Categories
ISH

ISH 12

Waƙar Godiya

1 Rana tana zuwa sa’ad da jama’a za su raira waƙa, su ce,

“Ina yabonka ya Ubangiji! A dā ka yi fushi da ni,

Amma yanzu kana yi mini ta’aziyya, ba za ka ƙara yin fushi da ni ba.

2 Allah ne Mai Cetona,

Zan dogara gare shi, ba zan ji tsoro ba.

Ubangiji ne yake ba ni iko da ƙarfi,

Shi ne Mai Cetona.”

3 Kamar yadda ruwan daɗi yake sa mai jin ƙishirwa farin ciki,

Haka nan jama’ar Allah suke farin ciki sa’ad da ya cece su.

4 A wannan rana jama’a za su raira waƙa, su ce,

“Ku yi wa Ubangiji godiya! Ku nemi taimako a gare shi!

Ku faɗa wa dukan sauran al’umma abin da ya aikata!

Ku faɗa musu irin girman da yake da shi!

5 Ku raira waƙa ga Ubangiji, saboda manyan ayyuka da ya aikata.

Bari dukan duniya ta ji labarin.

6 Bari dukan waɗanda suke zaune a Sihiyona su yi sowa su raira waƙa!

Gama Mai Tsarki, Allah na Isra’ila, mai girma ne,

Yana zaune tare da mutanensa.”

Categories
ISH

ISH 13

Annabci a kan Babila

1 Wannan shi ne saƙo a kan Babila, wanda Ishaya ɗan Amoz ya karɓa daga wurin Allah.

2 A kan tudun da yake faƙo ka kafa tutar yaƙi, ka ta da murya ka ba mayaƙa umarni, ka ɗaga hannu, ka ba su alamar kama yaƙi a ƙofofin birni mai alfarma.

3 Ubangiji ya kira mayaƙansa masu jin kansu, masu ƙarfin zuciya, domin su yi jahadi, su hukunta wa waɗanda suke fushi da su.

4 Ji hayaniyar da ake yi a duwatsu da amon babban taron jama’a. Amon al’ummai da mulkoki suna tattaruwa. Ubangiji Mai Runduna yana shirya mayaƙansa domin yaƙi.

5 Suna zuwa daga manisantan ƙasashe, daga kan iyakokin duniya. Ubangiji yana zuwa da fushinsa, ya lalatar da dukan ƙasar.

6 Ku yi ihu saboda shan azaba, ranar Ubangiji ta yi kusa. Ranar da Mai Iko Dukka zai kawo hallaka.

7 Hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.

8 Dukansu za su firgita, azaba za ta ci ƙarfinsu kamar mace wadda take shan azabar naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu za su cika da kunya.

9 Ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana ce ta zafin fushinsa. Za a mai da duniya jeji, a hallaka kowane mai zunubi.

10 Kowane tauraro, da kowace ƙungiyar taurari za su daina ba da haske. Rana za ta yi duhu lokacin da ta fito, wata kuwa ba zai ba da haske ba.

11 Ubangiji ya ce, “Zan kawo masifa a duniya. Zan hukunta dukan mugaye saboda zunubansu. Zan ƙasƙantar da kowane mai girmankai. Zan hukunta kowane mai izgili da mai mugunta.

12 Sauran da suka ragu za su fi zinariya wuyar samuwa.

13 Zan sa sammai su yi rawar jiki, duniya kuwa za a girgiza ta a inda take, a wannan rana sa’ad da ni, Ubangiji Mai Runduna, na nuna fushina.

14 “Baƙin da yake zaune a Babila za su gudu zuwa ƙasashensu, suna a warwatse kamar bareyin da suke tsere wa maharbansu, kamar tumakin da ba su da makiyayi.

15 Duk wanda aka kama za a soke shi ya mutu.

16 Sa’ad da suke cikin halin ƙaƙa naka yi, za a fyaɗa ‘ya’yansu ƙasa, su mutu. Za a washe gidajensu, a yi wa matansu faɗe.”

