Categories
IRM

IRM 6

Ajalin Urushalima da Yahuza

1 “Ya ku mutanen Biliyaminu, ku

gudu neman mafaka,

Daga cikin Urushalima!

Ku busa ƙaho a Tekowa,

Ku ba da alama a Bet-akkerem,

Gama masifa da babbar halaka sun

fito daga arewa.

2 Ya Sihiyona, ke kyakkyawar

makiyaya ce, zan hallaka abin da

kika hahhaifa.

3 Makiyaya da garkunansu za su zo

wurinki,

Za su kafa alfarwansu kewaye da ke,

Kowa zai yi kiwo a makiyayarki.

4 Za su ce, ‘Mu yi shiri mu fāɗa mata

da yaƙi!

Ku tashi, mu fāɗa musu da tsakar

rana!’

Sai kuma suka ce, ‘Kaitonmu, ga

rana tana faɗuwa, ta yi ruɗa-

kuyangi.

5 Mu tashi mu fāɗa mata da dare,

Mu lalatar da fādodinta.’ ”

6 Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Ku sassare itatuwanta,

Ku tula ƙasa kewaye da

Urushalima,

Dole in hukunta wannan birni

saboda ba kome cikinsa sai

zalunci,

7 Kamar yadda rijiya take da ruwa

garau,

Haka Urushalima take da

muguntarta,

Ana jin labarin kama-karya da na

hallakarwa a cikinta,

Kullum akwai cuce-cuce, da raunuka

a gabana,

8 Ku ji faɗaka, ya ku mutanen

Urushalima,

Don kada a raba ni da ku,

Don kada in maishe ku kufai,

Ƙasar da ba mazauna ciki.”

9 Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Za a kalace ringin Isra’ila sarai,

kamar yadda ake wa inabi,

Ka miƙa hannunka a kan rassanta

kamar mai tsinkar ‘ya’yan

inabi.”

10 Da wa zan yi magana don in faɗakar

da shi, don su ji?

Ga shi, kunnuwansu a toshe suke, su

ji,

Ga shi, maganar Ubangiji kuwa ta

zama abin ba’a a gare su,

Ba su marmarinta.

11-12 Don haka ina cike da fushin

Ubangiji

Na gaji da kannewa.

Ubangiji ya ce,

“Zan kwararo fushi kan yara da suke a

titi.

Da kuma kan tattaruwar samari.

Za a ɗauke mata da miji duka biyu,

Da tsofaffi, da waɗanda suka tsufa

tukub-tukub.

Za a ba waɗansu gidajensu, da

gonakinsu, da matansu,

Gama zan nuna ikona in hukunta

mazaunan ƙasar.

13 Gama daga ƙaraminsu zuwa babba,

Kowannensu yana haɗama ya ci

ƙazamar riba,

Har annabawa da firistoci,

Kowannensu ya shiga aikata rashin

gaskiya.

14 Sun warkar da raunin mutanena

sama sama,

Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali

kuwa ba lafiya.

15 Sun ji kunya sa’ad da suka aikata

abubuwan banƙyama?

Ba su ji kunya ba ko kaɗan.

Ko gezau ba su yi ba,

Don haka za su fāɗi tare da

fāɗaɗɗu,

Sa’ad da na hukunta su, za a

hamɓarar da su.

Ni Ubangiji na faɗa.”

16 Haka Ubangiji ya ce,

“Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba,

Ku nemi hanyoyin dā, inda hanya

mai kyau take,

Ku bi ta, don ku hutar da

rayukanku.

Amma suka ce, ‘Ai, ba za mu bi ta ba.’

17 Na sa muku matsara cewa, in kun ji

an busa ƙaho ku kula!

Amma suka ce, ‘Ba za mu kula ba.’

18 “Don haka, ku ji, ya ku al’ummai,

Ku sani, ku taron jama’a,

Don ku san abin da zai same ku.

19 Ki ji, ya ke duniya,

Ga shi, ina kawo masifa a kan

wannan jama’a,

Sakayyar ƙulle-ƙullensu,

Don ba su kula da maganata ba,

Sun ƙi dokokina.

20 Da wane nufi kuke kawo mini turare

daga Sheba,

Ko raken da kuke kawowa daga

ƙasa mai nisa?

Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa

ba,

Ba kuwa zan ji daɗin sadakokinku

ba.

21 Don haka, ni Ubangiji na ce,

Zan sa abin tuntuɓe a gaban wannan

jama’a,

Za su kuwa yi tuntuɓe, su fāɗi.

Iyaye tare da ‘ya’yansu, da

maƙwabci,

Do abokansu za su lalace.”

22 Haka Ubangiji ya ce,

“Ga shi, jama’a tana fitowa daga

ƙasar arewa.

Babbar al’umma ce,

Ta yunƙuro tun daga manisantan

wurare na duniya.

23 Suna riƙe da baka da māshi,

Mugaye ne marasa tausayi,

Motsinsu kamar ƙugin teku ne.

Suna haye a kan dawakai,

A jere kamar wanda ya yi shirin

yaƙi

Gāba da ke, ya ‘yar Sihiyona.”

24 Mutanen Urushalima sun ce,

“Mun ji labarin yaƙin,

Hannuwanmu suka yi rauni.

Azaba ta kama mu,

Ciwo irin na mai naƙuda.

25 Kada ku fita zuwa gona,

Kada kuma ku yi yawo a kan

hanya,

Gama abokin gāba yana da takobi,

Razana a kowane sashi.”

26 “Ya mutanena, ku sa tufafin makoki,

Ku yi birgima cikin toka,

Ku yi makoki mai zafi irin wanda

akan yi wa ɗa tilo,

Gama mai hallakarwa zai auko mana

nan da nan.”

27 Ubangiji ya ce wa Irmiya,

“Na maishe ka mai aunawa da mai

jarraba mutanena

Domin ka sani, ka auna

al’amuransu,

28 Su duka masu taurinkai ne, ‘yan

tawaye,

Suna yawo suna baza jita-jita.

Su tagulla ne da baƙin ƙarfe,

Dukansu lalatattu ne.

29 Ana zuga da ƙarfi,

Dalma ta ƙone,

Tacewar aikin banza ne,

Gama ba a fitar da mugaye ba.

30 Ana ce da su ƙwan maƙerar azurfa

ne,

Gama ni na ƙi su.”

