Categories
ZAB

ZAB 143

Addu’ar Neman Ceto da Kiyayewa

1 Ya Ubangiji ka ji addu’ata,

Ka kasa kunne ga roƙona!

Kai adali ne mai aminci,

Don haka ka amsa mini!

2 Ni bawanka, kada ka gabatar da ni a gaban shari’a,

Gama ba wanda ba shi da laifi a gare ka.

3 Maƙiyina ya tsananta mini,

Ya kore ni fata-fata.

Ya sa ni a kurkuku mai duhu,

Ina kama da waɗanda suka daɗe da mutuwa,

4 Don haka ina niyya in fid da zuciya,

Ina cikin damuwa mai zurfi.

5 Na tuna kwanakin baya,

Na tuna da dukan abin da ka yi,

Na tuna da dukan ayyukanka.

6 Na ɗaga hannuwana sama, ina addu’a gare ka,

Kamar busasshiyar ƙasa, raina yana jin ƙishinka.

7 Yanzu ka amsa mini, ya Ubangiji!

Na fid da zuciya duka!

Kada ka ɓuya mini,

Don kada in zama cikin waɗanda suke gangarawa zuwa lahira.

8 A gare ka nake dogara,

Da safe ka tuna mini da madawwamiyar ƙaunarka.

Addu’ata ta hau zuwa gare ka,

Ka nuna mini hanyar da zan bi.

9 Na tafi wurinka don ka kiyaye ni, ya Ubangiji,

Ka cece ni daga maƙiyana.

10 Kai ne Allahna,

Ka koya mini in aikata nufinka.

Ka sa in sami alherin Ruhunka.

Ka bi da ni a hanyar lafiya.

11 Ka cece ni, ya Ubangiji, kamar yadda ka alkawarta.

Saboda alherinka ka tsamo ni daga wahalaina!

12 Saboda ƙaunar da kake yi mini,

Ka kashe maƙiyana.

Ka hallakar da dukan waɗanda suke zaluntata.

Gama ni bawanka ne.

Categories
ZAB

ZAB 144

Addu’ar Neman Ceto da Wadata

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, mai kiyaye ni,

Ya hore ni don yaƙi,

Ya kuwa shirya ni don yaƙi.

2 Shi yake kiyaye ni,

Shi yake kāre ni,

Shi ne mafakata da Mai Cetona,

Wanda nake dogara gare shi

Don samun zaman lafiya.

Shi ne ya ɗora ni a kan al’ummai.

3 Ya Ubangiji wane ne mutum, har da kake lura da shi?

Wane ne ɗan adam kurum, har da kake kulawa da shi?

4 Shi kamar hucin iska yake,

Kwanakinsa kuwa kamar inuwa mai wucewa ne.

5 Ya Ubangiji, ka kware sararin sama, ka sauko,

Ka taɓa duwatsu, don su tuƙaƙo da hayaƙi.

6 Ka aiko da walƙiyar tsawa ta warwatsa maƙiyanka,

Ka harba kibanka, ka sa su sheƙa a guje!

7 Ka sunkuyo daga Sama,

Ka tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi, ka cece ni,

Ka cece ni daga ikon baƙi,

8 Waɗanda ba su taɓa faɗar gaskiya ba,

Sukan yi rantsuwar ƙarya.

9 Zan raira maka sabuwar waƙa, ya Allah,

Zan kaɗa garaya in raira maka waƙa.

10 Ka ba sarakuna nasara,

Ka kuma ceci bawanka Dawuda.

11 Ka cece ni daga mugayen abokan gābana,

Ka ƙwato ni daga ikon baƙi,

Waɗanda ba su taɓa faɗar gaskiya ba,

Sukan yi rantsuwar ƙarya.

12 Ka sa ‘ya’yanmu maza waɗanda suke cikin samartaka,

Su zama kamar itatuwan da yake girma da ƙarfi.

Ka sa ‘ya’yanmu mata

Su zama kamar al’amudai,

Waɗanda suke adanta kusurwoyin fāda.

13 Ka sa rumbunanmu su cika

Da kowane irin amfanin gona.

Ka sa tumakin da suke cikin saurukanmu

Su hayayyafa dubu dubu har sau goma,

14 Ka sa shanunmu su hayayyafa,

Kada su yi ɓari ko su ɓace.

Ka sa kada a ji kukan damuwa a kan titunanmu!