17 Ubangiji ya ce “Ina zuga mutanen Mediya, don su faɗa wa Babila da yaƙi. Ba su kula da azurfa ba, ba kuwa za a jarabce su da zinariya ba.

18 Da bakkuna da kibansu, za su karkashe samari. Ba za su nuna jinƙai ga jarirai ba, ba kuwa za su ji tausayin ‘yan yara ba.

19 Daular Babila ita ce mafi kyau duka, abin fāriya ce ga jama’arta. Amma ni Ubangiji, zan kaɓantar da ita kamar yadda na yi da Saduma da Gwamrata!

20 Ba wanda zai ƙara zama a cikinta. Ba wani Balaraben da yake yawo da zai kafa alfarwarsa a can. Ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.

21 Za ta zama wurin zaman namomin jejin hamada, inda mujiyoyi za su yi sheƙarsu. Jiminai za su zauna a can, awakin jeji za su yi ta warnuwa a cikin kufanta.

22 A hasumiyarta da fādodinta za a ji amsar ihun koke-koken kuraye da na diloli. Lokacin Babila ya yi! Kwanakinta sun kusa ƙarewa!”

Categories
ISH

ISH 14

Takama Gāba da Sarkin Babila

1 Ubangiji zai sāke yi wa jama’arsa Isra’ila jinƙai, ya zaɓe su su zama nasa. Zai sāke sa su zauna a ƙasarsu, baƙi ma za su zo su zauna tare da su.

2 Al’ummai da yawa za su taimaki jama’ar Isra’ila su koma ƙasarsu wadda Ubangiji ya ba su. A can sauran al’umma za su yi wa Isra’ila hidima kamar bayi. Waɗanda suka kama Isra’ilawa a dā yanzu Isra’ilawa za su kama su. Jama’ar Isra’ila za ta mallaki waɗanda suka taɓa zaluntarsu.

3 Ubangiji Allah kuwa zai sawwaƙe wa jama’ar Isra’ila azaba da wahala da suke sha, daga kuma aikin da aka tilasta su su yi.

4 Sa’ad da ya aikata wannan za su yi wa Sarkin Babila ba’a.

Za su ce, “Mugun sarkin ya fāɗi, ba zai ƙara zaluntar kowa ba!

5 Ubangiji ya ƙare mulkin mugun,

6 wanda yake zaluntar jama’a a husace, bai taɓa daina tsananta wa al’ummai ba, wanda ya ci da yaƙi.

7 Yanzu magana ta ƙare, duniya duka tana jin daɗin hutawa da salama. Kowa na ta raira waƙar murna.

8 Itatuwan fir da itatuwan al’ul na Lebanon suna murna da faɗuwar sarkin! Ba wanda zai tasar musu da sara!

9 “Lahira tana shirye-shiryen yi wa Sarkin Babila maraba. Fatalwan waɗanda suka yi iko a duniya suna kaiwa suna komowa a hargitse. Fatalwan sarakuna suna tashi daga gadajen sarautarsu.

10 Dukansu suka yi kira gare shi, suka ce, ‘Ashe, kai ma rarrauna ne kamarmu! Ka zama ɗaya daga cikinmu.

11 Dā ana ɗaukaka ka da kaɗe-kaɗen garaya, amma yanzu ga ka a lahira! Kana kwance a kan tsutsotsi. Kana rufe da tsutsotsi!’ ”

12 Ya Sarkin Babila, kai da kake tauraron asubahi mai haske, ka fāɗo daga sama. A dā ka ci al’ummai da yaƙi amma yanzu an fyaɗa ka ƙasa.

13 Ka yi niyyar hawan sama, ka sa gadon sarautarka a kan taurari mafi nisa. Ka zaci za ka zauna kamar sarki a kan dutsen nan na arewa, inda alloli suke tattare.