Categories
IRM

IRM 7

Ku Gyara Hanyoyinku da Ayyukanku

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce,

2 “Ka tafi ka tsaya a ƙofar Haikalin Ubangiji, ka yi shelar wannan magana, ka ce, su kasa kunne ga maganar Ubangiji, dukansu mutanen Yahuza, su da suke shiga ta ƙofofin nan don su yi wa Ubangiji sujada!

3 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, ni kuwa zan ƙyale ku, ku zauna a wannan wuri.

4 Kada ku amince da maganganun nan na ruɗarwa, cewa wannan shi ne Haikalin Ubangiji. Wannan shi ne Haikalin Ubangiji, wannan shi ne Haikalin Ubangiji!

5 “ ‘Idan dai kun gyara hanyoyinku, da ayyukanku bisa kan gaskiya, idan da gaskiya kuke aikata adalci ga junanku,

6 idan ba ku tsananta wa baƙo, ko maraya, ko gwauruwa, wato matar da mijinta ya rasu, idan ba ku zubar da jinin marar laifi a wannan wuri ba, idan kuma ba ku bi abin da zai cuce ku ba, wato gumaka,

7 sa’an nan zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasa wadda tuni na ba kakanninku har abada.

8 “ ‘Ga shi, kun amince da maganganu na ruɗami, marasa amfani.

9 Za ku yi ta yin sata, da kisankai, da zina, da rantsuwar ƙarya, da ƙona wa Ba’al turare, da bin waɗansu gumakan da ba ku sani ba?

10 Sa’an nan za ku zo ku tsaya a gabana a wannan Haikali, wanda ake kira da sunana, ku ce, “An cece mu,” don kawai ku ci gaba da yin dukan waɗannan abubuwan banƙyama?

11 Wannan Haikali wanda ake kira da sunana ya zama kogon mafasa a idanunku. Ga shi, ni da kaina na gani.’ ” in ji Ubangiji.

12 “ ‘Ku tafi Shilo wurin da na fara zaunar da sunana, ku ga abin da na yi mata saboda muguntar mutanena Isra’ila.

13 Yanzu kuwa saboda kun aikata waɗannan al’amura, sa’ad da na yi ta yi muku magana, amma ba ku kasa kunne ba, sa’ad da na kira ku, ba ku amsa ba,

14 domin haka zan yi wa Haikali wanda ake kira da sunana, wanda kuma kuka amince da shi, da kuma wurin da na ba ku, ku da kakanninku, kamar yadda na yi wa Shilo.

15 Zan kore ku daga gabana kamar yadda na yi wa dukan ‘yan’uwanku, dukan zuriyar Ifraimu.’ ”

Fushin Allah a kan Bin Gumaka

16 “Kai kuwa, Irmiya kada ka yi wa mutanen nan addu’a. Kada ka yi kuka ko addu’a dominsu, kada ka roƙe ni, gama ba zan ji ka ba.

17 Ba ka ga abin da suke yi a biranen Yahuza da titunan Urushalima ba?

18 Yara sukan tara itace, iyaye maza sukan haɗa wuta, iyaye mata sukan kwaɓa ƙullu don su yi wa gunkin nan wadda ake kira sarauniyar sama, waina. Sukan kuma miƙa wa gumaka hadayu na sha domin su tsokane ni.”

19 In ji Ubangiji, “Ni suke tsokana? Ashe, ba kansu ba ne don su ruɗar da kansu?”

20 Saboda haka ga abin da Ubangiji Allah ya ce, “Duba, zan kwarara fushina da hasalata a kan wannan wuri, a kan mutum duk da dabba, da akan itatuwan saura da amfanin gona. Zai yi ta cin wuta, ba kuwa za a kashe ba.”

Horon Yahuza saboda Tayarwa

21 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya ce, “Ku ba da hadayunku na ƙonawa da na sadakarku, ku ci naman.

22 A ranar da na fito da kakanninku daga ƙasar Masar, ban yi magana da su, ko na umarce su, a kan hadayun ƙonawa da na sadaka ba.

23 Amma na umarce su su yi biyayya da maganata, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena, su bi dukan al’amuran da na umarce su, domin lafiyarsu, don su zama lafiya.

24 Amma ba su yi biyayya ba, ba su kuma kula ba. Sai suka bi shawarar kansu da ta tattaurar muguwar zuciyarsu. Suka koma baya maimakon su yi gaba.

25 Tun daga ran da kakanninku suka fito ƙasar Masar, har zuwa yau na yi ta aika musu da dukan bayina annabawa kowace rana.

26 Duk da haka ba su saurare ni ba, ba su kula su ji ba, sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.

27 “Saboda haka za ka faɗa musu waɗannan abubuwa duka, amma ba za su ji ka ba. Za ka kira su, amma ba za su amsa ba.

28 Za ka faɗa musu ka ce, wannan ita ce al’ummar da ba ta yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnta ba, ba ta karɓi horo ba. Gaskiya kuma ta ƙare sam, ba ta a bakinsu.

29 “Ku aske gashin kanku, ku zubar da shi. Ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi ‘yan zamanin nan, ya rabu da su saboda fushinsa.

30 Ni Ubangiji, na faɗa, cewa mutanen Yahuza sun yi mugun abu a gabana. Suna ajiye gumakansu a Haikalina, sun ƙazantar da shi.

31 A cikin kwarin ɗan Hinnon sun gina bagade, mai suna Tofet, don su miƙa ‘ya’yansu mata da maza hadayar ƙonawa. Ni ban umarce su su yi haka ba, irin wannan abu ba shi a zuciyata.

32 Domin haka, ni Ubangiji na ce, kwanaki suna zuwa lokacin da ba za a ƙara faɗar Tofet, ko kwarin ɗan Hinnom ba, amma za a kira shi Kwarin Kisa, gama za a binne mutane a Tofet domin ba sauran wuri a ko’ina.

33 Gawawwakin mutanen nan za su zama abincin tsuntsaye da na namomin jeji, ba wanda zai kore su.

34 Zan sa muryar murna da ta farin ciki, da muryar ango da ta amarya su ƙare a biranen Yahuza da titunan Urushalima, gama ƙasar za ta zama kufai.”

Categories
IRM

IRM 8

1 “Ni Ubangiji na faɗa, cewa a wancan lokaci, za a fitar da ƙasusuwa daga kaburburan sarakunan Yahuza, da na sarakansu, da na firistoci, da na annabawa, da na mazaunan Urushalima.

2 Za a shimfiɗa su a rana, da a farin wata, da a gaban dukan rundunan sama, waɗanda suka ƙaunata, suka bauta wa, waɗanda suka nemi shawararsu, suka yi musu sujada. Ba za a tattara su a binne ba, amma za su zama juji a bisa ƙasa.