15 Mai farin ciki ce al’ummar

Da abin nan da aka faɗa ya zama gaskiya a gare ta.

Masu farin ciki ne jama’ar da Allahnsu shi ne Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 145

Waƙar Yabon Allah domin Alherinsa da Ikonsa

1 Zan yi shelar girmanka, ya Allahna, Sarkina,

Zan yi maka godiya har abada abadin.

2 Kowace rana zan yi maka godiya,

Zan yabe ka har abada abadin.

3 Ubangiji mai girma ne, dole ne a fifita yabonsa,

Girmansa ya fi ƙarfin ganewa.

4 Za a yabi abin da ka aikata daga tsara zuwa tsara,

Za su yi shelar manya manyan ayyukanka.

5 Mutane za su yi magana a kan darajarka da ɗaukakarka,

Ni kuwa zan yi ta tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.

6 Mutane za su yi magana a kan manya manyan ayyukanka,

Ni kuwa zan yi shelar girmanka.

7 Za su ba da labarin girmanka duka,

Su kuma raira waƙa a kan alherinka.

8 Ubangiji mai ƙauna ne, mai jinƙai, mai jinkirin fushi,

Cike da madawwamiyar ƙauna.

9 Shi mai alheri ne ga kowa,

Yana juyayin dukan abin da ya halitta.

10 Ya Ubangiji, talikanka duka za su yabe ka,

Jama’arka kuma za su yi maka godiya!

11 Za su yi maganar darajar mulkinka,

Su ba da labarin ikonka,

12 Domin haka dukan mutane za su san manyan ayyukanka,

Da kuma darajar ɗaukakar mulkinka.

13 Mulkinka, madawwamin mulki ne,

Sarki ne kai har abada.

14 Ubangiji, yakan taimaki dukan waɗanda yake shan wahala,

Yakan ta da waɗanda aka wulakanta.

15 Dukan masu rai suna sa zuciya gare shi,

Yana ba su abinci a lokacin da suke bukata,

16 Yana kuwa ba su isasshe,

Yakan biya bukatarsu duka.

17 Ubangiji mai adalci ne a abin da yake yi duka,

Mai jinƙai ne a ayyukansa duka.

18 Yana kusa da dukan waɗanda suke kira gare shi,

Waɗanda suke kiransa da zuciya ɗaya.

19 Yakan biya bukatar dukan waɗanda suke tsoronsa,

Yakan ji kukansu, ya cece su.

20 Yakan kiyaye dukan waɗanda suke ƙaunarsa,

Amma zai hallaka mugaye duka.

21 A kullum zan yabi Ubangiji,

Bari talikai duka su yabi sunansa mai tsarki har abada!

Categories
ZAB

ZAB 146

Yabon Allah Mai Ceto

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Ka yabi Ubanigji, ya raina!

2 Zan yabe shi muddin raina.

Zan raira waƙa ga Allahna dukan kwanakina.

3 Kada ka dogara ga shugabanni,

Ko kowane mutum da ba zai iya cetonka ba.

4 Sa’ad da suka mutu sai su koma turɓaya,

A wannan rana dukan shirye-shiryensu sun ƙare.

5 Mai farin ciki ne mutumin da Allah na Yakubu ne yake taimakonsa,

Yana kuma dogara ga Ubangiji Allahnsa,

6 Wanda ya halicci sama, da duniya, da teku,

Da dukan abin da yake cikinsu.

Kullum yakan cika alkawaransa.

7 A yanke shari’arsa yakan ba wanda aka zalunta gaskiya.

Yana ba da abinci ga mayunwata.

Ubangiji yakan kuɓutar da ɗaurarru.

8 Yakan ba makafi ganin gari.

Yakan ɗaukaka waɗanda aka wulakanta.

Yana ƙaunar jama’arsa, adalai.

9 Yakan kiyaye baƙi waɗanda suke zaune a ƙasar.

Yakan taimaki gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu.

Yakan lalatar da dabarun mugaye.

10 Ubangiji Sarki ne har abada!

Ya Sihiyona, Allahnki zai yi mulki har dukan zamanai!

Yabo Ya tabbata ga Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 147

Yabon Alherin Allah a kan Urushalima

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Abu mai kyau ne mu yabi Allahnmu,

Abu mai daɗi ne, daidai ne kuma, a yabe shi.

