Categories
ZAB

ZAB 3

Addu’ar Safe ta Dogara ga Allah

1 Ina da maƙiya da yawa, ya Ubangiji,

Da yawa kuma sun juya, suna gāba da ni!

2 Suna magana a kaina, suna cewa,

“Allah ba zai taimake shi ba!”

3 Amma kai, ya Ubangiji, kullum kana kiyaye ni daga hatsari,

Kana ba ni nasara,

Kana kuma maido mini da ƙarfin halina.

4 Na yi kira wurin Ubangiji domin taimako,

Ya kuwa amsa mini daga tsattsarkan dutsensa.

5 Na kwanta na yi barci,

Na kuwa tashi lafiya lau,

Gama Ubangiji yana kiyaye ni.

6 Ba na jin tsoron dubban abokan gāba

Waɗanda suka kewaye ni ta kowane gefe.

7 Ka zo, ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna!

Ka yi nasara a kan dukan abokan gābana,

Ka hallakar da dukan mugaye.

8 Ceto yana zuwa daga wurin Ubangiji,

Bari yă sa wa jama’arsa albarka!

Categories
ZAB

ZAB 4

Addu’ar Maraice ta Dogara ga Allah

1 Ka amsa mini sa’ad da na yi kira,

Ya Allah, madogarata!

Lokacin da nake shan wahala, ka zama mai taimakona.

Ka yi mini alheri, ka kuma saurari addu’ata!

2 Ku mutanen nan, sai yaushe za ku daina zagina?

Sai yaushe za ku daina ƙaunar abubuwan banza,

Da bin abin da yake na ƙarya?

3 Ku tuna fa, Ubangiji ne ya zaɓe ni domin in zama nasa,

Ya kuma ji ni lokacin da na yi kira gare shi.

4 Ku ji tsoro, ku daina aikata zunubinku,

Ku yi tunani da gaske a kan wannan

A kaɗaice, shiru, a ɗakunanku.

5 Ku miƙa wa Ubangiji hadayun da suka dace,

Ku kuma dogara gare shi.

6 Akwai mutane da yawa da suke cewa,

“Da ma a sa mana albarka!”

Ka dube mu da alheri, ya Ubangiji!

7 Farin cikin da ka ba ni mai yawa ne,

Fiye da na waɗanda suke da wadataccen hatsi da ruwan inabi.

8 Da zarar na kwanta, sai barci ya kwashe ni,

Kai kaɗai kake kiyaye ni sosai, ya Ubangiji.

Categories
ZAB

ZAB 5

Addu’ar Neman Tsari daga Mugaye

1 Ka kasa kunne ga kalmomina, ya Ubangiji,

Ka kuma ji ajiyar zuciyata.

2 Ya Sarkina, Allahna,

Ka kasa kunne ga kukana na neman taimako.

3 A gare ka zan yi addu’a, ya Ubangiji,

Da safe za ka ji muryata,

Da hantsi zan yi addu’ata,

In kuma jira amsa.

4 Kai ba Allah mai yarda da aikin kuskure ba ne,

Ba ka yarda da mugunta a gabanka.

5 Ba ka jurewa da ganin mutane masu fāriya,

Kana ƙin mugaye.

6 Kakan hallakar da duk maƙaryata,

Kakan raina masu ta da hankali da masu ruɗi.

7 Amma ni, ina iya zuwa wurinka,

Saboda ƙaunarka mai girma,

In yi sujada a tsattsarkan Haikalinka,

In kuma rusuna maka da bangirma.

8 Ina da abokan gāba da yawa, ya Ubangiji,

Ka bi da ni in aikata nufinka,

Ka kuma fayyace mini hanyarka domin in bi ta!

9 Abin da maƙiyana ke faɗa,

Ba abin da za a yarda da shi ba ne,

Su dai, so suke su hallakar kawai,

Bakinsu kamar buɗaɗɗen kabari yake,

Maganganunsu kuwa suna da taushi da kuma yaudara.

10 Ka kāshe su, ka hukunta su, ya Allah

Ka watsar da mugayen shirye-shiryensu,

Ka kore su daga gabanka sabili da yawan zunubansu,

Da kuma tayarwar da suke yi maka.

11 Duk waɗanda suka fake gare ka za su yi farin ciki,

Kullum za su yi ta raira waƙa domin murna.