3 Sauran mutanen muguwar tsaran nan waɗanda suke a wuraren da na warwatsa su, za su fi son mutuwa fiye da rayuwa. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”

Zunubi da Hukunci

4 “Ka faɗa musu, ka ce, ni Ubangiji na

ce,

‘Wanda ya fāɗi ba zai sāke tashi ba?

Idan wani ya kauce ba zai komo kan

hanya ba?

5 Me ya sa, mutanen nan na

Urushalima suke ratsewa, suke

komawa baya kullayaumin?

Sun riƙe ƙarya kan-kan

Sun ƙi komowa.

6 Na kula sosai, na saurara,

Amma ba wanda ya faɗi wata

maganar kirki,

Ba wanda ya taɓa barin muguntarsa,

Kowa cewa yake, “Me na yi?”

Kamar dokin da ya kutsa kai cikin

fagen fama.

7 Ko shamuwa ta sararin sama ma, ta

san lokatanta,

Tattabara da tsattsewa, da gauraka

suna kiyaye lokacin komowarsu.

Amma mutanena ba su san dokokina

ba.

8 Ƙaƙa za ku ce, “Muna da hikima,

Dokar Ubangiji tana tare da mu”?

Ga shi kuwa, alkalamin ƙarya na

magatakarda, ya yi ƙarya.

9 Za a kunyatar da masu hikima.

Za su tsorata, za a kuma tafi da su.

Ga shi, sun ƙi maganar Ubangiji.

Wace hikima suke da ita?

10 Saboda haka zan ba da matansu ga

waɗansu,

Gonakinsu kuma ga waɗanda suke

cinsu da yaƙi,

Saboda tun daga ƙarami har zuwa

babba

Kowannensu yana haɗamar cin

muguwar riba,

Tun daga annabawa zuwa firistoci

Kowannensu aikata ha’inci yake yi.

11 Sun warkar da raunin mutanena

sama sama,

Suna cewa, “Lafiya, lafiya,” alhali

kuwa ba lafiya.

12 Ko sun ji kunya

Sa’ad da suka aikata ayyuka masu

banƙyama?

A’a, ba su ji kunya ba ko kaɗan,

Fuskarsu ko gezau ba ta yi ba.

Domin haka za su faɗi tare da

fāɗaɗɗu,

Sa’ad da na hukunta su, za a ci su da

yaƙi.

Ni Ubangiji na faɗa.’

13 “Ni Ubangiji na ce,

‘Sa’ad da zan tattara su kamar

amfanin gona,

Sai na tarar ba ‘ya’ya a kurangar

inabi,

Ba ‘ya’ya kuma a itacen ɓaure,

Har ganyayen ma sun bushe.

Abin da na ba su kuma ya kuɓuce

musu.

Ni Ubangiji na faɗa.’ ”

14 Mutanen Urushalima sun ce,

“Don me muke zaune kawai?

Bari mu tattaru, mu tafi cikin

garuruwa masu garu,

Mu mutu a can,

Gama Ubangiji Allahnmu ya

ƙaddara mana mutuwa,

Ya ba mu ruwan dafi,

Domin mun yi masa laifi.

15 Mun sa zuciya ga salama, amma ba

lafiya,

Mun sa zuciya ga lokacin samun

warkewa,

Amma sai ga razana!

16 Daga Dan, an ji firjin dawakai.

Dakan ƙasar ta girgiza saboda

haniniyar ingarmunsu.

Sun zo su cinye ƙasar duk da abin

da suke cikinta,

Wato da birnin da mazauna

cikinsa.”

17 “Ni Ubangiji na ce, ‘Zan aiko muku

da macizai, da kāsā,

Waɗanda ba su da makari,

Za su sassare ku.’ ”

18 Baƙin cikina ya fi ƙarfin warkewa,

Zuciyata ta ɓaci ƙwarai!

19 Ku ji kukan jama’ata ko’ina a

ƙasar,

“Ubangiji, ba shi a Sihiyona

ne?

Sarkinta ba ya a cikinta ne?”

Ubangiji ya ce,

“Me ya sa suka tsokane ni da

sassaƙaƙƙun gumakansu,

Da baƙin gumakansu?”

20 Mutane suna ta cewa,

“Damuna ta ƙare, kaka kuma ta

wuce,

Amma ba a cece mu ba.”

21 Raunin da aka yi wa jama’ata,

Ya yi wa zuciyata rauni.

Ina makoki, tsoro kuma ya kama ni

ƙwarai.

22 Ba abin sanyayawa a Gileyad ne?

Ba mai magani a can ne?

Me ya sa ba a warkar da jama’ata

ba?

Categories
IRM

IRM 9

1 Da ma kaina ruwa ne kundum,

Idanuna kuma maɓuɓɓuga ne,

Da sai in yi ta kuka dare da rana,

Saboda an kashe jama’ata!

2 Da ma ina da wurin da zan fake a

hamada,

Da sai in rabu da mutanena, in tafi

can!

Gama dukansu mazinata ne,

Ƙungiyar mutane maciya amana.

3 Ubangiji ya ce,

“Sun tanƙwasa harshensu kamar

baka,

Ƙarya ce take rinjayar gaskiya a

ƙasar.

Suna ta cin gaba da aikata mugunta,

Ba su kuwa san ni ba.

4 “Bari kowane mutum ya yi hankali

da maƙwabcinsa,

Kada kuma ya amince da kowane

irin ɗan’uwa,

Gama kowane ɗan’uwa munafuki

ne,

Kowane maƙwabci kuma mai kushe

ne.

5 Kowane mutum yana ruɗin

maƙwabcinsa da abokinsa,

Ba mai faɗar gaskiya,

Sun koya wa harshensu faɗar

ƙarya.

Suna aikata laifi,

Sun rafke, sun kasa tuba.

6 Suna ƙara zalunci a kan zalunci,

Yaudara a kan yaudara,

Sun ƙi sanina,” in ji Ubangiji.

7 Saboda haka, Ubangiji Mai

Runduna, ya faɗa cewa,

“Zan tsabtace su, in gwada su,

Gama me zan yi kuma saboda

jama’ata?

8 Harshensu kibiya ce mai dafi, yana

faɗar ƙarya,

Kowa yana maganar alheri da

maƙwabcinsa

Amma a zuciyarsa yana shirya masa

maƙarƙashiya.

9 Ba zan hukunta su saboda waɗannan

al’amura ba?

