Categories
2 TAR

2 TAR 14

Sarki Asa na Yahuza

1 Sarki Abaija kuwa ya rasu, suka binne shi tare da kakanninsa a birnin Dawuda. Ɗansa Asa shi ya gāji gadon sarautarsa. Ƙasar ta sami sakewa har shekara goma a zamaninsa.

2 Asa ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa.

3 Ya kawar da baƙin bagadai da masujadai, ya rurrushe ginshiƙai, ya kuma tumɓuke Ashtarot.

4 Ya umarci Yahuza su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, su kiyaye doka, da umarni.

5 Daga cikin dukan biranen Yahuza, ya kawar da masujadai da bagadan ƙona turare. A zamaninsa an sami zaman lafiya a mulkinsa.

6 Ya giggina birane masu kagara a Yahuza, gama ƙasar tana zaman lafiya. A waɗannan shekaru bai yi yaƙi da kowa ba, saboda Ubangiji ya kawo masa salama.

7 Sai ya ce wa mutanen Yahuza, “Bari mu giggina waɗannan birane, mu kewaye su da garu, da hasumiya, da ƙofofi masu ƙyamare. Ƙasar tamu ce har yanzu, saboda mun nemi Ubangiji Allahnmu. Mun neme shi, ya kuwa ba mu salama a kowace fuska.” Suka yi ta gini, suka kuwa arzuta.

8 Sarki Asa kuwa yana da soja dubu ɗari uku (300,000) a Yahuza, ko wanne yana da kutufani da māshi, yana da soja dubu ɗari biyu da dubu tamanin (280,000) daga Biliyaminu, ‘yan baka ko wanne da garkuwarsa. Dukansu manyan jarumawa ne.

9 Sai Zera mutumin Habasha ya zo da soja zambar dubu (1,000,000) da karusa ɗari uku har Maresha, don ya yi yaƙi da su.

10 Don haka sai Asa ya fito ya gamu da shi, suka kuwa jā dāga a kwarin Zefata a Maresha.

11 Asa kuwa ya yi kuka ga Ubangiji Allahnsa, ya ce, “Ya Ubangiji, ba wani mai taimako kamarka, wanda zai yi taimako sa’ad da mai ƙarfi zai kara da marar ƙarfi, ka taimake mu, ya Ubangiji Allahnmu, gama a gare ka muke dogara, da sunanka kuma muka zo don mu yi yaƙi da wannan babbar runduna. Ya Ubangiji, kai ne Allahnmu, kada ka bar mutum ya rinjayi jama’arka.”

12 Ubangiji kuwa ya fatattaki Habashawa a gaban Asa da Yahuza, Habashawa kuwa suka gudu.

13 Sai Asa da jama’ar da suke tare da shi, suka runtume su har zuwa Gerar. Habashawa suka fāɗi duka, ko ɗaya, ba wanda ya ragu da rai, gama an ragargaza su a gaban Ubangiji da gaban sojojin. Mutane suka kwashe ganima mai yawa gaske.

14 Suka hallaka dukan birane da suke kewaye da Gerar, gama tsoron Ubangiji ya kama su. Suka washe dukan biranen, gama biranen suna cike da ganima.

15 Suka kware alfarwan masu kiwon dabbobi, suka kora tumaki, da raƙuma masu yawan gaske. Sa’an nan suka komo Urushalima.

Categories
2 TAR

2 TAR 15

Gyare-gyaren da Asa Ya Yi

1 Ruhun Allah kuwa ya sauko a kan Azariya ɗan Oded,

2 sai ya fita ya taryi Asa, ya ce masa, “Ka ji ni, ya Asa, kai da dukan Yahuza da Biliyaminu, Ubangiji yana tare da ku idan kuna tare da shi. Idan kuwa kun neme shi, za ku same shi, amma idan kun rabu da shi, shi ma zai rabu da ku.

3 Isra’ila kuwa ta daɗe ba ta bin Allah na gaskiya, ba ta da firist mai koya mata, ba ta kuma bin shari’a.

4 Amma lokacin da suke shan wahala suka juyo ga Ubangiji Allah na Isra’ila, suka neme shi, suka same shi.

5 A waɗancan lokatai, ba salama ga mai fita ko ga mai shiga, gama babban hargitsi ya wahalar da dukan mazaunan ƙasashe.

6 An kacancana su, al’umma tana gāba da al’umma, birni kuma gāba da birni, gama Allah ya yi ta wahalshe su da kowace irin wahala.

7 Amma ku sai ku yi ƙarfin hali, kada ku firgita, gama za a ba ku ladan aikinku.”

8 Da Asa ya ji irin kalmomin da annabi Azariya ɗan Oded ya hurta, sai ya yi ƙarfin zuciya, ya kawar da gumakan nan masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuza da ta Biliyaminu, daga kuma biranen da ya ci a ƙasar tuddai na Ifraimu. Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji wanda yake a ƙofar shirayin Haikalin Ubangiji.

9 Sai ya tattara dukan mutanen Yahuza da na Biliyaminu, da kuma na Ifraimu, da na Manassa, da na Saminu, waɗanda suke zaman baƙunci tare da su. Da yawa daga cikin Isra’ilawa suka yi ƙaura zuwa wurinsa, sa’ad da suka ga Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.