Kana kiyaye waɗanda suke ƙaunarka,

Suna kuwa matuƙar murna saboda kai.

12 Ka sa wa masu yi maka biyayya albarka, ya Ubangiji,

Alherinka yana kāre su kamar gārkuwa.

Categories
ZAB

ZAB 6

Addu’ar Neman Jinƙai a Lokacin Wahala

1 Ya Ubangiji, kada ka yi fushi, ka kuma tsauta mini!

Kada ka hukunta ni da fushinka!

2 Ka ji tausayina, gama na gaji tiƙis,

Ka wartsarkar da ni, gama na tafke sarai.

3 Duk na damu ƙwarai da gaske.

Sai yaushe wannan zai ƙare, ya Ubangiji?

4 Ya Ubangiji, ka zo ka cece ni,

Gama kana ƙaunata, ka kuɓutar da ni daga mutuwa.

5 Ba za a tuna da kai a lahira ba,

Ba wanda zai yabe ka a can!

6 Na gaji tiƙis saboda baƙin ciki,

Kowane dare gadona yakan jiƙe saboda kukana.

Matashin kaina ya yi sharkaf da hawaye.

7 Idanuna sun yi kumburi saboda yawan kuka,

Har da ƙyar nake iya gani,

Duk kuwa saboda abokan gābana!

8 Ku tafi daga nan, ku masu aikin mugunta!

Ubangiji yana jin kukana.

9 Yana kasa kunne ga kukana na neman taimako,

Yana kuwa amsa addu’o’ina.

10 Abokan gābana duka za su sha kunyar fāɗuwarsu,

Suna cikin matsanancin ruɗami,

Za a kwashe su farat ɗaya.

Categories
ZAB

ZAB 7

Addu’ar Neman a Yi Adalci

1 Ya Ubangiji, Allahna, na sami mafaka a wurinka,

Ka cece ni, ka tserar da ni daga dukan masu fafarata,

2 Idan ba haka ba kuwa, za su ɗauke ni,

Su tafi da ni zuwa wurin da ba wanda zai cece ni,

A can za su yayyage ni kamar zaki.

3 Ya Ubangiji, Allahna, idan na aikata ɗaya daga cikin waɗannan,

Wato idan na yi wa wani laifi,

4 Idan na ci amanar abokina,

Ko kuwa in na gwada wa maƙiyi fin ƙarfi ba dalili,

5 To, bari abokan gābana su fafare ni, su kama ni,

Bari su datse ni har ƙasa, su kuma kashe ni,

Su bar ni ƙasa, matacce!

6 Ka tashi da fushinka, ya Ubangiji,

Ka kuma tashi ka yi gāba da hasalar abokan gābana!

Ka tashi, ka taimake ni, gama adalci kake so a yi.

7 Ka tattaro dukan kabilun da suke kewaye da kai,

Ka yi mulki a kansu daga Sama.

8 Ya Ubangiji, kai ne alƙalin dukan mutane.

Ka shara’anta mini bisa ga adalcina,

Gama ba ni da laifi, ina kuma da kirki.

9 Ka tsai da muguntar mugaye,

Ina roƙonka, ka sāka wa mutanen kirki.

Kai Allah mai adalci ne,

Kana kuwa auna tunanin mutane, da marmarinsu.

10 Allah ne mai kiyaye ni,

Yakan ceci waɗanda suke yi masa biyayya.

11 Allah alƙali ne mai adalci,

Kullum kuwa yana kā da mugaye.

12 Idan mutane ba su tuba ba,

Allah zai wasa takobinsa,

13 Zai ɗana bakansa ya shirya shi,

Zai ɗauki makamansa masu dafi,

Ya kuma auna kibansa masu wuta.

14 Ka duba, yadda mugu yake tunanin mugunta a ransa,

Yana shisshirya wahala, yana kuma aikata ruɗi.

15 Yana haƙa rami mai zurfi a ƙasa,

Sa’an nan yă fāɗa ramin da ya haƙa!

16 Saboda haka muguntarsa ta hukunta shi ke nan,

Rikicin kansa ya yi masa lahani.

17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa,

Zan raira yabbai ga Ubangiji, Maɗaukaki.

Categories
ZAB

ZAB 8

Ɗaukakar Allah da Martabar Mutum

1 Ya Ubangiji, Ubangijinmu,

An san girmanka ko’ina a dukan duniya.

