Categories
IRM

IRM 16

Umarnin Ubangiji zuwa ga Irmiya

1 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,

2 “Ba za ka yi aure ka haifi ‘ya’ya mata da maza a wannan wuri ba.

3 Ga abin da ni Ubangiji na faɗa a kan ‘ya’ya mata da maza da aka haifa a wannan wuri, da kuma a kan iyayensu mata da maza da suka haife su a wannan ƙasa,

4 za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi makoki dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba. Za su zama juji. Takobi da yunwa za su kashe su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namomin jeji.”

5 Ubangiji kuma ya ce, “Kada ka shiga gidan da ake makoki, ko ka tafi inda ake baƙin ciki, kada ka yi baƙin ciki saboda su, gama na ɗauke salamata, da ƙaunata, da jinƙaina daga wurin jama’an nan.

6 Yaro da babba za su mutu a wannan ƙasa, ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi baƙin ciki dominsu ba. Ba kuwa wanda zai tsaga jikinsa ko ya aske kansa ƙwal dominsu.

7 Ba wanda zai ba mai makoki abinci don ya ta’azantar da shi saboda mamacin, ba kuma wanda zai ba shi abin sha don ya ta’azantar da shi saboda mahaifinsa ko mahaifiyarsa.

8 “Kada kuma ka shiga gidan da ake biki, ka zauna ka ci ka sha tare da su.

9 Gama ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, zan sa muryar murna, da ta farin ciki, da ta ango, da ta amarya, su ƙare a wurin nan a idonka da zamaninka.

10 “Sa’ad da ka faɗa wa mutanen nan wannan magana duka, za su kuwa ce maka, ‘Me ya sa Ubangiji ya hurta wannan babbar masifa a kanmu? Mene ne laifinmu? Wane irin zunubi muka yi wa Ubangiji Allahnmu?’

11 Sai ka faɗa musu cewa, Ubangiji ya ce, ‘Domin kakanninku sun rabu da ni, sun bi gumaka, sun bauta musu, sun yi musu sujada. Sun rabu da ni, sun ƙi kiyaye dokokina.

12 Ku kuma kun yi laifi fiye da na kakanninku. Kowannenku kuwa ya bi tattauran mugun nufin zuciyarsa, yana ƙin kasa kunne gare ni.

13 Don haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasa wadda ku ko kakanninku ba ku sani ba. A can za ku bauta wa gumaka dare da rana, gama ba zan nuna muku ƙauna ba.’

14 “Saboda haka, ga shi, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da ba za a ƙara cewa, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da jama’ar Isra’ila daga ƙasar Masar ba.’

15 Amma za a ce, ‘Na rantse da Ubangiji wanda ya fito da jama’ar Isra’ila daga ƙasar arewa, da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su,’ gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba kakanninsu.

16 “Ga shi, ina aiko da masunta da yawa,” in ji Ubangiji, “za su kuwa kama su, daga baya kuma zan aika da mafarauta da yawa, za su farauce su daga kowane tsauni, da tudu, da kogwannin duwatsu.

17 Gama ina ganin dukan ayyukansu, ba a ɓoye suke a gare ni ba, muguntarsu kuma ba a ɓoye take a gare ni ba.

18 Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, abin gādona kuma sun cika shi da abubuwansu na banƙyama.”

Addu’ar Irmiya ta Dogara ga Allah

19 “Ya Ubangiji, ƙarfina da kagarata,

Mafakata a ranar wahala,

A gare ka al’ummai za su zo,

Daga ƙurewar duniya, su ce,

‘Kakanninmu ba su gāji kome ba, sai

ƙarya,

Da abubuwan banza marasa

amfani.’

20 Mutum zai iya yi wa kansa alloli?

Ai, waɗannan ba alloli ba ne!”

21 Ubangiji ya ce,

“Saboda haka, ga shi, zan sa su sani,

Sau ɗayan nan kaɗai zan sa su su san

ikona da ƙarfina,

Za su kuma sani sunana Ubangiji

ne.”

Categories
IRM

IRM 17

Zunubin Yahuza Ya Yi Kanta

1 Ubangiji ya ce, “An rubuta zunubin mutanen Yahuza da alƙalamin ƙarfe, mai bakin yakutu. An zana shi a allon zuciyarsu da a zankayen bagadansu.

2 Idan sun tuna da ‘ya’yansu haka sun tuna da bagadansu da Ashtarot ɗinsu a gindin itatuwa masu duhuwa da kan tuddai masu tsayi.

3 Ku mazauna a tsaunuka da cikin saura, zan ba da dukiyarku da wadatarku ganima saboda dukan zunuban da kuka yi a dukan ƙasar.

4 Za ku rasa abin da yake hannunku daga cikin gādon da na ba ku. Zan sa ku bauta wa abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama da fushina wuta ta kama wadda za ta yi ta ci har abada.”

5 Ubangiji ya ce,

“La’ananne ne mutumin da yake

dogara ga mutum,

Wanda jiki ne makaminsa,

Wanda ya juya wa Ubangiji baya,

6 Gama yana kama da sagagi a

hamada,

Ba zai ga wani abu mai kyau yana

zuwa ba.

Zai zauna a busassun wuraren

hamada,

A ƙasar gishiri, inda ba kowa.

7 “Mai albarka ne mutumin da yake

dogara ga Ubangiji,

Wanda Ubangiji ne madogararsa.

8 Shi kamar itace ne wanda ake dasa a

bakin rafi

Wanda yake miƙa saiwoyinsa zuwa

cikin rafin,

Ba zai ji tsoron rani ba,

Kullum ganyensa kore ne,

Ba zai damu a lokacin fari ba,

Ba zai ko fasa yin ‘ya’ya ba.

9 “Zuciya ta fi kome rikici,

Cuta gare ta matuƙa,

Wa zai san kanta?

10 Ni Ubangiji nakan bincike tunani,

In gwada zuciya,

Domin in sāka wa kowane mutum

gwargwadon al’amuransa,

Da kuma gwargwadon ayyukansa.

