Categories
2 SAR

2 SAR 18

Sarki Hezekiya na Yahuza

1 A shekara ta uku ta sarautar Hosheya ɗan Ila Sarkin Isra’ila, Hezekiya ɗan Ahaz Sarkin Yahuza ya ci sarautar.

2 Yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya ci sarautar. Ya yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Abi, ‘yar Zakariya.

3 Ya aikata abin da yake mai kyau a gaban Ubangiji kamar yadda kakansa, Dawuda, ya yi.

4 Ya kawar da wuraren tsafi na kan tuddai, ya rurrushe ginshiƙai, ya sassare siffar Ashtoret. Ya kuma farfashe macijin tagulla wanda Musa ya yi, gama har zuwa lokacin jama’ar Isra’ila suna miƙa masa hadaya ta turaren ƙonawa. Aka ba macijin suna Nehushatan.

5 Hezekiya ya dogara ga Ubangiji Allah na Isra’ila. Ba a sami kamarsa a cikin dukan sarakunan Yahuza ba, waɗanda suka yi sarauta a gabansa, ko waɗanda suka yi bayansa.

6 Ya manne wa Ubangiji, bai bar binsa ba, ya kuma kiyaye umarnan da Ubangiji ya ba Musa.

7 Ubangiji kuwa ya kasance tare da shi, duk inda ya nufa sai ya sami albarka. Ya tayar wa Sarkin Assuriya, ya ƙi bautar masa.

8 Ya kuma bugi Filistiyawa har zuwa Gaza da iyakarta daga hasumiya zuwa birni mai garu.

Faɗuwar Samariya

9 A shekara ta huɗu ta sarautar sarki Hezekiya, a lokacin Hosheya ɗan Ila, Sarkin Isra’ila, yana da shekara bakwai da sarauta, sai Shalmanesar Sarkin Assuriya ya kawo wa Samariya yaƙi, ya kewaye ta.

10 A ƙarshen shekara ta uku, ya ci ta da yaƙi. A lokacin Hezekiya yana da shekara shida da sarauta, Hosheya kuwa yana da shekara tara da tasa sarauta.

11 Sarkin Assuriya kuwa ya kwashi Isra’ilawa zuwa Assuriya, ya ajiye su a Hala, da Habor a bakin kogin Gozan, da cikin garuruwan Mediyawa.

12 Ba su yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu ba, amma suka karya alkawarinsa har da dukan abin da Musa bawan Ubangiji ya umarta. Ba su kasa kunne ba, balle su aikata. Domin wannan Samariya ta faɗi.

Assuriyawa Sun Yi wa Urushalima Barazana

13 A shekara ta goma sha huɗu ta sarautar sarki Hezekiya, sai Sennakerib, Sarkin Assuriya, ya kawo wa dukan birane masu garu na Yahuza yaƙi, ya kuwa ci su.

14 Sai Hezekiya, Sarkin Yahuza, ya aika zuwa wurin Sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka ƙyale ni, duk abin da ka ɗora mini zan ɗauka.” Sai Sarkin Assuriya ya ce wa Hezekiya Sarkin Yahuza ya ba shi talanti ɗari uku na azurfa, da talanti talatin na zinariya.

15 Hezekiya kuwa ya ba shi dukan azurfar da take cikin Haikalin Ubangiji, da wanda yake cikin baitulmali na gidan sarki.

16 A lokacin sai Hezekiya ya kankare zinariyar da aka dalaye ƙofofi da madogaran ƙofofin Haikalin Ubangiji da ita, ya ba Sarkin Assuriya.

17 Sai Sarkin Assuriya ya aiki Tartan, da Rabsaris, da Rabshake, tare da sojoji da yawa daga Lakish zuwa ga sarki Hezekiya a Urushalima. Suka haura zuwa Urushalima, suka tsaya kusa da wuriyar ruwan kududdufi wanda yake kan tudu, wanda yake a kan karauka zuwa wurin wanki.

18 Sa’ad da suka kira sarki, sai Eliyakim ɗan Hilkiya, wanda yake wakilin gidan sarki, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci, suka fito.

19 Sa’an nan Rabshake ya ce musu, “Ku faɗa wa Hezekiya, cewa mai girma, Sarkin Assuriya ya ce, ‘Ga wa kake dogara?

20 Kana tsammani maganganu kurum su ne dabara da ƙarfin yin yaƙi? To, ga wa ka dogara har da ka tayar mini?

21 Ga shi yanzu, kana dogara ga Masar, wannan karyayyen sandan kyauro, wanda yakan yi wa hannun mutumin da yake tokarawa da shi sartse. Haka Fir’auna Sarkin Masar, yake ga dukan waɗanda suke dogara gare shi.’

22 “Amma idan ka ce mini, ‘Ina dogara ga Ubangiji Allahnmu,’ to, ba masujadansa na kan tuddai da bagadansa ne Hezekiya ya rurrushe ba? Yana ce wa mutanen Yahuza da Urushalima, ‘Za ku yi sujada a gaban wannan bagade a Urushalima?’

23 Sai ka zo, ku daidaita da ubangidana, Sarkin Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu (2,000), idan za ka iya samun mahayansu.

24 Ba ka isa ka kara da ko mafi ƙanƙanta na shugabannin sojojin maigidana ba, amma har kana dogara ga Masar don samun karusai da mahaya?

25 Kana tsammani, ba da yardar Ubangiji ba ne na kawo wa wurin nan yaƙi don a hallaka shi? Gama Ubangiji ya ce mini, ‘Ka kai wa wannan ƙasa yaƙi don ka hallaka ta.’ ”

26 Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa, suka ce wa Rabshake, “Muna roƙonka, ka yi magana da mu barorinka da harshen Aramiya gama muna jinsa, kada ka yi magana da mu da harshen Yahudanci, har mutanen da suke kan garu su ji.”

27 Amma Rabshake ya ce musu, “Ai, ubangidana bai aike ni in yi wannan magana ga ubangidanku da ku kaɗai ba, amma ga dukan mutanen da suke zaune a kan garu, waɗanda aka ƙaddara su tare da ku don su ci najasarsu su sha fitsarinsu.”

28 Sa’an nan Rabshake ya tsaya, ya yi kira da ƙarfi da harshen Yahudanci, ya ce, “Ku ji maganar mai girma, Sarkin Assuriya!

29 Sarki ya ce, ‘Kada ku yarda Hezekiya ya ruɗe ku, gama ba zai iya cetonku daga hannuna ba.

30 Kada kuma ku yarda Hezekiya ya sa ku dogara ga Ubangiji da cewa lalle Ubangiji zai cece ku, ba za a kuma ba da wannan birni a hannun Assuriya ba.’

31 Kada ku kasa kunne ga Hezekiya, gama Sarkin Assuriya ya ce, ‘Ku yi amana da ni, ku fito zuwa wurina. Kowane ɗayanku kuwa zai ci ‘ya’yan inabinsa da ‘ya’yan ɓaurensa, ya kuma sha ruwa daga cikin randarsa,

32 har lokacin da zan zo in kwashe ku, in kai ku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasa mai yalwar hatsi, da ruwan inabi,da abinci, da gonakin inabi, da itatuwan zaitun, da zuma, don ku rayu, kada ku mutu! Kada kuma ku yarda Hezekiya ya yaudare ku da cewa Ubangiji zai cece ku.

33 Ko akwai wani allah daga cikin allolin al’ummai, wanda ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannun Sarkin Assuriya?