10 Suka taru a Urushalima a wata na uku na shekara ta goma sha biyar ta sarautar Asa.

11 A ran nan suka miƙa wa Ubangiji hadayun bijimai ɗari bakwai, da tumaki dubu bakwai (7,000) daga cikin ganimar da suka kwaso.

12 Sai suka ƙulla alkawari, cewa za su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu da dukan zuciyarsu da ransu.

13 Duk wanda kuma bai nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila ba, za a kashe shi, ko yaro ko babba, ko mace ko namiji.

14 Sai suka rantse wa Ubangiji da murya mai ƙarfi, suna sowa, suna busa kakaki da ƙaho.

15 Dukan Yahuza ta yi murna saboda rantsuwar, gama da zuciya ɗaya suka rantse, suka kuwa neme shi da iyakar aniya, sun kuwa same shi. Don haka Allah ya hutasshe su a kowane al’amari.

16 Asa kuma ya tuɓe tsohuwarsa, Ma’aka, daga matsayinta na sarauniya don ta ƙera wata siffa mai banƙyama ta Ashtoret. Sai Asa ya sare siffar nan, ya niƙe ta, ya ƙone a rafin Kidron.

17 Amma ba a kawar da masujadan da yake Isra’ila ba, duk da haka zuciyar Asa sarai take, ba wani aibi duk kwanakinsa.

18 Sai ya shigar da sadakar da shi da tsohonsa suka keɓe don Haikalin Ubangiji, wato azurfa, da zinariya, da kwanoni da tasoshi, da finjalai iri iri.

19 Ba a kuma ƙara yin wani yaƙi ba har shekara ta talatin da biyar ta mulkinsa Asa.

Categories
2 TAR

2 TAR 16

Asa ya Haɗa Kai da Ben-hadad

1 A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, sai Ba’asha, Sarkin Isra’ila, ya haura ya fāɗa wa Yahuza da yaƙi, ya gina Rama don ya hana kowa fita, ko shiga wurin Asa, Sarkin Yahuza.

2 Sa’an nan Asa ya ɗebo azurfa da zinariya daga dukiyar da take cikin Haikalin, da na fādar sarki, ya aika wa Ben-hadad da su, wato Sarkin Suriya, wanda yake zaune a Dimashƙu, yana cewa,

3 “Bari mu haɗa kai, da ni da kai kamar yadda ubana da naka suka yi. Ga shi, na aika maka da azurfa da zinariya. Ka tafi ka warware haɗa kan da yake tsakaninka da Ba’asha, Sarkin Isra’ila, don ya janye ya rabu da ni.”

4 Ben-hadad kuwa ya kasa kunne ga sarki Asa, ya aika da shugabannin rundunan sojojinsa suka yi yaƙi da biranen Isra’ila. Suka ci Iyon, da Dan, da Abel-bet-ma’aka, da dukan biranen ajiya na Naftali.

5 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina gina Rama, ya bar aikin da yake yi.

6 Sa’an nan sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuza, suka kwashe duwatsun da katakan da Ba’asha yake gina Rama da su, ya gina Geba da Mizfa da su.

Annabi Hanani

7 A lokacin nan sai Hanani, maigani, ya zo wurin Asa, Sarkin Yahuza, ya ce masa, “Da yake ka dogara ga Sarkin Suriya, maimakon ka dogara ga Ubangiji Allahnka, shi ya sa rundunar sojojin Sarkin Suriya ta kuɓuta daga hannunka.

8 Ai, Habashawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da karusai da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, sai ya bashe su a hannunka.

9 Idon Ubangiji fa, yana kai da komowa ko’ina a duniya don ya nuna ikonsa ga dukan waɗanda suka dogara gare shi da zuciya ɗaya. Ka yi wauta a cikin wannan al’amari. Tun daga yanzu har zuwa nan gaba za ka yi ta fama da yaƙoƙi.”

10 Sai Asa ya yi fushi da maiganin, ya sa shi a kurkuku saboda maganar da ya yi masa, gama ya husata da shi ƙwarai. A wannan lokaci kuma sai Asa ya ƙuntata wa waɗansu daga cikin jama’a.

Ƙarshen Mulkin Asa

11 Ayyukan Asa, daga farko har zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuza da na Isra’ila.

12 A shekara ta talatin da tara ta mulkin Asa, sai wani ciwo ya kama shi a ƙafa. Ciwon kuwa ya tsananta ƙwarai, duk da haka Asa bai nemi taimakon Ubangiji ba, sai na magori.

13 Asa fa ya rasu bayan shekara biyu da ciwon, a shekara ta arba’in da ɗaya ta mulkinsa.

14 Aka binne shi a kabarin da shi da kansa ya haƙa a birnin Dawuda. Aka sa shi a makara wadda aka cika da kayan ƙanshi da na turare yadda gwanayen aikin turare suka shirya, suka hura babbar wuta don su darajanta shi.

Categories
2 TAR

2 TAR 17

Mulkin Yehoshafat ya Kahu

1 Yehoshafat ɗansa kuwa ya gāji gadon sarautarsa, ya kahu sosai gāba da Isra’ila.

2 Ya sa sojoji a kowane birni mai kagara a Yahuza, ya kuma sa ƙungiyoyin sojoji masu tsaro a ƙasar Yahuza, da kuma a biranen Ifraimu waɗanda tsohonsa Asa ya ci da yaƙi.

