Categories
K. MAG

K. MAG 23

1 Sa’ad da ka zauna cin abinci tare da babban mutum, ka tuna da yadda yake.

2 Idan kai mai son ci da yawa ne sai ka kanne.

3 Kada ka yi haɗamar kyakkyawan abincin da yake gabanku, zai yiwu wayo yake so ya yi maka.

4 Ka zama mai isasshiyar hikima, kada ka gajiyar da kanka garin ƙoƙarin neman dukiya.

5 Kuɗinka sun iya ƙarewa kamar ƙyiftawar ido, kamar suna da fikafikai su tashi kamar gaggafa.

6 Kada ka ci abincin marowaci, ko ka yi haɗamar kyakkyawan abincin da ya sa a gabanka.

7 Zai ce, “Bari a ƙara maka,” amma ba haka yake nufi ba. Kamar gashi yake a cikin maƙogwaronka.

8 Za ka harar da abin da ka ci, dukan daɗin bakinka zai tafi a banza.

9 Kada ka yi wa wawa magana irin ta haziƙai, gama ba zai yaba da maganarka ba.

10 Kada ka kuskura ka kawar da shaidar iyaka, ko ka ƙwace gonar marayu.

11 Ubangiji Mai Iko shi ne kāriyarsu, shi zai yi magana dominsu.

12 Ka mai da hankali ga malaminka, ka koyi dukan abin da kake iyawa.

13 Kada ka bar yaro ba horo, gama ko ka duke shi ba za a kashe shi ba.

14 Lalle ne za ka ceci ransa.

15 Ɗana, idan ka zama mai hikima zan yi murna ƙwarai.

16 Zan yi murna idan na ji kana faɗar magana da hikima.

17 Kada ka yi ƙyashin masu aikata zunubi tsoron Ubangiji kaɗai za ka sa a gaba.

18 Idan haka ta samu za ka yi farin ciki nan gaba.

19 Ka saurara, ya ɗana, ka zama mai hikima. Ka yi tunani mai zurfi a kan hanyarka.

20 Kada ka zauna da mashayan ruwan inabi, ko masu haɗama.

21 Gama bugaggu da ruwan inabi da masu zarin ci za su zama matalauta. Idan iyakar abin da kake yi daga ci sai barci ne, nan da nan za ka ga kana saye da tsummoki.

22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, gama da ba dominsa ba, da ba ka, sa’ad da mahaifiyarka ta tsufa ka nuna mata godiyarka.

23 Gaskiya, da hikima, da ilimi, da hankali, sun cancanta a saye su, kome tamaninsu.

24 Mahaifin adali yana da dalilin yin murna. Zai yi fāriya a kan ɗa mai hikima.

25 Ka sa mahaifinka da mahaifiyarka su yi fāriya da kai, ka sa mahaifiyarka farin ciki.

26 Ɗana ka mai da hankali sosai, irin zamana ya zamar maka kyakkyawan misali.

27 Karuwa, da mata mazinata, tarkon mutuwa ne su.

28 Sukan laɓe su jira ka kamar mafasa, suna sa mutane da yawa su zama marasa aminci.

29 Wa ake yi wa kaito? Wa yake da baƙin ciki? Wane ne mafaɗaci? Wa yake yin gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan ido?

30 Sai riƙaƙƙen mashayi wanda yake gaurayar ruwan inabi.

31 Kada ka bar ruwan inabi ya jarabce ka, ko da yake ja wur yake, har kana iya ganin kanka a cikin ƙoƙon, yana kuwa da kyan gani sa’ad da kake motsa shi.

32 Kashegari za ka ji kamar maciji mai dafi ne ya sare ka.

33 Idanunka za su riƙa gane-gane, ba za ka iya tunani ko ka faɗi magana sosai ba.

34 Za ka ji kamar kana can cikin teku, jirin teku na ɗibarka kana lilo a kan rufin jirgin ruwa da yake tangaɗi.

35 Za ka ce, “Lalle an doke ni, sosai an daddoke ni amma ban san lokacin ba, me ya sa ban farka ba? Ina bukatar in ƙara sha.”

Categories
K. MAG

K. MAG 24

1 Kada ka ji ƙyashin mugaye, kada ka yi ƙoƙarin yin abuta da su.

2 Duk tunaninsu na yin mugunta ne, a duk lokacin da suka buɗe bakinsu sai sun cuci wani.

3 An gina gidaje a kan harsashin hikima da fahimi.

4 Ta wurin ilimi a kan ƙawata ɗakuna da kyawawan kayayyaki masu tamani.

5 Mai hikima ƙaƙƙarfa ne, i, mai ilimi yana daɗa ƙarfi.

6 Banda wannan ma, dole ne ka shisshirya a natse kafin ka kama yaƙi. Bisa ga shawarwarin da za ka samu ne za ka yi nasara.