34 Ina allolin Hamat, da na Arfad, da na Sefarwayim, da na Hena, da na Iwwa? Sun ceci Samariya daga hannuna ne?

35 Daga cikin dukan allolin ƙasashe, wane ne ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannuna har da Ubangiji zai ceci Urushalima daga hannuna?’ ”

36 Sai mutanen suka yi tsit, ba wanda ya ce masa uffan, gama sarki ya umarta cewa kada a tanka masa.

37 Sa’an nan Eliyakim ɗan Hilkiya, wanda yake wakilin gidan sarki, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci, suka zo wurin Hezekiya da tufafinsu ketattu, suka faɗa masa irin maganar da Rabshake ya yi.

Categories
2 SAR

2 SAR 19

An Ceci Yahuza daga Sennakerib

1 Da sarki Hezekiya ya ji wannan magana, sai ya kyakketa tufafinsa, ya sa rigar makoki, sa’an nan ya shiga Haikalin Ubangiji.

2 Sai ya aiki Eliyakim wakilin gidan sarki, da Shebna magatakarda, da manyan firistoci, saye da tufafin makoki zuwa wurin annabi Ishaya, ɗan Amoz,

3 su ce masa, “Hezekiya ya ce, yau ranar wahala ce, da ta cin mutunci, da ta shan kunya, ga shi, ‘ya’ya suna gab da a haife su, amma ba ƙarfin da za a yi yunƙuri a haife su.

4 Mai yiwuwa ne Ubangiji Allahnka ya ji dukan maganganun da Rabshake ya yi wanda ubangidansa, Sarkin Assuriya, ya aiko don yi wa Allah mai rai ba’a. Bari Ubangiji Allahnka ya hukunta masa saboda maganganunsa, sai ka yi addu’a saboda sauran da suka ragu.”

5 Sa’ad da fādawan sarki Hezekiya suka iso wurin Ishaya,

6 sai ya aike da amsa, ya ce musu, “Ku faɗa wa ubangidanku, Ubangiji ya ce, ‘Kada ka ji tsoron maganganun da ka ji daga bakin barorin Sarkin Assuriya, waɗanda suka saɓe ni.

7 Ga shi, zan sa wani ruhu a cikinsa da zai ji jita-jita, har ya koma ƙasarsa, zan sa a kashe shi da takobi a ƙasarsa.’ ”

8 Rabshake kuwa ya koma, ya tarar Sarkin Assuriya yana yaƙi da Libna, gama ya ji labari sarki ya riga ya bar Lakish.

9 Da sarki ya ji labari Tirhaka, Sarkin Habasha, ya fito don ya yi yaƙi da shi, sai ya sāke aikar manzanni wurin Hezekiya, ya ce,

10 “Ku faɗa wa Hezekiya Sarkin Yahuza, kada ya yarda Allahnsa wanda yake dogara gare shi ya yaudare shi da yi masa alkawari, cewa Sarkin Assuriya ba zai ci Urushalima ba.

11 Ya ji abin da Sarkin Assuriya ya yi wa dukan ƙasashe yadda ya hallaka su sarai. To, shi zai kuɓuta?

12 Allolin al’ummai sun cece su ne? Wato al’umman da kakannina suka hallaka, wato Gozan, da Haran, da Rezef, da mutanen Eden da suke Telassar.

13 Ina Sarkin Hamat, da Sarkin Arfad, da sarkin birnin Sefarwayim, da Sarkin Hena, da Sarkin Iwwa?”

14 Hezekiya ya karɓi wasiƙa daga hannun manzannin ya karanta ta, sa’an nan ya shiga Haikalin Ubangiji, ya buɗe ta, ya ajiye ta a gaban Ubangiji.

15 Sa’an nan ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Isra’ila, kai da kake zaune a kan gadon sarautarka, kai kaɗai ne Allah a dukan mulkokin duniya, kai ne ka yi sama da ƙasa.

16 Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka yi. Ka buɗe idanunka, ya Ubangiji, ka gani, ka kuma ji irin maganar Sennakerib wadda ya aiko don a yi wa Allah mai rai ba’a.

17 A gaskiya kam, ya Ubangiji, sarakunan Assuriya sun lalatar da al’ummai da ƙasashensu.

18 Sun jefar da gumakansu cikin wuta, gama su ba Allah ba ne, amma ayyukan hannuwan mutane ne, waɗanda aka yi da itace da dutse, saboda haka an iya a hallaka su.

19 Yanzu ya Ubangiji Allahnmu, ina roƙonka ka cece mu daga hannunsa domin dukan mulkokin duniya su sani kai kaɗai ne Allah, ya Ubangiji.”

20 Sa’an nan Ishaya, ɗan Amoz, ya aika wa Hezekiya cewa, “Ubangiji Allah na Isra’ila ya ji addu’arka, ya kuma amsa.”

21 Ubangiji ya ce, “Birnin Urushalima ya yi maka dariya, kai Sennakerib, yana yi maka ba’a.

22 Wa kake tsammani ka yi wa ba’a har da zagi? Ba ka ga girmana ba, ni Allah Mai Tsarki na Isra’ila?

23 Ka aiki manzanninka su nuna mini girmankai saboda ka ci duwatsu mafi tsayi da karusanka, har ma ka ci duwatsun Lebanon. Ka yi fariyar a kan ka datse itatuwan al’ul mafi tsayi da na fir, har kuma ka shiga har can tsakiyar kurmi.

24 Ka yi fariya a kan gina rijiyoyi, ka sha ruwan baƙuwar ƙasa, ƙafafun sojojinka kuma sun tattake Kogin Nilu, ya ƙafe.

25 “Ba ka taɓa ji ba, cewa na ƙaddara wannan tun dā? Abin da yake faruwa yanzu, na shirya shi tun tuni, yadda za ka mai da birane masu garu su zama kufai.

26 Mazauna cikinsu suka rasa ƙarfi, suka damu, suka ruɗe. Suka zama kamar ciyawar saura, ko kuma ciyawar da ta tsiro a rufin soro, da iskar gabas mai zafi ta busa, har ta bushe.

27 “Na san zamanka, da fitarka, da shigowarka, da fushin da kake yi da ni.

28 Na ji irin fushinka da girmankanka, yanzu kuwa zan sa ƙugiya a hancinka, linzami kuma a bakinka, in komar da kai baya, ta hanyar da ka biyo.”

29 Sa’an nan Ishaya ya ce wa sarki Hezekiya, “Wannan zai zama alama a gare ka. A wannan shekara za ku ci gyauro, a shekara ta biyu za ku ci gyauron gyauron, a shekara ta uku kuwa za ku shuka ku girbe, ku dasa inabi a gonakin inabi, ku ci ‘ya’yansu.

30 Ringin mutanen gidan Yahuza za su yi saiwa a ƙasa, sa’an nan su ba da ‘ya’ya a sama.

31 Gama daga Urushalima ringi zai fito, daga Dutsen Sihiyona kuma waɗanda suka tsira za su fito. Kishin Ubangiji ne zai yi wannan.”

32 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Sarkin Assuriya ba zai zo birnin ba, ko ya harba kibiya, ko ya zo kusa da shi da garkuwa, ko ya tsiba masa tudu.

33 Zai koma ta hanyar da ya zo. Ba zai shiga wannan birni ba.

34 Gama zan tsare wannan birni, in cece shi don kaina, da kuma don bawana Dawuda.”

35 A daren nan, sai mala’ikan Ubangiji ya tafi ya kashe Assuriyawa a sansaninsu, mutum dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar (185,000). Sa’ad da mutanen Isra’ila suka tashi da sassafe, sai suka ga gawawwakin nan kwance.