Ba zan sāka wa al’umma irin

wannan ba?”

10 Zan yi kuka in yi kururuwa saboda

tsaunuka,

Zan yi kuka saboda wuraren kiwo,

Domin sun bushe sun zama marasa

amfani.

Ba wanda yake bi ta cikinsu.

Ba a kuma jin kukan shanu,

Tsuntsaye da namomin jeji, sun gudu

sun tafi.

11 “Ni Ubangiji na ce, zan mai da

Urushalima tsibin kufai,

Wurin zaman diloli,

Zan kuma mai da biranen Yahuza

kufai, inda ba kowa.”

Za a Rushe Birni a Kai su Zaman Talala

12 Wa yake da isasshiyar hikimar da zai fahimci wannan? Wa Ubangiji ya faɗa masa don ya sanar? Me ya sa ƙasar ta lalace ta zama kufai, har ba wanda yake iya ratsa ta, kamar hamada?

13 Sai Ubangiji ya ce, “Saboda sun bar dokata wadda na sa a gabansu, ba su yi biyayya da maganata ko su yi aiki da ita ba.

14 Amma suka taurare, suka biye wa zuciyarsu, suka bi Ba’al, kamar yadda kakanninsu suka koya musu.

15 Domin haka, ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, zan ciyar da mutanen nan da abinci mai ɗaci, in shayar da su da ruwan dafi.

16 Zan watsa su cikin sauran al’umma waɗanda su da kakanninsu ba su san su ba, zan sa takobi ya bi su don in hallaka su.

17 “Haka ni Ubangiji Mai Runduna na

ce,

Ku yi tunani, ku kirawo mata masu

makoki su zo,

Ku aika wa gwanaye fa.”

18 Jama’a suka ce,

“Su gaggauta, su ta da murya,

Su yi mana kuka da ƙarfi,

Har idanunmu su cika da hawaye,

Giranmu kuma su jiƙe sharaf.

19 “Gama ana jin muryar kuka daga

Sihiyona cewa,

‘Ga yadda muka lalace! Aka kunyatar

da mu ɗungum!

Don mun bar ƙasar, domin sun

rurrushe wuraren zamanmu.’ ”

20 Irmiya ya ce,

“Ya ku mata, ku ji maganar

Ubangiji,

Ku kasa kunne ga maganar da ya

faɗa,

Ku koya wa ‘ya’yanku mata kukan

makoki,

Kowacce ta koya wa maƙwabciyarta

waƙar makoki,

21 Gama mutuwa ta shiga tagoginmu,

Ta shiga cikin fādodinmu,

Ta karkashe yara a tituna,

Ta kuma karkashe samari a dandali.

22 Ubangiji ya ce mini,

‘Ka yi magana, cewa gawawwakin

mutane za su fāɗi tuli

Kamar juji a saura,

Kamar dammunan da masu girbi

suka ɗaura,

Ba wanda zai tattara su.’ ”

23 Ubangiji ya ce, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa, kada mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa, kada kuma mawadaci ya yi fariya da wadatarsa.

24 Amma bari wanda zai yi fariya, ya yi fariya a kan cewa ya fahimce ni, ya kuma san ni. Ni ne Ubangiji mai yin alheri, da gaskiya, da adalci a duniya, gama ina murna da waɗannan abubuwa, ni Ubangiji na faɗa.”

25 Ubangiji ya ce, “Kwanaki suna zuwa sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya,

26 da Masar, da Yahuza, da Edom, da ‘ya’yan Ammon, maza, da na Mowab, da dukan waɗanda suke zaune a hamada, da waɗanda suke yi wa kansu sanƙo, gama dukan al’umman nan marasa kaciya ne, dukan jama’ar Isra’ila kuma marasa kaciya ne a zuci.”

Categories
IRM

IRM 10

Gumaka da Allah na Gaskiya

1 Ya jama’ar Isra’ila, ku ji jawabin da Ubangiji yake yi muku.

2 Ubangiji ya ce,

“Kada ku koyi abubuwan da

al’ummai suke yi,

Kada ku ji tsoron alamun da suke a

sama,

Ko da yake al’ummai suna jin

tsoronsu.

3 Gama al’adun mutane na ƙarya ne,

Daga cikin jeji aka sare wani itace,

Gwanin sassaƙa ya sassaƙa shi da

gizago.

4 Mutane sukan yi masa ado na azurfa

da zinariya,

Sukan ɗauki guduma su kafa shi da

ƙusoshi,

Don kada ya motsa.

5 Gumakansu dodon gona suke, a

cikin gonar kabewa,

Ba su iya yin magana,

Ɗaukarsu ake yi domin ba su iya

tafiya!

Kada ku ji tsoronsu.

Gama ba su da ikon aikata mugunta

ko alheri.”

6 Ya Ubangiji, ba wani kamarka,

Kai mai girma ne,

Sunanka kuma yana da girma da

iko.

7 Wane ne ba zai ji tsoronka ba, ya

Sarkin dukan al’ummai?

Ka isa a ji tsoronka,

Gama babu kamarka a cikin dukan

masu hikima na al’ummai,

Da kuma cikin dukan mulkokinsu,

Ba wani kamarka.

8 Dukansu dakikai ne wawaye,

Koyarwar gumaka ba wani abu ba

ne, itace ne kawai!

9 An kawo fallayen azurfa daga

Tarshish,

Da zinariya kuma daga Ufaz,

Aikin gwanaye da maƙeran

zinariya.

Tufafinsu na mulufi ne da shunayya,

duka aikin gwanaye.

10 Amma Ubangiji shi ne Allah na

gaskiya,

Shi Allah mai rai ne,

Shi Sarki ne madawwami.

Saboda hasalarsa duniya ta girgiza,

Al’ummai ba za su iya jurewa da

fushinsa ba.

11 Haka za ku faɗa musu, “Gumakan da ba su yi sammai da duniya ba, za su lalace a duniya da a ƙarƙashin sammai.”

12 Shi ne, ta wurin ikonsa ya yi duniya,

Ta wurin hikimarsa ya kafa ta,

Ta wurin basirarsa kumaya ya shimfiɗa

sammai.

13 Sa’ad da ya yi murya akan ji ƙugin

ruwa a cikin sammai

Yakan kawo ƙasashi daga ƙurewar

duniya,

Yakan yi walƙiyoyi saboda ruwan

sama,

Daga cikin taskokinsa yakan kawo

iska.