14 Kai ka ce za ka hau can bisa kan taurari, ka zama kamar Mai Iko Dukka.

15 Amma a maimakon haka an saukar da kai a sashe mafi zurfi a lahira.

16 Matattu za su zura maka ido su yi mamaki. Za su yi tambaya su ce, “Ashe, ba wannan mutum ba ne ya girgiza duniya, ya sa mulkoki suka jijjigu?

17 Wannan shi ne wanda ya hallaka birane, ya mai da duniya hamada, wanda bai taɓa sakin ɗaurarru ko ya bar su su koma gida ba?”

18 Dukan sarakunan duniya suna kwance a cikin manya manyan kaburburansu,

19 amma kai ba ka sami kabari ba, jefar da gawarka aka yi don ta ruɓe. Aka hautsuna gawarka da gawawwakin mayaƙan da aka kashe cikin yaƙi. Tare da su aka jefa ka gangaren dutse, aka tattake.

20 Ba za a binne ka kamar sauran sarakuna ba, saboda ka lalata da ƙasarka, ka karkashe mutanenka. Daga cikin mugayen iyalinka ba wanda zai ragu.

21 A fara yanyanka su! ‘Ya’ya maza na sarkin nan za su mutu saboda zunuban kakanninsu. Daga cikinsu ba wanda zai taɓa mallakar duniya, ko ya cika ta da birane.

Allah Zai Hallaka Babila

22 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan fāɗa wa Babila da yaƙi, in lalata ta, ba abin da zan bari, ko yara, ba wanda zai ragu. Ni, Ubangiji, na faɗi wannan.

23 Zan su Babila ta zama fadama, mujiyoyi za su zauna a can. Zan kuwa share Babila da tsintsiyar da za ta share kome. Ni, Ubangiji Mai Runduna, na faɗa.”

Allah Zai Hallaka Assuriya

24 Ubangiji Mai Runduna ya rantse, ya ce, “Abin da na riga na shirya, haka zai faru. Abin da na yi niyyar yi, za a yi.

25 Zan hallaka Assuriyawa a ƙasata ta Isra’ila, in tattake su a kan duwatsuna. Zan ‘yantar da jama’ata daga karkiyar Assuriyawa, daga nauyin da suka tilasta musu su ɗauka.

26 Abin da na shirya zan yi wa duniya, shi ne in miƙa hannuna domin in hukunta wa al’ummai.”

27 Ubangiji Mai Runduna ne ya ƙudura ya yi wannan, ya miƙa dantsensa don ya yi hukunci, ba kuwa mai iya hana shi.

Annabci a kan Filistiya

28 Wannan shi ne jawabin da aka yi shelarsa a shekarar da sarki Ahaz ya rasu.

29 Ku mutanen Filistiya, sandan da ake dūkanku da shi ya karye, amma kada wannan ya zamar muku dalilin murna. Gama idan wani maciji ya mutu, wani mafi mugunta zai maye gurbinsa. Ƙwan maciji yake ƙyanƙyashe maciji mai tashi sama!

30 Ubangiji zai zama makiyayin jama’arsa wadda take talauce, zai kuma sa su zauna lafiya. Amma ku Filistiyawa, zai aukar muku da matsananciyar yunwa, wadda ba za ta bar ko ɗayanku da rai ba.

31 Ku yi kururuwa, ku yi kuka na neman taimako, dukanku biranen Filistiya! Ku razana dukanku! Ƙurar da ta murtuke tana zuwa daga arewa, mayaƙa ne, ba kuwa matsorata a cikinsu.

32 Ƙaƙa za mu amsa wa manzannin da suka zo gare mu daga Filistiya? Za mu faɗa musu, cewa Ubangiji ya tabbatar da Sihiyona, jama’arsa da suke shan wahala kuwa za su sami zaman lafiya a can.

Categories
ISH

ISH 15

Annabci a kan Mowab

1 Wannan shi ne jawabi a kan Mowab.

Biranen Ar da Kir, an hallaka su dare ɗaya, ƙasar ta yi tsit, ba kowa.