36 Sennakerib Sarkin Assuriya, kuwa ya tashi, ya koma gida, ya zauna a Nineba.

37 Sa’ad da yake yin sujada a haikalin gunkinsa Nisrok, sai ‘ya’yansa, Adrammelek da Sharezer, suka kashe shi da takobi, sa’an nan suka tsere zuwa ƙasar Ararat. Sai ɗansa guda, wato Esar-haddon ya gāji gadon sarautarsa.

Categories
2 SAR

2 SAR 20

Ciwon Hezekiya da Warkewarsa

1 A waɗannan kwanaki sai Hezekiya ya yi rashin lafiya har yana gab da mutuwa. Sai annabi Ishaya, ɗan Amoz, ya zo wurinsa, ya ce masa, “Ubangiji ya ce, ka kintsa gidanka, gama mutuwa za ka yi, ba za ka warke ba.”

2 Hezekiya kuwa ya juya fuskarsa bango, ya yi roƙo ga Ubangiji, yana cewa,

3 “Ka tuna da ni yanzu, ya Ubangiji, ina roƙonka, da yadda na yi tafiya a gabanka da aminci, da zuciya ɗaya, na aikata abin da yake mai kyau a gabanka.” Sai ya yi ta rusa kuka.

4 Kafin Ishaya ya fita daga filin tsakiyar fādar, sai Ubangiji ya yi magana da shi, ya ce,

5 “Ka koma, ka faɗa wa Hezekiya sarkin jama’ata cewa, ‘Ni Ubangiji Allahn kakanka, Dawuda, na ji roƙonka, na kuma ga hawayenka, saboda haka zan warkar da kai, a rana ta uku kuwa za ka haura zuwa Haikalin Ubangiji.

6 Zan ƙara maka shekara goma sha biyar. Zan kuwa cece ka, kai da wannan birni daga hannun Sarkin Assuriya, zan tsare wannan birni don kaina da kuma don bawana, Dawuda.’ ”

7 Sai Ishaya ya ce, “Ku yi masa farsa da ɓaure, marurun zai warke.”

8 Hezekiya kuwa ya ce wa Ishaya, “Mece ce alama, cewa Ubangiji zai warkar da ni har in haura zuwa Haikalin Ubangiji a rana ta uku?”

9 Sai Ishaya ya ce, “Wannan ita ce alama daga wurin Ubangiji, Ubangiji zai cika alkawarin da ya yi. Ƙaƙa kake so, inuwa ta yi gaba da taki goma, ko kuwa ta yi baya da taki goma?”

10 Hezekiya ya amsa, ya ce, “Ai, ya fi sauƙi inuwa ta yi gaba da taki goma da ta yi baya da taki goma.”

11 Sai annabi Ishaya ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya komar da inuwa baya da taki goma, bayan da ta riga ta wuce a matakin sarki Ahaz.

Hezekiya ya Karɓi Manzanni daga Babila

12 A lokacin nan sai Merodak-baladan, ɗan Baladan, Sarkin Babila, ya ji labarin rashin lafiyar Hezekiya, sai ya aiki manzanni da wasiƙa da kyautai su kai wa Hezekiya,

13 Hezekiya kuwa ya marabce su, ya kuma nuna musu dukan taskokin dukiyarsa na azurfa, da na zinariya, da na turare, da na mai mai daraja, da na makaman yaƙinsa, da dukan abin da yake akwai a cikin ɗakunan ajiyarsa. Ba abin da ya rage daga cikin gidansa, ko a mulkinsa wanda bai nuna musu ba.

14 Sai annabi Ishaya ya tafi wurin sarki Hezekiya ya ce masa, “Daga ina ne waɗannan mutane? Me suka ce maka?”

Hezekiya ya amsa, ya ce, “Sun zo daga ƙasa mai nisa, wato Babila.”

15 Ishaya ya ce, “Me suka gani a fādarka?”

Hezekiya ya ce, “Sun ga duk abin da yake ciki, ba wani abu kuma daga cikin taskokina da ban nuna musu ba.”

16 Sa’an nan Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji abin da Ubangiji ya ce,

17 ‘Lokaci yana zuwa da za a kwashe duk abin da yake cikin gidanka, da abin da kakanninka suka tanada, zuwa Babila.

18 Za a kuma kwashe waɗansu ‘ya’yanka da ka haifa zuwa Babila, can za a maishe su babani a fādar Sarkin Babila.’ ”

19 Sarki Hezekiya kuwa ya fahimci za a yi zaman lafiya da salama a zamaninsa, don haka ya amsa ya ce, “Jawabin da ka kawo mini daga wurin Ubangiji yana da kyau.”

Rasuwar Hezekiya

20 Sauran ayyukan Hezekiya da dukan ƙarfinsa, da yadda ya yi tafki da wuriyar ruwa don ya kawo ruwa cikin birnin, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

21 Hezekiya kuwa ya rasu. Sai ɗansa, Manassa, ya gāji gadon sarautarsa.

Categories
2 SAR

2 SAR 21

Sarki Manassa na Yahuza

1 Manassa yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi shekara hamsin da biyar yana sarauta a Urushalima. Sunan tsohuwarsa kuwa Hefziba.

2 Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji, gama ya aikata abubuwa masu banƙyama waɗanda al’umman da Ubangiji ya kora a gaban jama’ar Isra’ila suka aikata.

3 Gama ya gina matsafai a kan tuddai waɗanda Hezekiya tsohonsa ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai, ya kuma yi gunkiyan nan, wato Ashtoret, kamar yadda Ahab, Sarkin Isra’ila, ya yi. Ya yi wa taurari sujada, ya bauta musu.

4 Ya gina bagadai a Haikalin Ubangiji inda Ubangiji ya ce, “A Urushalima zan sa sunana.”

5 Ya gina wa taurarin sama bagadai a farfajiya biyu ta Haikalin Ubangiji.

6 Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa ya kuma aikata sihiri, ya yi dūba. Ya yi ma’amala da masu mabiya da mayu. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.

7 Siffar gunkiyan nan Ashtoret wadda ya yi, ya kafa ta a Haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Sulemanu, “A cikin wannan Haikali a Urushalima wadda na zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila zan tabbatar da sunana har abada.

8 Ba zan sa jama’ar Isra’ila su ƙara fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da bawana Musa ya umarce su.”

9 Amma mutanen Yahuza ba su kasa kunne ba. Manassa kuma ya yaudare su, suka aikata mugunta fiye da abin da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban jama’ar Isra’ila suka aikata.

10 Ubangiji kuwa ya yi magana ta wurin bayinsa annabawa ya ce,

11 “Tun da yake Manassa, Sarkin Yahuza, ya aikata waɗannan abubuwa masu banƙyama, ya kuma aikata mugayen abubuwa fiye da dukan abin da Amoriyawa, waɗanda suka riga shi, suka aikata, ya kuma sa mutanen Yahuza su yi zunubi saboda gumakansa,

12 saboda haka ni Ubangiji Allah na Isra’ila, zan aukar wa Urushalima da mutanen Yahuza da masifa irin wadda duk wanda ya ji labarinta, sai ya kusa suma.

13 Zan gwada Urushalima da magwajin Samariya da kuma ma’aunin gidan Ahab. Zan kuma suɗe Urushalima kamar yadda mutum yakan suɗe akushi sa’an nan ya kifar da shi.