7 Kalmomi masu hikima sun yi wa wawa zurfin ganewa ƙwarai, ba shi da ta cewa sa’ad da ake magana a kan muhimman abubuwa.

8 Idan a ko yaushe shirye-shiryen mugunta kake, za ka yi suna a kan kuta tashin hankali.

9 Kowace irin dabarar da wawa yake tunani a kanta zunubi ne. Jama’a suna ƙin mutum mai rainako.

10 Idan ba ka da ƙarfi a lokacin hargitsi, hakika ka tabbata marar ƙarfi.

11 Kada ka ji nauyin ceton wanda ake janye da shi zuwa inda za a kashe shi.

12 Mai yiwuwa ne ka ce kai ba ruwanka, amma Allah ya sani, yana kuwa auna manufofinka. Yana lura da kai, ya kuwa sani. Yakan sāka wa mutane a kan abin da suke aikatawa.

13 Ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau. Kamar yadda kakin zuma yake da zaƙi a harshenka,

14 haka ilimi da hikima suke da amfani ga ranka. Ka same su, a gaba za ka yi farin ciki.

15 Kada ka shirya dabarun yi wa amintacce ƙwace, ko ka ƙwace masa gidansa, wannan mugunta ce.

16 Ko sau nawa amintaccen mutum ya faɗi, ba abin damuwa ba ne, gama a ko yaushe zai sāke tashi, amma masifa takan hallaka mugaye.

17 Kada ka yi murna sa’ad da bala’i ya aukar wa maƙiyinka.

18 Ubangiji zai sani in kana murna, ba kuwa zai so haka ba, mai yiwuwa ne ba zai hukunta shi ba.

19 Kada ka damu saboda mugaye, kada ka yi ƙyashin masu aikata abin da ba daidai ba.

20 Gama mugun mutum ba shi da sa zuciya, ba abin da zai sa zuciya a kansa nan gaba.

21 Ɗana, ka yi tsoron Ubangiji, ka kuma ji tsoron sarki, kada ka yi harkar kome da mutanen da suka tayar musu.

22 Irin waɗannan mutane sukan hallaka farat ɗaya. Ka taɓa yin tunani a kan bala’in da Allah ko sarki sukan aukar?

Waɗansu sauran Karin Magana na Hikima

23 Masu hikima kuma sun faɗi waɗannan abu.

Kuskure ne alƙali ya yi son zuciya.

24 Idan ya kuɓutar da mugu, kowane mutum da yake a duniya zai la’anta shi ya ƙi shi.

25 Alƙalan da suke hukunta wa mai laifi kuwa, za su arzuta, su ji daɗin kyakkyawan suna.

26 Amsar gaskiya ita ce alamar abuta ta ainihi.

27 Kada ka gina gidanka ka kafa shi, sai ka gyara gonakinka, ka tabbata za ka sami abin zaman gari.

28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isasshen dalili ba, ko ka faɗi ƙarya a kansa.

29 Kada ka ce, “Zan yi masa daidai da yadda ya yi mini, zan rama masa!”

30 Na ratsa ta gonakin inabin wani malalaci, dakiki,

31 suna cike da ƙayayuwa, ciyayi sun sha kansu, katangar dutse da take kewaye da su ta faɗi.

32 Da na dubi wannan, na yi tunani a kansa, ya zamar mini ishara.

33 “Yi ta ruruminka, ci gaba da barcinka, rungume hannuwanka don ka shaƙata.”

34 Amma sa’ad da kake ta sharar barci fatara za ta auka maka kamar ƙungiyar ‘yan fashi.

Categories
K. MAG

K. MAG 25

Waɗansu sauran Karin Magana na Sulemanu

1 Ga waɗansu sauran karin maganar Sulemanu waɗanda magatakardan Hezekiya Sarkin Yahuza suka juya.

2 Muna girmama Allah saboda abin da ya rufe, muna girmama sarakuna saboda abin da suka ba da bayaninsa.

3 Ba ku taɓa sanin abin da sarki yake tunani ba, gama tunaninsa sun fi ƙarfinmu. Kamar nisan sararin sama suke ko zurfafan teku.