11 “Kamar makwarwar da ta kwanta

kan ƙwan da ba ita ta nasa ba,

Haka yake ga wanda ya sami dukiyar

haram,

Yana gaɓar ƙarfinsa, za ta rabu da

shi,

A ƙarshe zai zama wawa.”

12 Kursiyi mai daraja,

Da aka sa a bisa tun daga farko,

Wurin ke nan inda Haikalinmu

yake.

13 Ya Ubangiji, begen Isra’ila,

Duk waɗanda suka rabu da kai, za su

sha kunya.

Waɗanda suka ba ka baya a duniya

za a rubuta su

Domin sun rabu da Ubangiji,

maɓuɓɓugar ruwan rai.

Irmiya Ya Roƙi Ubangiji ya Kiyaye Shi

14 Ubangiji, ka warkar da ni, zan kuwa

warke,

Ka cece ni, zan kuwa cetu,

Gama kai ne abin yabona.

15 Ga shi, suna ce mini,

“Ina maganar Ubangiji take?

Ta zo mana!”

16 Amma ni ban yi gudun zaman

makiyayi a gabanka ba,

Ban kuma so zuwan ranar bala’i ba,

Ka kuwa sani.

Abin da ya fito daga bakina kuwa,

A bayyane yake gare ka.

17 Kada ka zamar mini abin razana,

Kai ne mafakata cikin ranar masifa,

18 Bari waɗanda suka tsananta mini su

sha kunya,

Amma kada ka bar ni in kunyata.

Bari su tsorata,

Amma kada ka bar ni in tsorata.

Ka aukar musu da ranar masifa,

Ka hallaka su riɓi biyu!

A kan Kiyaye Ranar Asabar

19 Haka Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi ka tsaya a ƙofar Biliyaminu, wadda sarakunan Yahuza suke shiga da fita ta cikinta, ka kuma tafi dukan ƙofofin Urushalima.

20 Ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuza, da dukan Yahuza, da dukan mazaunan Urushalima, waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.

21 Haka Ubangiji ya ce, ku yi hankali saboda rayukanku, kada ku ɗauki kaya a ranar Asabar, ko ku shigar da kowane abu ta ƙofofin Urushalima.

22 Kada ku ɗauki kaya, ku fita da shi daga gidajenku a ranar, ko ku yi kowane irin aiki, amma ku kiyaye ranar Asabar da tsarki, kamar yadda na umarci kakanninku.’

23 Amma duk da haka ba su kasa kunne, ko su mai da hankali ba. Amma suka taurare don kada su ji, su karɓi koyarwa.

24 “ ‘Amma idan kun kasa kunne gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofin wannan birni a ranar Asabar ba, amma kuka kiyaye ranar Asabar da tsarki, ba ku yi aiki a cikinta ba,

25 sa’an nan ne sarakuna waɗanda za su zauna a kan gadon sarautar Dawuda, za su shiga ta ƙofofin wannan birni, suna hawan karusai, da dawakai, su da sarakunansu, da jama’ar Yahuza da mazaunan Urushalima. Za a zauna a wannan birni har abada.

26 Mutane za su zo daga biranen Yahuza da wuraren da yake kewaye da Urushalima, daga ƙasar Biliyaminu, da ta Shefela, da ta ƙasar tuddai, da kuma ta Negeb, suna kawo hadayu na ƙonawa da sadakoki, da hadayu na sha, da na turare, za su kuma kawo hadayu na godiya a Haikalin Ubangiji.

27 Amma idan ba ku kasa kunne gare ni ba, ba ku kuwa kiyaye ranar Asabar da tsarki ba, kun kuma ɗauki kaya kun shiga ta ƙofofin Urushalima a ranar Asabar, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wuta. Za ta kuwa cinye fādodin Urushalima, ba kuwa za ta kasu ba.’ ”

Categories
IRM

IRM 18

Irmiya a Gidan Maginin Tukwane

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce,

2 “Ka tashi, ka gangara zuwa gidan maginin tukwane, a can zan yi maka magana.”

3 Sai na gangara zuwa gidan maginin tukwanen, na iske shi yana ginin tukwane a kan na’urar ginin tukwanen.

4 Abin da yake ginawa ya lalace a hannunsa, sai ya sāke gina wani abu dabam da yumɓu ɗin, yadda ya ga dama.

5 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini,

6 “Ya jama’ar Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku kamar yadda maginin tukwanen nan ya yi ba? Duba, kamar yadda yumɓu yake a hannun maginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya ku jama’ar Isra’ila.

7 A duk lokacin da na ce zan tumɓuke, in kakkarya in hallaka wata al’umma, ko wani mulki,

8 idan wannan al’umma da na yi magana a kanta, ta juyo, ta tuba daga mugayen ayyukanta, zan janye masifar da na yi niyyar aukar mata.

9 A duk kuma lokacin da na ce zan gina, in kafa wata al’umma, ko wani mulki,

10 amma idan al’ummar ta aikata mugunta a gabana, ta ƙi saurarawa ga maganar, zan janye alherin da na yi niyyar yi mata.

11 Saboda haka yanzu, sai ka faɗa wa jama’ar Yahuza da mazaunan Urushalima, ka ce, haka Ubangiji ya faɗa, ‘Ga shi, na shirya muku masifa, ina tsara wahalar da za ta same ku. Bari kowannenku ya koma ya bar muguwar hanyarsa, ya gyara al’amuransa da ayyukansa.’

12 Amma za su ce, ‘Wannan ba abin da za mu kula da shi ba ne, mu ra’ayinmu za mu bi, kowannenmu kuwa zai yi bisa ga nufin tattaurar muguwar zuciyarsa.’

13 “Domin haka ni Ubangiji na ce,

‘Ka tambayi sauran al’umma.

Wa ya taɓa jin irin wannan?

Budurwa Isra’ila, ta yi mugun abu

ƙwarai!

14 Dusar ƙanƙara mai danshi ta taɓa

rabuwa da tsaunukan Lebanon?

Ko ruwan rafuffuka mai sanyi na kan

dutse ya taɓa ƙonawa?

15 Amma mutanena sun manta da ni,

Sun ƙona wa gumaka turare.

