannatu, sai ya ba ta babban rabo guda ɗaya, gama yana ƙaunarta, amma Ubangiji ya kulle mahaifarta.

6 Kishiyarta takan tsokane ta don ta ji haushi, gama Ubangiji ya hana mata haihuwa.

7 Haka aka yi ta yi kowace shekara, duk lokacin da suka tafi domin yin sujada, sai Feninna ta tsokane ta. Don haka Hannatu ta yi ta kuka, ta ƙi cin abinci.

8 Elkana mijinta kuwa, ya ce mata, “Hannatu, me ya sa kike kuka? Me ya sa kike ƙin cin abinci? Me ya sa zuciyarki ta ɓaci? Ni ban fi ‘ya’ya maza goma a gare ki ba?”

Hannatu da Eli

9 Wata rana a Shilo bayan da sun gama cin abinci, sai Hannatu ta tashi. Eli, firist, kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar masujadar Ubangiji.

10 Hannatu tana fama da baƙin ciki ƙwarai, sai ta yi addu’a, tana kuka da ƙarfi ga Ubangiji.

11 Ta yi wa’adi, ta ce, “Ya Ubangiji Mai Runduna, idan lalle ka dube ni, ni baiwarka, ka tuna da ni, ba ka manta da ni baiwarka ba, amma ka ba ni ɗa, ni ma sai in ba da shi ga Ubangiji dukan kwanakinsa, aska kuwa ba za ta taɓa kansa ba.”

12 Eli kuwa ya lura da bakin Hannatu sa’ad da take yin addu’a.

13 Gama ta yi addu’ar a zuci, ba a jin muryarta, sai dai leɓun motsi. Don haka Eli ya zaci tana maye ne,

14 ya kuwa ce mata, “Sai yaushe za ki daina maye? Ki daina shan ruwan inabi.”

15 Hannatu kuwa ta amsa ta ce, “Ba haka ba, ya shugabana, ni mace ce da take baƙin ciki ƙwarai. Ni ban sha ruwan inabi, ko wani abu mai sa maye ba, amma ina faɗa wa Ubangiji dukan abin da yake a zuciyata.

16 Kada ka zaci ni ‘yar iska ce. Ni dai ina faɗar damuwata da tsokanar da ake yi mini ne.”

17 Sai Eli ya ce mata, “Ki sauka lafiya, Allah na Isra’ila ya amsa miki roƙonki.”

18 Ita kuma ta amsa, ta ce, “Bari baiwarka ta sami tagomashi a gare ka.” Sa’an nan ta tafi, ta ci abinci. Ba ta ƙara ɓata ranta ba.

Haihuwar Sama’ila da Miƙawarsa

19 Elkana da iyalinsa suka tashi tun da sassafe suka yi wa Ubangiji sujada, sa’an nan suka koma gidansu a Rama. Elkana fa ya kwana da matarsa, Hannatu. Ubangiji kuwa ya tuna da ita.

20 Ta yi juna biyu, ta haifa ɗa, ta raɗa masa suna Sama’ila, wato “Na roƙo shi daga wurin Ubangiji.”

21 Elkana da iyalinsa duka suka tafi Shilo domin su miƙa wa Ubangiji hadaya ta shekara shekara, ya kuma cika wa’adinsa.

22 Amma Hannatu ba ta tafi ba, sai ta ce wa mijinta, “Da zarar an yaye yaron, zan kai shi domin ya zauna a gidan Ubangiji muddin ransa.”

23 Elkana ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi kyau, ki jira har ki yaye shi, Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Hannatu ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta.

24 Sa’ad da ta yaye yaron, sai ta ɗauke shi, ta kuma ɗauki bijimi bana uku, da mudun gari, da salkar ruwan inabi, ta kai shi ɗakin Ubangiji a Shilo, yaron kuwa yana ɗan ƙarami.

25 Sai suka yanka bijimin, suka kuma kai yaron wurin Eli.

26 Sa’an nan Hannatu ta ce, “Gafara dai, ba ka tuna da ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana roƙon Ubangiji.