4 Ka tace azurfa, gwani kuwa zai yi wani kyakkyawan abu da ita.

5 A kawar da mugayen mashawarta daga gaban sarki, hukumarsa za ta shahara a kan adalci.

6 Sa’ad da kake tsaye a gaban sarki, kada ka nuna kai wani abu ne, kana kai kanka inda Allah bai kai ka ba.

7 Gara a roƙe ka ka hau zuwa babban matsayi, da a faɗa maka ka ba da wurin da kake ga wanda ya fi ka maƙami.

8 Kada ka yi garajen kai ƙara a majalisa. Idan wani mashaidi ya nuna kai kake da kuskure, me za ka yi?

9 Idan kai da maƙwabcinka kun saɓa, ku daidaita a tsakaninku, kada a tona asiri.

10 Mai yiwuwa ne wani ya ji ya zarge ku, ba za ku taɓa rabuwa da wannan kunya ba.

11 Manufar da aka bayyana sosai kamar zubin zinariya take wanda aka yi a kan azurfa.

12 Faɗakarwar da mutumin da ya gogu da al’amuran duniya ya yi ga wanda yake da niyya ya kasa kunne, tamaninta ya fi na zoben zinariya, ko kayan ado da aka yi da zinariya tsantsa.

13 Amintaccen manzo yakan wartsakar da wanda ya aike shi, kamar ruwan sanyi yake a lokacin zafi.

14 Mutanen da suke yin alkawari, ba su cikawa, kamar holoƙo suke, hadirin kaka.

15 Rinjayen da aka yi cikin haƙuri yakan rushe ƙaƙƙarfar tsayayya, har ma yakan i wa masu ƙarfin gaske.

16 Kada ka kuskura ka sha zuma gaba da kima, in ya yi maka yawa za ka yi hararwa.

17 Kada ka cika ziyartar maƙwabcinka, ko zai gaji da kai har ya ƙi ka.

18 Mutumin da yakan faɗi ƙarairayi a kan maƙwabcinsa, shi kamar kakkaifan takobi ne, ko kulki, ko kibiya mai tsini.

19 Dogara ga marar aminci a lokacin hargitsi, kamar ƙoƙarin yin tauna da ruɓaɓɓun haƙora ne, ko yin tafiya da mai gurguwar ƙafa,

20 ko kuma ka yi ƙoƙarin jin ɗumi ta wurin tuɓe tufafinka a ranar da ake sanyi.

Raira waƙa ga mai baƙin ciki kamar marmasa gishiri a kan rauni ne.

21 Idan maƙiyinka yana jin yunwa ka cishe shi, idan yana jin ƙishi ka ba shi abin sha.

22 Za ka sa ya sha kunya, Ubangiji kuma zai sāka maka.

23 Iskar arewa takan kawo ruwan sama, haka kuma jita-jita takan kawo fushi.

24 Gara zama a saƙo da zama a gida ɗaya tare da mata mai mita.

25 Jin labari mai daɗi wanda ba ka zato, yana kamar shan ruwan sanyi ne a sa’ad da ka sha rana kana jin ƙishi.

26 Mutumin kirki wanda yakan yarda da mugun yana tunasshe ka da ƙazantattun maɓuɓɓuga ko rijiya mai dafi.

27 Kamar yadda shan zuma da yawa ba shi da kyau a gare ka, haka kuma ƙoƙarin neman yabo mai yawa yake.

28 Idan ba ka iya danne fushinka ba, ka zama mai kasala kamar birnin da ba shi da garuka, yana buɗe don a faɗa masa.

Categories
K. MAG

K. MAG 26

1 Yabo bai dace da wawa ba, kamar yadda dusar ƙanƙara ba ta dace da lokacin zafi ba, ko ruwan sama a lokacin girbi.

2 La’ana ba za ta kama ka ba, sai dai in ka cancance ta. Tana kamar tsuntsayen da suke firiya da dare ba za su sauka ba.

3 Sai ka fyaɗi doki, ka sa wa jaki linzami, wawa kuma sai ka doke shi.

4 Idan ka amsa tambayar wauta, ka zama wawa daidai da mutumin da ya yi tambayar.

5 Ka amsa wauta ga tambayar wauta, wanda ya yi tambayar zai gane wawancinsa.

6 Mutumin da ya sa wawa ya isar masa da saƙo ya datse ƙafafunsa, yana nemar wa kansa wahala.

7 Wawa yakan yi amfani da karin magana kamar yadda tauyayyen mutum yake amfani da ƙafafunsa.

8 Wanda ya yabi wawa yana kama da wanda ya ɗaura dutse a majajjawa.

9 Karin magana a bakin wawa kamar sukar ƙaya ce a hannun mai maye.

10 Wanda ya ɗauki wawa aiki yana cutar duk wanda aikin ya shafa.

11 Wawan da yake maimaita aikin wautarsa yana kama da kare mai yin amai ya koma ya tanɗe.

12 Gwamma riƙaƙƙen wawa da mutum mai ganin kansa mai hikima ne.

13 Don me malalaci yakan kasa fita daga gida? Zaki yake tsoro?

14 Malalaci yana ta jujjuyawa a gadonsa kamar yadda ƙyauren ƙofa take juyawa.

15 Malalaci yana sa hannu cikin ƙwaryar abinci, amma ya kāsa kaiwa bakinsa.

16 Malalaci yana ganin kansa mai hikima ne fiye da mutum bakwai waɗanda suke da dalilai a kan ra’ayinsu.

17 Mutumin da ya tsoma baki cikin jayayyar da ba ta shafe shi ba sa’ad da yake wucewa, yana kama da mutum wanda yake kama kare a kunne.