Sun yi tuntuɓe a cikin al’amuransu,

a hanyoyin dā,

Sun bi ɓarayin hanyoyi, ba su bi

karauka ba.

16 Sun mai da ƙasarsu abar

banƙyama,

Abin raini har abada.

Duk wanda ya wuce ta wurin zai

razana ya kaɗa kansa.

17 Haka zan warwatsa su

Kamar yadda iskar gabas take yi, a

gaban abokan gābansu,

Zan juya musu baya, ba za su ga

fuskata ba,

A ranar masifarsu.’ ”

Maƙarƙashiyar Mutane da Addu’ar Irmiya

18 Sa’an nan suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya, gama firist ba zai bar bin shari’a ba. Haka nan ma masu hikima ba za su bar yin shawara ba, haka nan kuma annabi ba zai bar yin magana ba! Ku zo mu kai ƙararsa, kada mu kula da abin da zai faɗa.”

19 Irmiya kuwa ya yi addu’a ya ce,

“Ya Ubangiji, ka kasa kunne gare ni,

ka ji ƙarar maƙiyana!

20 Daidai ne a rama alheri da

mugunta?

Duk da haka sun kafa wa raina tarko.

Ka tuna yadda na tsaya a gabanka,

Na yi maganar alheri a kansu,

Domin ka janye fushinka daga gare

su.

21 Saboda haka ka kawo wa ‘ya’yansu

yunwa,

Ka bashe su ga takobi,

Bari matansu su rasa ‘ya’ya,

mazansu su mutu,

Ka sa annoba ta kashe mazansu,

A kashe samarinsu da takobi a

yaƙi.

22 Bari a ji kururuwa daga gidajensu,

Saboda maharan da ka aika musu

farat ɗaya,

Gama sun haƙa rami don in fāɗa,

Sun kafa wa ƙafafuna tarkuna.

23 Amma ya Ubangiji,

Ka san dukan maƙarƙashiyarsu,

su kashe ni,

Kada ka gafarta musu muguntarsu,

kada kuma ka shafe zunubinsu

daga gabanka.

Ka sa a jefar da su daga gabanka,

Ka yi da su sa’ad da kake fushi!”

Categories
IRM

IRM 19

Fasasshen Tulu

1 Ubangiji ya ce mini, “Tafi ka sayo tulu a wurin maginin tukwane. Sa’an nan kuma ka ɗauki waɗansu daga cikin dattawan jama’a, da waɗansu manyan firistoci,

2 ku tafi kwarin ɗan Hinnom na mashigin Ƙofar Kasko, ka yi shelar maganar da zan faɗa maka a can.

3 Za ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya ku sarakunan Yahuza da mazaunan Urushalima, Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce, zan kawo wata irin masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.

4 Ga shi, mutanen nan sun rabu da ni, sun ƙazantar da wannan wuri sun ƙona wa gumaka turare, waɗanda su, ko kakanninsu, ko sarakunan Yahuza, ba su san su ba. Sun cika wannan wuri da jinin marasa laifi.

5 Sun gina wa Ba’al masujadai don su miƙa masa ‘ya’yansu maza hadayar ƙonawa, abin da ban umarta ba, ban kuma ba da izni ba, ban ma yi tunanin haka ba.

6 Saboda haka rana tana zuwa da ba za a ƙara ce da wannan wuri Tofet, ko kwarin ɗan Hinnom ba, amma za a ce da shi Kwarin Kisa.

7 A wannan wuri zan wofinta dabarun Yahuza da na Urushalima, zan sa a kashe jama’arsu da takobi, a gaban abokan gābansu, ta hannun waɗanda suke neman ransu. Zan ba da gawawwakinsu su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namomin jeji.

8 Zan mai da wannan birni abin ƙyama, abin raini, dukan wanda ya wuce wurin zai yi mamaki, ya yi tsaki saboda dukan masifun da suka auka wa birnin.

9 Zan sa su ci naman ‘ya’yansu mata da maza. Kowa zai ci naman maƙwabcinsa cikin damuwa a lokacin da za a kewaye su da yaƙi, zai sha wahala daga wurin abokan gābansa da waɗanda suke neman ransa.’

10 “Sa’an nan sai ka fasa tulun a gaban mutanen da suka tafi tare da kai,

11 ka kuwa ce musu, ‘Ubangiji Mai Runduna ya ce, haka zai farfasa jama’a, da wannan birni kamar yadda aka fashe tulun maginin tukwanen, ba kuwa zai gyaru ba. Za a binne mutane a Tofet domin za a rasa makabartar da za a binne su.

12 Haka zai yi wa wurin nan da mazauna cikinsa, ya mai da birnin nan kamar Tofet.

13 Gidajen Urushalima da gidajen sarakunan Yahuza da dukan gidaje waɗanda a kan rufinsu aka ƙona wa rundunar sararin sama turare, aka zuba wa gumaka hadayu na sha, za su ƙazantu kamar Tofet.’ ”

14 Sa’an nan Irmiya ya komo daga Tofet, inda Ubangiji ya aike shi don ya yi annabci, sai ya tsaya a fili na Haikalin Ubangiji, ya ce wa dukan jama’a,

15 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Ga shi, ina aukar wa wannan birni da dukan garuruwansa dukan masifu da na ambata a kansa, domin sun taurare zukatansu, sun ƙi jin maganata.’ ”

Categories
IRM

IRM 20

Saɓani Tsakanin Irmiya da Fashur Firist

1 Sa’ad da Fashur, firist, ɗan Immer, shugaban Haikalin Ubangiji ya ji Irmiya yana annabci a kan waɗannan abubuwa,

2 sai ya sa aka yi wa Irmiya dūka, aka kuma sa shi cikin turu a ƙofar Biliyaminu, a Haikalin Ubangiji.

3 Kashegari sa’ad da Fashur ya fitar da Irmiya daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashur ba, amma ya ba ka suna Magormissabib, wato razana ta kowace fuska.