Yabonka ya kai har sammai,

2 Yara da jarirai suna raira shi,

Ka gina kagara saboda magabtanka,

Domin ka tsai da maƙiyanka da abokan gābanka.

3 Sa’ad da na duba sararin sama, wanda ka yi,

Da wata da taurari waɗanda ka sa a wuraren zamansu,

4 Wane ne mutum, har da kake tunawa da shi,

Mutum kurum, har da kake lura da shi?

5 Duk da haka in banda kai ba wanda ya fi shi,

Ka naɗa shi da daraja da girma!

6 Ka sa shi ya yi mulkin dukan abin da ka halitta,

Ka ɗora shi a kan dukan abubuwa,

7 Tumaki da shanu, har ma da namomin jeji,

8 Da tsuntsaye da kifaye,

Da dukan halittar da suke cikin tekuna.

9 Ya Ubangiji, Ubangijinmu,

An san girmanka ko’ina a dukan duniya!

Categories
ZAB

ZAB 9

Godiya ga Allah saboda Adalcinsa

1 Zan yabe ka da zuciya ɗaya, ya Ubangiji,

Zan hurta dukan abubuwa masu banmamaki da ka yi.

2 Zan raira waƙa da farin ciki sabili da kai,

Zan raira yabo gare ka, ya Maɗaukaki!

3 Magabtana sun jā da baya da suka gan ka,

Suka faɗi, suka mutu.

4 Kai da kake alƙali mai adalci

Ka zauna a kursiyinka,

Ka kuwa yi shari’ar da ta yi mini daidai.

5 Ka kā da arna,

Ka kuma hallakar da mugaye,

Ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba.

6 An hallaka abokan gābanmu har abada,

Ka lalatar da biranensu,

An kuma manta da su sarai.

7 Amma Ubangiji sarki ne har abada,

Ya kafa kursiyinsa domin yin shari’a.

8 Yana mulkin duniya da adalci,

Yana yi wa mutane shari’a da gaskiya.

9 Ubangiji mafaka ne ga waɗanda ake zalunta,

Wurin ɓuya a lokatan wahala.

10 Waɗanda suka san ka za su amince da kai, ya Ubangiji,

Ba za ka ƙyale duk wanda ya zo gare ka ba.

11 Ku yabi Ubangiji, shi da yake mulki a Sihiyona!

Ku faɗa wa kowace al’umma abin da ya yi!

12 Allah yana tunawa da waɗanda suke shan wuya,

Ba ya mantawa da kukansu,

Yana kuma hukunta waɗanda suke cutarsu.

13 Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai!

Ka dubi irin wulakancin da maƙiya suka yi mini!

Ka kuɓutar da ni daga mutuwa, ya Ubangiji,

14 Domin in iya tsayawa a gaban jama’ar Urushalima,

In faɗa musu dukan abin da ya sa nake yabonka.

Zan yi farin ciki saboda ka cece ni.

15 Arna sun haƙa rami sun kuwa fāɗa ciki,

Sun ɗana tarko, ya kuwa kama su.

16 Ubangiji ya bayyana kansa ta wurin shari’arsa mai adalci,

Mugaye sun kama kansu da abubuwan da suka aikata.

17 Mutuwa ce maƙarar dukan mugaye,

Da dukan waɗanda suke ƙin Allah.

18 Ba kullum ne ake ƙyale masu bukata ba,

Ba za a danne sa zuciyar waɗanda ake zalunta ba har abada.

19 Ka zo, ya Ubangiji! Kada ka bari mutane su gagare ka!

Ka kawo arna a gabanka, ka hukunta su.

20 Ka sa su ji tsoro, ya Ubangiji,

Ka sa su sani su mutane ne kawai.

Categories
ZAB

ZAB 10

Addu’ar Neman Hamɓare Mugaye

1 Ya Ubangiji, me ya sa kake can nesa?

Me ya sa ka ɓoye kanka a lokacin wahala?

2 Mugaye suna fāriya, suna kuma tsananta wa matalauta,

Ɗana tarkon da suka yi yă kama su.

3 Mugun mutum yana fāriya da mugayen manufofinsa,

Mai haɗama yakan zagi Ubangiji ya kuma ƙi shi.

4 Mugun mutum da girmankansa yana cewa, “Ba Allah!”

Wannan ne abin da mugu yake tunani.

5 Yakan yi nasara a dukan abin da yake yi.

Ba zai fahimci hukuncin Allah ba,

Yana yi wa abokan gābansa duban raini.