3 Ubangiji kuwa yana tare da Yehoshafat saboda ya bi halin tsohonsa da ya yi da fari, bai kuwa nemi Ba’al ba.

4 Ya nemi Allah na ubansa, ya bi umarnansa. Bai bi halin Isra’ila ba.

5 Saboda haka ne Ubangiji ya ba shi ikon riƙon wannan mulki. Yahuza duka kuwa ta kawo wa Yehoshafat haraji, ya kuwa zama riƙaƙƙen mai dukiya, wanda kuma ake girmamawa.

6 Zuciyarsa ta ƙarfafa cikin al’amuran Ubangiji. Ya kawar da masujadai, da Ashtarot daga ƙasar Yahuza.

7 A shekara ta uku ta sarautarsa, sai ya aika da ma’aikatansa, su Ben-hail, da Obadiya, da Zakariya, da Netanel, da kuma Mikaiya don su yi koyarwa a biranen Yahuza.

8 Tare da su kuma akwai Lawiyawa, da Shemaiya, da Netaniya, da Zabadiya, da Asahel, da Shemiramot, da Jonatan, da Adonaija, da Tobiya, da Tob-adonaija, tare da waɗannan Lawiyawa akwai firistoci, Elishama da Yehoram.

9 Suka koyar a Yahuza, suna tare da Littafin Shari’ar Ubangiji, wato Attaura. Suka shiga ko’ina a biranen Yahuza suka koyar da jama’a.

Gawurtar Yehoshafat

10 Tsoron Ubangiji kuwa ya kama dukan mulkokin ƙasashen da suke kewaye da Yahuza, har ba su iya fāɗa wa Yehoshafat da yaƙi ba.

11 Sai waɗansu daga cikin Filistiyawa suka kawo wa Yehoshafat kyautai da azurfa domin haraji. Larabawa ma suka kawo masa raguna dubu bakwai da ɗari bakwai (7,700), da bunsurai dubu bakwai da ɗari bakwai (7,700).

12 Yehoshafat ya daɗa ƙasaita, ya giggina kagarai, da biranen ajiya a Yahuza.

13 Yana kuwa da manya manyan wuraren ajiya a biranen Yahuza.

Yana kuma da gwarzayen sojoji masu yawa a Urushalima.

14 Ga jimillar sojojin bisa ga gidajen kakanninsu. Na Yahuza mai shugabannin dubu dubu, shugaba Adana yana shugabancin sojoji dubu ɗari uku (300,000) gwarzaye.

15 Mai bi masa, sai shugaba Yehohanan yana shugabancin sojoji dubu ɗari biyu da dubu tamanin (280,000).

16 Mai biye da Yehohanan kuma shi ne shugaba Amasiya, ɗan Zikri, wanda ya ba da kansa don bauta wa Ubangiji, shi kuma yana shugabancin sojoji dubu ɗari biyu (200,000) gwarzaye.

17 Na Biliyaminu kuma sarkin yaƙi shi ne Eliyada, gwarzo ne, yana shugabancin sojoji dubu ɗari biyu (200,000), ‘yan baka da garkuwa.

18 Na biye da Eliyada kuma shi ne shugaba Yehozabad wanda yake da sojoji dubu ɗari da dubu tamanin (180,000) shirayayyu don gabza yaƙi.

19 Waɗannan suke yi wa sarki hidima, banda waɗanda sarki ya sa a birane masu kagara ko’ina a Yahuza.

Categories
2 TAR

2 TAR 18

Annabi Mikaiya Ya Gargaɗi Ahab

1 Yehoshafat ya arzuta, ya kuma sami ɗaukaka sai ya yi ma’amala da Ahab ta wurin aurayya.

2 Bayan ‘yan shekaru sai ya kai wa Ahab ziyara a Samariya. Ahab kuwa ya yanka tumaki masu yawan gaske, da bijimai da yawa, domin Yehoshafat da mutanen da suke tare da shi. Ahab ya rinjaye shi don su fāɗa wa Ramot-gileyad da yaƙi.

3 Sai Ahab, Sarkin Isra’ila, ya ce wa Yehoshafat, Sarkin Yahuza, “Za ka tafi tare da ni zuwa Ramot-gileyad?”

Sai ya amsa, ya ce, “Ni ma kamarka ne, jama’ata kuma kamar jama’arka ce, za mu je yaƙin tare da kai.”

4 Yehoshafat kuma ya ce wa Sarkin Isra’ila, “Sai ka nemi faɗar Ubangiji tukuna.”

5 Ahab kuwa ya tattara annabawa, mutum ɗari huɗu, ya ce musu, “Mu je mu faɗa wa Ramot-gileyad da yaƙi, ko in haƙura?”

Sai suka ce, “Ka tafi, gama Allah zai ba da ita a hannun sarki.”

6 Amma Yehoshafat ya ce, “Ba wani annabin Ubangiji a nan wanda za mu tambaye shi kuma?”

7 Sai Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Akwai sauran mutum guda wanda za mu iya neman nufin Ubangiji daga gare shi, shi ne Mikaiya, ɗan Imla, amma na ƙi shi saboda ba ya yin annabcin kirki a kaina, sai dai na rashin alheri kullum.”

Amma Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya faɗi haka.”

8 Sa’an nan Sarkin Isra’ila ya kira wani jarumi ya ce masa, “Maza ka kawo Mikaiya ɗan Imla.”

9 A sa’an nan Sarkin Isra’ila, da Yehoshafat, Sarkin Yahuza, suna zaune kowa a gadon sarautarsa, kowane ya caɓa ado, suna kuwa zaune a filin da yake ƙofar Samariya. Dukan annabawa kuwa suna ta yin annabci a gabansu.