2 Ubangiji yana rayar da Urushalima,

Yana komo da waɗanda aka kai su baƙunci a wata ƙasa.

3 Yakan warkar da masu karyayyiyar zuciya,

Yakan ɗaure raunukansu.

4 Ya ƙididdige yawan taurari,

Yakan kira kowanne da sunansa.

5 Ubangijinmu mai girma ne, Mai Iko Dukka,

Saninsa ya fi gaban aunawa.

6 Yakan ɗaukaka masu tawali’u,

Amma yakan ragargaza mugaye har ƙasa.

7 Ku raira waƙar yabo ga Ubangiji,

Ku yabi Allah da garaya.

8 Ya shimfiɗa gajimare a sararin al’arshi.

Ya tanada wa duniya ruwan sama,

Ya sa ciyayi su tsiro a kan tuddai.

9 Yakan ba dabbobi abincinsu,

Yakan ciyar da ‘ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kuka gare shi.

10 Ba ya jin daɗin ƙarfafan dawakai,

Ba ya murna da jarumawan mayaƙa.

11 Amma yana jin daɗin waɗanda suke tsoronsa,

Yana jin daɗin waɗanda suke dogara da madawwamiyar ƙaunarsa.

12 Ya Urushalima, ki yabi Ubangiji,

Ya Sihiyona, ki yabi Allahnki.

13 Shi yake riƙe da ƙofofinki da ƙarfi,

Yakan sa wa jama’arki albarka.

14 Yakan kiyaye kan iyakar ƙasarki lafiya,

Yakan kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.

15 Yakan ba da umarni,

Nan da nan umarnin yakan iso duniya.

16 Yakan aiko da dusar ƙanƙara mai kauri kamar ulu,

Ya watsa jaura kamar ƙura.

17 Yakan aiko da ƙanƙara kamar duwatsu,

Ba wanda yake iya jurewa da sanyin da yakan aiko!

18 Sa’an nan yakan ba da umarni,

Ƙanƙara kuwa ta narke,

Yakan aiko da iska, ruwa kuwa yakan gudu.

19 Yana ba Yakubu saƙonsa,

Koyarwarsa da dokokinsa kuma ga Isra’ila.

20 Bai yi wa sauran al’umma wannan ba,

Domin ba su san dokokinsa ba.

Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 148

Bari dukan Halittar Allah su yi Yabonsa

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Ku yabi Ubangiji daga sama,

Ku da kuke zaune a tuddan sama.

2 Ku yabe shi dukanku mala’ikunsa,

Ku yabe shi, ku dukan rundunansa na sama!

3 Ku yabe shi, ku rana da wata,

Ku yabe shi, ku taurari masu haskakawa!

4 Ku yabe shi, ku sammai mafi tsayi duka!

Ku yabe shi, ku ruwayen da kuke bisa sararin sama!

5 Bari su duka su yabi sunan Ubangiji!

Ya umarta, sai suka kasance.

6 Ta wurin umarninsa aka kafa su

A wurarensu har abada,

Ba su kuwa da ikon ƙi.

7 Ku yabi Ubangiji daga duniya,

Ku yabi Ubangiji, ku dodanin ruwa da dukan zurfafan teku.

8 Ku yabe shi, ku walƙiya, da ƙanƙara, da dusar ƙanƙara,

Da gizagizai, da ƙarfafan iska waɗanda suke biyayya da umarnansa!

9 Ku yabe shi, ku tuddai da duwatsu,

Da itatuwa ‘ya’ya da kurama.

10 Ku yabe shi dukanku dabbobi, na gida da na jeji,

Masu rarrafe da tsuntsaye!

11 Ku yabe shi, ku sarakuna da dukan kabilai,

Ku yabe shi, ku shugabanni da dukan hukumomi.

12 Ku yabe shi ku samari da ‘yan mata!

Ku yabe shi, ku tsoffafi da yara!

13 Bari dukansu su yabi sunan Ubangiji,

Sunansa ya fi dukan sauran sunaye girma,

Ɗaukakarsa kuwa tana bisa duniya da samaniya!

14 Ya sa al’ummarsa ta yi ƙarfi,

Domin dukan jama’arsa su yabe shi

Jama’arsa Isra’ila, wadda yake ƙauna ƙwarai!

Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 149

Bari Isra’ilawa su Yabi Ubangiji

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Ku raira sabuwar waƙa ga Ubangiji

Ku yabe shi cikin taron jama’arsa masu aminci!