18-19 Mutum wanda yakan ruɗi maƙwabcinsa sa’an nan ya ce, wasa yake yi kawai, yana kama da mahaukaci wanda yake wasa da wuta, da kibau, da mutuwa.

20 Idan ba itace wuta takan mutu, haka kuma idan ba mai gulma ba za a yi jayayya ba.

21 Kamar yadda gawayi yake ga garwashin wuta, itace kuma ga wuta, haka mai gardama yake ga jayayya.

22 Kamar yadda lomar abinci mai daɗi takan gangara can cikin ciki haka maganar mai gulma take.

23 Bakin da ba ya faɗar gaskiya, da zuciya mai ƙiyayya suna kama da kaskon da aka dalaye da azurfar da ba a tace ba.

24 Mai yin ƙiyayya yakan ɓoye ta da maganar bakinsa, yana kuma ƙunshe da munafunci.

25 Sa’ad da yake magana mai kyau kada ka gaskata shi, domin zuciyarsa tana cike da mugunta.

26 Ko da yake kila zai ɓoye ƙiyayyarsa, duk da haka muguntarsa za ta bayyana ga mutane.

27 Wanda ya haƙa ramin mugunta shi zai faɗa ciki, wanda kuma ya mirgino dutse, zai fāɗo a kansa.

28 Maƙaryaci yana ƙin wanda ya yi wa ƙarya, mai daɗin baki kuma yakan aikata ɓarna.

Categories
K. MAG

K. MAG 27

1 Kada ka yi fāriya a kan abin da za ka yi gobe domin ba ka san abin da zai faru daga yanzu zuwa gobe ba.

2 Bari waɗansu su yabe ka ko da baƙi ne, faufau kada ka yabi kanka.

3 Dutse da yashi suna da nauyi ƙwarai, amma nauyin wahalar da wawa zai haddasa ya fi nasu duka.

4 Fushi mugun abu ne mai hallakarwa, amma duk da haka bai kai ga kishi ba.

5 Gara ka tsauta wa mutum a fili da ka bar shi ya zaci ba ka kula da shi ba sam.

6 Aboki aboki ne ko da ya cuce ka, amma maƙiyi ko ya rungume ka kada ka sake!

7 Wanda ya ƙoshi ba zai ko kula da zuma ba, amma wanda yake jin yunwa abinci mai ɗaci zaƙinsa yake ji.

8 Mutumin da ya bar gida yana kama da tsuntsun da ya bar sheƙarsa.

9 Turare da man ƙanshi sukan sa ka ji daɗi, haka abuta ta ainihi takan ƙara maka ƙarfi.

10 Kada ka manta da abokanka, ko abokan mahaifinka. Idan kana shan wahala kada ka nemi taimako wurin ɗan’uwanka. Maƙwabci na kusa yana iya taimakonka fiye da ɗan’uwan da yake nesa.

11 Ɗana, ka zama mai hikima, ni kuwa zan yi farin ciki, zan iya amsa kowace irin sūkar da wani zai yi mini.

12 Mutum mai hankali yakan hango hatsari ya kauce masa, amma mutumin da ba shi da kula, yakan kutsa kai ciki, daga baya ya yi da na sani.

13 Ka karɓe tufar wanda ya zamar wa baƙo lamuni, da kuma wanda ya zama lamunin karuwa.

14 In ka farkar da abokinka da babbar murya tun da sassafe, daidai ne da zaginsa.

15 Mace mai mita kamar ɗiɗɗigar ruwa take ba ƙaƙƙautawa.

16 Kaƙa za ka iya sa ta ta kame bakinta? Ka taɓa ƙoƙarin tsai da iska? Ko kuwa ka taɓa ƙoƙarin dintsi mai a tafin hannunka?

17 Daga wurin mutane mutane suke koyo, kamar yadda a kan wasa ƙarfe da ƙarfe.

18 Ka lura da itacen ɓaure, zai yi ‘ya’ya ka ci. Baran da ya lura da maigidansa za a girmama shi.

19 Yadda kake ganin fuskarka a ruwa, haka kake ganin kanka a zuciyarka.

20 Muradin mutum kamar lahira yake, a kullum ba ya ƙoshi.

21 Da wuta ake gwada azurfa da zinariya, amma yabon da ake yi wa mutum shi ne magwajinsa.

22 Ko da za ka doki wawa ka bar shi tsakanin rai da mutuwa, duk da haka yana nan da wautarsa kamar yadda yake.

23 Ka lura da garkunan tumakinka da na shanunka da kyau iyakar iyawarka,

24 domin dukiya ba ta tabbata har abada, al’ummai ma haka ne.