10 Sai Zadakiya ɗan Kena’ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Suriyawa har su hallaka!’ ”

11 Dukan annabawa kuma suka yi annabci, suna cewa, “Ka haura zuwa Ramot-gileyad ka ci nasara, gama Ubangiji zai ba da ita a hannun sarki.”

12 Jarumin fa da ya je ya kira Mikaiya ɗin, ya ce masa, “Ka kula fa, dukan maganganun da annabawa suke yi, sun yi wa sarki daɗi. Don haka kai ma ka yi maganar da za ta gamshi sarki kamar yadda suka yi.”

13 Amma Mikaiya ya ce, “Na rantse da Ubangiji abin da Allahna ya faɗa mini, shi zan faɗa.”

14 Da Mikaiya ya zo gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Mikaiya, mu haura zuwa Ramot-gileyad mu fāɗa mata da yaƙi, ko in haƙura?”

Mikaiya kuwa ya amsa, ya ce, “Ka haura, gama za ka ci nasara, gama za a bashe su a hannunka.”

15 Amma sarki ya ce masa, “Har sau nawa zan rantsar da kai don kada ka faɗa mini kome, sai gaskiya da sunan Ubangiji?”

16 Mikaiya kuwa ya ce, “Ina ganin dukan Isra’ilawa a warwatse bisa tsaunuka, kamar tumakin da ba su da makiyayi. Ubangiji kuma ya ce, ‘Waɗannan ba su da makiyayi, bari dukansu, kowa ya koma gidansa da salama.’ ”

17 Sarkin Isra’ila fa ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka ba, cewa ba zai yi annabcin alheri game da ni ba, sai na rashin alheri?”

18 Sai Mikaiya ya ce, “Ji maganar Ubangiji, na ga Ubangiji yana zaune a bisa kursiyinsa, dukan rundunan sama suna tsaye dama da shi da hagu da shi.

19 Sai Ubangiji ya ce, ‘Wa zai ruɗi Ahab, Sarkin Isra’ila, don ya haura zuwa Ramot-gileyad ya fāɗi?’ Sai wannan ya faɗi abu kaza, wancan kuma ya faɗi abu kaza.

20 Sai wani ruhu ya zo ya tsaya a gaban Ubangiji, ya ce, ‘Ni zan ruɗe shi.’ Sai Ubangiji ya ce masa, ‘Ta ƙaƙa?’

21 Sai ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakin dukan annabawansa.’ Sa’an nan Ubangiji ya ce, ‘To, za ka ruɗe shi har ka yi nasara. Je ka, ka yi haka nan.’

22 “Saboda haka Ubangiji ya sa ruhun ƙarya a bakunan annabawanka, gama Ubangiji ya faɗa, masifa za ta same ka.”

23 Sai Zadakiya ɗan Kena’ana, ya matso ya mari Mikaiya a kumatu ya ce, “Ta wace hanya ruhun Ubangiji ya fita daga gare ni ya zo ya yi magana da kai.”

24 Mikaiya kuwa ya ce, “Za ka gani a ranar da ka shiga ƙuryar ɗaki na can ciki don ɓuya.”

25 Sai Sarkin Isra’ila ya ce, “Ku kama Mikaiya, ku komar da shi wurin Amon mai mulkin birnin, da yarima Yowash.

26 Ku ce, ‘Sarki ya ce ku sa wannan mutum a kurkuku, ku ciyar da shi da ɗan abinci da ruwa kaɗan har in komo lafiya.’ ”

27 Sai Mikaiya ya ce, “Idan har ka komo lafiya, wato Ubangiji bai yi magana da ni ba ke nan.” Sai ya ce, “Ku ji, ya ku jama’a duka.”

Mutuwar Ahab

28 Sarkin Isra’ila fa, da Yehoshafat Sarkin Yahuza, suka haura zuwa Ramot-gileyad.

29 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama, in shiga yaƙi, amma kai, sai ka sa rigunanka.” Sarkin Isra’ila kuwa ya ɓad da kama, suka shiga yaƙi.

30 Sarkin Suriya ya umarci shugabannin karusansa, ya ce, “Kada ku yi yaƙi da yaro ko babba, sai dai da Sarkin Isra’ila, shi kaɗai.”

31 Sa’ad da shugabannin karusai suka ga Yehoshafat, suka ce, “Wannan ne Sarkin Isra’ila,” sai suka juya suka yi yaƙi da shi. Amma Yehoshafat ya yi kururuwa, Ubangiji Allah ya kuɓutar da shi, Allah kuwa ya kawar da su daga gare shi.

32 Da shugabannin karusai suka ga, ashe, ba Sarkin Isra’ila ba ne, sai suka daina binsa suka juyo.

33 Amma wani mutum ya harba kibiya haka kawai, ya sami Sarkin Isra’ila a mahaɗin kafaɗa. Sai sarkin ya ce wa wanda yake korar karusarsa, “Juya ka fitar da ni daga wurin yaƙin, gama an yi mini rauni.”

34 Ran nan yaƙin ya tsananta, Sarkin Isra’ila kuma ya jingina a cikin karusarsa, yana fuskantar Suriyawa har maraice, rana na fāɗuwa yana rasuwa.