2 Mutanen Dibon sun hau kan tuddai don su yi kuka a matsafarsu. Mutanen Mowab suna kuka da baƙin ciki saboda biranen Nebo da Medeba, sun aske kawunansu da gyammansu saboda baƙin ciki.

3 Mutane a tituna sun sa tsummoki a jikinsu, suka taru a filayen taruwa na birni da a kan rufin ɗakuna, sai makoki suke suna ta kuka.

4 Mutanen Heshbon da na Eleyale suka yi kuka da ƙarfi, har ana iya jin kukansu daga Yahaza. Har mayaƙa ma sun yi rawar jiki, zuciyarsu ta karai.

5 Zuciyata ta yi kuka ainun saboda Mowab! Mutane sun gudu zuwa cikin garin Zowar. Waɗansu sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka, waɗansu sun tsere zuwa Horonayim, suna hargowa saboda baƙin ciki.

6 Rafin Nimra ya ƙafe, ciyawar da take gefensa ta bushe, ba sauran wani ɗanyen abu.

7 Mutane sun haye kwarin Larabawa, suna ƙoƙari su tsere da dukan abin da suka mallaka.

8 A ko’ina a kan iyakokin Mowab, sai ƙugin kukansu ake ji. Ana kuwa ji daga garuruwan Eglayim da Biyer-elim.

9 A garin Dibon, kogin ya yi ja wur da jini, Allah kuwa ya tanada wa mutanen wurin abin da ya fi wannan muni. Hakika za a yi wa duk wanda ya ragu a Mowab mummunan kisa.

Categories
ISH

ISH 16

1 Daga birnin Sela a hamada, mutanen Mowab za su aiko da kaiwar rago ga mai mulki a Urushalima.

2 Za su dakata a gaɓar kogin Arnon, za su yi ta kai da kawowa kamar tsuntsayen da aka kora daga sheƙunansu.

3 Suna ce wa mutanen Yahuza, “Ku faɗa mana abin da za mu yi. Ku kāre mu, ku bar mu mu huta a inuwarku mai sanyi kamar inuwar itace da tsakar rana. Mu ‘yan gudun hijira ne, ku ɓoye mu inda ba wanda zai gan mu.

4 Ku bar mu mu zauna ƙasarku. Ku kāre mu daga masu neman hallaka mu.”

Zalunci da hallakarwa za su ƙare, masu lalatar da ƙasar za su ƙare.

5 Sa’an nan wani daga cikin zuriyar Dawuda zai zama sarki. Zai mallaki jama’a da aminci da ƙauna. Zai aikata abin da yake daidai da hanzari, zai sa a aikata adalci.

6 Mutanen Yahuza sun ce, “Mun ji irin fāriyar da mutanen Mowab suke yi. Mun sani su masu girmankai ne, masu ruba, amma fankamarsu ta banza ce.”

7 Mutanen Mowab za su yi kuka saboda wahalar da suke sha. Dukansu za su yi kuka sa’ad da suka tuna da kyakkyawan abincin da suka riƙa ci a birnin Kir-hareset. Za a kore su har su fid da zuciya.

8 Gonakin da suke kusa da Heshbon, da gonakin inabin da suke Sibma an lalatar da su, gonakin inabin nan waɗanda ruwan inabinsu suke sa masu mulkin al’ummai su bugu. Da kurangunsu sun taɓa yaɗuwa zuwa gabas har suka kai birnin Yazar da cikin hamada, wajen yamma kuma sai da suka dangana da gefen Tekun Gishiri.

9 Yanzu ina kuka saboda gonakin inabin Sibma kamar yadda na yi wa na Yazar. Na zub da hawayena saboda Heshbon da Eleyale, domin ba a sami kaka mai albarka ba, wadda za ta sa mutane yin murna.