25 Ka yanki ingirici, lokacin da yake toho kana iya yankar ciyawa a gefen tuddai.

26 Kana iya yin tufafi da ulun tumakinka, kana iya sayen gona da kuɗin awakinka.

27 Madarar awakinka za ta zama abincinka kai da iyalinka, da kuma barorinka ‘yan mata.

Categories
K. MAG

K. MAG 28

Mugaye da Adalai

1 Mugun mutum yakan gudu, alhali kuwa ba mai korarsa, amma amintaccen mutum kamar zaki yake, ba shi da tsoro.

2 Al’umma za ta ƙarfafa ta jure idan shugabanninta masu basira ne, masu hankali. Amma idan ƙasar mai aikata zunubi ce za ta sami shugabanni da yawa.

3 Mai mulki wanda yake zaluntar talakawa, ya zama kamar ruwa mai lalatar da amfanin gona.

4 Wanda ba ya bin doka tare da mugaye yake, amma idan kana bin doka kai abokin gāban mugaye ne.

5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada sun san ta sosai.

6 Gara ka zama matalauci mai aminci da ka zama mawadaci, marar aminci.

7 Saurayi wanda ya kiyaye doka mai basira ne shi, amma wanda yake abuta da ‘yan iska zai zama mai jawo wa mahaifinsa kunya.

8 Idan kana tara dukiya ta wurin ba da bashi da ruwa kana kuma ƙwarar jama’a, dukiyarka za ta koma ga wanda yake yi wa talakawa alheri.

9 Idan ka ƙi biyayya ga doka, Allah zai ƙi jin addu’o’inka.

10 Idan ka yaudari mutumin kirki don ya faɗa cikin mugunta, kai kanka ne za ka fāɗa cikin tarkon da ka haƙa. Marar laifi kuwa zai sami babban sakamako.

11 Attajirai, a ko yaushe, zato suke su masu hikima ne, amma matalauci mai tunani ya fi sanin abin da yake daidai.

12 Sa’ad da mutanen kirki suke sarauta, kowa da kowa yakan yi biki, amma sa’ad da mugaye suka kama mulki mutane sukan riƙa ɓuya.

13 Ba za ka taɓa cin nasara a zamanka ba muddin kana ɓoye laifofinka. Ka hurta zunubanka ka tuba, sa’an nan Allah zai yi maka jinƙai.

14 Mutumin da yake tsoron Ubangiji ko yaushe, zai yi farin ciki, amma idan ya taurare zai lalace.

15 Talakawa ba su da wani taimako sa’ad da suke ƙarƙashin mulkin mugun. Abin tsoro ne shi kamar zaki mai ruri, ko beyar mai sanɗa.

16 Mai mulki wanda ba shi da basira yakan zama mai mugun tsanani. Amma wanda yake ƙin rashin aminci, ko ta ƙaƙa zai daɗe yana mulki.

17 Mutumin da yake da laifin kisankai, yana haƙa wa kansa kabari da gaggawa. Kada ka yi ƙoƙarin hana shi.

18 Ka yi aminci za ka zauna lafiya, idan kuwa ka yi rashin aminci za ka fāɗi.

19 Manomin da yake aiki sosai, zai sami wadataccen abinci, amma mutanen da suke zaman banza ko yaushe, za su zama matalauta.

20 Amintaccen mutum zai cika kwanakinsa lafiya, amma idan kana so ka sami dukiya dare ɗaya, za a hukunta ka.

21 Nuna sonkai mugun abu ne, waɗansu alƙalai sukan aikata mugunta saboda ‘yar ƙaramar rashawa.

22 Mutum mai haɗama yana gaggawar samun dukiya, bai kuwa sani ba, ashe, fatara ce za ta same shi.

23 Wanda ya tsauta wa mutum zai sami yabo daga baya, fiye da wanda ya yi masa daɗin baki.

24 Wanda yake yi wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa sata, yana kuwa tsammani ba laifi ba ne, daidai da ɓarawo yake.