14 Zan jefar da ragowar gādona, in bashe su a hannun abokan gāba, za su zama ganima da abin waso ga dukan abokan gābansu,

15 saboda sun aikata mugunta a gabana, suka tsokane ni in yi fushi tun ranar da kakanninsu suka fito daga Masar har wa yau.”

16 Banda wannan kuma Manassa ya kashe adalai har ya cika Urushalima daga wannan gefe zuwa wancan da jininsu, banda zunubin da ya sa mutanen Yahuza su yi, har suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji.

17 Sauran ayyukan Manassa, da dukan abin da ya aikata, da zunubin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

18 Manassa ya mutu, aka binne shi a lambun gidansa a gonar Uzza. Ɗansa Amon ya gāji gadon sarautarsa.

Sarki Amon na Yahuza

19 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Meshullemet, ‘yar Haruz na Yotba.

20 Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji kamar yadda tsohonsa, Manassa ya yi.

21 Ya bi halin tsohonsa duka. Ya bauta wa gumakan da tsohonsa ya bauta wa, ya kuma yi musu sujada.

22 Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai bi tafarkin Ubangiji ba.

23 Fādawansa kuwa suka ƙulla masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a gidansa.

24 Amma mutanen ƙasar suka kashe waɗannan da suka yi wa sarki Amon maƙarƙashiyar. Sai suka naɗa Yosiya ɗan sarki, ya gāji tsohonsa.

25 Sauran ayyukan da Amon ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

26 Aka binne shi a kabarinsa na gonar Uzza. Ɗansa Yosiya ya gāji sarautarsa.

Categories
2 SAR

2 SAR 22

Sarki Yosiya na Yahuza

1 Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya ci sarauta, ya yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Yedida, ‘yar Adaya na Bozkat.

2 Ya yi abin da yake mai kyau a gaban Ubangiji. Ya bi dukan halin kakansa, Dawuda, bai kauce dama ko hagu ba.

Yosiya da Littafin Shari’a

3 A shekara ta goma sha takwas ta sarautarsa, sai ya aiki Shafan ɗan Azaliya, wato jikan Meshullam, magatakarda, zuwa Haikalin Ubangiji, ya ce,

4 “Ka tafi wurin Hilkiya babban firist domin a lasafta yawan kuɗin da aka kawo cikin Haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tattara daga wurin jama’a.

5 A ba da kuɗin a hannun masu lura da ma’aikata waɗanda suke gyaran Haikalin Ubangiji, su kuma su ba waɗanda suke gyaran Haikalin,

6 wato masu sassaƙa, da magina, domin a sayi katako da dutsen da aka haƙo don gyaran Haikalin.

7 Kada a tambaye su yadda suka kashe kuɗin da aka sa a hannunsu, gama su amintattu ne.”

8 Hilkiya babban firist kuwa ya ce wa Shafan magatakarda, “Na iske littafin dokoki a cikin Haikalin Ubangiji.” Hilkiya kuwa ya ba Shafan littafin, shi kuwa ya karanta shi.

9 Sai Shafan magatakarda ya tafi ya faɗa wa sarki cewa, “Baranka ya kwashe kuɗin da ya tarar a Haikali, na kuwa ba masu lura da ma’aikatan Haikalin Ubangiji.”

10 Ya kuma ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Ya kuwa karanta wa sarki littafin.

11 Sa’ad da sarki ya ji maganar da take cikin littafin dokoki, sai ya kece tufafinsa.

12 Sa’an nan ya umarci Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikaiya, da Shafan magatakarda, da Asaya baran sarki cewa,

13 “Ku tafi ku yi tambaya ga Ubangiji saboda ni, da jama’a, da dukan mutanen Yahuza a kan maganar littafin nan da aka samo, gama Ubangiji ya yi fushi da muƙwarai saboda kakanninmu domin ba su bi maganar littafin nan ba, har da za su yi dukan abin da aka rubuta mana.”

14 Sai Hilkiya firist, da Ahikam, da Akbor, da Shafan, da Asaya suka tafi wurin annabiya Hulda, matar Shallum ɗan Tikwa, wato jikan Harhas, mai tsaron ɗakin da ake ajiye tufafi. A Urushalima take zaune a sabuwar unguwa. Suka kuwa yi magana da ita.

15 Sai ta ce musu, “Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, a faɗa wa mutumin da ya aiko ku gare ni,

16 ‘Ga shi, zan aukar da masifa a wurin nan, da a mazaunan wurin, bisa ga dukan maganar littafin nan wanda Sarkin Yahuza ya karanta,

17 domin sun rabu da ni, sun ƙona turare ga gumaka don su tsokane ni in yi fushi da aikin hannuwansu. Saboda haka fushina zai ƙuna a kan wurin nan, ba kuwa zai huce ba.’

18 Amma a kan Sarkin Yahuza, wanda ya aiko ku, ku tambayar masa Ubangiji, ku faɗa masa Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘A kan maganar da ka ji,

19 da yake zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gabana sa’ad da ka ji yadda na yi magana gāba da wannan wuri, da kuma mazaunansa, cewa zai zama kufai da la’ana, kai kuwa ka keta tufafinka, ka yi kuka a gabana, hakika na ji kukanka.

20 Domin haka, ba za ka ga hukuncin da yake zuwa a kan Urushalima ba, za a kai ka cikin kabarinka lafiya.’ ”

Mutanen kuwa suka mayar wa sarki Yosiya da wannan magana.

Categories
2 SAR

2 SAR 23

Gyare-gyaren da Yosiya Ya Yi

1 Sarki Yosiya kuwa ya aika, aka tattaro masa dukan dattawan Yahuza da na Urushalima.

2 Sa’an nan ya haura zuwa Haikalin Ubangiji tare da dukan jama’ar Yahuza, da dukan mazaunan Urushalima, da firistoci, da annabawa, da jama’a duka, ƙanana da manya. Sai ya karanta musu dukan maganar littafin alkawarin da aka iske a Haikalin Ubangiji.

3 Sarki ya tsaya kusa da ginshiƙi ya yi alkawari ga Ubangiji, cewa zai bi Ubangiji da zuciya ɗaya, da dukan ransa. Zai kiyaye umarnansa, da farillansa, da dokokinsa, ya bi maganar alkawarin da aka rubuta a littafin. Dukan jama’a kuma suka yi alkawarin.

4 Sa’an nan sarki Yosiya ya umarci Hilkiya, babban firist, da firistoci masu daraja ta biyu, da masu tsaron ƙofa, su fitar da tasoshin da aka yi wa Ba’al, da Ashtoret, da dukan taurarin sama, daga cikin Haikalin Ubangiji. Sai ya ƙone su a bayan Urushalima a saurar Kidron, sa’an nan ya kwashe tokarsu zuwa Betel.

5 Ya kuma tuɓe firistocin gumaka waɗanda sarakunan Yahuza suka naɗa domin su ƙona turare a matsafai na kan tuddai a garuruwan Yahuza, da kewayen Urushalima, da firistoci waɗanda suka ƙona turare ga Ba’al, da rana, da wata, da taurari, da dukan rundunan sama.

6 Sai sarki ya fitar da gunkiyan nan Ashtoret, daga cikin Haikalin Ubangiji a Urushalima, ya kai Kidron, ya ƙone ta a ƙoramar Kidron, ta zama toka, ya kuwa watsar da tokar a makabarta.

