Categories
ZAB

ZAB 53

Muguntar Mutane

1 Wawaye sukan ce wa kansu, “Ba Allah.”

Dukansu sun lalace, sun aikata mugayen al’amura,

Ba wanda yake aikata abin da yake daidai.

2 Daga Sama Allah ya dubi mutane,

Ya ga ko akwai masu hikima

Waɗanda suke yi masa sujada.

3 Amma dukansu sun koma baya,

Su duka mugaye ne,

Ba wanda yake aikata abin da yake daidai,

Babu ko ɗaya.

4 Allah ya ce, “Ashe, ba su sani ba?

Ashe, mugayen nan jahilai ne?

Ta wurin yi wa jama’ata fashi suke rayuwa,

Ba sa yin addu’a gare ni.”

5 Amma sa’an nan za su firgita ƙwarai,

Irin yadda ba su taɓa yi ba,

Gama Allah ya warwatsa ƙasusuwan maƙiyanka.

Ya kore su sarai, saboda ya ƙi su.

6 Dā ma ceto ya zo ga Isra’ila daga Sihiyona!

Sa’ad da Allah ya sāke arzuta jama’arsa,

Zuriyar Yakubu za ta yi farin ciki,

Jama’ar Isra’ila kuwa za ta yi murna.

Categories
ZAB

ZAB 54

Addu’ar Neman Tsari daga Maƙiyi

1 Ka cece ni ta wurin ikonka, ya Allah,

Ka cece ni ta wurin ƙarfinka!

2 Ka ji addu’ata, ya Allah,

Ka saurari kalmomina!

3 Masu girmankai sun tasar mini,

Mugaye suna nema su kashe ni,

Mutanen da ba su kula da Allah ba.

4 Na sani Allah ne mai taimakona,

Na sani Ubangiji shi ne mai tsarona!

5 Ubangiji ya hukunta wa maƙiyana da irin muguntarsu!

Gama zai hallaka su saboda shi mai aminci ne.

6 Da murna zan miƙa maka hadaya,

Zan yi maka godiya, ya Ubangiji,

Domin kai mai alheri ne.

7 Ka cece ni daga dukan wahalaina,

Na kuwa ga an kori maƙiyana.

Categories
ZAB

ZAB 55

Addu’ar Neman Taimako

1 Ka ji addu’ata, ya Allah,

Kada ka ƙi jin roƙona!

2 Ka saurare ni, ka amsa mini,

Gama damuwata ta gajiyar da ni tiƙis.

3 Hankalina ya tashi saboda yawan kurarin maƙiyana,

Saboda danniyar mugaye.

Sukan jawo mini wahala,

Suna jin haushina suna ƙina.

4 Azaba ta cika zuciyata,

Tsorace-tsoracen mutuwa sun yi mini nauyi.

5 Tsoro da rawar jiki sun kama ni,

Na cika da razana.

6 Na ce, “Da a ce ina da fikafikai kamar kurciya,

Da sai in tashi, in tafi, in nemi wurin hutawa!

7 In tafi can nesa,

In yi wurin zamana a hamada.

8 Zan hanzarta in nemi mafaka

Daga iska mai ƙarfi da hadiri.”

9 Ka hallaka su, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu,

Gama na ga hargitsi da tawaye a birni.

10 Dare da rana suna ta yawo a kan garu suna ta kewaye birnin,

Birnin kuwa cike yake da laifi da wahala.

11 Akwai hallaka a ko’ina,

Tituna suna cike da azzalumai da ‘yan danfara.

12 Da a ce maƙiyina ne yake mini ba’a,

Da sai in jure.

Da a ce abokin gābana ne yake shugabancina,

Da sai in ɓuya masa.

13 Amma kai ne, aminina,

Abokin aikina ne, abokina ne kuma!

14 Dā mukan yi taɗi da juna ƙwarai,

Mukan tafi Haikali tare da sauran jama’a.

15 Allah ya sa mutuwa ta auko wa maƙiyana ba labari,

Allah ya sa su gangara ƙasar matattu da ransu!

Mugunta tana cikin gidajensu da zukatansu.

16 Amma ina kira ga Allah, yă taimake ni,

Ubangiji kuwa zai cece ni.

17 Koke-kokena da nishe-nishena

Suna hawa zuwa gare shi da safe, da tsakar rana, da dad dare,

Zai kuwa ji muryata.

18 Zai fisshe ni lafiya

Daga yaƙe-yaken da nakan yi da magabtana masu yawa.

19 Allah, shi wanda yake mulki tun fil azal,

Zai ji ni, zai kore su.