25 Mutum mai haɗama yana haddasa tashin hankali, amma wanda ya dogara ga Ubangiji zai sami wadar zuci.

26 Wanda yake dogara ga son zuciyarsa, wawa ne, amma wanda yake tafiya cikin hikima zai kuɓuta.

27 Wanda yake bayarwa ga matalauta, ba zai talauce ba, amma wanda bai kula da su ba, mutane da yawa za su la’ance shi.

28 Mutane sukan ɓuya sa’ad da mugaye suka sami iko, amma sa’ad da iko ya fita daga hannunsu adalai sukan ƙaru.

Categories
K. MAG

K. MAG 29

1 Wanda ake ta tsauta wa a kai a kai, amma ya taurare, ba makawa tasa ta ƙare farat ɗaya.

2 Sa’ad da masu adalci suke mulki, jama’a sukan yi murna, amma sa’ad da mugaye suke mulki, jama’a sukan yi nishi.

3 Wanda yake ƙaunar hikima yana faranta zuciyar mahaifinsa.

Amma wanda yake abuta da karuwai zai lalatar da dukiyarsa.

4 Sarkin da yake aikata adalci ƙasarsa za ta yi ƙarƙo, amma wanda yake karɓar rashawa zai lalatar da ƙasar.

5 Mutum wanda yake yi wa maƙwabcinsa daɗin baƙi yana kafa wa kansa tarko.

6 Laifin mugun zai zama tarko a gare shi, amma adali zai raira waƙa, ya yi farin ciki.

7 Adali yana sane da hakkin matalauta, amma mugun bai san wannan ba.

8 Ashararai sukan sa wa birni wuta, amma masu hikima sukan kwantar da hasala.

9 Idan gardama ta shiga tsakanin mai hikima da wawa, sai wawa ya yi ta fushi, ko kuwa ya yi ta dariya, gardamar dai ba za ta ƙare ba.

10 Mutane masu kisankai suna ƙin amintaccen mutum, amma adalai za su kiyaye ransa.

11 Wawa yakan nuna fushinsa ko yaushe, amma mutum mai hikima yakan kanne fushinsa.

12 Idan mai mulki yana kasa kunne ga maganganun ƙarya, dukan ma’aikatansa za su zama maƙaryata.

13 Matalauci da azzalumi suna tarayya a abu ɗaya, wato dukansu Ubangiji ne yake ba su ganin gari.

14 Idan sarki yana yi wa talakawa shari’ar gaskiya, zai daɗe yana mulki.

15 Horo da tsautawa suna ba da hikima, amma yaron da aka sangarta zai jawo wa mahaifiyarsa kunya.

16 Sa’ad da mugaye suke mulki, laifofi suka ƙaru, amma adalai za su ga faɗuwar waɗannan mutane.

17 Ka hori ɗanka zai daɗaɗa maka rai, ya kuma faranta maka zuciya.

18 Inda ba a bin faɗar Allah, jama’a za su kangare, amma mai farin ciki ne wanda yake kiyaye dokar Allah.

19 Bara ba ya horuwa ta wurin magana kawai, gama ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba.

20 Ka ga mutum mai garajen yin magana? To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi.

21 Baran da aka shagwaɓa tun yana yaro, a ƙarshe zai ɗauki kansa tankar magājin gida.

22 Mutum mai saurin fushi yakan ta da faɗa, mai zafin rai kuma yakan aikata laifi da yawa.

23 Girmankan mutum zai jawo masa ƙasƙanci, amma za a girmama mai tawali’u.

24 Abokin ɓarawo mugun maƙiyin kansa ne, yana jinsa yana ta rantsuwa, amma ba zai ce kome ba.

25 Jin tsoron mutane tarko ne, amma wanda ya dogara ga Ubangiji za a ɗaukaka shi.

26 Mutane da yawa sukan nemi farin jini daga wurin mai mulki, amma Ubangiji ne yake yi wa mutum adalci.

27 Mutum marar gaskiya abin ƙyama ne ga adali, adali kuma abin ƙyama ne ga mugun.

Categories
K. MAG

K. MAG 30

Hikimar Agur

1 Waɗannan su ne maganar Agur ɗan Yake, da ya yi wa Etiyel da Yukal,

2 “Hakika wautata ta sa na zama kamar dabba ba mutum ba,

Ba ni kuwa da fahimi irin na mutum.

3 Ban koyi hikima ba,

Ban kuwa san kome game da Allah ba.

4 Wa ya taɓa hawa cikin Sama ya sauko?

Wa ya taɓa kama iska cikin tafin hannunsa?

Wa ya taɓa ƙunshe ruwa cikin rigarsa?

Wa kuma ya kafa iyakar duniya?

Ina sunansa, ina kuma sunan ɗansa?

Hakika ka sani!

5 “Kowace maganar Allah takan tabbata. Shi garkuwa ne ga waɗanda suke fakewa a wurinsa.