7 Ya rurrushe ɗakunan karuwai mata da maza da suke a Haikalin Ubangiji, wato wurin da mata suke saƙa labulan gunkiyar.

8 Ya fitar da dukan firistoci daga cikin garuruwan Yahuza, sa’an nan ya lalatar da matsafai na kan tuddai inda firistoci suka ƙona turare, tun daga Geba har zuwa Biyer-sheba. Ya kuma rurrushe matsafai na kan tuddai waɗanda suke a ƙofofin shiga ƙofar Joshuwa, hakimin birnin, waɗanda suke hagu da ƙofar birnin.

9 Duk da haka firistoci matsafai na kan tuddai ba su haura zuwa bagaden Ubangiji a Urushalima ba, amma suka ci abinci marar yisti tare da ‘yan’uwansu.

10 Ya kuma lalatar da Tofet, wurin da yake kwarin ‘ya’yan Hinnom, don kada kowa ya ƙara miƙa ɗansa ko ‘yarsa hadaya ta ƙonawa ga Molek.

11 Ya kawar da dawakan da sarakunan Yahuza suka keɓe wa rana, a ƙofar Haikalin Ubangiji, kusa da shirayin Natan-melek shugaban shirayin da yake cikin farfajiya. Haka kuma ya ƙone karusai waɗanda aka yi wa rana.

12 Ya rurrushe, ya kuma farfasa bagaden da yake bisa rufin benen Ahaz, waɗanda sarakunan Yahuza suka gina, da kuma bagaden da Manassa ya gina a farfajiya biyu ta Haikalin Ubangiji. Sai ya watsar da tokar da ƙurar a rafin Kidron.

13 Ya kuma lalatar da matsafai na kan tuddan da suke gabashin Urushalima, kudu da Dutsen Hallaka, waɗanda Sulemanu Sarkin Isra’ila, ya gina wa Ashtoret gunkiyar Sidoniyawa, da Kemosh gunkin Mowab, da Milkom gunkin Ammonawa.

14 Ya rurrushe ginshiƙai, ya sassare siffofin gumakan, sa’an nan ya rufe wurarensu da ƙasusuwan mutane.

15 Yosiya ya kuma rushe bagaden da yake a Betel, wanda Yerobowam ɗan Nebat ya gina, wanda ya sa mutanen Isra’ila su yi zunubi, tare da tudun, ya farfashe duwatsun, ya niƙe su, sun zama gari, ya kuma ƙone Ashtoret.

16 Da Yosiya ya waiwaya, sai ya ga kaburbura a kan dutse. Ya aika a kwaso ƙasusuwan da suke cikin kaburburan, sai ya ƙone su a bisa bagaden, ya lalatar da shi kamar yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin annabi.

17 Ya kuma ce, “Kabarin wane ne wancan da nake gani?”

Sai mutanen Betel suka ce masa, “Ai,kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuza ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”

18 Sarki kuwa ya ce, “A bar shi yadda yake, kada wani ya taɓa ƙasusuwansa.”

Sai suka bar ƙasusuwan annabin da ya zo daga Samariya.

19 Dukan matsafai na kan tuddai da suke a garuruwan Samariya waɗanda sarakunan Isra’ila suka gina, har suka sa Ubangiji ya yi fushi, Yosiya ya watsar da su. Ya yi da su kamar yadda ya yi a Betel.

20 Ya kuma karkashe dukan firistocin matsafai na kan tuddai a bisa bagadan da suke can. Ya ƙone ƙasusuwansu a bisa bagadan. Sa’an nan ya komo Urushalima.

An Kiyaye Idin Ƙetarewa

21 Sarki Yosiya kuwa ya umarci dukan mutane, ya ce, “Ku kiyaye Idin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku kamar yadda aka rubuta a littafin alkawari.”

22 Gama ba a ƙara kiyaye Idin Ƙetarewa ba tun daga zamanin hakimai waɗanda suka yi hukuncin Isra’ila, ko a zamanin sarakunan Isra’ila da na Yahuza,

23 sai dai a shekara ta goma sha takwas ta sarautar sarki Yosiya an kiyaye Idin Ƙetarewa ɗin nan ga Ubangiji a Urushalima.

Yosiya Ya Yi Sāke-sāke

24 Yosiya kuma ya kori dukan masu mabiya, da masu maita, da kawunan gidaje, da gumaka, da dukan abubuwa masu banƙyama da ake gani a ƙasar Yahuza, da a Urushalima, don ya sa maganar dokokin da aka rubuta a littafin da Hilkiya firist ya tarar a Haikalin Ubangiji ta kahu.

25 A gabansa, ko bayansa ba wani sarki kamarsa, wanda ya juyo ga Ubangiji da zuciya ɗaya da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa domin ya bi dukan dokokin Musa.

Fushin Ubangiji a kan Yahuza

26 Duk da haka Ubangiji bai huce daga fushinsa mai zafi da yake yi da jama’ar Yahuza ba, saboda yawan tsokanar da Manassa ya yi masa.

27 Ubangiji kuwa ya ce, “Zan kawar da jama’ar Yahuza daga gabana kamar yadda na kawar da jama’ar Isra’ila. Zan yi watsi da birnin nan da na zaɓa, wato Urushalima, da Haikalin da na ce sunana zai kasance a wurin.”

Rasuwar Yosiya

28 Sauran ayyukan Yosiya da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

29 A zamaninsa Fir’auna-neko, Sarkin Masar, ya tafi ya tasar wa Sarkin Assuriya da yaƙi a Kogin Yufiretis. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna-neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Magiddo.

30 Fādawansa kuwa suka ɗauko gawarsa a karusa daga Magiddo, suka kawo Urushalima, suka binne a kabarinsa.

Sai jama’ar ƙasa suka naɗa Yehowahaz ɗan Yosiya sarki a matsayin tsohonsa.

Sarki Yehowahaz na Yahuza

31 Yehowahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Hamutal ‘yar Irmiya na Libna.

32 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda kakanninsa suka yi.

33 Fir’auna-neko ya sa shi a kurkuku a Ribla a ƙasar Hamat, don kada ya yi mulki a Urushalima. Ya kuma sa ƙasar ta riƙa ba da gandu, wato haraji, talanti ɗari na azurfa da talanti guda na zinariya.

34 Sai Fir’auna-neko ya sarautar da Eliyakim ɗan Yosiya a matsayin tsohonsa. Ya sāke masa suna ya sa masa suna Yehoyakim. Ya ɗauki Yehowahaz ya tafi da shi Masar, can ya mutu.

35 Yehoyakim yakan ba Fir’auna azurfa da zinariya, ya kuwa sa wa ƙasar haraji don ya sami kuɗin da Fir’auna ya umarta. Ya tilasta wa kowa ya biya azurfa da zinariya bisa ga yadda ya sa masa don ya ba Fir’auna-neko.

Sarki Yehoyakim na Yahuza

36 Yehoyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan tsohuwarsa kuwa Zebida, ‘yar Fediya mutumin Ruma.

37 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda dukan kakanninsa suka yi.

Categories
2 SAR

2 SAR 24

1 A zamanin Yehoyakim ne Nebukadnezzar Sarkin Babila ya kawo wa Yahuza yaƙi, Yehoyakim kuwa ya zama baransa har shekara uku daga nan kuma ya tayar masa.

2 Ubangiji kuwa ya sa ƙungiyar maharar Kaldiyawa, da ta Suriyawa, da ta Mowabawa, da ta Ammonawa su yi gāba da Yahuza, su hallaka su bisa ga maganar Ubangiji, wadda ya faɗa wa bayinsa annabawa.

3 Hakika haka ya faru ga Yahuza bisa ga umarnin Ubangiji domin a kawar da su daga gaban Ubangiji saboda dukan zunubin Manassa da ya aikata,

4 saboda kuma marasa laifi waɗanda ya kashe, gama ya cika Urushalima da jinin marasa laifi, Ubangiji kuwa ba zai gafarta wa Manassa ba.