27 Na roƙi Ubangiji wannan yaro, Ubangiji kuwa ya biya mini bukatata da na roƙa a gare shi.

28 Saboda haka nake miƙa shi ga Ubangiji muddin ransa. Ya zama na Ubangiji.”

A can ya yi wa Ubangiji sujada.

Categories
1 SAM

1 SAM 2

Waƙar Hannatu

1 Hannatu kuwa ta yi addu’a ta ce,

“Ubangiji ya cika zuciyata da murna.

Ina farin ciki da abin da ya yi.

Ina yi wa maƙiyana dariya,

Ina matuƙar murna domin Allah ya taimake ni.

2 “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji,

Babu wani mai kama da shi,

Ba mai kiyaye mu kamar Allahnmu.

3 Kada ku ƙara yin magana ta girmankai,

Ku daina maganganunku na fariya,

Gama Ubangiji Allah shi ne masani,

Yana kuma auna dukkan aikin da mutum ya yi.

4 An kakkarya bakunan ƙarfafan sojoji,

Amma rarrauna ya zama mai ƙarfi.

5 Ƙosassun mutane suna ƙodago saboda abinci,

Masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa.

Bakarariya ta haifi ‘ya’ya bakwai,

Wadda ta haifi ‘ya’ya da yawa kuwa

ta rasa su duka.

6 Ubangiji ne yake kashewa, ya kuma rayar,

Yana kai mutane kabari,

Ya kuma tā da su.

7 Yakan sa waɗansu mutane su zama

matalauta,

Waɗansu kuwa attajirai.

Yakan ƙasƙantar da waɗansu,

Ya kuma ɗaukaka waɗansu.

8 Yakan tā da matalauci daga cikin ƙura,

Yakan ɗaga mai bukata daga zaman baƙin ciki.

Ya sa su zama abokan ‘ya’yan sarki,

Ya ɗora su a wurare masu maƙami.

Harsashin ginin duniya na Ubangiji ne,

A kansu ya kafa duniya.

9 “Zai kiyaye rayukan amintattun

mutanensa,

Amma mugayen mutane za su lalace cikin duhu,

Ba ƙarfin mutum yake sa ya yi nasara ba.

10 Za a hallakar da maƙiyan Ubangiji,

Zai yi musu tsawa daga Sama.

Ubangiji zai hukunta dukan duniya,

Zai ba sarkinsa iko,

Zai sa zaɓaɓɓen sarkinsa ya zama

mai nasara.”

11 Sa’an nan Elkana ya koma gidansa a Rama, amma yaron ya zauna a Shilo, yana aikin Ubangiji a hannun Eli, firist.

‘Ya’yan Eli Maza

12 ‘Ya’yan Eli, maza kuwa, ba su da kirki, ba su kula da Ubangiji ba,

13 Ko ka’idodi game da abin da firistoci za su karɓa a hannun jama’a. A maimakon haka, lokacin da mutum ya je domin ya miƙa hadayarsa, sai baran firist ya zo da rino a hannunsa a sa’ad da ake dafa naman.

14 Sai ya caka rinon a cikin tukunyar, to, duk abin da ya cako wannan ya zama na firist. Haka suka yi ta yi wa dukan Isra’ilawa da suka zo miƙa hadaya a Shilo.

15 Tun kuma kafin a ƙona kitse, baran firist ɗin yakan zo ya ce wa wanda yake yin hadayar. “Ka ba ni wanda firist zai gasa, gama ba zai karɓi dafaffen nama daga gare ka ba, sai dai ɗanye.”

16 Idan mutumin ya ce, “To, bari a ƙona kitsen tukuna, sa’an nan ka ɗibi iyakar abin da kake bukata,” sai baran firist ɗin ya ce, “A’a, tilas ne ka ba ni yanzu, idan kuwa ba haka ba, zan ɗiba ƙarfi da yaji!”

17 Zunubin ‘ya’yan nan maza na Eli ya yi yawa a gaban Ubangiji, gama sun wulakanta hadayar Ubangiji ƙwarai da gaske.

Sama’ila a Shilo

18 Yaron nan Sama’ila yana ta aiki gaban Ubangiji, yana sāye da falmaran.

19 A kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka ‘yar rigar ado, ta kai masa a sa’ad da ita da mijinta sukan tafi miƙa hadayarsu ta shekara shekara.