6 Kada ka yi ƙari a kan maganarsa, don kada ya tsauta maka, a kuma bayyana kai maƙaryaci ne.”

Waɗansu Karin Magana kuma

7 Abu biyu na roƙe ka, kada ka hana mini su kafin in mutu.

8 Ka kawar da ƙarya nesa da ni. Kada ka ba ni talauci ko dukiya, sai dai ka ba ni abinci daidai da bukatata,

9 don kada in wadata, har in yi musunka, in ce, “Wane ne Ubangiji?” Kada kuwa in yi talauci har in yi sata in saɓi sunan Allahna.

10 Kada ka kushe bara a wurin maigidansa domin kada ka yi laifin da zai sa a la’ance ka.

11 Akwai waɗansu mutane da sukan zagi iyayensu maza, ba sukan kuma nuna godiya ga iyayensu mata ba.

12 Akwai waɗansu mutanen da suke ganin kansu tsarkaka ne, alhali kuwa ƙazamai ne su.

13 Akwai waɗansu mutane da suke yi wa jama’a ƙallon raini suna ɗaurin gira.

14 Akwai waɗansu mutane waɗanda haƙoransu takuba ne, mataunansu kuma wuƙaƙe ne, don su cinye matalauta da masu fatara daga duniya.

15-16 Matsattsaku tana da ‘ya’ya mata biyu, ana kiransu, “Ba ni, Ba ni.”

Akwai abu uku da ba su ƙoshi, i, har huɗu ma da ba su cewa, “Ya isa,” wato

lahira,

macen da ba ta haihuwa,

ƙasa wadda ba ta ƙoshi da ruwa,

wuta wadda ba ta cewa, “Ya isa.”

17 Idan ɗa ya raina mahaifi, ya kuma yi wa mahaifiya ba’a hankakin kwari za su ƙwaƙule masa idanu, ‘ya’yan mikiya za su cinye.

18-19 Akwai abu uku, i, har huɗu ma, waɗanda ban iya fahimtar su ba, wato

yadda gaggafa take tashi a sararin sama,

yadda maciji yake jan ciki a kan dutse,

yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku,

Sha’anin namiji da ‘ya mace.

20 Ga yadda al’amarin mazinaciya yake, takan yi sha’aninta sa’an nan ta yi wanka ta ce, “Ban yi laifin kome ba!”

21-23 Akwai abu uku, i, har huɗu ma waɗanda duniya ba ta jurewa da su, wato

bara da ya zama sarki,

wawa da ya ƙoshi da abinci,

mummunar mace da ta sami miji,

baiwar da ta gāji uwargijiyarta.

24-28 Akwai ƙananan abubuwa huɗu a duniya, amma suna da hikima ƙwarai, wato

tururuwa talikai ne marasa ƙarfi, amma duk da haka sukan tanadi abincinsu da rani,

remaye ba ƙarfafa ba ne, duk da haka suna yi wa kansu gidaje a cikin duwatsu,

fara ba su da sarki, amma duk da haka suna tafiya sahu-sahu.

ƙadangare ma wanda ka iya kama shi a hannu, amma yana zama a cikin fādodin sarakuna.

29-31 Akwai abu uku, i, har huɗu ma da suke da kwarjini da taƙama a tafiyarsu, wato

Zaki wanda ya fi dukan dabbobi ƙarfi, ba ya ratse wa kowa daga cikinsu,

bunsuru da zakara mai taƙama,

sarkin da yake tafiya gaban jama’arsa.

32 Idan ka yi wauta kana ta ɗaukaka kanka, ko kuwa kana shirya mugunta, ka tsaya ka yi tunani!

33 Gama kaɗa madara takan kawo mai, murɗa hanci takan sa a yi haɓo, tsokanar fushi takan kawo jayayya.

Categories
K. MAG

K. MAG 31

Shawara ga Sarki

1 Wannan ita ce maganar sarki Lamuwel wadda uwarsa ta koya masa.

2 “Mene ne, ɗana? Mene ne, ya ɗana ne cikina? Mene ne, ɗana na wa’adi?

3 Kada ka ba da ƙarfinka ga mata, kada kuwa ka mai da hankali gare su, waɗanda suke hallaka sarakuna.

4 Bai dace ba, ya Lamuwel, bai dace ba ko kaɗan, sarakuna su sha ruwan inabi, ko masu mulki su yi marmarin barasa,

5 don kada su sha su manta da doka, su kuma kauce wa gaskiya a shari’ar waɗanda aka zalunta.

6 A ba da barasa ga wanda yake cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi kuma ga waɗanda suke cikin ɓacin rai.

7 Bari ya sha don ya manta da talaucinsa, don kada kuma ya ƙara tunawa da ɓacin ransa.

8 “Ka yi magana domin bebaye, domin kuma hakkin dukan waɗanda ba su da wani mataimaki.(1Sam 19.4; Ayu 29.12-17)

9 Ka yi magana dominsu, ka yi shari’ar adalci, ka kiyaye hakkin matalauta da masu bukata.”

Yabon Macen Kirki

10 Wa yake iya samun cikakkiyar mace? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.

11 Mijinta yakan amince da ita, ba kuwa zai yi hasara ba.

12 Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakinta.