4 Haka Ubangiji ya ce, ‘Ga shi, zan maishe ka abin tsoro ga kai kanka, da dukan abokanka. Abokan gābansu za su kashe su da takobi a kan idonka. Zan ba da dukan Yahuza a hannun Sarkin Babila, shi kuwa zai kwashe waɗansu ya kai bautar talala a Babila, ya kuma kashe waɗansu da takobi.

5 Banda haka kuma zan ba da dukan dukiyar wannan birni, da dukan ribarsa, da dukan abubuwa masu tamani, da dukan dukiyar sarakunan Yahuza, ga abokan gābansu, waɗanda za su washe su, su kama su, su kai Babila.

6 Kai kuma, Fashur, da dukan waɗanda suke a gidanka, za ku tafi bauta a Babila, za ku shiga Babila, a can za ku mutu, a can za a binne ku, kai da abokanka waɗanda ka yi wa annabcin ƙarya.’ ”

Kukan Irmiya

7 “Ya Ubangiji ka ruɗe ni, na kuwa

ruɗu,

Ka fi ni ƙarfi, ka kuwa rinjaye ni.

Na zama abin dariya dukan yini,

Kowa yana ta yi mini ba’a.

8 Duk lokacin da zan yi magana,

Nakan ta da murya in yi magana da

ƙarfi cewa,

‘Hargitsi da hallakarwa!’

Gama saboda maganar Ubangiji na

zama abin zargi,

Da abin ba’a dukan yini.

9 Idan na ce, ‘Ba zan ambaci Ubangiji

ba,

Ban zan ƙara yin magana da sunansa

ba,’

Sai in ji damuwa a zuciyata,

An kulle ta a ƙasusuwana,

Na gaji da danne ta a cikina,

Ba zan iya jurewa ba.

10 Na ji mutane da yawa suna sa mini

laƙabi cewa,

‘Razana ta kowace fuska,’

Suna cewa, ‘Mu la’anta shi!

Mu la’anta shi!’

Har ma da abokaina shaƙiƙai

Suna jira su ga fāɗuwata.

Suka ce, ‘Watakila a ruɗe shi,

Sa’an nan ma iya rinjayarsa

Mu ɗauki fansa a kansa.’

11 Amma Ubangiji kana tare da ni

Kamar jarumi mai bantsoro,

Don haka masu tsananta mini za su

yi tuntuɓe,

Ba za su rinjaye ni ba.

Za su sha kunya ƙwarai,

Gama ba za su yi nasara ba.

Ba za a manta da su ba.

12 Ya Ubangiji Mai Runduna, mai

gwada adali,

Mai ganin zuciya duk da tunani,

Ka sa in ga sakayyar da za ka yi

musu,

Gama a gare ka nake kawo

ƙarata.”

13 Ku raira waƙa ga Ubangiji!

Ku yabi Ubangiji!

Gama ya kuɓutar da ran mabukaci

daga hannun mugaye.

14 La’ananniya ce ranar da aka haife

ni,

Kada ranar da uwata ta haife ni ta yi

albarka!

15 La’ananne ne mutum da ya kai wa

mahaifina labari

Cewa, “An haifa maka ɗa,” don ya

sa shi farin ciki.

16 Bari wannan mutum ya zama kamar

biranen da Ubangiji ya kaɓantar

ba tausayi.

Bari ya ji kuka da safe,

Da rana kuma ya ji gangamin yaƙi,

17 Domin bai kashe ni tun ina ciki ba.

Da ma cikin uwata ya zama mini

kabari,

In yi ta kwanciya a ciki har abada.

18 Me ya sa na fito daga cikin mahaifa,

Don in ga wahala da baƙin ciki,

Don kwanakin raina su ƙare da

kunya?

Categories
IRM

IRM 21

An Yi Faɗi a kan Faɗuwar Urushalima

1 Wannan ita ce maganar Ubangiji wadda ya faɗa wa Irmiya sa’ad da sarki Zadakiya ya aiki Fashur ɗan Malkiya, da Zafaniya firist, ɗan Ma’aseya, wurin Irmiya cewa,

2 “Ka tambayar mana Ubangiji, gama Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya kawo mana yaƙi. Ko Ubangiji zai yi mana al’amuran nan nasa masu ban al’ajabi kamar yadda ya saba, ya sa Sarkin Babila ya janye, ya rabu da mu?”

3 Sai Irmiya ya ce musu,

4 “Ku faɗa wa Zadakiya, Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Ga shi, zan juyo kayan yaƙin da suke hannunka waɗanda kake yaƙi da su gāba da Sarkin Babila, da sojojinsa, waɗanda suka kewaye garun birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.

5 Ni kaina zan yi yaƙi da kai da dukan ƙarfina, da hasalata, da dukan zafin fushina.

6 Zan kuwa kashe mazaunan birnin nan, mutum da dabba, da babbar annoba.

7 Bayan wannan zan ceci Zadakiya Sarkin Yahuza, shi da bayinsa, da mutanen birnin nan waɗanda suka tsira daga annoba, da takobi, da yunwa, zan bashe su a hannun Nebukadnezzar Sarkin Babila, da hannun abokan gābansu, da waɗanda suke neman rayukansu. Zai kashe su da takobi, ba zai ji tausayinsu, ko ya rage waɗansunsu, ko ya ji juyayinsu ba.’

8 “Sai ka faɗa wa wannan jama’a, ka ce, ‘Ni Ubangiji na ce, ga shi, na sa tafarkin rai da na mutuwa a gabanku.

9 Shi wanda ya zauna a birnin nan zai mutu da takobi, da yunwa, da annoba, amma shi wanda ya fita ya ba da kansa ga Kaldiyawa waɗanda suke kewaye da ku zai rayu ya tserar da ransa.

10 Gama na ƙudura zan kawo wa wannan birni masifa, ba alheri ba. Zan bashe shi a hannun Sarkin Babila, shi kuwa zai ƙone shi da wuta.’ ”

Annabci a kan Sarakunan Yahuza

11 “Sai ka faɗa wa gidan sarautar Yahuza cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji,

12 Ya gidan Dawuda, ni Ubangiji na ce,

Ku aikata adalci kowace safiya.