5 Sauran ayyukan Yehoyakim da dukan abin da ya yi an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

6 Yehoyakim ya rasu. Ɗansa Yekoniya ya gāji gadon sarautarsa.

7 Sarkin Masar kuma bai sāke fitowa daga Masar ba, gama Sarkin Babila ya ƙwace dukan ƙasar da take ta Sarkin Masar, tun daga rafin Masar har zuwa Kogin Yufiretis.

An Kama Sarki Yekoniya da Manya na Yahuza

8 Yekoniya yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Nehushta ‘yar Elnatan, mutumin Urushalima.

9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda tsohonsa ya yi.

10 A zamaninsa ne sojojin Nebukadnezzar Sarkin Babila suka zo Urushalima, suka kewaye ta da yaƙi.

11 Nebukadnezzar ya zo birnin lokacin da sojojinsa suka kewaye birnin da yaƙi.

12 Sai Yekoniya Sarkin Yahuza ya ba da kansa ga Sarkin Babila shi da tsohuwarsa, da fādawansa da hakimansa. Sarkin Babila ya kama shi yana da shekara takwas da sarautar,

13 ya kuma kwashe dukan dukiyar da take cikin Haikalin Ubangiji, da dukiyar da take cikin gidan sarki. Sai ya farfashe tasoshin zinariya da suke cikin Haikalin Ubangiji, waɗanda Sulemanu Sarkin Isra’ila, ya yi. Ya aikata abin da Ubangiji ya riga ya faɗa.

14 Nebukadnezzar ya kwashe dukan mutanen Urushalima, da dukan hakimai da dukan jarumawa, da masu sana’a, da maƙera, har sun kai dubu goma (10,000). Ba wanda ya ragu sai dai matalautan ƙasar.

15 Ya tafi da Yekoniya a Babila, shi da tsohuwarsa, da fādawansa, da masu maƙami na ƙasar.

16 Sarkin Babila ya kai kamammu Babila, wato jarumawa dubu bakwai (7,000), masu sana’a da maƙera dubu ɗaya (1,000), dukansu ƙarfafa ne, sun isa zuwa yaƙi.

17 Sai Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya naɗa Mattaniya ɗan’uwan tsohon Yekoniya sarki a maimakon Yekoniya sa’an nan ya ba shi suna Zadakiya.

Sarki Zadakiya na Yahuza

18 Zadakiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan tsohuwarsa Hamutal, ‘yar Irmiya, mutumin Libna.

19 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda Yehoyakim ya yi.

20 Ubangiji kuwa ya husata ƙwarai da mutanen Urushalima da dukan mutanen Yahuza, sai ya kore su daga gabansa.

Faɗuwar Urushalima

Zadakiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babila.

Categories
2 SAR

2 SAR 25

1 A shekara ta tara ta sarautar Zadakiya a kan rana ta goma ga watan goma, sai Nebukadnezzar Sarkin Babila, tare da sojojinsa, ya kawo wa Urushalima yaƙi. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina mata kagarai.

2 Aka kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta sarautar Zadakiya.

3 A kan rana ta tara ga watan huɗu, yunwa ta tsananta a birnin gama ba abinci domin mutanen ƙasar.

4 Sai aka huda garun birnin, sarki da mayaƙa suka tsere da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu kusa da gonar sarki, suka bi ta hanyar Araba, ko da yake Kaldiyawa suna kewaye da birnin.

5 Amma sojojin Kaldiyawa suka runtumi sarki suka kamo shi a filayen Yariko. Sojojinsa duka suka watse, suka bar shi.

6 Da suka kama sarkin, sai suka kawo shi wurin Sarkin Babila a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.

7 Aka kashe ‘ya’yansa maza a idonsa, sa’an nan aka ƙwaƙule masa idanu, aka kuma ɗaure shi da sarƙa, aka kai shi Babila.

Cin Yahuza

8 A shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar Sarkin Babila, a rana ta bakwai ga watan biyar, sai Nebuzaradan, mashawarcin sarki, shugaban sojojinsa kuma, ya shiga Urushalima.

9 Ya ƙone Haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gidajen urushalima. Ya ƙone kowane babban gida.

10 Dukan sojojin Kaldiyawa waɗanda suke tare da shugaban, suka rushe garun da yake kewaye da Urushalima.

11 Sai Nebuzaradan shugaban sojojin, ya kwashe sauran mutanen da suka ragu a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babila, da sauran da suka ragu, ya kwashe ya kai su zaman talala.

12 Amma shugaban sojojin ya bar matalautan ƙasar su zama masu gyaran inabi, da masu noma.

13 Sai Kaldiyawa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalansu, da kwatarniyar ruwa na tagullar da take cikin Haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagullar zuwa Babila.

14 Suka kuma kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da cokula, da tasoshin tagulla da ake amfani da su don hidimar Haikali.

15 Suka kuma kwashe farantan wuta da daruna. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban sojojin ya kwashe.

16 Tagullar da Sulemanu ya yi abubuwan nan da su, wato ginshiƙai biyu, da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.

17 Tsayin kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne. A kan kowane ginshiƙi akwai dajiyar tagulla, wadda tsayinta ya kai kamu uku. Akwai raga da rumman na tagulla kewaye da dajiyar.

An Kwashe Mutanen Yahuza zuwa Babila

18 Nebuzaradan kuma ya tafi da Seraiya babban firist, da Zafaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofa.

19 Daga cikin birnin kuma ya tafi da wani shugaban sojoji, da ‘yan majalisar sarki mutum biyar, da magatakardan shugaban sojoji wanda ya tattara jama’ar ƙasar, da mutum sittin na ƙasar waɗanda aka samu a birnin.

20 Nebuzaradan shugaban sojoji ya kai su wurin Sarkin Babila a Ribla ta ƙasar Hamat.

21 Sarkin Babila kuwa ya kashe su a can.

Haka aka kai mutanen Yahuza zuwa zaman talala.

Gedaliya Gwamnan Yahuza

22 A kan sauran waɗanda suka ragu a ƙasar Yahuza, waɗanda Sarkin Babila, Nebukadnezzar, ya bari, ya naɗa musu Gedaliya ɗan Ahikam, wato jikan Shafan, ya zama hakiminsu.

23 Sa’ad da shugabannin mayaƙa su da mayaƙansu suka ji Sarkin Babila ya naɗa Gedaliya ya zama hakimi, sai suka zo tare da mutanensu wurin Gedaliya a Mizfa, wato su Isma’ilu ɗan Netaniya, da Yohenan ɗan Kareya, da Seraiya ɗan Tanhumet, mutumin Netofa, da Yazaniya mutumin Ma’aka.

24 Sai Gedaliya ya rantse musu, su da mutanensu, cewa kada su ji tsoron barorin Kaldiyawa, su zauna a ƙasar, su bauta wa Sarkin Babila, haka zai fi zamar musu alheri.

25 Amma a watan bakwai, sai Isma’ilu ɗan Netaniya, wato jikan Elishama, daga gidan sarauta, ya zo tare da mutum goma ya fāda wa Gedaliya, ya kashe shi tare da Yahudawa da Kaldiyawa da suke tare da shi a Mizfa.

26 Sai dukan mutane, manya da ƙanana, da shugabannin mayaƙa, suka tashi, suka gudu zuwa Masar, gama sun ji tsoron Kaldiyawa.