2 Ki yi murna, ke Isra’ila, sabili da Mahaliccinki,

Ku yi farin ciki, ku jama’ar Sihiyona, sabili da Sarkinku!

3 Ku yabi sunansa, kuna taka rawa,

Ku kaɗa bandiri da garayu, kuna yabonsa.

4 Ubangiji yana jin daɗin jama’arsa,

Yakan girmama mai tawali’u ya sa ya ci nasara.

5 Bari jama’ar Allah su yi farin ciki saboda cin nasararsu,

Su raira waƙa don farin ciki.

6 Bari su yi sowa da ƙarfi

Sa’ad da suke yabon Allah, da takubansu masu kaifi.

7 Don su ci nasara bisa al’ummai,

Su kuma hukunta wa jama’a,

8 Su ɗaure sarakunansu da sarƙoƙi,

Su ɗaure shugabanninsu da sarƙoƙin baƙin ƙarfe,

9 Su hukunta wa al’ummai, kamar yadda Allah ya umarta.

Wannan shi ne cin nasarar jama’ar Allah!

Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 150

Ku Yabi Ubangiji

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Ku yabi Allah a cikin Haikalinsa!

Ku yabi ƙarfinsa a sama!

2 Ku yabe shi saboda manyan abubuwa

Waɗanda ya aikata!

Ku yabi mafificin girmansa!

3 Ku yabe shi da kakaki!

Ku yabe shi da garayu da molaye!

4 Ku yabe shi da bandiri kuna taka rawa!

Ku yabe shi da garayu da sarewa!

5 Ku yabe shi da kuge!

Ku yabe shi da kuge masu amo!

6 Ku yabi Ubangiji dukanku rayayyun talikai.

Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Categories
K. MAG

K. MAG 1

Amfanin Karin Magana

1 Karin maganar Sulemanu, ɗan Dawuda, Sarkin Isra’ila.

2 Ga Karin magana da za su taimake ka ka rarrabe da hikima, da kyakkyawar shawara, da fahimtar ma’anar zurfafan karin magana,

3 da yadda za ka karɓi koyarwa ta hanyar hikima, da adalci, da gaskiya, da sanin abin da yake daidai.

4 Sukan sa marar sani ya zama masani, sukan koya wa samari yadda za su zama masu amfani.

5 Waɗannan karin magana sukan ƙara wa masu ilimi hikima, sukan zama jagora ga masana,

6 don su fahimci ɓoyayyiyar ma’anar da take cikin karin magana, da mawuyatan al’amura waɗanda masu hikima suka ƙago.

7 In kana so ilimi dole ne ka fara da tsoron Ubangiji. Jahilai ba su san darajar hikima ba, sun kuwa ƙi su koya.

Gargaɗi da Faɗaka

8 Ɗana, ka kasa kunne ga koyarwar mahaifinka, ka mai da hankali ga abin da mahaifiyarka take faɗa.

9 Koyarwarsu za ta inganta halinka, ta zama kayan ado kamar kyakkyawan rawani a kanka, ko kyakkyawan abin wuya a wuyanka, don su ƙara maka kyau.

10 Ɗana sa’ad da masu zunubi suka jarabce ka, kada ka yarda

11 in suka ce maka, “Zo mu tafi mu nemi wani mutum mu kashe, mu je, mu fāɗa wa marasa laifi mu ji daɗi!

12 Ba mu damu da ransu da lafiyarsu ba, mu dai mu tafi mu kashe su, mu hallaka su ɗungum.

13 Za mu sami dukiya iri iri, mu cika gidajenmu da ganima!

14 Ka zo ka haɗa kai da mu, dukanmu kuwa za mu raba abin da muka sato.”

15 Ɗana, kada ka gama kanka da irin waɗannan mutane, ka yi nesa da su.

16 Ba su kasalar aikata mugunta, kullum a shirye suke su yi kisankai.

17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idon tsuntsun da ake so a kama.

18 Amma waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko. Ba za su kama kome ba, sai rayukansu.

19 Yin fashi yakan zama sanadin mutuwar ɗan fashi a koyaushe. Wannan shi ne abin da yakan sami kowane mutum da ya kama sana’ar sata.