20 Eli kuwa yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, ya ce, “Ubangiji ya ba ka waɗansu ‘ya’ya ta wurin matan nan a maimakon wanda kuka ba Ubangiji.”

Bayan wannan sai su koma gida.

21 Ubangiji ya sa wa Hannatu albarka, ta haifi ‘ya’ya maza uku da mata biyu. Yaron nan Sama’ila kuwa ya girma a gaban Ubangiji.

Eli da ‘Ya’yansa Maza

22 Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin dukan abin da ‘ya’yansa maza suke yi wa Isra’ilawa, da yadda suke kwana da matan da suke aiki a ƙofar alfarwa ta sujada.

23 Sai ya ce musu, “Me ya sa kuke irin waɗannan abubuwa? Gama kowa yana faɗa mini irin mugayen abubuwan da kuke aikatawa.

24 Haba ‘ya’yana, ku bari! Jama’ar Ubangiji suna ta magana a kan wannan mugun abu.

25 Idan mutum ya yi wa wani laifi, Allah yakan kāre shi, amma idan mutum ya yi wa Ubangiji zunubi, wa zai kāre shi?”

Amma ba su ji maganar mahaifinsu ba, gama Ubangiji ya riga ya yi shirin kashe su.

Annabci a kan Gidan Eli

26 Yaron nan Sama’ila ya yi ta girma da samun tagomashi a gaban Ubangiji da kuma mutane.

27 Wani annabi ya zo wurin Eli da saƙo daga wurin Ubangiji ya ce, “Sa’ad da kakanka Haruna da iyalinsa suke bauta wa Fir’auna a Masar, na bayyana kaina gare shi.

28 Na zaɓi iyalinsa daga dukan kabilan Isra’ila domin su zama firistocina, su riƙa aiki a bagade, suna ƙona turare, su riƙa ɗaukar keɓaɓɓen akwatina cikin yi mini aiki. Na kuma yardar musu su sami rabonsu daga hadayun da aka ƙona a kan bagade.

29 Me ya sa kuke haɗama a kan hadayuna da sadakokin da na umarta? Eli, don me kake girmama ‘ya’yanka fiye da ni, ka bar su suna ta cinye rabo mafi kyau na hadayun jama’ata Isra’ila?

30 Ni Ubangiji Allah na Isra’ila, na yi alkawari a dā cewa, ‘Kai da iyalinka da danginka za ku yi mini aikin firist har abada.’ Amma yanzu na ce ba zan yarda da wannan ba. Waɗanda suke girmama ni, zan girmama su. Waɗanda suke raina ni zan ƙasƙantar da su ƙwarai.

31 Ga shi, lokaci yana zuwa da zan karkashe samari cikin iyalinka da danginka, har da ba za a sami wanda zai rayu har ya tsufa a gidanka ba.

32 Za ka kasance da damuwa da jin kishi, za ka duba dukan albarkun da zan sa wa Isra’ila, amma a gidanka ba za a taɓa samun wanda zai rayu har ya tsufa ba.

33 Zan dai bar ɗaya daga zuriyarka da rai, zai yi mini aikin firist, amma zai makance ya fid da zuciya ga kome. Dukan sauran zuriyarka kuwa za su yi mutuwa ƙarfi da yaji.

34 Lokacin da ‘ya’yanka biyu, Hofni da Finehas, za su mutu rana ɗaya wannan zai nuna maka abin da na faɗa sai ya cika.

35 Zan zaɓar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so ya yi, zan kuwa ba shi zuriya da ko yaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.

36 Dukan wanda ya ragu daga zuriyarka zai je wurin sarki ya roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa ya taimaki firistoci da aiki domin ya sami abin da zai ci.”

Categories
1 SAM

1 SAM 3

Ubangiji Ya Kira Sama’ila

1 Yaron nan Sama’ila yana yi wa Ubangiji aiki a hannun Eli. A lokacin nan Ubangiji bai cika yin magana da mutane ba, ba safai kuma ake samun wahayi ba.