Ku ceci wanda aka yi masa ƙwace

daga hannun mai matsa masa,

Don kada hasalata ta tashi kamar

wuta,

Ta yi ƙuna, har ba mai iya kashe

ta,

Saboda mugayen ayyukanku.

13 Ga shi, ina gāba da ku, ya ku

mazaunan kwarin,

Ya dutsen da yake a fili,’ in ji

Ubangiji.

‘Ku da kuke cewa, wa zai iya

gangarowa wurinku,

Ko kuwa wa zai shiga wurin

zamanku?

14 Zan hukunta ku bisa ga ayyukanku,’

in ji Ubangiji,

‘Zan sa wa jejin ƙasar wuta.

Za ta cinye duk abin da yake kewaye da

ita.’ ”

Categories
IRM

IRM 22

1 Haka Ubangiji ya faɗa, “Ka tafi ka gangara zuwa gidan Sarkin Yahuza, ka faɗi wannan magana a can,

2 ka ce, ‘Ka ji maganar Ubangiji, ya Sarkin Yahuza, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda kai da barorinka, da mutanenka waɗanda suke shiga ta ƙofofin nan.

3 Haka Ubangiji ya ce, ka yi gaskiya da adalci, ka ceci wanda ake masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka cuci baƙo, ko maraya, ko gwauruwa, wato matar da mijinta ya rasu, kada kuma ka zubar da jinin marasa laifi a wannan wuri.

4 Hakika idan ka kiyaye wannan magana, sa’an nan sarakunan da za su zauna a kan gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan gida da karusai da dawakai, su da barorinsu da jama’arsu.

5 Amma idan ba ka kula da waɗannan zantuttuka ba, na rantse da zatina,’ in ji Ubangiji, ‘wannan fāda ta zama kufai.’ ”

6 Abin da Ubangiji ya ce ke nan a kan fādar Sarkin Yahuza,

“Kyanta kamar Gileyad take a gare

ni,

Kamar kuma ƙwanƙolin Lebanon.

Duk da haka zan maishe ta hamada,

Birnin da ba kowa ciki.

7 Zan shirya waɗanda za su hallaka

ta.

Kowannensu da makamansa,

Za su sassare zaɓaɓɓun itatuwan

al’ul ɗinta, a jefa su a wuta.

8 “Al’ummai masu yawa za su wuce ta gefen wannan birni, kowane mutum zai ce wa maƙwabcinsa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’

9 Za su amsa, su ce, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada ga gumaka, suka bauta musu.’ ”

10 Ku mutanen Yahuza, kada ku yi

kuka saboda sarki Yosiya,

Kada ku yi makokin rasuwarsa,

Amma ku yi kuka ƙwarai saboda

ɗansa Yehowahaz.

Sun ɗauke shi, sun tafi da shi, ba zai

ƙara komowa ba,

Ba kuma zai ƙara ganin ƙasar da

aka haife shi ba.

11 Gama haka Ubangiji ya ce a kan Yahowahaz, ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, wanda ya gāji sarautar ubansa, Yosiya, wanda ya tafi ya bar wurin nan. Ba zai ƙara komowa nan ba.

12 Amma a wurin da suka kai shi zaman talala, a can zai mutu, ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.

13 Kaiton wanda ya gina gidansa ta

hanyar rashin adalci,

Benayensa kuma ta hanyar rashin

gaskiya.

Wanda ya sa maƙwabcinsa ya yi

masa aiki a banza,

Bai ba shi hakkinsa ba.

14 Kaiton wanda ya ce,

“Zan gina wa kaina babban gida

Da waɗansu irin benaye

musamman.”

Ya yi masa tagogi,

Ya manna masa itacen al’ul,

Sa’an nan ya yi masa jan shafe.

15 Kana tsammani kai sarki ne,

Da yake ƙasarka ta itacen al’ul

ce?

Amma ubanka ya ci, ya sha,

Ya yi gaskiya, ya aikata adalci,

Ya kuwa zauna lafiya.

16 Ya biya wa matalauta da masu

bukata hakkinsu,

Ya kuwa yi kyau.

Abin da ake nufi da sanina ke nan,

In ji Ubangiji.

17 Amma ka sa idonka da zuciyarka ga

ƙazamar riba,

Da zubar da jinin marar laifi,

Da yin zalunci da danniya.

18 Domin haka ga abin da Ubangiji ya ce a kan Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza,

“Ba za su yi makoki dominsa ba, ko

su ce,

‘Wayyo ɗan’uwanmu!’ ko, ‘Wayyo

‘yar’uwarmu!’

Ba za su yi makoki dominsa ba, su

ce,

‘Wayyo ubangidanmu!’ ko ‘Wayyo mai martaba!’

19 Za a binne shi kamar jaki,

Za a ja shi a yar a bayan ƙofofin

Urushalima.”

20 Ku haura zuwa Lebanon, ku yi

kuka,

Ku ta da muryarku cikin Bashan,

Ku yi kuka daga Abarim,

Gama an hallakar da dukan

ƙaunatattunku.

21 Ubangiji ya yi muku magana a

lokacin wadatarku.

Amma kun ce, “Ba za mu kasa

kunne ba!”

Wannan shi ne halinku tun kuna

samari,

Don ba ku yi biyayya da murya

Ubangiji ba.

22 Iska za ta kwashe shugabanninku,

Za a kai ƙaunatattunku cikin

bauta,

Sa’an nan za ku sha kunya ku ruɗe,

Saboda dukan muguntarku.

23 Ya ku mazaunan Lebanon,

Waɗanda suke zaune cikin itatuwan

al’ul,

Irin nishin da za ku yi sa’ad da azaba

ta same ku,

Azaba ce irin ta mace mai

naƙuda!

24 “Ni Ubangiji na rantse da raina, ko da Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, zoben hatimi ne a yatsan hannun damana, duk da haka zan kwaɓe shi,

25 in bashe shi a hannun waɗanda suke neman ransa, da a hannun wanda yake jin tsoronsa, wato Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da Kaldiyawa.