An fitar da Yekoniya daga Kurkuku

27 A rana ta ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu, a shekara ta talatin da bakwai ta ɗaurin Yekoniya Sarkin Yahuda, sai Ewil-merodak da ya zama Sarkin Babila ya yi wa Yekoniya alheri, ya sake shi a shekarar da ya ci sarautar.

28 Ya yi masa magana mai kyau, ya kuma ba shi matsayi fiye da sarakunan da suke tare da shi a Babila.

29 Sai Yekoniya ya tuɓe tufafinsa na kurkuku. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har muddin ransa.

30 Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.

Categories
1 TAR

1 TAR 1

Zuriyar Nuhu

1 Adamu ya haifi Shitu, Shitu ya haifi Enosh,

2 Enosh ya haifi Kenan, Kenan ya haifi Mahalalel, Mahalalel ya haifi Yared,

3 Yared ya haifi Anuhu, Anuhu ya haifi Metusela, Metusela ya haifi Lamek.

4 Lamek ya haifi Nuhu, Nuhu ya haifi Shem, da Ham, da Yafet.

Zuriyar Yafet Nuhu

5 ‘Ya’yan Yafet, maza ke nan, Gomer, da Magog, da Madai, da Yawan, da Tubal, da Meshek, da Tiras.

6 ‘Ya’yan Gomer, maza, su ne Ashkenaz, da Rifat, da Togarma.

7 ‘Ya’yan Yawan, maza, su ne Elisha, da Tarshish, da Kittim, da Rodanim.

Zuriyar Ham

8 ‘Ya’yan Ham, maza, su ne Kush, da Mizrayim, da Fut, da Kan’ana.

9 ‘Ya’yan Kush, maza, su ne Seba, da Hawila, da Sabta, da Ra’ama, da Sabteka. ‘Ya’yan Ra’ama, maza, su ne Sheba da Dedan.

10 Kush shi ne mahaifin Lamirudu wanda shi ne ya fara ƙasaita a duniya.

11 Mizrayim shi ne mahaifin jama’ar Ludawa, da Anamawa, da Lehabawa, da Naftuhawa,

12 da Fatrusawa, da Kasluhawa tushen Filistiyawa ke nan, da Kaftorawa.

13 Kan’ana shi ne mahaifin Sidon ɗan farinsa, da Het,

14 da Yebusiyawa, da Amoriyawa, da Girgashiyawa,

15 da Hiwiyawa, da Arkiyawa, da Siniyawa,

16 da Arwadiyawa, da Zemariyawa, da Hamatiyawa.

Zuriyar Shem

17 ‘Ya’yan Shem, maza, su ne Elam, da Asshur, da Arfakshad, da Lud, da Aram, da Uz, da Hul, da Geter, da Meshek.

18 Arfakshad shi ne mahaifin Shela, Shela kuma shi ne mahaifin Eber.

19 ‘Ya’ya biyu maza ne aka haifa wa Eber. Sunan ɗayan Feleg, saboda a lokacinsa ne aka karkasa duniya, sunan ɗan’uwansa kuwa Yokatan.

20 Yokatan shi ne mahaifin Almoda, da Shelef, da Hazarmawet, da Yera,

21 da Adoniram, da Uzal, da Dikla,

22 da Ebal, da Abimayel, da Sheba,

23 da Ofir, da Hawila, da Yobab. Waɗannan duka su ne ‘ya’yan Yokatan, maza.

24 Shem ya haifi Arfakshad, Arfakshad ya haifi Shela,

25 Shela ya haifi Eber, Eber ya haifi Feleg, Feleg ya haifi Reyu,

26 Reyu ya haifi Serug, Serug ya haifi Nahor, Nahor ya haifi Tera,

27 Tera ya haifi Abram, wato Ibrahim ke nan.

Zuriyar Isma’ilu da Ketura

28 ‘Ya’yan Ibrahim, maza, su ne Ishaku da Isma’ilu.

29 Ga zuriyarsu. Nabayot shi ne ɗan farin Isma’ilu, sa’an nan sai Kedar, da Abdeyel, da Mibsam,

30 da Mishma, da Duma, da Massa, da Hadad, da Tema,

31 da Yetur, da Nafish, da Kedema. Waɗannan su ne ‘ya’yan Isma’ilu, maza.

32 ‘Ya’ya maza na Ketura, wato ƙwarƙwarar Ibrahim, su ne Zimran, da Yokshan, da Medan, da Madayana, da Yisbak, da Shuwa. ‘Ya’yan Yokshan, maza, su ne Sheba, da Dedan.

33 ‘Ya’yan Madayana, maza, su ne Efa, da Efer, da Hanok, da Abida, da Eldaya. Waɗannan duka su ne ‘ya’yan Ketura, maza.

Zuriyar Isuwa

34 Ibrahim shi ne mahaifin Ishaku. ‘Ya’yan Ishaku, maza, su ne Isuwa da Isra’ila.

35 ‘Ya’yan Isuwa, maza, su ne Elifaz, da Reyuwel, da Yewush, da Yalam da Kora.

36 ‘Ya’yan Elifaz, maza, su ne Teman, da Omar, da Zeho, da Gatam, da Kenaz, da Tima, da Amalek.

37 ‘Ya’yan Reyuwel, maza kuwa, su ne Nahat, da Zera, da Shamma, da Mizza.

38 ‘Ya’yan Seyir, maza kuma, su ne Lotan, da Shobal, da Zibeyon, da Ana, da Dishon, da Ezer, da kuma Dishan.

39 ‘Ya’yan Lotan, maza, su ne Hori, da Hemam. Timna ce ‘yar’uwar Lotan.

40 ‘Ya’yan Shobal, maza, su ne Alwan, da Manahat, da Ebal, da Sheho, da Onam.

‘Ya’yan Zibeyon, maza su ne Aiya da Ana.

41 Dishon shi ne ɗan Ana. ‘Ya’yan Dishon, maza kuwa, su ne Hemdan, da Eshban, da Yitran, da Keran.

42 ‘Ya’yan Ezer, maza, su ne Bilhan, da Zayawan, da Akan. ‘Ya’yan Dishan, maza, su ne Uz da Aran.

43-50 Waɗannan su ne sarakunan da suka yi sarauta a ƙasar Edom kafin wani Sarkin Isra’ila ya ci sarauta.

Bela ɗan Beyor, sunan birninsa kuwa Dinhaba

Yobab ɗan Zera na Bozara

Husham na ƙasar Teman

Hadad ɗan Bedad na Awit, wanda ya kori Madayanawa a filin Mowab

Samla na Masrek

Shawul na Rehobot wadda take bakin Kogin Yufiretis

Ba’al-hanan ɗan Akbor

Hadad na Fau, sunan matarsa kuma Mehetabel ‘yar Matred, wato jikar Mezahab

51 Hadad kuwa ya rasu. Sarakunan Edom su ne Timna, da Alwa, da Yetet,

52 da Oholibama, da Ila, da Finon,

53 da Kenaz, da Teman, da Mibzar,

54 da Magdiyel, da Iram.

Categories
1 TAR

1 TAR 2

‘Ya’yan Isra’ila

1 Waɗannan su ne ‘ya’yan Isra’ila, maza, Ra’ubainu, da Saminu, da Lawi, da Yahuza, da Issaka, da Zabaluna,

2 da Dan, da Yusufu, da Biliyaminu, da Naftali, da Gad, da Ashiru.