Categories
2 TAR

2 TAR 19

Annabi Yehu Ya Tsauta wa Yehoshafat

1 Yehoshafat Sarkin Yahuza ya koma gidansa a Urushalima lafiya.

2 Sai Yehu maigani, ɗan Hanani, ya fita domin ya tarye shi, ya ce wa sarki Yehoshafat, “Za ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci maƙiyan Ubangiji? Saboda haka hasalar Ubangiji za ta same ka.

3 Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da gumakan Ashtarot daga ƙasar, ka sa zuciyarka ga neman Allah.”

Yehoshafat Ya Zaɓi Alƙalai

4 Yehoshafat ya yi zamansa a Urushalima, ya sāke shiga jama’a, tun daga Biyer-sheba har zuwa ƙasar tuddai ta Ifraimu, ya komar da su zuwa wurin Ubangiji, Allah na kakanninsu.

5 Sai ya naɗa alƙalai a ƙasar, a dukan biranen Yahuza masu kagara, birni birni.

6 Sai ya ce wa alƙalan, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.

7 Yanzu fa ku yi tsoron Ubangiji. Ku lura da abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu bai yarda da rashin yin adalci ba, ko son zuciya, ko karɓar rashawa.”

8 Yehoshafat kuma ya naɗa waɗansu Lawiyawa, da firistoci, da waɗansu shugabannin iyalan Isra’ilawa, saboda su yi shari’a tsakani da Ubangiji, su daidaita tsakanin masu jayayya. A Urushalima za su zauna.

9 Sai ya umarce su ya ce, “Haka za ku yi saboda tsoron Ubangiji, ku yi aminci, ku yi da zuciya ɗaya kuma.

10 A duk lokacin da ‘yan’uwanku daga birane suka kawo muku maganar wata shari’a, wadda ta shafi zub da jini, ko karya shari’a, ko umarni, ko dokoki, ko farillai, sai ku koya musu, don kada su aikata laifi a gaban Ubangiji, don kada hasala ta same ku, ku da ‘yan’uwanku. Abin da za ku yi ke nan, don kada ku yi laifi.

11 Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji. Zabadiya, ɗan Isma’ilu mai mulkin gidan Yahuza, shi ne shugabanku a kan dukan al’amuran da suke na wajen sarki. Lawiyawa kuwa su zama muhimman ma’aikatanku. Kada ku ji tsoro a cikin aikinku, Ubangiji kuwa ya kasance tare da masu gaskiya.”

Categories
2 TAR

2 TAR 20

Yaƙi da Mowab, da Ammon, da Edom

1 Bayan wannan sai mutanen Mowab, da mutanen Ammon, tare da waɗansu daga cikin Me’uniyawa, suka zo su yi yaƙi da Yehoshafat.

2 Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat cewa, “Mutane masu yawan gaske suna zuwa su yi yaƙi da kai daga Edom, da kuma teku, har sun iso Hazazon-tamar,” wato En-gedi.

3 Sai Yehoshafat ya ji tsoro ya himmatu ga neman Ubangiji, ya kuma sa a yi shela, a yi azumi a dukan Yahuza.

4 Yahuza suka tattaru don su nemi taimako daga wurin Ubangiji. Daga cikin dukan biranen Yahuza, mutane suka zo don su nemi Ubangiji.

5 Sai Yehoshafat ya tsaya a gaban taron jama’ar Yahuza da na Urushalima, a Haikalin Ubangiji, a gaban sabuwar farfajiya,

6 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na kakanninmu, kai ne Allah na cikin Sama, kai ne kuma kake mulkin dukan al’umman duniya. A gare ka iko da ƙarfi suke, don haka ba wanda ya isa ya jā da kai.

7 Ya Allahnmu, kai ne ka kori jama’ar ƙasan nan a gaban jama’arka Isra’ila, ka kuma ba da ita har abada ga zuriya masoyinka Ibrahim.

8 Suka kuwa zauna a cikinta, suka gina Wuri Mai Tsarki saboda sunanka cewa,

9 ‘Idan wani mugun abu ya same mu, kamar takobi, ko hukunci, ko annoba, ko yunwa, to, za mu tsaya a gaban wannan gida, a gabanka kuma, gama sunanka yana cikin gidan nan, idan mun yi maka kuka saboda wahalarmu, kai kuwa za ka ji, ka cece mu.’

10 “Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.

11 Dubi irin sakayyar da suka zo su yi mana, so suke su kore mu daga mallakarka, wanda ka gādar mana.

12 Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Ba mu da ƙarfin da za mu yi yaƙi da wannan babban taro da suke zuwa su yi yaƙi da mu. Mun rasa abin da za mu yi, amma a gare ka muke zuba ido.”

13 A sa’an nan kuwa mutanen Yahuza suna tsaye a gaban Ubangiji, su da ƙananansu, da matansu, da ‘ya’yansu.

14 A tsakiyar taron sai Ruhun Ubangiji ya sauka a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benaiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, Balawe, na ‘ya’yan Asaf, maza.

15 Sai Yahaziyel ya ce, “Ku ji, ku dukanku, mutanen Yahuza, da mazaunan Urushalima, da sarki Yehoshafat, ga abin da Ubangiji yake faɗa muku, ‘Kada ku ji tsoro, ko ku razana saboda wannan babban taro, gama wannan yaƙi ba naku ba ne, amma na Allah ne.