10 Ba wanda yake farin ciki a cikin sauruka masu dausayi. Ba wanda yake sowa ko waƙa a cikin gonakin inabi. Ba mai matse ruwan inabi, sowar murna ta ƙare.

11 Na yi nishi da ɓacin zuciya a kan Mowab, na yi nishi da baƙin ciki saboda Kir-heres.

12 Mutanen Mowab sun gajiyar da kansu da zuwa wurin matsafarsu na kan dutse da masujadarsu, suna addu’a, amma ba zai amfana musu kome ba.

13 Wannan shi ne jawabin da Ubangiji ya riga ya yi a kan Mowab.

14 Yanzu Ubangiji ya ce, “A shekara uku daidai, dukiyar Mowab mai yawan nan za ta ƙare. Daga cikin ɗumbun mutanenta ‘yan kaɗan ne kaɗai za su ragu, za su kuma zama marasa ƙarfi.”

Categories
ISH

ISH 17

Annabci a kan Dimashƙu

1 Wannan shi ne jawabi a kan Dimashƙu.

Ubangiji ye ce, “Dimashƙu ba za ta ƙara zama birni ba, za ta zama tsibin kufai ne kawai.

2 Za a watse a bar biranen Suriya har abada. Za su zama makiyayar tumaki da shanu. Ba wanda zai tsoratar da su.

3 Ba za a kāre Isra’ila ba, Dimashƙu kuma za ta rasa ‘yancinta. Suriyawan da suka ragu za su sha wulakanci kamar mutanen Isra’ila. Ni, Ubangiji Mai Runduna, na faɗa.”

Hukunci a kan Isra’ila

4 Ubangiji ya ce, “Rana taba zuwa, ran da girman Isra’ila zai ƙāre, fatara za ta gāje gurbin dukiyarsu.

5 Isra’ila za ta zama kamar gonar da aka girbe, aka yanke amfaninta, ta zama marar kome kamar gona a kwarin Refayawa sa’ad da aka ɗebe amfaninta. Mutane kima ne kurum za su ragu.

6 Isra’ila kuma za ta zama kamar itacen zaitun wanda aka karkaɗe ‘ya’yansa, aka bar biyu ko uku kawai a ƙwanƙolin itacen, ko kuma aka bar huɗu ko biyar a rassansa. Ni Ubangiji Allah na Isra’ila, na faɗa.”

7 A wannan rana, mutane za su juyo neman taimako ga Mahaliccinsu, Allah Mai Tsarki na Isra’ila.

8 Ba za su ƙara dogara ga bagaden da suka yi da hannuwansu ba, ko kuwa su dogara ga ayyukan hannuwansu, ko keɓaɓɓun wuraren da suke wa gumaka sujada, ko bagadai don ƙona turare.

9 A wannan rana, za a watse a bar birane masu ƙaƙƙarfar kagara su zama kufai a jeji kuwa kamar rassan da aka watsar a gaban jama’ar Isra’ila.

10 Isra’ila, kin manta da Allah wanda ya kuɓutar da ke, wanda ya kāre ki kamar babban dutse. Kin dasa wa kanki lambuna masu ni’ima don ki yi wa gumaka sujada.

11 Amma ko da za su toho su yi fure a safiyar da kuka dasa su, duk da haka ba za a girbe kome ba. Wahala ce kaɗai da azabar da ba ta warkuwa.

An Ci Al’ummai, Abokan Gāba

12 Al’ummai masu iko sun hargitse suna ta rugugi kamar rurin teku, kamar karon manyan raƙuman ruwa.

13 Al’ummai sun ci gaba kamar sukuwar raƙuman ruwa, amma Allah ya tsauta musu suka kuwa janye, aka kora su kamar ƙura a gefen dutse, kamar kuma tattaka a cikin guguwa.