Zuriya Yahuza

3 ‘Ya’yan Yahuza, maza, su ne Er, da Onan, da Shela. Waɗannan uku Batshuwa Bakan’aniya, ita ce ta haifa masa su. Amma Er, ɗan farin Yahuza, mugu ne a gaban Ubangiji, don haka Ubangiji ya kashe shi.

4 Surukarsa Tamar, matar ɗansa kuma ta haifa masa Feresa da Zera. Yahuza yana da ‘ya’ya maza biyar.

5 ‘Ya’yan Feresa, maza kuwa, su ne Hesruna da Hamul.

6 ‘Ya’yan Zera, maza, su ne Zabdi da Etan, da Heman, da Kalkol, da Darda. Su biyar ke nan.

7 Karmi shi ne mahaifin Akan wanda ya jawo wa Isra’ila wahala a kan abin da aka haramta.

8 Etan yana da ɗa guda ɗaya, shi ne Azariya.

9 ‘Ya’yan Hesruna, maza, waɗanda aka haifa masa, su ne Yerameyel, da Arama, da kuma Kalibu.

10 Arama shi ne mahaifin Amminadab. Amminadab kuma shi ne mahaifin Nashon, shugaban ‘ya’yan Yahuza.

11 Nashon shi ne mahaifin Salmon. Salmon kuwa shi ne mahaifin Bo’aza.

12 Bo’aza kuma shi ne mahaifin Obida. Obida shi ne mahaifin Yesse.

13 Yesse shi ne mahaifin Eliyab ɗan farinsa, sa’an nan sai Abinadab da Shimeya,

14 da Netanel, da Raddai,

15 da Ozem, da Dawuda. Su ‘ya’ya maza bakwai ke nan.

16 ‘Yan’uwansu mata kuwa su ne Zeruya da Abigail.

‘Ya’yan Zeruya, maza, su ne Abishai, da Yowab, da Asahel, su uku ke nan.

17 Abigail ta haifi Amasa. Mahaifin Amasa shi ne Yeter daga zuriyar Isma’ilu.

18 Azuba, matar Kalibu ɗan Hesruna ta haifa masa ‘ya’ya maza. Matarsa Yeriyot kuma ta haifi ‘ya’ya maza, su ne Yesher, da Shobab, da Ardon.

19 Sa’ad da Azuba ta rasu sai Kalibu ya auri Efrata wadda ta haifa masa Hur.

20 Hur shi ne mahaifin Uri, Uri kuwa shi ne mahaifin Bezalel.

21 Bayan haka sai Hesruna ya shiga wurin ‘yar Makir mahaifin Gileyad, wadda ya aura sa’ad da yake da shekara sittin da haihuwa. Ta haifa masa Segub.

22 Segub shi ne mahaifin Yayir wanda yake da birane ashirin da uku a ƙasar Gileyad.

23 Amma sai Geshur da Aram suka ƙwace garuruwan Hawwotyayir ɗin daga gare su, har da Kenat da ƙauyukanta, garuruwa sittin. Duk waɗannan su ne zuriyar Makir mahaifin Gileyad.

24 Bayan rasuwar Hesruna, Abaija, matarsa, ta haifa masa Ashur, mahaifin Tekowa.

25 ‘Ya’yan Yerameyel ɗan farin Hesruna, su ne Arama ɗan fari, sa’an nan Buna, da Oren, da Ozem, da Ahaija.

26 Sai Yerameyel ya auro wata mace, sunanta Atara. Ita ce mahaifiyar Onam.

27 ‘Ya’yan Arama, ɗan farin Yerameyel, su ne Ma’az, da Yamin, da Eker.

28 ‘Ya’yan Onam, maza, su ne Shammai da Yada. ‘Ya’yan Shammai, maza, su ne Nadab da Abishur.

29 Sunan matar Abishur Abihail, ta haifa masa Aban da Molid.

30 ‘Ya’yan Nadab, maza, su ne Seled da Affayim, amma Seled ya rasu bai bar ‘ya’ya ba.

31 Ɗan Affayim shi ne Ishi. Ɗan Ishi kuwa shi ne Sheshan. Ɗan Sheshan shi ne Alai.

32 ‘Ya’yan Yada, maza, ɗan’uwan Shammai, su ne Yeter da Jonatan. Amma Yeter ya rasu bai bar ‘ya’ya ba.

33 ‘Ya’yan Jonatan su ne Felet da Zaza. Waɗannan su ne zuriyar Yerameyel.

34 Sheshan ba shi da ‘ya’ya maza, sai dai ‘ya’ya mata. Amma yana da wani bara Bamasare mai suna Yarha.

35 Sai Sheshan ya aurar wa Yarha baransa da ‘yarsa, ita kuwa ta haifar masa Attai.

36 Attai shi ne mahaifin Natan, Natan kuma shi ne mahaifin Zabad.

37 Zabad kuwa shi ne mahaifin Eflal, Eflal shi ne ya haifi Obida.

38 Obida shi ne mahaifin Yehu, Yehu kuma shi ne mahaifin Azariya.

39 Azariya shi ne mahaifin Helez, Helez shi ne mahaifin Eleyasa.

40 Eleyasa shi ne mahaifin Sisamai, Sisamai shi ne mahaifin Shallum.

41 Shallum shi ne mahaifin Yekamiya, Yekamiya shi ne mahaifin Elishama.

42 Ɗan Kalibu, ɗan’uwan Yerameyel, shi ne Mesha ɗan farinsa wanda ya haifi Zif. Zif ya haifi Maresha wanda ya haifi Hebron.

43 ‘Ya’yan Hebron, maza, su ne Kora, da Taffuwa, da Rekem, da Shema.

44 Shema shi ne mahaifin Raham wanda ya kafa Yorkeyam. Rekem kuwa shi ne mahaifin Shammai.

45 Shammai shi ne mahaifin Mayon, Mayon kuwa shi ne mahaifin Bet-zur.

46 Efra ƙwarƙwarar Kalibu, ta haifi Haran, da Moza, da Gazez. Haran shi ne mahaifin Gazez.

47 ‘Ya’yan Yadai, maza, su ne Regem, da Yotam, da Geshan, da Felet, da Efa, da Sha’af.

48 Ma’aka, ƙwarƙwarar Kalibu, ta haifi Sheber da Tirhana.

49 Ta kuma haifi Sha’af mahaifin Madmanna, da Shewa mahaifin Makbena, da mahaifin Gibeya.

‘Yar Kalibu ita ce Aksa.

50 Waɗannan su ne zuriyar Kalibu, maza.

‘Ya’yan Hur, maza, wato ɗan farin Efrata, su ne Shobal wanda ya kafa Kiriyat-yeyarim,

51 da Salma, shi kuwa ya kafa Baitalami, da Haref ɗansa kuma wanda ya kafa Bet-gader.

52 Shobal yana da waɗansu ‘ya’ya maza, su ne Rewaiya da wanda yake kakan rabin Manahatiyawa,

53 da iyalan da suke a Kiriyat-yeyarim, da na Itiriyawa, da na Futiyawa, da na Shumatiyawa, da na Mishraiyawa. Daga waɗannan ne Zoratiyawa da Eshtawoliyawa suka fito.

54 Salma, wanda ya kafa Baitalami, shi ne kakan mutanen Netofa, da na Atarot-bet-yowab, da rabin Manahatiyawa, da Zoratiyawa.

55 Iyalan gwanayen rubutu waɗanda suka zauna a Yabez, su ne Tiratiyawa, da Shimeyatiyawa, da Sukatiyawa. Su ne Keniyawa na Hammat, Hammat kuwa shi ne mahaifin mutanen Rekab.