16 Ku gangara ku fāɗa musu gobe. Ga shi kuwa, za su haura ta hawan Ziz, za ku tarar da su a ƙarshen kwarin a gabashin jejin Yeruyel.

17 Ba ku za ku yi wannan yaƙi ba, ku dai, ku jā dāga, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ciwo muku, ya Yahuza da Urushalima. Kada ku ji tsoro ko ku razana, gobe ku fita ku tsaya gāba da su, gama Ubangiji yana tare da ku.’ ”

18 Yehoshafat fa ya sunkuyar da kansa ƙasa, dukan Yahuza da mazaunan Urushalima kuma suka fāɗi ƙasa a gaban Ubangiji, suna masa sujada.

19 Sai Lawiyawa daga Kohatawa da Koratiyawa suka tashi tsaye suka yabi Ubangiji Allah na Isra’ila da babbar murya.

20 Sai suka tashi da sassafe suka tafi jejin Tekowa. Sa’ad da suka fita sai Yehoshafat ya tsaya, ya ce, “Ku saurara gare ni, ku mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima. Ku gaskata da Ubangiji Allahnku, za ku kahu. Ku gaskata annabawansa, za ku ci nasara.”

21 Sa’ad da ya yi shawara da jama’a, sai ya zaɓi waɗanda za su raira waƙa ga Ubangiji, su yabe shi a natse sa’ad da suke tafe a gaban runduna, su ce,

“Ku yi godiya ga Ubangiji,

Saboda madawwamiyar ƙaunarsa

Tabbatacciya ce har abada.”

22 Sa’ad da suka fara raira waƙa, suna yabo, sai Ubangiji ya sa wa mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, ‘yan kwanto, ‘yan kwanton kuwa suka fatattake su.

23 Gama mutanen Ammon da na Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka kansu da kansu.

24 Da mutanen Yahuza suka zo hasumiyar tsaro ta jeji, suka duba sai suka ga gawawwaki kawai a kwance, ba wanda ya tsira.

25 Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna ta kwasar ganimar saboda yawanta.

26 Sai suka taru a kwarin Beraka, wato albarka, a rana ta huɗu, a nan suka yabi Ubangiji. Don haka har wa yau ake kiran wurin, “Kwarin Beraka.”

27 Sai kowane mutumin Yahuza da na Urushalima, tare da Yehoshafat shugabansu, suka koma Urushalima suna murna, gama Ubangiji ya sa su yi farin ciki saboda maƙiyansu.

28 Suka shigo Urushalima da molaye da garayu, da ƙaho zuwa Haikalin Ubangiji.

29 Tsoron Ubangiji kuwa ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji Ubangiji ya yi yaƙi da maƙiyan Isra’ilawa.

30 Mulkin Yehoshafat kuwa ya sami salama, gama Allahnsa ya ba shi hutawa a kowane gefe.

Ƙarshen Mulkin Yehoshafat

31 Yehoshafat ya yi mulkin Yahuza. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan tsohuwarsa Azuba, ‘yar Shilhi.

32 Ya bi tafarkin tsohonsa, Asa, bai kuwa kauce ba, ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji.

33 Duk da haka ba a kawar da masujadai ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.

34 Sauran ayyukan Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin tarihin Yehu ɗan Hanani, wanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.

35 Bayan haka sai Yehoshafat, Sarkin Yahuza, ya haɗa kai da Ahaziya Sarkin Isra’ila, wanda ya aikata mugunta.

36 Ya haɗa kai da shi, suka gina jiragen ruwa don su riƙa zuwa Tarshish. A Eziyon-geber suka gina jiragen ruwan.

37 Sai Eliyezer ɗan Dodawahu mutumin Maresha, ya yi annabci gāba da Yehoshafat, ya ce, “Saboda ka haɗa kanka da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Don haka jiragen ruwa suka farfashe, suka kāsa tafiya Tarshish.

Categories
2 TAR

2 TAR 21

1 Yehoshafat ya rasu, aka binne shi a birnin Dawuda tare da kakanninsa, ɗansa kuma ya gāji gadon sarautarsa.

Sarki Yoram na Yahuza

2 Yoram yana da ‘yan’uwa maza, su ne Azariya, da Yehiyel, da Zakariya, da Azariya, da Maikel da kuma Shefatiya. Waɗannan ‘ya’ya maza ne na Yehoshafat, Sarkin Yahuza.

3 Tsohonsu ya ba su kyautai da yawa na azurfa da zinariya, da abubuwa masu daraja, da birane masu garu a Yahuza, amma ya ba da mulkin ga Yoram, saboda shi ne ɗan fari.

4 Sa’ad da Yoram ya hau gadon sarautar tsohonsa, ya kahu sosai, sai ya karkashe dukan ‘yan’uwansa da takobi, ya kuma karkashe waɗansu daga cikin sarakunan Yahuza.

5 Yoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya hau gadon sarauta, ya kuwa yi mulki a Urushalima shekara takwas.

6 Ya yi yadda sarakunan Isra’ila suka yi, kamar yadda gidan Ahab ya yi, gama matarsa ‘yar Ahab ce. Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji.

7 Duk da haka Ubangiji bai yarda ya hallaka gidan Dawuda ba, saboda alkawarin da ya riga ya yi da Dawuda, gama ya riga ya alkawarta zai ba shi haske, shi da ‘ya’yansa maza har abada.