14 Da maraice sukan ba da tsoro, amma da safe ba su! Wannan ita ce ƙaddarar duk wanda ya washe ƙasarmu!

Categories
ISH

ISH 18

Annabci a kan Habasha

1 A hayin kogunan Habasha akwai wata ƙasa inda ake jin amon fikafikai.

2 Daga waccan ƙasar wakilai sukan gangaro daga Kogin Nilu a cikin jiragen ruwa da aka yi da iwa. Ku koma gida, ku manzanni masu gaggawa! Ku kai saƙo ƙasarku, can a mafarin Kogin Nilu, zuwa ga al’ummarku mai ƙarfi mai iko, zuwa ga dogayen mutanenku masu sulɓin jiki, waɗanda ake jin tsoronsu ko’ina a duniya.

3 Kowane mutum da yake a duniya ya kasa kunne, kowannen da yake zaune a duniya, ya duba tutar, alama da za a ɗaga sama a ƙwanƙolin duwatsu, ya kasa kunne ga busar ƙaho!

4 Ubangiji ya ce mini “Zan duba daga samaniya a hankali kamar yadda raɓa take saukowa a natse da gumin dare a lokacin girbi, hasken rana kuma a yini.

5 Kafin a tattara ‘ya’yan inabi, sa’ad da furanni duka suka karkaɗe, ‘ya’yan inabi suna ta nuna, haka magabta za su hallaka Habasha a sawwaƙe kamar yadda ake faffalle rassan kurangar inabi da wuƙa.

6 Za a bar gawawwakin sojojinsu a fili domin tsuntsaye da namomin jeji su zama abincin tsuntsaye da bazara, abincin namomin jeji kuma a lokacin sanyi.”

7 A wannan lokaci Ubangiji Mai Runduna zai karɓi hadayu daga wannan ƙasa, a mafarin Kogin Nilu, wato wannan ƙaƙƙarfar al’umma mai iko, waɗannan dogayen mutane masu sulɓin jiki, waɗanda ake jin tsoronsu ko’ina a duniya. Za su zo Dutsen Sihiyona, inda ake yi wa Ubangiji Mai Runduna sujada.

Categories
ISH

ISH 19

Annabci a kan Masar

1 Wannan shi ne jawabi a kan Masar.

Ubangiji yana zuwa Masar a kan girjije a sukwane. Gumakan Masarawa za su yi rawar jiki a gabansa, zuciyar Masarawa za ta karai.

2 Ubangiji ya ce, “Zan ta da hargitsi a yi yaƙin basasa a Masar, ɗan’uwa ya yi gāba da ɗan’uwa, maƙwabci kuma gaba da maƙwabci. Biranen da suke hamayya za su yi faɗa da juna, sarakunan da suke hamayya kuma za su yi faɗa saboda neman iko.

3 Zan warware shirye-shiryen Masarawa in sa ku karai. Za su roƙi taimako ga gumakansu, za su je kuma su yi shawara da mabiyansu, su kuma nemi shawarar kurwar matattu.

4 Zan ba da Masarawa a hannun azzalumi a hannun mugun sarki kuma da zai mallake su. Ni, Ubangiji Mai Runduna, na faɗi wannan.”

5 Ruwan Kogin Nilu zai ƙafe, a hankali kogin zai bushe.

6 Mazaunan kogin za su ji wari sa’ad da yake ƙafewa a hankali. Iwa da jema za su bushe.

7 Dukan amfanin gonakin da aka shuka a gaɓar Kogin Nilu za su bushe, iska ta fyauce su.

8 Duk wanda sana’arsa ta kama kifi ce a Kogin Nilu zai yi ƙugi ya yi kuka, gama ƙugiyoyinsa da tarunansa za su zama marasa amfani.

9 Waɗanda suke yin tufafin lilin za su fid da zuciya,

10 shugabanni da ma’aikata za su karai su kuma damu.

11 Shugabannin birnin Zowan wawaye ne! Mutanen Masar mafi hikima za su ba da gurguwar shawara! Ta ƙaƙa za su iya dosar sarki su faɗa masa, cewa su ne suka gāji masana da sarakuna na dā can?