14 Kowane mutum dakiki ne, marar

ilimi,

Kowane maƙerin zinariya zai sha

kunya saboda gumakansa,

Gama siffofinsa ƙarya ne,

Ba numfashi a cikinsu.

15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne,

A lokacin da za a hukunta su za su

lalace.

16 Gama shi ba kamar waɗannan yake

ba,

Shi na Yakubu ne.

Shi ne ya yi dukan kome,

Kabilan Isra’ilawa gādonsa,

Sunansa Ubangiji Mai Runduna.

Risɓewar Yahuza

17 Ku tattara kayayyakinku,

Ku mazaunan wurin da aka kewaye

da yaƙi.

18 Gama haka Ubangiji ya ce,

“Ga shi, ina jefar da mazaunan

ƙasar daga ƙasarsu a wannan

lokaci,

Zan kawo musu wahala, za su kuwa

ji jiki.”

19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka

yi mini.

Raunina mai tsanani ne,

Amma na ce, lalle wannan azaba ce,

Tilas in daure da ita.

20 An lalatar da alfarwata,

Dukan igiyoyi sun tsintsinke,

‘Ya’yana maza sun bar ni, ba su

nan.

Ba wanda zai kafa mini alfarwata

Ya kuma rataya labulena.

21 Makiyayan dakikai ne,

Ba su roƙi Ubangiji ba,

Don haka ba su sami wadata ba,

An watsa dukan garkensu.

22 Ku ji fa, an ji ƙishin-ƙishin! Ga shi

kuma, yana tafe.

Akwai babban hargitsin da ya fito

daga arewa,

Don a mai da biranen Yahuza kufai,

wurin zaman diloli.

23 “Ya Ubangiji, na sani al’amuran

mutum ba a hannunsa suke ba,

Ba mutum ne yake kiyaye takawarsa

ba

24 Ka tsauta mini, ya Ubangiji, amma

da adalcinka,

Ba da fushinka ba, don kada ka

wofinta ni.

25 Ka kwarara hasalarka a kan sauran

al’umma da ba su san ka ba,

Da a kan jama’ar da ba su kiran

sunanka,

Gama sun cinye Yakubu,

Sun cinye shi, sun haɗiye shi,

Sun kuma mai da wurin zamansa

kufai.”

Categories
IRM

IRM 11

An Ta da Alkawari

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya cewa,

2 “Ka ji maganar wannan alkawari, sa’an nan ka faɗa wa mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima.

3 Ka faɗa musu cewa, ‘In ji Ubangiji Allah na Isra’ila, la’ananne ne wanda bai kula da maganar alkawarin nan ba.

4 Wato alkawarin da na yi da kakanninku a lokacin da na fito da su daga ƙasar Masar, daga cikin tanderun ƙarfe. Na faɗa musu su yi biyayya da maganata, su aikata dukan abin da na umarce su. Ta haka za su zama mutanena, ni kuma in zama Allahnsu.

5 Sa’an nan zan cika maganar rantsuwa da na rantse wa kakanninku, da na ce zan ba su ƙasa wadda take cike da albarka kamar yadda yake a yau.’ ”

Irmiya ya ce, “Amin, amin, ya Ubangiji.”

6 Ubangiji kuma ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuza da titunan Urushalima duka, cewa su ji maganar alkawarin nan, su aikata.

7 Lokacin da na fito da kakanninsu daga ƙasar Masar na faɗakar da su musamman, na yi ta faɗakar da su har wannan rana, ina cewa, ‘Ku yi biyayya da maganata.’

8 Amma duk da haka ba su yi biyayya ba, ba su kuma kasa kunne ba. Kowa ya bi tattaurar zuciyarsa mai mugunta. Domin haka na kawo musu dukan maganar alkawarin nan wanda na umarce su su yi, amma ba su yi ba.”

9 Ubangiji ya kuma ce mini, “Akwai tawaye a cikin mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima.

10 Sun koma a kan laifofin kakanninsu, waɗanda suka ƙi jin maganata, suka bi gumakansu don su bauta musu, jama’ar Isra’ila da na Yahuza sun ta da alkawarina wanda na yi da kakanninsu.

11 Saboda haka ni Ubangiji na ce, ‘Ga shi, ina kawo musu masifa wadda ba za su iya tsere mata ba, ko da za su yi kuka gare ni ba zan ji su ba.

12 Sa’an nan biranen Yahuza da mazaunan Urushalima za su tafi, su yi kuka ga gumaka waɗanda suka ƙona musu turare, amma ba za su iya cetonsu a lokacin wahalarsu ba.

13 Gama yawan gumakansu sun kai yawan biranensu. Yawan bagadan da suke da su kuma sun kai yawan titunan Urushalima, abin kunya, bagadan ƙona wa Ba’al turare ne.’

14 Don haka kada ka yi wa waɗannan mutane addu’a. Kada ka yi kuka ko addu’a dominsu, gama ba zan kasa kunne gare su ba, ko da sun yi kirana a lokacin wahalarsu.”

15 Ubangiji ya ce, “Wane iko ƙaunatacciyata take da shi cikin Haikalina, da ya ke ta aikata mugayen ayyuka? Ko alkawarai da naman hadayu za su iya kawar miki da ƙaddararki, har da za ki yi taƙama?

16 Dā na kira ki itacen zaitun mai duhuwa, kyakkyawa, mai kyawawan ‘ya’ya, amma da ƙugin babbar iska za a cinna miki wuta, za ta kuwa cinye rassanki.”

17 Ubangiji Mai Runduna, wanda ya dasa ku, ya hurta masifar da za ta same ku saboda muguntar da mutanen Isra’ila da na Yahuza suka yi, suka tsokane ni in yi fushi saboda suna ƙona wa Ba’al turare.

An Shirya Maƙarƙashiya don a Kashe Irmiya

18 Ubangiji ya sanasshe ni,

Na kuwa sani,

Sa’an nan ya nuna mini mugayen

ayyukansu.

19 Amma ina kama da lafiyayyen ɗan

rago,

Wanda aka ja zuwa mayanka,

Ashe, ni suke ƙulla wa munafuncin!

Ni kuwa ban sani ba, da suke cewa,

“Bari mu lalatar da itacen duk da

‘ya’yansa.

Bari mu datse shi daga ƙasar masu

rai,

Har da ba za a ƙara tunawa da

sunansa ba.”

20 Amma ya Ubangiji Mai Runduna,

mai shari’ar adalci,

Kakan gwada zuciya da tunani,

Ka yarda mini in ga sakayyar da za

ka yi mini a kansu,

Gama a gare ka na danƙa

maganata.