8 A zamaninsa Edomawa suka tayar wa Yahuza, suka naɗa wa kansu sarki.

9 Sai Yoram ya wuce, shi da shugabannin sojojinsa tare da dukan karusansa. Sai ya tashi da dare ya fatattaki Edomawa waɗanda suka kewaye shi, shi da shugabannin karusansa.

10 Har wa yau Edom ya tayar wa Yahuza. A wannan lokaci kuma Libna ta tayar wa mulkinsa, saboda Yoram ya rabu da bin Ubangiji Allah na kakanninsa.

11 A kan wannan kuma, ya yi masujadai a tuddan ƙasar Yahuza, ya sa mutanen Urushalima su zama marasa aminci, ya sa Yahuza ta ratse.

12 Sai annabi Iliya ya rubuta masa wasiƙa ya ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na tsohonka Dawuda ya ce, ‘Da yake ba ka bi halin tsohonka Yehoshafat ba, da halin Asa Sarkin Yahuza,

13 amma ka bi irin halin sarakunan Isra’ila, har ka sa Yahuza da mazaunan Urushalima su zama marasa aminci, yadda gidan Ahab ya yi, ka kuma karkashe ‘yan’uwanka, waɗanda kuke uba ɗaya, waɗanda suka fi ka kirki,

14 ga shi, ni Ubangiji zan aukar da babbar abboba a kan jama’arka, da ‘ya’yanka maza, da matanka, da a kan abin da ka mallaka duka.

15 Kai da kanka kuma za ka kamu da ciwon hanji mai tsanani, saboda tsananin ciwo, hanjinka zai tsintsinke ya yi ta zuba kowace rana.’ ”

16 Sai Ubangiji ya kuta Filistiyawa da Larabawan da suke kusa da Habashawa, su yi gāba da Yoram.

17 Suka zo suka faɗa wa Yahuza da yaƙi. Suka washe dukan dukiyar da aka samu a gidan sarki, suka tafi da ita. Suka kuma kwashe ‘ya’yansa, da matansa, ba wanda aka bar masa, sai Ahaziya autansa.

18 Bayan haka kuma, sai Ubangiji ya sa masa ciwon hanji wanda ba shi warkuwa.

19 Ana nan a ƙarshen shekara biyu, sai cutar ta sa hanjinsa ya zubo, ya kuwa rasu saboda tsananin ciwo. Jama’arsa ba su hura masa wuta ta girmamawa kamar yadda aka yi wa kakanninsa ba.

20 Yana da shekara talatin da biyu, ya ci sarauta, ya yi shekara takwas yana mulki a Urushalima, ba wanda ya yi baƙin cikin mutuwarsa. Aka binne shi a birnin Dawuda, amma ba a kaburburan sarakuna ba.

Categories
2 TAR

2 TAR 22

Sarki Ahaziya na Yahuza

1 Sai mazaunan Urushalima suka naɗa Ahaziya, autansa, ya gāji gadon sarauta, saboda ƙungiyar mutanen da suka zo tare da Larabawa a sansanin sun karkashe dukan ‘yan’uwansa maza. Ahaziya ɗan Yoram Sarkin Yahuza, ya fara mulki.

2 Ahaziya yana da shekara arba’in da biyu sa’ad da ya ci sarauta, ya kuwa yi mulki shekara guda a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Ataliya jikar Omri.

3 Ya kuma bi gurbin gidan Ahab, gama tsohuwarsa ita ce mai ba shi shawarar yadda zai aikata mugunta.

4 Ya kuwa aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar gidan Ahab, gama su ne mashawartansa bayan rasuwar tsohonsa, wato shawarar da ta kai shi ga lalacewa.

5 Ya kuwa bi shawararsu. Ya tafi tare da Yehoram ɗan Ahab, Sarkin Isra’ila, don su yi yaƙi da Hazayel Sarkin Suriya, a Ramot-gileyad. Suriyawa kuwa suka yi wa Yehoram rauni.

6 Don haka sai ya koma Yezreyel don ya yi jiyyar raunukan da aka yi masa a Rama, sa’ad da suka yi yaƙi da Hazayel Sarkin Suriya. Sai Ahaziya ɗan Yoram, Sarkin Yahuza, ya gangara don ya gai da Yehoram ɗan Ahab a Yezreyel wanda yake rashin lafiya.

Yehu Ya kashe Ahaziya

7 Allah ya ƙaddara hallakar Ahaziya ta zo ta wurin ziyarar da ya kai wa Yehoram. Gama sa’ad da ya zo, sai ya fita tare da Yehoram don su yi yaƙi da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya keɓe don ya kakkaɓe gidan Ahab.

8 Sa’ad da Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya gamu da sarakunan Yahuza, da ‘ya’yan ‘yan’uwan Ahaziya, maza, suna yi wa Ahaziya hidima, sai ya karkashe su.

9 Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama suka ce, “Shi jikan Yehoshafat ne wanda ya nemi Ubangiji da zuciya ɗaya.”

Don haka a gidan Ahaziya ba wanda ya isa ya riƙe mulkin.

Sarauniya Ataliya ta Yahuza

10 Da Ataliya tsohuwar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta karkashe duk ‘yan sarautar gidan Yahuza.

11 Amma sai Yehosheba, ‘yar sarki Yoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya, ta sace shi daga cikin ‘ya’yan sarki waɗanda aka kashe su ta sa shi da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba ‘yar sarki Yoram, matar Yehoyada firist, ta yi, gama ita ‘yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya ta kashe shi.