2 Wata rana da dare Eli wanda ya kusa makancewa har ba ya iya gani sosai, yana kwance a masujada.

3 Fitilar Ubangiji kuwa tana ci. Sama’ila kuma yana kwance a masujada inda akwatin alkawarin Allah yake.

4 Ubangiji kuwa ya kira Sama’ila. Sama’ila ya ce, “Na’am.”

5 Ya sheƙa zuwa wurin Eli, ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.”

Amma Eli ya ce masa, “Ban kira ka ba, koma ka kwanta.” Sai Sama’ila ya koma ya kwanta.

6 Ubangiji ya sāke kiran Sama’ila. Sama’ila ya tashi ya tafi wurin Eli, ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.”

Amma Eli ya ce, “Ban kira ka ba, ɗana koma ka kwanta.”

7 (Sama’ila dai bai san Ubangiji ba tukuna, gama Ubangiji bai riga ya fara magana da shi ba.)

8 Ubangiji kuma ya kira Sama’ila sau na uku. Sai kuma Sama’ila ya tashi ya nufi Eli, ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.”

Sa’an nan Eli ya gane Ubangiji ne yake kiran yaron,

9 saboda haka Eli ya ce wa Sama’ila ya koma ya kwanta, idan an sāke kiransa sai ya ce, “Ya Ubangiji, ka yi magana, gama bawanka yana kasa kunne.” Sama’ila kuwa ya koma ya kwanta.

10 Ubangiji kuma ya zo ya tsaya, ya yi kira kamar dā, ya ce, “Sama’ila! Sama’ila!”

Sama’ila ya amsa ya ce, “Ka yi magana, gama bawanka yana kasa kunne.”

11 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Zan yi wa Isra’ilawa wani abu, duk wanda ya ji kuwa zai razana.

12 A ranar zan cika abin da na faɗa game da Eli da iyalinsa daga farko har zuwa ƙarshe.

13 Na fāɗa masa zan hukunta gidansa har abada saboda ‘ya’yansa sun faɗi mugayen maganganu a kaina. Eli kuwa ya sani, amma bai kwaɓe su ba.

14 Domin haka na faɗa da ƙarfi, cewa laifin gidan Eli ba za a yi kafararsa da sadaka, ko da hadaya ba har abada.”

15 Sama’ila ya kwanta har safiya, sa’an nan ya buɗe ƙofofi. Amma ya ji tsoron faɗa wa Eli wahayin.

16 Amma Eli ya kira shi, ya ce, “Ya ɗana, Sama’ila.”

Sama’ila ya ce, “Ga ni.”

17 Eli ya tambaye shi, ya ce, “Me Ubangiji ya faɗa maka? Kada ka ɓoye mini. Allah zai hukunta ka idan ka ɓoye mini abin da ya faɗa maka.”

18 Sama’ila kuwa ya faɗa masa kome da kome, bai ɓoye masa kome ba. Sai Eli ya ce, “Ai, Ubangiji ne, bari ya yi abin da ya yi masa daidai.”

19 Sama’ila fa ya yi girma, Ubangiji yana tare da shi. Dukan maganarsa kuwa Ubangiji yana cika ta.

20 Dukan mutanen Isra’ila fa daga wannan kusurwar ƙasa zuwa wancan, sun tabbata Sama’ila annabin Ubangiji ne.

21 Ubangiji kuma ya yi ta bayyana a Shilo inda ya bayyana kansa ga Sama’ila, ya kuma yi magana da shi. Duk lokacin da Sama’ila ya yi magana dukan mutanen Isra’ila suna kasa kunne.

Categories
1 SAM

1 SAM 4

Filistiyawa Sun Ƙwace Akwatin Alkawari

1 A wannan lokaci Isra’ilawa suka yi shiri su yi yaƙi da Filistiyawa, Isra’ilawa suka kafa sansaninsu a Ebenezer, Filistiyawa kuma suka kafa nasu a Afek.

2 Filistiyawa suka shirya su fara yaƙi. Bayan yaƙi mai zafi, sai Filistiyawa suka ci Isra’ilawa, suka kashe mutane wajen dubu huɗu (4,000) a bakin dāga.

3 Da sojojin da suka ragu suka koma sansani, sai shugabannin Isra’ila suka ce, “Me ya sa Ubangiji ya sa Filistiyawa suka ci mu yau? Bari mu kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Shilo ya kasance tare da mu, ya cece mu daga ikon abokan gābanmu.”