21 Saboda haka ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka, da suka ce, “Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji, in ba haka ba, da hannunmu za mu kashe ka.”

22 Domin haka ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ga shi kuwa, zan hukunta su, za a kashe samarinsu da takobi, ‘ya’yansu mata da maza, yunwa za ta kashe su.

23 Ba wanda zai ragu daga cikin mutanen Anatot, gama zan kawo wa mutanen Anatot masifa, a shekarar hukuncinsu.”

Categories
IRM

IRM 12

Fatawar Irmiya da Amsar Ubangiji

1 Ya Ubangiji, kai adali ne sa’ad da na kawo ƙara a gare ka.

Duk da haka zan bayyana ƙarata a

gabanka,

Me ya sa mugaye suke arziki cikin

harkarsu?

Me ya sa dukan maciya amana suke

zaman lafiya,

Suna kuwa ci gaba?

2 Kai ka dasa su, sun kuwa yi saiwa,

Suna girma, suna kuma ba da

‘ya’ya,

Sunanka na a cikin bakinsu, amma

kana nesa da zuciyarsu.

3 Amma kai, ya Ubangiji, kana sane da

ni, kana ganina,

Kai kanka kake gwada tunanina.

Ka jawo su kamar tumaki zuwa

mayanka,

Ka ware su domin ranar yanka.

4 Sai yaushe ƙasar za ta daina

makoki,

Ciyawar kowace saura kuma ta daina

yin yaushi?

Saboda muguntar mazaunan ƙasar

ne dabbobi da tsuntsaye suka

ƙare,

Domin mutanen suna cewa, “Ba zai

ga ƙarshenmu ba.”

5 Ubangiji ya ce,

“Idan kai da mutane kun yi tseren

ƙafa sun gajiyar da kai,

Yaya za ka iya gāsa da dawakai?

Idan ka fāɗi a lafiyayyiyar ƙasa,

Ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?

6 Gama har da ‘yan’uwanka da gidan

mahaifinka,

Sun ci amanarka,

Suna binka da kuka,

Kada ka gaskata su,

Ko da yake suna faɗa maka

maganganu masu daɗi.”

7 Ubangiji ya ce,

“Na bar jama’ata.

Na rabu da gādona,

Na ba da wanda raina yake ƙauna a

hannun maƙiyansa.

8 Abin gādona ya zama mini kamar

zaki a cikin kurmi,

Ya ta da murya gāba da ni,

Domin haka na ƙi shi.

9 Ashe, abin gadon nan nawa ya zama

dabbare-dabbaren tsuntsun nan ne

mai cin nama?

Tsuntsaye masu cin nama sun kewaye

shi?

Tafi, ka tattaro namomin jeji,

Ka kawo su su ci.

10 Makiyaya da yawa sun lalatar da

gonar inabina.

Sun tattake nawa rabo,

Sun mai da nawa kyakkyawan rabo

kufai da hamada.

11 Sun maishe shi kufai, ba kowa,

Yana makoki a gare ni,

Ƙasar duka an maishe ta kufai,

Amma ba wanda zuciyarsa ta damu a

kan wannan.

12 A kan dukan tsaunukan nan na

hamada

Masu hallakarwa sun zo,

Gama takobin Ubangiji yana ta kisa

Daga wannan iyakar ƙasa zuwa

waccan,

Ba mahalukin da yake da salama.

13 Sun shuka alkama, sun girbe

ƙayayuwa,

Sun gajiyar da kansu, amma ba su

amfana da kome ba.

Za su sha kunya saboda abin da suke

girbe,

Saboda zafin fushin Ubangiji.”

14 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan mugayen maƙwabtan Isra’ila waɗanda suka taɓa gādon da ya ba jama’arsa Isra’ila su gada. “Saboda haka zan tumɓuke su daga cikin ƙasarsu. Zan kuma tumɓuke mutanen Yahuza daga cikinsu.

15 Bayan na tumɓuke su kuma, zan sāke yi musu jinƙai, in komar da su, kowanne zuwa gādonsa.

16 Zai zama kuwa, idan za su himmantu su koyi al’amuran jama’ata, su yi rantsuwa da sunana, su ce, ‘Da zatin Ubangiji,’ kamar yadda suka koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za a gina su a tsakiyar jama’ata.

17 Amma idan wata al’umma za ta ƙi kasa kunne, to, sai in tumɓuke ta ɗungum, in hallaka ta, in ji Ubangiji.”

Categories
IRM

IRM 13

Misali da Abin Ɗamara

1 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, ya ce, “Tafi ka sayo lilin na yin ɗamara, ka sha ɗamara da shi kada kuwa ka tsoma shi a ruwa.”

2 Sai na sayo abin ɗamara kamar yadda Ubangiji ya ce, na sha ɗamara da shi.

3 Ubangiji kuma ya sāke yin magana da ni sau na biyu,

4 ya ce, “Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi Kogin Yufiretis, ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”

5 Sai na tafi, na ɓoye shi a Yufiretis kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.

6 Bayan an ɗan daɗe, sai Ubangiji ya ce mini, “Tashi, ka tafi Yufiretis, ka ɗauko abin ɗamara wanda na umarce ka ka ɓoye a can.”

7 Sai na tafi Yufiretis, na haƙa na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi. Amma abin ɗamara ya lalace, ba shi da sauran amfani.

8 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,

9 “Haka zan lalatar da alfarmar Yahuza da yawan alfarmar Urushalima.

10 Wannan muguwar jama’a, wadda ta ƙi jin maganata, wadda ta taurare, ta bi son zuciyarta, ta kuma bi gumaka ta bauta musu, ta yi musu sujada, za ta zama kamar abin ɗamaran nan, wanda ba shi da sauran amfani.

11 Gama kamar yadda abin ɗamara yakan kame tam a gindin mutum, haka na sa dukan mutanen Isra’ila da dukan mutanen Yahuza su manne mini domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.”

Misali da Tulun Ruwan Inabi

12 “Sai ka faɗa musu wannan magana cewa, ‘Ni Ubangiji Allah na Isra’ila na ce, a cika kowane tulu da ruwan inabi.’ Su kuwa za su ce maka, sun sani sarai za a cika kowane tulu da ruwan inabi.

13 Sa’an nan za ka faɗa musu, Ubangiji ya ce, ‘Ga shi, zan sa dukan mazaunan ƙasar su bugu da ruwan inabi, wato sarakunan da suka hau gadon sarautar Dawuda, da firistoci, da annabawa, da dukan mazaunan Urushalima.