Ba abin da suka iya yi a kai,

Domin ba su tsoron Allah.

20 Abokina na dā,

Ya yi wa abokansa faɗa,

Ya ta da alkawarinsa.

21 Kalmominsa sun fi mai taushi,

Amma ƙiyayya tana a zuciyarsa,

Kalmominsa sun fi mai sulɓi,

Amma suna yanka kamar kakkaifan takobi.

22 Ka gabatar da wahalarka ga Ubangiji,

Zai kuwa taimake ka,

Ba zai bari a ci nasara a kan mutumin kirki ba, faufau.

23 Amma kai, ya Allah, za ka jefar da masu kisankai, da maƙaryata can ƙasa cikin zurfafa,

Kafin su kai rabin kwanakinsu a duniya.

Amma ni, zan dogara gare ka.

Categories
ZAB

ZAB 56

Addu’ar Dogara ga Allah

1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah,

Gama mutane sun tasar mini,

Maƙiyana suna tsananta mini koyaushe!

2 Dukan yini maƙiyana suna tasar mini,

Waɗanda suke faɗa da ni sun cika yawa.

3 Sa’ad da nake jin tsoro, ya Maɗaukaki,

A gare ka nake dogara.

4 Ga Allah nake dogara, ina yabon alkawarinsa,

Gare shi na dogara, ba zan ji tsoro ba.

Me mutum kawai zai yi mini?

5 Maƙiyana suke ta wahalshe ni dukan yini,

A kan kowane abu da nake yi,

Kullum suna ta tunanin yadda za su cuce ni!

6 Sukan taru a ɓoye,

Suna kallon duk abin da nake yi.

Suna sa zuciya za su iya kashe ni.

7 Ka hukunta su, ya Allah saboda muguntarsu,

Da fushinka ka kori waɗannan mutane!

8 Ka san irin wahalar da nake sha,

Kana riƙe da lissafin yawan hawayena.

Ashe, ba a rubuce suke a littafinka ba?

9 A ranar da na yi kira gare ka,

Za a komar da abokan gābana baya,

Gama na sani Allah yana tare da ni!

10 Ina dogara ga Allah, ina yabon alkawarinsa,

Ina dogara ga Ubangiji, ina yabon alkawarinsa.

11 A gare shi nake dogara,

Ba zan ji tsoro ba.

Me mutum kawai zai yi mini?

12 Zan miƙa maka abin da na yi alkawari, ya Allah,

Zan miƙa maka hadaya ta godiya.

13 Domin ka cece ni daga mutuwa,

Ka hana a ci nasara a kaina.

Saboda haka a gaban Allah nake tafiya

A hasken da yake haskaka wa masu rai.

Categories
ZAB

ZAB 57

Addu’ar Neman Kuɓuta daga Tsanani

1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi jinƙai,

Gama na zo gare ka neman tsira.

Zan sami kāriya a ƙarƙashin fikafikanka,

Sai dukan hatsari ya wuce.

2 Zan yi kira ga Allah, Maɗaukaki,

Zan yi kira ga Allah, mai biyan dukan bukatata.

3 Daga sammai Allah zai amsa mini,

Zai kori waɗanda suka tasar mini,

Allah zai nuna mini madawwamiyar ƙaunarsa da amincinsa.

4 Raina yana tsakiyar zakoki,

Na kwanta a tsakiyar waɗanda suka yi niyyar cinye mutane.

Haƙoransu kamar māsu da kibau suke,

Harsunansu masu kaifi ne kamar takobi.

5 Ka bayyana girmanka ya Allah, a sararin sama,

Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!

6 Maƙiyana sun kafa tarko don su kama ni,

Damuwa ta fi ƙarfina.

Sun yi wushefe a kan hanyata,

Amma su da kansu suka fāɗa a ciki.

7 A shirye nake, ya Allah,

Na shirya sosai!

Zan raira waƙoƙi in yabe ka!

8 Ka farka, ya raina!

Ku farka, molona da garayata!

Zan sa rana ta farka!

9 Zan gode maka a cikin sauran al’umma, ya Ubangiji!

Zan yabe ka a cikin jama’a!

10 Madawwamiyar ƙaunarka ta kai har sammai,

Amincinka kuma har sararin sammai.

11 Ka bayyana girmanka, ya Allah, a sararin sama,

Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!

Categories
ZAB

ZAB 58

Addu’a domin A Hukunta Mugaye

1 Hakika za ku yanka daidai, ku manya?

Za ku shara’anta wa mutane daidai?