26 Zan jefar da shi da uwarsa a wata ƙasa inda ba a haife shi ba, a can zai mutu.

27 Amma ƙasan nan da suke marmarin komowa cikinta, ba za su koma cikinta ba.”

28 Ashe, Yekoniya kamar fasasshen

tulu yake,

Wanda ba wanda ya kula da shi?

Me ya sa aka watsar da shi da

‘ya’yansa,

A ƙasar da ba su sani ba?

29 Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa!

Ki ji maganar Ubangiji!

30 Haka Ubangiji ya ce,

“Rubuta wannan mutum, marar

‘ya’ya.

Mutumin da ba zai yi albarka a duk

kwanakinsa ba.

Gama ba wani daga zuriyarsa

Da zai gāji gadon sarautar Dawuda,

Ko ya yi mulki kuma a Yahuza.”

Categories
IRM

IRM 23

Komowar waɗanda suka Ragu

1 “Taku ta ƙare! Makiyayan da suka lalatar, suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.

2 Haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya faɗa a kan makiyayan jama’arsa. “Kun warwatsar da garkena kun kore su, ba ku lura da su ba. Ni ma haka zan yi da ku saboda muguntarku, ni Ubangiji na faɗa.

3 Sa’an nan zan tattaro sauran garkena daga wuraren da aka warwatsa su, zan komo da su cikin garkensu, zan sa su hayayyafa su riɓaɓɓanya.

4 Zan sa makiyayan da za su lura da su. Ba kuwa za su ƙara jin tsoro, ko razana ba, ba kuma wanda zai ɓace, ni Ubangiji na faɗa.

5 “Ga shi, ni Ubangiji na ce, kwanaki

suna zuwa,

Sa’ad da zan tsiro da wani mai adalci

daga zuriyar Dawuda

Wanda zai ci sarauta.

Zai yi sarauta da hikima,

Zai aikata abin da yake daidai a

ƙasar.

6 A zamaninsa za a ceci Yahuza,

Isra’ila kuwa za ta zauna lafiya.

Sunan da za a kira shi da shi ke

nan,

‘Ubangiji Adalcinmu.’

7 “Saboda haka, ga shi, kwanaki suna zuwa, ni Ubangiji na faɗa, sa’ad da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da jama’ar Isra’ila daga cikin ƙasar Masar ba,’

8 amma za su ce, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa, daga kuma dukan ƙasashen da ya warwatsa su!’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu ta kansu.”

Jawabi a kan Annabawan Ƙarya

9 A kan annabawa kuwa, zuciyata ta

karai,

Dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa,

Saboda Ubangiji da kuma maganarsa

mai tsarki.

Na zama kamar mashayi, wanda ya

bugu da ruwan inabi,

10 Gama ƙasar cike take da mazinata,

Saboda la’ana, ƙasar za ta yi

makoki,

Wuraren kiwo na jeji sun bushe,

Manufarsu mugunta ce,

Ba su mori ƙarfinsu a inda ya

kamata ba.

11 “Annabi da firist, dukansu biyu

marasa tsoron Allah ne,

Har a cikin Haikalina na tarar da

muguntarsu.”

Ubangiji ya faɗa.

12 “Saboda haka hanyarsu za ta zama

da santsi da duhu,

Inda za a runtume su, su fāɗi.

Gama zai kawo musu masifa a

shekarar da za su sha

hukuncinsu.”

Ubangiji ya faɗa.

13 “A cikin annabawan Samariya,

Na ga abu marar kyan gani.

Da sunan Ba’al suke yin annabci,

Suna ɓad da jama’ata Isra’ila

14 Amma cikin annabawa na

Urushalima,

Na ga abin banƙyama.

Suna yin zina, suna ƙarya,

Suna ƙarfafa hannuwan masu aikata

mugunta,

Saboda haka ba wanda ya juya ga

barin muguntarsa,

Dukansu suna kama da Saduma,

Mazaunanta kuwa kamar

Gwamrata.”

15 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce a kan annabawa,

“Ga shi, zan ciyar da su da abinci

mai ɗaci,

In shayar da su da ruwan dafi.

Daga wurin annabawan Urushalima

Rashin tsoron Allah ya fito ya

mamaye dukan ƙasar.”

16 Ubangiji Mai Runduna ya ce wa

mazaunan Urushalima,

“Kada ku kasa kunne ga maganar

annabawa,

Gama sukan cika kunnuwanku da

ƙarairayi.

Suna faɗar ganin damarsu,

Ba faɗar Ubangiji ba.

17 Suna ta faɗa wa waɗanda suke raina

maganar Ubangiji cewa,

‘Za ku zauna lafiya!’

Ga kowane mai bin nufin tattaurar

zuciyarsa,

‘Ba masifar da za ta same ka.’ ”

18 Irmiya ya ce, “Gama wane ne a cikin annabawan nan ya taɓa neman shawarar Ubangiji don ya fahimci maganarsa, ko kuwa wane ne ya taɓa kasa kunne don ya ji maganarsa?

19 Ga shi, hadirin hasalar Ubangiji ya

taso,

Kamar iskar guguwa,

Zai tashi a bisa kan mugaye.

20 Ubangiji ba zai huce ba,

Sai ya aikata nufin zuciyarsa.

Amma sai daga baya za ku gane

sarai.”

21 Ubangiji ya ce,

“Ni ban aiki waɗannan annabawa

ba,

Duk da haka sun tafi,

Ban kuwa yi musu magana ba,

Amma sun yi annabci.

22 Amma da a ce sun tsaya cikin

shawarata,

Da sun yi shelar maganata ga

jama’ata,

Da sun juyar da su daga muguwar

hanyarsu,

Da mugayen ayyukansu.

23 “Ni Allah na kusa ne kaɗai,

Banda na nesa?” In ji Ubangiji.

24 “Mutum ya iya ɓoye kansa a wani

lungu

Inda ba zan iya ganinsa ba?” In ji

Ubangiji.

“Ashe, ban cika sammai da duniya

ba?

25 Na ji abin da annabawan nan suka ce, su da suke annabcin ƙarya da sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki!’