6 Yana ce wa kansa “Ba zan taɓa fāɗuwa ba,

Ba zan taɓa shan wahala ba.”

7 Maganganunsa suna cike da zage-zage, da ƙarairayi, da barazana,

Yana da saurin faɗar maganganun ƙiyayya da na mugunta.

8 Yakan ɓuya cikin ƙauyuka,

Yă jira a can har yă kashe marasa laifi.

Yakan yi sanɗa, ya kama kāsassu,

9 Yakan jira a inda ya ɓuya kamar zaki.

Yakan kwanta yana fakon wanda zai kama,

Har ya kama shi da tarkonsa ya tafi da shi!

10 Yakan ragargaza kāsasshe,

Yă gwada masa ƙarfi, yă ci nasara a kansa.

11 Mugun mutum yakan ce wa kansa, “Allah bai kula ba!

Ya rufe idonsa, ba zai taɓa ganina ba.”

12 Ya Ubangiji, ka zo ka cece ni!

Kada ka manta da waɗanda ake zaluntarsu, ya Allah!

13 Yaya mugun zai riƙa raina Allah,

Har yă riƙa ce wa kansa, “Ba zai hukunta ni ba”?

14 Amma kana gani, kana kuma lura da masu shan wuya, da masu ɓacin rai,

Koyaushe kuma a shirye kake ka yi taimako.

Mutum wanda ba shi da mai taimako yakan danka kansa gare ka,

Gama kullum kakan taimaki masu bukata.

15 Ka karya ikon mugaye, masu mugunta,

Ka hukunta su saboda muguntarsu,

Har hukuncinsu ya cika sarai.

16 Ubangiji sarki ne har abada abadin,

Arna kuma za su ɓace daga ƙasarsa.

17 Za ka saurara ga addu’o’in masu kaɗaici, ya Ubangiji,

Za ka ba su ƙarfin hali.

18 Za ka ji koke-koken waɗanda ake zalunta da na marayu,

Ka yi shari’ar da za su ji daɗi,

Domin kada ‘yan adam su ƙara haddasa wata razana.

Categories
ZAB

ZAB 11

Mafakar Adalai

1 Na dogara ga Ubangiji domin zaman lafiya,

Wauta ce idan kun ce mini,

“Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu,

2 Domin mugaye sun ja bakkunansu,

Sun kuma ɗana kibansu

Domin su harbi mutanen kirki a duhu.

3 Ba abin da mutumin kirki zai iya yi

Sa’ad da kome ya lalace.”

4 Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa,

Yana da kursiyinsa a Sama.

Yana kallon dukan mutane

Yana sane da abin da suke yi.

5 Yana auna masu kirki da mugaye dukka,

Yana ƙin marar bin doka gaba ɗaya.

6 Yakan aukar da garwashin wuta

Da kibritu mai cin wuta a kan mugaye,

Yakan hukunta su da harshen wuta mai ƙuna.

7 Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar kyawawan ayyuka,

Masu yi masa biyayya za su zauna a gabansa.

Categories
ZAB

ZAB 12

Addu’ar Neman Taimako

1 Ka cece ni, ya Ubangiji,

Ba sauran mutanen kirki,

Ba kuma za a sami amintattun mutane ba.

2 Dukan mutane suna yi wa juna ƙarya,

Suna ruɗin junansu da yaudara.

3 Ka sa harsunan nan masu yaudara su yi shiru,

Ya Ubangiji, ka rufe bakunan nan masu fāriya!

4 Sukan ce, “Za mu yi magana yadda muka ga dama,

Ba kuwa wanda zai hana mu.

Wane ne yake da ikon faɗa mana abin da za mu faɗa?”

5 Ubangiji ya ce, “Amma zan zo yanzu,

Domin ana zaluntar masu bukata,

Waɗanda aka tsananta musu kuma, suna nishi don zafi.

Zan ba su zaman lafiya da suke nema!”

6 Alkawaran Ubangiji abin dogara ne,

Alkawarai ne na ainihi kamar azurfa

Da aka tace har sau bakwai cikin matoya.

7 Ka kiyaye lafiyarmu, ya Ubangiji,

Ka kiyaye mu daga irin waɗannan mutane.

8 Akwai mugaye ko’ina, suna ta yanga,

Suna ta yabon abin da yake mugunta.