2 A’a, tunanin muguntar da za ku aikata kaɗai kuke yi,

Kuna aikata laifofin ta da hargitsi a ƙasar.

3 Mugaye, laifi suke yi dukan kwanakinsu,

Tun daga ranar da aka haife su suke ta faɗar ƙarya.

4 Cike suke da dafi kamar macizai,

Sukan toshe kunnuwansu kamar kuraman gamsheƙa,

5 Wanda ba ya jin muryar gardi,

Ko kuma waƙar gwanin sihiri.

6 Ka kakkarya haƙoransu, ya Allah,

Ka ciccire fiƙoƙin waɗannan zakoki masu zafin rai, ya Ubangiji!

7 Bari su ɓace kamar ruwan da ya tsanye,

Bari a murtsuke su kamar ciyayi a hanya.

8 Bari su zama kamar katantanwu waɗanda sukan narke su yi yauƙi,

Allah ya sa su zama kamar jinjirin da aka haifa matacce.

Wanda bai taɓa ganin hasken rana ba.

9 Kafin tukunya ta ji zafin wuta,

Da zafin fushi, Allah zai watsar da su tun suna da rai.

10 Adalai za su yi murna sa’ad da suka ga an hukunta masu zunubi,

Za su wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.

11 Mutane za su ce, “Hakika an sāka wa adalai,

Hakika akwai Allah wanda yake shara’anta duniya!”

Categories
ZAB

ZAB 59

Addu’ar Neman Ceto daga Maƙiya

1 Ka cece ni daga maƙiyana, ya Allahna,

Ka kiyaye ni daga waɗanda suka tasar mini!

2 Ka cece ni daga waɗannan mugaye,

Ka tsirar da ni daga masu kisankan nan!

3 Duba! Suna jira su auka mini,

Mugaye suna taruwa gāba da ni,

Ba domin wani zunubi ko wani laifin da na yi ba,

4 Ba domin na yi wani laifi ba, ya Ubangiji,

Har da suka gaggauta gāba da ni.

Kai da kanka ka gani, ya Allah na Isra’ila!

Ka tashi ka taimake ni.

5 Ka tashi, ya Ubangiji, Allah Maɗaukaki, ka taimake ni,

Ka tashi ka hukunta al’ummai,

Kada ka yi wa waɗannan mugaye, maciya amana, jinƙai!

6 Da maraice suka komo,

Suna yaƙe haƙora kamar karnukan da suke yawo ko’ina a birni.

7 Ji abin da suke fada!

Harsunansu suna kama da takuba a bakinsu,

Duk da haka suna ta tambaya, suna cewa, “Wa zai ji mu?”

8 Amma kai dariya kake yi musu, ya Ubangiji,

Ka mai da al’ummai duka abin bandariya!

9 Mai tsarona, kai ne kake kiyaye ni,

Kai ne mafakata, ya Allah.

10 Allahna wanda yake ƙaunata, zai zo gare ni,

Zai sa in ga an kori magabtana.

11 Kada ka kashe su, ya Allah, don kada jama’ata su manta.

Ka watsar da su da ikonka, ka hallaka su ya Ubangiji mai kiyaye mu!

12 Zunubi na cikin leɓunansu, maganganunsu na zunubi ne,

Da ma a kama su saboda girmankansu,

Domin suna la’antarwa, suna ƙarya!

13 Da fushinka ka hallaka su,

Ka hallaka su ɗungum.

Sa’an nan jama’a za su sani Allah yana mulkin Isra’ila,

Mulkinsa ya kai ko’ina a duniya!

14 Da maraice maƙiyana suka komo,

Suna yaƙe haƙora kamar karnukan da suke yawo ko’ina a birni.

15 Suna kai da kawowa ko’ina neman abinci,

In ba su sami abin da ya ishe su ba,

Sukan yi gunaguni.

16 Amma zan raira waƙa a kan ikonka,

Kowace safiya zan raira waƙa da ƙarfi

Ga zancen madawwamiyar ƙaunarka.

Kai mafaka ne a gare ni,

Wurin ɓuya a kwanakin wahala.

17 Zan yabe ka, mai tsarona,

Allah ne mafakata,

Allah wanda ya ƙaunace ni.

Categories
ZAB

ZAB 60

Addu’ar Neman Taimako

1 Ka rabu da mu, ya Allah, har aka ci nasara a kanmu,

Ka yi fushi da mu, amma yanzu sai ka juyo wurinmu!

2 Ka sa ƙasar ta girgiza, ka tsaga ta.

Yanzu sai ka warkar da tsaguwarta, gama tana gab da fāɗuwa!