14 Zan sa su kara da junansu, iyaye maza da ‘ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi, ko juyayi, ko jinƙai ba za su sa in fasa hallaka su duka ba.’ ”

Yahuza bai Tuba ba, za a Kai shi Zaman Talala

15 Ku kasa kunne, ku ji,

Kada ku yi girmankai, gama

Ubangiji ya yi magana.

16 Ku girmama Ubangiji Allahnku,

Kafin ya kawo duhu,

Kafin kuma ƙafafunku su yi tuntuɓe

a kan dutse, da duhu duhu,

Sa’ad da kuke neman haske, sai ya

maishe shi duhu,

Ya maishe shi duhu baƙi ƙirin.

17 Amma idan ba za ku ji ba,

Raina zai yi kuka a ɓoye saboda

girmankanku,

Idanuna za su yi kuka ƙwarai, za su

zub da hawaye,

Domin an kai garken Ubangiji zuwa

bauta.

18 Ubangiji ya ce wa Irmiya,

“Ka faɗa wa sarki da sarauniya,

uwarsa, su sauka daga gadon

sarautarsu,

Domin an tuɓe kyakkyawan rawanin

sarautarsu daga kansu.

19 An kulle biranen Negeb,

Ba wanda zai buɗe su,

Yahuza duka an kai ta zaman dole,

Dukanta an kai ta zaman dole.

20 “Ku ta da idanunku, ku ga waɗanda

suke zuwa daga arewa!

Ina kyakkyawan garken nan da aka

ba ku?

21 Me za ku ce sa’ad da aka naɗa muku

shugabanni,

Waɗanda ku da kanku kuka koya

musu, suka zama abokanku?

Ashe, azabai ba za su auko muku ba

Kamar yadda sukan auko wa mace

mai naƙuda?

22 Idan kun ce a zuciyarku,

‘Me ya sa waɗannan abubuwa suka

same mu?’

Saboda yawan zunubanku ne,

Shi ya sa an tone tsiraicinku,

Aka wahalshe ku.

23 Mutumin Habasha zai iya sāke

launin fatar jikinsa?

Ko kuwa damisa za ta iya sāke

dabbare-dabbarenta?

Idan haka ne, ku kuma za ku iya yin

nagarta,

Ku da kuka saba da yin mugunta.

24 Zan warwatsar da ku

Kamar yadda iskar hamada take

watsar da ƙaiƙayi.”

25 Ubangiji ya ce, “Wannan shi ne

rabonku,

Rabon da na auna muku, ni Ubangiji

na faɗa.

Domin kun manta da ni, kun dogara

ga ƙarairayi,

26 Ni kaina kuma zan kware muku

suturarku ta rufe fuskarku

Don a ga tsiraicinku.

27 Na ga abubuwanku masu

banƙyama,

Wato zinace-zinacenku, da haniniya

kamar dawakai,

Da muguwar sha’awarku ta

karuwanci a kan tuddai da filaye,

Ya Urushalima, taki ta ƙare!

Har yaushe za a tsarkake ki?”

Categories
IRM

IRM 14

Babban Fari

1 Maganar da Ubangiji ya yi wa Irmiya a kan fari ke nan,

2 “Yahuza tana makoki,

Ƙofofin biranenta suna lalacewa,

Mutanenta suna kwance a ƙasa,

suna makoki,

Urushalima tana kuka da babbar

murya.

3 Manyan mutanenta sun aiki

barorinsu su ɗebo ruwa.

Da suka je maɓuɓɓuga, sai suka

tarar ba ruwa.

Sai suka koma da tulunansu

haka nan,

An kunyatar da su, an ƙasƙantar

da su,

Suka lulluɓe kansu don kunya.

4 Saboda ƙasar ta bushe,

Tun da ba a yi ruwa a kanta ba,

Manoma sun sha kunya,

Suka lulluɓe kansu don kunya.

5 Barewa ma a saura takan gudu,

Ta bar ɗanta sabon haihuwa,

Domin ba ciyawa.

6 Jakunan jeji suna tsaye a kan tuddan

da ba ciyawa,

Suna haki kamar diloli,

Idanunsu ba su gani

Domin ba abinci.”

7 Irmiya ya ce,

“Ko da yake zunubanmu su ne

shaidunmu,

Ya Ubangiji, ka yi taimako saboda

sunanka!

Gama kāsawarmu ta yi yawa,

Domin mun yi maka zunubi.

8 Ya kai, wanda kake begen Isra’ila,

Mai Cetonta a lokacin wahala,

Ƙaƙa ka zama kamar baƙo a ƙasar?

Kamar matafiyi wanda ya kafa

alfarwarsa a gefen hanya don ya

kwana, ya wuce?

9 Ƙaƙa ka zama kamar wanda bai san

abin da zai yi ba,

Kamar jarumin da ya kasa yin

ceto?

Duk da haka, ya Ubangiji, kana nan

a tsakiyarmu.

Da sunanka ake kiranmu,

Kada ka bar mu!”

10 Haka Ubangiji ya ce a kan waɗannan mutane, “Sun cika son yawaceyawace, ba su iya zama wuri ɗaya, don haka ni Ubangiji, ban yarda da su ba, zan tuna da laifofinsu in hukunta zunubansu.”

11 Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin lafiyar jama’an nan.

12 Ko da sun yi azumi, ba zan ji kukansu ba, ko da sun miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta sha, ba zan karɓe su ba. Amma zan hallaka su da takobi, da yunwa, da annoba.”

13 Sai na ce, “Ya Ubangiji Allah, ga shi, annabawa sun faɗa musu, sun ce, ‘Ba za ku ga takobi ko yunwa ba, amma zan ba ku dawwamammiyar salama a wannan wuri.’ ”

14 Ubangiji kuwa ya ce mini, “Annabawa, annabcin ƙarya suka yi da sunana. Ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba, ban kuma yi magana da su ba. Annabcin da suke yi muku na wahayin ƙarya ne, dubar da suke yi marar amfani ce, tunaninsu ne kawai.

15 Domin haka ga abin da ni Ubangiji na ce a kan annabawan da suke yin annabci da sunana, ko da yake ban aike su ba, waɗanda suke cewa, ‘Takobi da yunwa ba za su shigo ƙasan nan ba.’ Za a hallaka su da takobi da yunwa.

16 Mutanen da suka yi wa annabci, za a jefar da su waje a kan titunan Urushalima, a karkashe su da yunwa da takobi, ba wanda zai binne su, da su, da matansu, da ‘ya’yansu mata da maza. Zan sa muguntarsu ta koma kansu.