12 Sarkin Masar, ina mashawartan nan naka masu hikima? Watakila za su iya faɗa maka shirye-shiryen da Ubangiji Mai Runduna ya yi domin Masar.

13 Shugabannin Zowan da na Memfis wawaye ne. Su ake zaton za su bi da al’ummar, amma sai suka bi da su a karkace.

14 Ubangiji ne ya sa su ba da gurguwar shawara. Sakamakon haka sai Masar ta yi ta aikata dukan abu a hugunce, tana tangaɗi kamar bugagge wanda santsi na kwasarsa cikin aman da ya yi.

15 A Masar duka, attajiri da matalauci, ƙarami ko babba, ba wanda zai iya yin wani taimako.

16 Lokaci zai yi in da zuciyar mutanen Masar za ta narke kamar mata. Za su yi rawar jiki da razana lokacin da suka ga Ubangiji Mai Runduna ya miƙa hannunsa don ya hukunta su.

17 Mutanen Masar za su firgita saboda Yahuza, kowane lokaci za su tuna da ƙaddarar da Ubangiji Mai Runduna ya shirya dominsu.

18 A wannan rana, za a yi amfani da harshen Ibrananci a birane biyar na Masar. Mutanen da suke can za su riƙa yin rantsuwarsu da sunan Ubangiji Mai Runduna. Za a sa wa ɗaya daga cikin biranen nan suna, “Birnin Hallaka.”

19 A wannan rana, za a gina wa Ubangiji bagade a ƙasar Masar, za a keɓe masa ginshiƙi na dutse a kan iyakar Masar.

20 Za su zama alamu na kasancewar Ubangiji Mai Runduna a Masar. Sa’ad da aka zalunci mutanen da suke can, za su yi kira ga Ubangiji su nemi taimako, zai aika musu wanda zai kuɓutar da su.

21 Ubangiji zai bayyana kansa ga mutanen Masar, sa’ad da ya yi haka kuwa, za su karɓe shi, su yi masa sujada, su kuma kawo masa hadayu da sadakoki. Za su yi masa alkawarai ƙwarara, su kuwa cika abin da suka alkawarta.

22 Ubangiji zai hukunta Masarawa, amma zai warkar da su. Za su juyo gare shi, shi kuma zai ji addu’o’insu ya warkar da su.

23 A wannan rana, za a yi wata babbar hanya tsakanin Masar da Assuriya. Mutanen ƙasashen nan biyu za su yi ta kai da kawowa tsakaninsu, al’ummai biyu za su yi sujada tare.

24 A wannan rana, za a lasafta Isra’ila tare da Masar da Assuriya, waɗannan al’ummai uku za su zama albarka ga dukan duniya.

25 Ubangiji Mai Runduna zai sa musu albarka, ya ce, “Zan sa muku albarka, ke Masar, jama’ata, da suke Assuriya wadda na halitta, da ke kuma Isra’ila zaɓaɓɓiyar jama’ata.”

Categories
ISH

ISH 20

Assuriya Za Ta Ci Masar da Habasha

1 Bisa ga umarnin Sargon, Sarkin Assuriya, sai sarkin yaƙin Assuriya ya fāɗa wa Ashdod, birnin Filistiyawa, da yaƙi.

2 A wannan lokaci Ubangiji ya riga ya faɗa wa Ishaya ɗan Amoz, cewa ya tuɓe tsummokin da yake saye da su, ya kuma tuɓe takalmansa. Shi kuwa ya yi biyayya ya yi ta yawo tsirara, ba kuma takalmi a ƙafarsa.

3 Sa’ad da aka ci Ashdod, sai Ubangiji ya ce, “Bawana Ishaya ya yi ta yawo tsira, ba kuma takalmi a ƙafarsa har shekara uku. Wannan ita ce alamar abin da zai faru a ƙasa Masar da Habasha.