3 Ka sa jama’arka su sha wahala ƙwarai,

Ka ba mu ruwan inabin da ya bugar da mu.

4 Ka ta da tuta ga masu tsoronka,

Domin su juya su gudu daga abokin gāba.

5 Ka cece mu da ƙarfinka, ka amsa addu’ata,

Domin jama’ar da kake ƙauna ta sami cetonka.

6 A tsattsarkan wurinsa, Allah ya faɗa ya ce,

“Da nasara zan raba Shekem,

Da nasara kuma zan rarraba Sukkot ga jama’ata.

7 Gileyad tawa ce, har da Manassa ma,

Ifraimu ne kwalkwalina,

Yahuza kuma sandana ne na sarauta.

8 Amma zan yi amfani da Mowab kamar kwanon wanki,

Edom kuwa kamar akwatin takalmina.

Zan yi sowar nasara a kan Filistiyawa.”

9 Ya Allah, wa zai kai ni birni mai kagara?

Wa zai kai ni Edom?

10 Da gaske ka yashe mu ke nan?

Ba za ka yi tafiya tare da sojojinmu ba?

11 Ka taimake mu, mu yaƙi abokan gāba,

Domin taimako irin na mutum banza ne!

12 Idan Allah yana wajenmu,

Za mu yi nasara,

Zai kori abokan gābanmu.

Categories
ZAB

ZAB 61

Dogara ga Kiyayewar Allah

1 Ya Allah, ka ji kukana,

Ka ji addu’ata!

2 Sa’ad da nake nesa da gida, zuciyata ta karai,

Zan yi kira gare ka!

Ka kai ni lafiyayyiyar mafaka.

3 Kai ne kāriyata mai ƙarfi

Da take kiyaye ni daga maƙiyana.

4 Ka yarda in zauna a alfarwarka dukan kwanakin raina,

Ka yarda in sami zaman lafiya a ƙarƙashin fikafikanka.

5 Ya Allah, kā ji alkawaraina,

Kā kuwa ba ni abin da ya dace,

Tare da waɗanda suke ɗaukaka ka.

6 Ka ƙara wa sarki tsawon rai,

Ka sa ya rayu dukan lokaci!

7 Ka sa ya yi mulki har abada a gabanka, ya Allah,

Ka tsare shi da madawwamiyar ƙaunarka, da amincinka.

8 Don haka zan yi ta raira waƙar yabonka kullayaumin,

A sa’ad da nake miƙa maka abin da na alkawarta.

Categories
ZAB

ZAB 62

Allah ne kaɗai Mafaka

1 Ga Allah kaɗai na dogara,

Cetona daga gare shi yake fitowa.

2 Shi kaɗai ne mai kiyaye ni, Mai Cetona,

Shi ne kariyata,

Ba kuwa za a yi nasara da ni ba sam.

3 Har yaushe dukanku za ku fāɗa wa wani don ku yi nasara da shi,

Kamar rusasshen garu,

Ko kuma dangar da ta fāɗi?

4 Ba abin da kuke so, sai ku ƙasƙantar da shi daga maƙaminsa na daraja,

Kuna jin daɗin yin ƙarairayi.

Kuna sa masa albarka,

Amma a zuciyarku la’antarwa kuke yi.

5 Ga Allah kaɗai na dogara,

A gare shi na sa zuciyata.

6 Shi kaɗai ne mai kiyaye ni, Mai Cetona,

Shi ne kariyata,

Ba kuwa za a yi nasara da ni ba sam.

7 Cetona da darajata daga Allah ne,

Shi ne ƙaƙƙarfan makiyayina,

Shi ne mafakata.

8 Ya jama’ata, ku dogara ya Allah a kowane lokaci!

Ku faɗa masa dukan wahalarku,

Gama shi ne mafakarmu.

9 Talakawa kamar shaƙar numfashi suke,

Manyan mutane, su ma haka suke marasa amfani.

Ko an auna su a ma’auni, sam ba su da nauyin kome,

Sun fi numfashi shakaf.

10 Kada ku dogara da aikin kama-karya.

Kada ku sa zuciya za ku ci ribar kome ta wurin fashi.

In kuwa dukiyarku ta ƙaru,

Kada ku dogara gare ta.

11 Sau ɗaya Allah ya faɗa,

Sau biyu na ji, cewa Allah yake da iko.

12 Madawwamiyar ƙauna, ta Ubangiji ce.

Kai kanka, ya Ubangiji, kake sāka wa

Kowane mutum bisa ga ayyukansa.