12 Yowash yana ɓoye a Haikalin Allah har shekara shida, a lokacin da Ataliya take mulkin ƙasar.

Categories
2 TAR

2 TAR 23

An Ƙwace wa Ataliya Mulki

1 A shekara ta bakwai sai Yehoyada ya yi ƙarfin hali, ya haɗa kansa da shugabanni na ɗari ɗari, wato Azariya ɗan Yeroham, da Isma’ilu ɗan Yehohanan, da Azariya ɗan Obed, da Ma’aseya ɗan Adaya, da kuma Elishafat ɗan Zikri.

2 Sai suka shiga ko’ina cikin Yahuza, suka tattaro Lawiyawa daga dukan biranen Yahuza, da shugabannin gidajen kakannin Isra’ila, suka kuwa zo Urushalima.

3 Sai dukan taron suka yi wa sarki alkawari, a Haikalin Allah. Yehoyada ya ce musu, “Wannan shi ne ɗan sarki, sai ya ci sarauta kamar yadda Ubangiji ya faɗa a kan ‘ya’yan Dawuda, maza.

4 Ga abin da za ku yi. Sulusin firistoci da Lawiyawa waɗanda ba su aiki ran Asabar, su za su yi tsaron ƙofofi.

5 Sulusinsu kuma a fādar sarki, ɗayan sulusin kuwa a gangare, sauran jama’a duka kuwa a filayen Haikalin Ubangiji.

6 Amma kada kowa ya shiga Haikalin Ubangiji, sai dai firistoci da Lawiyawa masu hidima, su ne za su iya shiga, gama su tsarkaka ne. Amma dukan jama’a su kiyaye shari’a, kada su shiga Wuri Mai Tsarki na Ubangiji.

7 Lawiyawa za su kewaye sarkin, ko wanne da makamansa a hannu, duk wanda ya shiga ɗakin, sai a kashe shi. Su kuma kasance tare da sarki in zai shiga ko zai fita.”

8 Sai Lawiyawa da dukan Yahuza suka yi yadda Yehoyada, firist, ya umarta. Kowannensu ya kawo mutanensa waɗanda ba su aiki ran Asabar, da masu kama aiki ran Asabar, gama Yehoyada, firist, bai sallami ƙungiyoyin ba.

9 Sai Yehoyada firist, ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin Haikalin Allah.

10 Sai ya sa mutane duka su yi tsaron sarki, ko wanne da makami a hannu, tun daga gefen kudu har gefen arewa na Haikalin, da kuma kewaye da bagade da Haikali.

11 Sai ya kawo ɗan sarkin, ya sa masa kambi, ya ba shi dokoki goma, aka yi shela aka ce shi ne sarki. Yehoyada da ‘ya’yansa maza suka naɗa shi, suka ce, “Ran sarki ya daɗe!”

12 Sa’ad da Ataliya ta ji sowar mutane, suna ta ribibi suna yabon sarki, sai ta shiga Haikalin Ubangiji wurin jama’a.

13 Sa’ad da ta duba, sai ga sarki yana tsaye wajen ginshiƙin bakin ƙofa, ga shugabanni da masu busa ƙaho kewaye da sarkin. Dukan jama’a suna murna, suna busa ƙaho, mawaƙa kuma da kayan kaɗe-kaɗe da na bushe-bushensu, suna shugabancin shagalin. Sai Ataliya ta yayyage tufafinta ta ce, “Tawaye! Tawaye!”

14 Sai Yehoyada, firist, ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku kawo ta a tsakiyar sojoji, duk wanda ya bi ta a kashe shi da takobi.” Gama firist ɗin ya ce, “kada ku kashe ta a Haikalin Ubangiji.”

15 Sai suka kama ta. Da suka kai Ƙofar Doki ta fādar sarki, sai suka kashe ta a can.

Gyare-gyaren Yehoyada

16 Sai Yehoyada da dukan jama’a, da sarkin, suka ɗauki alkawari za su zama jama’ar Ubangiji.

17 Sai dukan jama’a suka tafi gidan Ba’al, suka rushe shi, suka kuma ragargaza bagadansa, da siffofinsa. Suka kashe Mattan, firist ɗin Ba’al, a gaban bagadan.

18 Yehoyada kuma ya sa matsaran da za su yi tsaron Haikalin Ubangiji a ƙarƙashin ikon firistoci, Lawiyawa, waɗanda Dawuda ya shirya don su lura da Haikalin Ubangiji, su miƙa hadayu na ƙonawa ga Ubangiji, yadda aka rubuta a Attaura ta Musa, da murna da waƙa kamar yadda Dawuda ya shirya.

19 Ya kuma sa ‘yan tsaron ƙofa a ƙofofin Haikalin Ubangiji, don kada wani marar tsarki na kowane iri ya shiga.

20 Sai ya sa shugabanni, da dattawa, da masu mulki, da dukan jama’ar ƙasar, suka rufa wa sarki baya, daga Haikalin Ubangiji suka bi ta Ƙofar Bisa zuwa fādar sarki. Suka zo suka zaunar da sarki a gadon sarauta.

21 Dukan jama’ar ƙasar suka yi murna, zaman lafiya ya komo birnin, bayan da an kashe Ataliya.