4 Sai suka aika zuwa Shilo aka kawo akwatin alkawarin Ubangiji Mai Runduna, wanda yake zaune a tsakanin kerubobi. ‘Ya’yan nan na Eli, maza guda biyu, wato Hofni da Finehas, suna tare da akwatin alkawarin.

5 Da akwatin alkawarin Ubangiji ya iso sansanin, sai dukan mutanen Isra’ila suka yi sowa da ƙarfi, har ƙasa ta amsa.

6 Da Filistiyawa suka ji amon sowar suka ce, “Ina ma’anar irin wannan babbar sowa a sansanin Ibraniyawa?” Da suka gane akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga sansanin,

7 sai Filistiyawa suka tsorata, suka ce, “Allah ya shiga sansanin, kaitonmu, gama ba a taɓa yin irin wannan abu ba.

8 Mun shiga uku, wa zai cece mu daga hannun allolin nan masu iko? Waɗannan suka karkashe Masarawa a hamada!

9 Ya ku Filistiyawa, ku yi ƙarfin hali, ku yi jaruntaka don kada ku zama bayin Ibraniyawa kamar yadda suka zama bayinku, ku yi jaruntaka ku yi yaƙi.”

10 Filistiyawa kuwa suka yi yaƙi gadan-gadan, suka ci mutanen Isra’ila. Mutanen Isra’ila suka gudu, kowa ya nufi gidansa. Aka kashe Isra’ilawa da yawa, wato mutum dubu talatin (30,000).

11 Aka kuma ƙwace akwatin alkawarin Ubangiji, ‘ya’yan Eli guda biyu, Hofni da Finehas kuma, aka kashe su.

Mutuwar Eli

12 Wani mutumin kabilar Biliyaminu ya gudu daga dāgar yaƙin ya zo Shilo da tufafinsa ketattu ga kuma ƙura a kansa.

13 Sa’ad da ya iso, Eli yana zaune a kujerarsa a bakin hanya, yana jira, gama zuciyarsa ta damu saboda akwatin alkawarin Allah. Da mutumin ya shiga gari ya ba da labari, dukan garin ya ruɗe da kuka.

14 Sa’ad da Eli ya ji kukan, sai ya tambaya ya ce, “Me ake wa kuka?” Mutumin kuwa ya gaggauta zuwa wurin Eli ya faɗa masa.

15 (Eli yana da shekara tasa’in da takwas, ya kuwa makance ɗungum.)

16 Mutumin ya ce wa Eli, “Yau daga wurin yaƙin na tsere, na gudo gida.”

Eli ya ce, “Dana, me ya faru?”

17 Sai wanda ya kawo labarin ya ce, “Isra’ilawa sun gudu a gaban Filistiyawa, an kashe mutane da yawa, har ma da ‘ya’yanka biyu, Hofni da Finehas, sun rasu, an kuma ƙwace akwatin alkawarin Allah.”

18 Da aka ambaci akwatin alkawari, sai Eli ya tuntsura da baya daga inda yake zaune a bakin ƙofar gari, wuyansa kuwa ya karye, ya mutu, gama shi tsoho ne, mai ƙiba. Ya shekara arba’in yana shugabancin Isra’ila.

Mutuwar Matar Finehas

19 Surukar Eli, matar Finehas, tana da juna biyu, ta kusa haihuwa. Sa’ad da ta ji labari an ƙwace akwatin alkawarin Allah, surukinta kuma da mijinta sun rasu, sai ta kama naƙuda farat ɗaya, ta haihu.

20 Tana bakin mutuwa, matan kuwa da take taimakonta suka ce mata, “Ki yi ƙarfin hali, gama kin haifi ɗa namiji.” Amma ba ta amsa ba, ba ta kuma kula ba.

21 Sai ta sa wa yaron suna Ikabod, wato ɗaukaka ta rabu da Isra’ila domin an ƙwace akwatin alkawarin Allah, domin kuma surukinta da mijinta sun rasu.

22 Ta ce, “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila, gama an ƙwace akwatin alkawarin Allah.”