13 Takan samo ulu da lilin, ta yi saƙa da hannuwanta da farin ciki.

14 Takan kawo abincinta daga nesa, kamar fatake.

15 Takan yi asubanci ta shirya wa iyalinta abinci, ta kuma shirya wa ‘yan matan gidanta aike-aiken da za su yi.

16 Takan lura da gona sosai kafin ta saya, da ribar da ta ci take dasa gonar inabi.

17 Takan himmantu ta yi aiki tuƙuru.

18 Ta sani akwai riba a cikin kasuwancinta. Fitilarta na ci dare farai.

19 Da hannunta take kaɗi, tana kuma saƙa da hannuwanta.

20 Takan yi wa matalauta da masu fatara karamci.

21 Ba ta jin tsoron lokacin sanyi gama ‘ya’yanta duka suna da tufafi masu ƙauri.

22 Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa, tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.

23 Mijinta sananne ne a dandali, sa’ad da yake zaune tare da dattawan gari.

24 Takan yi riguna na lilin ta sayar, takan kuma sayar wa fatake da abin ɗamara.

25 Wadata da mutunci su ne suturarta. Ba ta jin tsoron tsufa.

26 Tana magana da hikima. Koyarwarta ta alheri ce.

27 Tana lura da al’amuran ‘ya’yanta da kyau. Ba ruwanta da ƙyuya.

28 ‘Ya’yanta sukan tashi su gode mata, mijinta kuma yana yabonta.

29 Ya ce, “Mata da yawa sun yi abin yabo, amma ke kin fi su duka.”

30 Kayan tsari da jamali duk banza ne, amma mace mai tsoron Ubangiji, ita ce abar yabo.

31 A yi mata cikakken yabo saboda ayyukanta, za a yabi ayyukanta a dandali.

Categories
M. HAD

M. HAD 1

Kome Banza Ne

1 Maganar Mai Wa’azi ɗan Dawuda, Sarkin Urushalima.

2 Banza a banza ne, in ji Mai Hadishi,

Banza a banza ne, dukan kome banza ne.

3 Wace riba ce mutum zai samu daga cikin aikinsa,

Da yake yi a duniya?

4 Zamani yakan wuce, wani zamani kuma ya zo,

Amma abadan duniya tana nan yadda take.

5 Rana takan fito, takan kuma faɗi,

Sa’an nan ta gaggauta zuwa wurin fitowarta.

6 Iska takan hura zuwa kudu, ta kuma hura zuwa arewa,

Ta yi ta kewayawa, har ta koma inda ta fito.

7 Kowane kogi yakan gangara zuwa teku,

Amma har yanzu teku ba ta cika ba.

Ruwan yakan koma mafarin kogin,

Ya sāke gangarawa kuma.

8 Kowane abu yana sa gajiya,

Gajiyar kuwa ta fi gaban magana.

Idanunmu ba sā ƙoshi da gani,

Haka kuma kunnuwanmu ba sā ƙoshi da ji.

9 Abin da ya faru a dā, shi zai sāke faruwa,

Abin da aka yi a dā, shi za a sāke yi.

A duniya duka ba wani abu da yake sabo.

10 Da akwai wani abu da za a ce,

“Duba, wannan sabon abu ne”?

Abin yana nan tuntuni kafin zamaninmu.

11 Ba wanda yake iya tunawa da abin da ya faru a dā,

Da abin da zai faru nan gaba.

Ba wanda zai iya tunawa da abin da zai faru

A tsakanin wannan lokaci da wancan.

Abin da Mai Hadishi Ya Kware da Shi

12 Ni Mai Hadishi sarki ne, na sarauci Isra’ilawa a Urushalima.

13 Na ɗauri aniya in jarraba, in bincika dukan abubuwan da ake yi a duniyan nan.

Allah ya ƙaddara mana abu mai wuya.

14 Na ga dukan abin da ake yi a duniya, duk aikin banza ne da ɓata lokaci kawai.

15 Ba za a iya miƙar da abin da ya tanƙware ba, ba kuma za a iya ƙidaya abin da ba shi ba.

16 Na ce wa kaina, “Na zama babban mutum, na fi duk wanda ya taɓa mulkin Urushalima hikima. Hakika na san hikima da ilimi.”

17 Na ɗaura aniya in san bambancin da yake tsakanin ilimi da wauta, da a tsakanin hikima da gāɓanci. Amma na gane harbin iska nake yi kawai.

18 Gwargwadon hikimarka gwargwadon damuwarka, gwargwadon ƙarin iliminka gwargwadon jin haushinka.