26 Har yaushe ƙarya za ta fita daga zuciyar annabawan nan masu annabcin ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗin da yake a zuciyarsu?

27 Suna zaton za su sa mutanena su manta da sunana ta wurin mafarkansu da suke faɗa wa junansu, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana saboda Ba’al.

28 Bari annabin da yake da mafarki ya faɗi mafarkinsa, amma wanda yake da maganata ya faɗe ta da aminci. Me ya haɗa ciyawa da alkama? Ni Ubangiji na faɗa.

29 Maganata kamar wuta ce, kamar guduma mai farfashe dutse. Ni Ubangiji na faɗa.

30 Domin haka, ga shi, ina gāba da annabawan da suke satar maganata daga wurin junansu. Ni Ubangiji na faɗa.

31 Ina kuma gāba da annabawan da suke faɗar ra’ayin kansu, sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya faɗa.’

32 Ina kuma gāba da annabawan da suke annabcin mafarkansu na ƙarya, suna kuwa faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu, saboda rashin hankalinsu. Ni ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan jama’a ba ko kaɗan, ni Ubangiji na faɗa.”

33 “Kai Irmiya, sa’ad da wani mutum daga cikin mutanen nan, ko annabi, ko firist ya tambaye ka cewa, ‘Mece ce nawayar Ubangiji?’ Sai ka ce masa, ‘Ku ne nawayar, zan kuwa rabu da ku,’ ni Ubangiji na faɗa.

34 Idan annabi ko firist, ko wani daga cikin jama’a, ya ce, ‘Nawayar Ubangiji,’ zan hukunta shi duk da iyalin gidansa.

35 Haka kowannenku zai ce wa maƙwabcinsa da ɗan’uwansa, ‘Wace amsa Ubangiji ya bayar? Me Ubangiji ya faɗa?’

36 Amma ba za ku ƙara ambatar nawayar Ubangiji ba, gama maganar kowane mutum za ta zama nawaya, ga shi, kun ɓata maganar Allah mai rai, Ubangiji Mai Runduna, Allahnmu.

37 Haka za ka faɗa wa annabi, ‘Wace amsa Ubangiji ya bayar? Me Ubangiji ya faɗa?’

38 Amma idan kun ce, ‘Nawayar Ubangiji,’ ga abin da ni Ubangiji na ce, tun da yake kun faɗi wannan magana, wato ‘Nawayar Ubangiji,’ alhali kuwa na aika muku cewa, kada ku ce, ‘Nawayar Ubangiji,’

39 saboda haka, hakika zan ɗaga in jefar da ku daga gabana, da ku da birni wanda na ba ku, ku da kakanninku.

40 Zan sa ku zama abin zargi da abin kunya har abada, ba kuwa za a manta da wannan ba.”

Categories
IRM

IRM 24

Kwando Biyu na ‘Ya’yan Ɓaure

1 Bayan da Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya kama Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, daga Urushalima, ya kai shi bautar talala a Babila, tare da sarakunan Yahuza, da gwanayen sana’a, da maƙera, dukansu, ya kawo su Babila. Sai Ubangiji ya nuna mini wannan wahayi. Na ga kwando biyu na ɓaure, an ajiye su a gaban Haikalin Ubangiji.

2 A ɗaya kwandon akwai ɓaure masu kyau, kamar nunan fari. A ɗayan kuwa marasa kyau ne, ba mai iya cinsu.

3 Sai Ubangiji ya ce mini, “Irmiya, me ka gani?”

Sai na ce, “’Ya’yan ɓaure, akwai masu kyau ƙwarai, akwai kuma marasa kyau ƙwarai, har da ba za su ciwu ba.”

4 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini,

5 “Haka ni Ubangiji Allah na Isra’ila na ce, kamar kyawawan ɓauren nan, haka nake ganin mutanen Yahuza waɗanda aka kai su bautar talala a ƙasar Kaldiyawa.

6 Zan lura da su da kyau, in kuma komo da su a wannan ƙasa. Zan gina su, ba zan rushe su ba. Zan kafa su, ba zan tumɓuke su ba.

7 Zan ba su zuciyar da za su sani ni ne Ubangiji. Za su kuwa zama jama’ata, ni kuwa zan zama Allahnsu, gama za su komo wurina da zuciya ɗaya.

8 “Ni Ubangiji na ce, zan mai da Zadakiya Sarkin Yahuza, da sarakunansa, da sauran mutanen Urushalima da suka ragu a ƙasar, da mutanen da suka tafi Masar, kamar ruɓaɓɓen ɓauren nan da suka lalace har ba su ciwuwa.

9 Zan maishe su abin ƙyama da masifa ga mulkokin duniya duka. Za su zama abin zargi, da karin magana, da ba’a, da la’ana a dukan wuraren da zan warwatsa su.

10 Zan aika musu da takobi, da yunwa, da annoba har an hallaka su sarai daga cikin ƙasar da na ba su, su da kakanninsu.”

Categories
IRM

IRM 25

Za a Zama Kufai har Shekara Saba’in

1 A shekara ta huɗu ta mulkin Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, Ubangiji ya yi wa Irmiya magana a kan dukan mutanen Yahuza. A shekarar da Nebukadnezzar ya ci sarautar Babila,

2 a shekarar ce, annabi Irmiya ya yi wa dukan mutanen Yahuza da dukan mazaunan Urushalima magana cewa,

3 “Shekaru ashirin da uku ke nan tun daga shekara ta goma sha uku ta mulkin Yosiya, ɗan Amon, Sarkin Yahuza, har zuwa yau, Ubangiji ya yi mini magana, ni kuwa na yi ta faɗa muku, amma ba ku ji ba.

4 Ba ku saurara ba, ba ku kasa kunne don ku ji ba, ko da yake Ubangiji ya yi ta aiko muku da dukan bayinsa annabawa,

5 yana cewa, ‘Sai kowane ɗayanku ya juyo daga mugun halinsa da mugayen ayyukansa don ya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku, ku da kakanninku tun daga zamanin dā har abada.