4 Sarkin Assuriya zai kwashe kamammun yaƙi waɗanda ya kama a ƙasashen nan biyu, ya tafi da su tsirara. Matasa da manya kuma ba takalmi a ƙafafunsu, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar.

5 Waɗanda suke dogara ga Habasha, suna kuwa fāriya da Masar, za su ruɗe, sa zuciyarsu zai wargaje.

6 A wannan rana mutanen da suke zaune a gaɓar Filistiyawa za su ce, ‘Dubi abin da ya faru ga jama’ar da muka dogara da su don su tsare mu daga Sarkin Assuriya! Ƙaƙa za mu yi mu tsira?’ ”

Categories
ISH

ISH 21

Annabci a kan Babila

1 Wannan shi ne jawabi a kan Babila.

Kamar yadda guguwa take tasowa daga hamada, haka masifa za ta auko daga wata ƙasa mai razanarwa.

2 Na ga wahayi na waɗansu mugayen abubuwa, wato na cin amana da hallakarwa.

Rundunar sojojin Elam, ku kama yaƙi! Rundunar sojojin Mediya ku kewaye birane da yaƙi. Allah zai kawar da wahalar da Babila ta haddasa.

3 Abin da na gani, da abin da na ji a wahayin, ya razanar da ni, ya sa ni cikin azaba kamar ta mace mai naƙuda.

4 Kaina ya yi yum, ina ta rawar jiki saboda tsoro. Ina ta marmarin maraice ya yi, amma bai kawo mini kome ba, sai razana.

5 A wahayin na ga an shirya biki, an shisshimfiɗa darduma inda waɗanda aka gayyata za su zauna. Suna ci suna sha. Farat ɗaya sai aka ji umarni cewa, “Jarumawa! Ku shirya garkuwoyinku.”

6 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Tafi ka sa mai tsaro, ka faɗa masa ya riƙa ba da labarin abin da ya gani.

7 Idan ya ga mutane biyu biyu suna zuwa a kan dawakai, waɗansu kuma a kan raƙuma da jakuna, ka faɗa masa ya lura da su sosai.”

8 Mai tsaro ya ce, “Ya mai girma, ina ta tsaro dare da rana a wurin da aka sa ni.”

9 Farat ɗaya sai ga su sun zo! Suna tafe a kan dawakai biyu biyu. Sai mai tsaro ya ba da labari cewa, “Babila ta fāɗi! Dukan gumakan da suke yi wa sujada an ragargaza su har ƙasa.”

10 Ya jama’ata, an buga ku kamar yadda ake bugun alkama a masussuka. Amma yanzu na kawo muku albishir wanda na ji daga wurin Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila.

Annabci a kan Edom

11 Wannan shi ne jawabi a kan Edom.

Wani daga Edom ya kira ni ya ce, “Ya mai tsaro, gari ya kusa wayewa? Ka gaya mini har sai yaushe zai waye?”

12 Sai na amsa na ce, “Gari zai waye, amma za a sāke yin dare! Idan kana so ka sāke yin tambaya, sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”

Annabci a kan Arabiya

13 Wannan shi ne jawabi a kan Arabiya.

Ya ku jama’ar Dedan, waɗanda ayarorinku suka yi zango a ƙasar Arabiya wadda take faƙo,

14 ku ba jama’a waɗanda suka zo gare ku masu jin ƙishi ruwa su sha. Ya ku jama’ar ƙasar Tema, ku ba ‘yan gudun hijira abinci.

15 Mutane suna gudu don su tsere wa takuban da za su kashe su, da bakkunan da za su harbe su, su kuma tsere wa dukan hatsarorin yaƙi.

16 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Saura shekara ɗaya tak girman kabilar Kedar zai ƙare.

17 Jarumawan Kedar su ne maharba, amma sai kaɗan za su ragu daga cikinsu, ni, Ubangiji Allah na Isra’ila, na faɗa.”