17 “Irmiya, ka faɗa wa mutanen baƙin

ciki da ya same ka,

Ka ce, ‘Bari idanuna su yi ta zub da

hawaye dare da rana,

Kada su daina, saboda an buge

budurwa, ‘yar jama’ata,

An yi mata babban rauni da dūka

mai tsanani.

18 Idan na tafi cikin saura,

Sai in ga waɗanda aka kashe da

takobi!

Idan kuma na shiga birni,

Sai in ga waɗanda suke ta fama da

yunwa!

Gama annabi da firist, sai harkarsu

suke ta yi a ƙasar,

Amma ba su san abin da suke yi

ba.’ ”

Mutane Sun Roƙi Ubangiji

19 “Ka ƙi Yahuza ke nan ɗungum?

Ranka kuma yana jin ƙyamar

Sihiyona ne?

Me ya sa ka buge mu, har da ba za

mu iya warkewa ba?

Mun zuba ido ga samun salama,

amma ba wani abin alheri da ya

zo.

Mun kuma sa zuciya ga warkewa,

amma sai ga razana.

20 Mun san muguntar da muka yi, ya

Ubangiji,

Da wadda kakanninmu suka yi,

Gama mun yi maka zunubi.

21 Saboda darajar sunanka, kada ka

wulakanta mu,

Kada kuma ka ƙasƙantar da

darajar kursiyinka,

Ka tuna da alkawarin da ka yi

mana,

Kada ka ta da shi.

22 A cikin gumakan al’ummai akwai

mai iya sa a yi ruwa?

Sammai kuma su yi yayyafi?

Ashe, ba kai ne ba, ya Ubangiji

Allahnmu?

Domin haka a gare ka muke sa

zuciya,

Gama kai ne mai yin waɗannan

abubuwa duka.”

Categories
IRM

IRM 15

Fushin Ubangiji da Yahuza bai Huce Ba

1 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da a ce Musa da Sama’ila za su tsaya a gabana, duk da haka zuciyata ba za ta komo wurin mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana su yi tafiyarsu!

2 Sa’ad da suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu cewa, Ubangiji ya ce,

‘Waɗanda suke na annoba, su tafi ga

annoba!

Waɗanda suke na takobi, su tafi ga

takobi!

Waɗanda suke na yunwa, su tafi ga

yunwa!

Waɗanda suke na bauta, su tafi ga

bauta!’

3 Zan sa musu masu hallakarwa huɗu,” in ji Ubangiji, “da takobi don kisa, da karnuka don yayyagawa, da tsuntsayen sararin sama, da dabbobin duniya don su cinye, su hallakar.

4 Zan kuma sa su zama abin banƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manassa ɗan Hezekiya, Sarkin Yahuza ya aikata a Urushalima.

5 “Wa zai ji tausayinki, ya

Urushalima?

Wa zai yi baƙin ciki dominki?

Wa kuma zai ratso wurinki don ya

tambayi lafiyarki?

6 Ni Ubangiji na ce, kun ƙi ni, kuna ta

komawa da baya,

Don haka na nuna ikona gāba da ku,

na hallaka ku,

Na gaji da jin tausayinku!

7 Na sheƙe su da abin sheƙewa a

ƙofofin garuruwan ƙasar.

Na sa ‘ya’yansu su mutu, na hallaka

mutanena,

Ba su daina yin mugayen ayyukansu

ba.

8 Na yawaita gwauraye, wato mata da

mazansu suka mutu,

Fiye da yashin teku.

Na kawo wa uwayen samari mai

hallakarwa da tsakar rana.

Na sa azaba da razana su auka musu

farat ɗaya.

9 Ita wadda ta haifi ‘ya’ya bakwai ta

yi yaushi ta suma,

Ranarta ta faɗi tun lokaci bai yi ba,

An kunyatar da ita, an wulakantar

da ita.

Waɗanda suka ragu daga cikinsu

Zan bashe su ga takobi gaban abokan

gābansu.

Ni Ubangiji na faɗa.”

10 Kaitona, ya mahaifiyata, da kika haife ni, mai jayayya mai gardama da kowa cikin dukan ƙasar! Ban ba da rance ba, ba kuma wanda ya ba ni rance, duk da haka dukansu suna zagina.

11 Ubangiji ya ce mini, “Zan keɓe ka domin alheri, hakika zan sa abokan gaba su yi roƙo gare ka a lokacin bala’i da kuma lokacin damuwa.

12 Wa zai iya karya ƙarfe ko tagulla daga arewa?”

13 Ubangiji ya ce mini, “Zan ba da wadatarku da dukiyarku ganima kyauta, saboda dukan zunubanku a dukan ƙasar.

14 Zan sa ku bauta wa abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina ya kama kamar wuta, zai yi ta ci har abada.”

15 Sa’an nan Irmiya ya ce, “Ya

Ubangiji, ka sani.

Kai ne, ka ziyarce ni,

Ka kuma sāka wa waɗanda suke

tsananta mini.

Ka sani saboda kai nake shan zargi.

16 Maganarka da na samu na ci.

Maganarka kuwa ta zama abar

murna a gare ni,

Ta faranta mini zuciya.

Gama ana kirana da sunanka,

Ya Ubangiji Allah Mai Runduna.

17 Ban zauna cikin ƙungiyar masu

annashuwa ba.

Ban kuwa yi murna ba,

Na zauna ni kaɗai saboda kana tare

da ni,

Gama ka sa na cika da haushi.

18 Me ya sa azabata ta ƙi ƙarewa,

Raunukana kuma ba su warkuwa,

Sun kuwa ƙi warkewa?

Za ka yaudare ni kamar rafi,

Ko kamar ruwa mai ƙafewa?”

19 “Domin haka ga abin da ni, Ubangiji

na ce,

Idan ka komo sa’an nan zan kawo

ka.

Za ka tsaya a gabana.

Idan ka hurta abin da yake gaskiya

ba na ƙarya ba,

Za ka zama kakakina.

Za su komo gare ka,

Amma kai ba za ka koma wurinsu

ba.

20 Zan maishe ka garun tagulla saboda

waɗannan mutane,

Za su yi yaƙi da kai, amma ba za

su yi nasara a kanka ba,

Gama ina tare da kai don in cece ka,

in kuɓutar da kai.

21 Zan kuɓutar da kai daga hannun

mugaye,

Zan ɓamɓare ka daga hannun

marasa tausayi.”