6 Kada ku bi gumaka, ku bauta musu, ku yi musu sujada, ko ku tsokane ni da ayyukan hannuwanku, sa’an nan ba zan hore ku ba.’

7 Duk da haka ba ku kasa kunne gare shi ba, shi Ubangiji ya faɗa, sai kuka tsokane shi da ayyukan hannuwanku. Wannan kuwa zai cuce ku.

8 “Domin haka Ubangiji Mai Runduna ya ce, ‘Tun da yake kun ƙi yin biyayya da maganata,

9 zan aiko kabilai daga arewa da bawana Nebukadnezzar, Sarkin Babila. Zan kawo su, su yi yaƙi da ƙasan nan da mazaunanta, da dukan al’umman da take kewaya da ita. Zan hallaka su sarai, in sa su zama abin ƙyama, da abin raini, da abin zargi har abada.

10 Banda haka zan kawar da muryar sowa da ta farin ciki, da ta ango da ta amarya, da amon dutsen niƙa daga gare su. Zan kashe hasken fitilunsu.

11 Ƙasar duka za ta zama kufai marar amfani, waɗannan al’ummai za su bauta wa Sarkin Babila har shekara saba’in.

12 Sa’an nan bayan cikar shekara saba’in ɗin, zan hukunta Sarkin Babila da ƙasarsa, wato ƙasar Kaldiyawa. Zan maishe ta kango har abada, saboda zunubinsa.

13 Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abin da na faɗa gāba da ita. Dukan abin da aka rubuta a wannan littafi, wato dukan abin da Irmiya ya yi annabcinsa gāba da dukan al’umman nan.

14 Al’ummai da yawa da manyan sarakuna za su bautar da su, ni kuwa zan yi musu sakayya bisa ga ayyukan hannuwansu.’ ”

Hukuncin da Allah zai Yi wa Al’ummai

15 Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce mini, “Ka karɓi ƙoƙon ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.

16 Za su sha, su yi tangaɗi su yi hauka saboda takobin da zan aiko a cikinsu.”

17 Sai na karɓi ƙoƙon daga wurin Ubangiji, na sa dukan al’umman da Ubangiji ya aike ni gare su, su sha daga cikinsa.

18 Urushalima, da biranen Yahuza, da sarakunanta, da shugabanninta, za su zama kango da abin ƙyama da abin raini, da abin la’ana. Haka yake a yau.

19-26 Ga lissafin sauran da za su sha

ƙoƙon.

Fir’auna Sarkin Masar da kuma

barorinsa, da sarakunansa,

Dukan jama’arsa, da dukan

baƙin da suke tare da su,

dukan sarakunan ƙasar Uz,

dukan sarakunan ƙasar

Filistiyawa, wato Ashkelon, da

Gaza, da Ekron, da saura na

Ashdod,

Edom da Mowab, da ‘ya’yan

Ammon maza,

dukan sarakunan Taya, da dukan

sarakunan Sidon,

dukan sarakunan da suke gaɓar

Bahar Rum da waɗanda suke a

tsibiran tekun,

Dedan, da Tema, da Buz, da

dukan waɗanda suke yi wa

kansu sanƙo,

dukan sarakunan Arabiya,

dukan sarakunan tattarmukan

mutane da suke zaune a

hamada,

dukan sarakunan Zimri, da dukan

sarakunan Elam, da dukan

sarakunan Mediya,

dukan sarakunan arewa, na nesa

da na kusa bi da bi.

Dukan mulkokin da suke fuskar duniya za su sha daga ciki. Daga nan sai Sarkin Babila a bayansu duka, zai sha nasa.

27 “Za ka kuma faɗa musu cewa, ‘In ji Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ku sha, ku bugu, ku yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku tashi saboda takobin da zan aiko muku.’

28 Idan kuwa sun ƙi su karɓi ƙoƙon daga hannunka su sha sai ka faɗa musu cewa, ‘Ubangiji Mai Runduna ya ce, dole ne ku sha!

29 Gama ga shi, na fara sa masifa ta yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana. To, kuna tsammani ba za a hukunta ku ba? Sai an hukunta ku, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.’

30 “Kai Irmiya kuma sai ka yi annabcin dukan waɗannan magana gāba da su, ka faɗa musu cewa,

‘Ubangiji zai yi ruri daga Sama,

Zai yi magana daga wurin zamansa

mai tsarki,

Zai yi wa garkensa ruri da ƙarfi

ƙwarai,

Zai yi ihu kamar masu matse

‘ya’yan inabi,

Zai yi gāba da dukan mazaunan

duniya.

31 Za a ji hayaniya har iyakar duniya,

Gama Ubangiji yana da ƙara game

da al’ummai,

Zai shiga hukunta wa dukan ‘yan

adam,

Zai kashe mugaye da takobi,

Ubangiji ya faɗa.’ ”

32 Haka Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Ga masifa tana tahowa daga

al’umma zuwa al’umma,

Hadiri kuma yana tasowa daga

dukan manisantan wurare na

duniya.

33 Waɗanda Ubangiji ya kashe a

wannan rana,

Za su zama daga wannan bangon

duniya zuwa wancan.

Ba za a yi makoki dominsu ba,

Ba kuwa za a tattara gawawwakinsu

a binne ba.

Za su zama taki ga ƙasa.

34 “Ku yi makoki, ku yi kuka, ku

makiyaya,

Ku yi ta birgima a cikin toka ku

iyayengijin garke,

Gama ranar da za a yanka ku da

ranar da za a warwatsa ku ta zo,

Za ku fāɗi kamar zaɓaɓɓen kasko.

35 Ba mafakar da ta ragu domin

makiyaya,

Iyayengijin garken ba za su tsira ba.

36 Ji kukan makiyayan,

Da kukan iyayengijin garken,

Gama Ubangiji yana lalatar da wurin

kiwonsu.

37 Garkunan da suke zaune lafiya kuwa,

an yi kaca-kaca da su

Saboda zafin fushin Ubangiji.

38 Ya rabu da wurin ɓuyarsa kamar

zaki,

Gama ƙasarsu ta zama marar

amfani,

Saboda takobin Ubangiji, da kuma

zafin fushinsa.”