Hikima Tana Kira

20 Ku kasa kunne! Hikima tana kira a tituna da a kasuwoyi.

21 Tana kira da ƙarfi a ƙofofin birni, a duk inda mutane suke tattaruwa.

22 Ta ce, “Wawayen mutane! Har yaushe za ku yi ta kasancewa haka? Har yaushe za ku daina jin daɗin yi wa mai ilimi ba’a? Faufau ba za ku taɓa koya ba?

23 Ku kasa kunne lokacin da nake tsauta muku, zan ba ku shawara mai kyau, mu yi tarayya cikin ilimina.

24 Ina ta kiranku ina gayyatarku ku zo, amma ba ku kula ba, ba ku mai da hankali gare ni ba.

25 Kun ƙi bin shawarwarina duka, ba ku yarda in gyara kuskurenku ba.

26 Saboda haka, lokacin da kuke shan wahala, zan yi muku dariya. Zan yi muku ba’a lokacin da razana ta auka muku,

27 sa’ad da ta zo muku kamar hadiri mai ƙaƙƙarfar iska mai wahalarwa, sa’ad da kuke shan azaba da damuwa.

28 Sa’an nan za ku kira gare ni, amma ba za ku same ni ba. Za ku neme ni a ko’ina, amma ba za ku same ni ba.

29 Domin ba ku taɓa sanin amfanin ilimi ba, kun ƙi tsoron Ubangiji a kullum.

30 Ba ku taɓa yarda da shawarata ba, ko ku yarda in gyara kuskurenku.

31 Saboda haka za ku karɓi sakayyarku, ayyukanku za su cuce ku.

32 Marasa sani sukan mutu saboda ba su yarda da hikima ba. Wawaye kuwa sukan hallaka saboda rashin kulawarsu.

33 Amma duk wanda ya kasa kunne gare ni, zai zauna lafiya. Ba abin da zai same shi, ba abin da zai tsorata shi.”

Categories
K. MAG

K. MAG 2

Sakamakon Neman Hikima

1 Ɗana, ka koyi abin da nake koya maka, sam kada ka manta da abin da na faɗa maka ka yi.

2 Ka kasa kunne ga abin da yake na hikima, ka yi ƙoƙari ka fahimce shi.

3 I, ka roƙi ilimi da tsinkaya.

4 Ka nema da iyakar ƙoƙarinka kamar yadda za ka nemi azurfa, ko kowace irin ɓoyayyiyar dukiya.

5 Idan ka yi za ka san abin da ake nufi da tsoron Ubangiji. Za ka yi nasara a kan koyon sanin Allah.

6 Ubangiji ne yake ba da hikima. Ilimi da fahimi kuwa suna cikin kalmominsa.

7 Shi yake tanada wa adalai taimako da kiyayewa, wato mutane masu aminci.

8 Yakan kiyaye waɗanda suke lura da kyau, ya kiyaye waɗanda suke dogara gare shi.

9 Idan ka kasa kunne gare ni za ka san abin da yake daidai, da abin da yake gaskiya, da abin da yake na kirki. Za ka san abin da za ka yi.

10 Za ka zama mai hikima, iliminka zai faranta maka rai.

11 Tsinkayarka da fahiminka za su tsare ka.

12 Za su hana ka aikata mugayen ayyuka, za su nisantar da kai daga mutane masu ta da hargitsi da irin maganganunsu,

13 mutane waɗanda suka bar zaman adalci don su zauna cikin duhun zunubi,

14 waɗanda suke jin daɗin yin laifi, suna nishaɗi cikin mugunta.

15 Ba za a dogara da su ba, ba kuwa za a iya amincewa da su ba.

16 Za a nisantar da kai daga mazinaciya, wadda take ƙoƙari ta lalatar da kai da daɗin bakinta,

17 marar aminci ga mijinta, wadda ta manta da tsarkakan alkawaran da ta ɗauka.

18 Idan ka tafi gidanta ka kama hanyar mutuwa. Tafiya can kama hanyar zuwa lahira ne.

19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa. Ba zai ƙara komowa ga hanyar rai ba.

20 Saboda haka dole ka bi hanyar da mutanen kirki suka bi, ka bi gurbin adalai.

21 Mutane adalai, masu kamewa, su ne za su zauna ƙasarmu.

22 Amma Allah zai fizge mugaye daga ƙasar, ya kuma tumɓuke masu zunubi kamar yadda ake tumɓuke shuke-shuke daga ƙasa.