Categories
IRM

IRM 46

Annabci a kan Masar

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan sauran al’umma.

2 Ya yi magana game da sojojin Fir’auna, Sarkin Masar, waɗanda suke a bakin Kogin Yufiretis a Karkemish, waɗanda Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya ci su da yaƙi a shekara ta huɗu ta sarautar Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza.

3 Masarawa suka yi ihu, suka ce,

“Ku shirya kutufani da garkuwa,

Ku matso zuwa wurin yaƙi!

4 Ku ɗaura wa dawakanku sirdi, ku

hau!

Ku tsaya a wurarenku da kwalkwali

a ka!

Ku wasa māsunku!

Ku sa kayan yaƙi!”

5 Ubangiji ya yi tambaya ya ce,

“Me nake gani?

Sun tsorata, suna ja da baya,

An ci sojojinsu, suna gudu,

Ba su waiwayen baya, akwai tsoro a

kowane sashi.”

6 Masu saurin gudu ba za su tsere ba,

Haka nan kuma jarumi,

A arewa a gefen Kogin Yufiretis,

Sun yi tuntuɓe, sun fādi.

7 Wane ne wannan mai tashi kamar

Kogin Nilu,

Kamar kogunan da ruwansu yake

ambaliya?

8 Masar tana tashi kamar Nilu,

Kamar kogunan da ruwansu yake

ambaliya.

Masar ta ce, “Zan tashi, in rufe

duniya,

Zan hallaka birane da mazauna

cikinsu.”

9 Ku haura, ku dawakai,

Ku yi sukuwar hauka, ku karusai!

Bari sojoji su fito,

Mutanen Habasha da Fut masu

riƙon garkuwoyi,

Da mutanen Lud, waɗanda suka iya

riƙon baka.

10 Wannan rana ta Ubangiji, Allah Mai

Runduna ce,

Ranar ɗaukar fansa ce don ya rama

wa maƙiyansa.

Takobi zai ci, ya ƙoshi,

Ya kuma sha jininsu, ya ƙoshi,

Gama Ubangiji Allah Mai Runduna

zai hallaka maƙiyansa,

A arewa, a bakin Kogin Yufiretis.

11 Ku mutanen Masar, ku haura zuwa

Gileyad

Don ku samo ganye!

A banza kuke morar magunguna,

Ba za ku warke ba.

12 Kunyarku ta kai cikin sauran

al’umma,

Kukanku kuma ya cika duniya.

Soja na faɗuwa bisa kan soja.

Dukansu biyu sun faɗi tare.

13 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan zuwan Nebukadnezzar, Sarkin Babila, don ya yi yaƙi da ƙasar Masar.

14 “Ku yi shelarsa cikin garuruwan

Masar,

Cikin Migdol, da Memfis, da

Tafanes,

Ku ce, ‘Ku tsaya, ku yi shiri,

Gama takobi yana cin waɗanda suke

kewaye da ku!’

15 Me ya sa gunkinka, Afis, ya fāɗi,

Wato bijimi, gunkinka bai tsaya ba?

Domin Ubangiji ya tunkuɗe shi

ƙasa!

16 Sun yi ta fāɗuwa,

Suna faɗuwa a kan juna,

Sai suka ce, ‘Mu tashi mu koma

wurin mutanenmu,

Zuwa ƙasar haihuwarmu, mu gudu

daga takobin azzalumi!’

17 “Ku ba Fir’auna Sarkin Masar

sabon suna,

‘Mai yawan surutu, wanda bai rifci

zarafi ba!’

18 Ni wanda sunana Ubangiji Mai

Runduna Sarki ne,

Na rantse da raina, wani zai ɓullo,

Kamar Tabor a cikin tsaunuka,

Ko kuwa kamar Karmel a bakin

teku.

19 Ya ku mazaunan Masar,

Ku shirya kayanku don zuwa bauta,

Gama Memfis za ta lalace, ta zama

kufai,

Ba mai zama a ciki.

20 “Masar kyakkyawar karsana ce,

Amma bobuwa daga arewa ta aukar

mata!

21 Sojojin ijararta kamar ‘yan maruƙa

ne, masu yawan kitse,

Sun ba da baya, sun gudu, ba su

tsaya ba,

Domin ranar masifarsu ta zo,

Lokacin halakarsu ya yi.

22 Masar tana gudu, tana huci kamar

maciji,

Gama abokan gābanta suna zuwa da

ƙarfi,

Za su faɗo mata da gatura kamar

masu saran itatuwa.

23 Ni Ubangiji na ce, za su sari

kurminta,

Ko da yake ba su ƙirguwa,

Gama suna da yawa kamar fara,

Ba su lasaftuwa.

24 Za a kunyatar da mutanen Masar,

An bashe su a hannun mutanen

arewa.”

25 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya ce, “Ga shi, zan hukunta Amon na No, da Fir’auna, da Masar, tare da allolinta, da sarakunanta, wato Fir’auna, tare da waɗanda suke dogara gare shi.

26 Zan bashe su a hannun waɗanda suke neman ransu, wato a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da shugabanninsa. Daga baya kuma mutane za su zauna a Masar kamar dā. Ni Ubangiji na faɗa.

27 “Ya bawana Yakubu, kada ka ji

tsoro,

Kada ka firgita, ya Isra’ila.

Gama zan cece ka daga ƙasa mai

nisa,

Zan ceci zuriyarka daga ƙasar

bautarsu.

Yakubu zai komo, ya yi zamansa da

rai kwance,

Ba wanda zai razanar da shi.

28 Ni Ubangiji na ce,

Kada ka ji tsoro, ya bawana

Yakubu,

Gama ina tare da kai.

Zan hallaka dukan sauran al’umma

sarai inda na kora ka.

Amma ba zan hallaka ka sarai ba.

Zan hukunta ka yadda ya kamata,

Ba zan bar ka ba hukunci ba.”

Categories
IRM

IRM 47

Jawabin Ubangiji a kan Filistiyawa

1 Kafin Fir’auna ya ci Gaza da yaƙi Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan Filistiyawa.

2 Ubangiji ya ce,

“Ga shi, ruwa yana tasowa daga

arewa,

Zai zama kogi da yake ambaliya.

Zai malala bisa ƙasa da dukan abin

da yake cikinta,

Da birni da mazauna cikinsa,

Maza za su yi kuka,

Dukan mazaunan ƙasar za su yi kuka.

3 Da jin takawar kofatan dawakai,

Da amon karusai da ƙafafun karusai,

Ubanni ba su juya, su dubi

‘ya’yansu ba,

Domin hannuwansu sun yi laƙwas,

4 Domin lokacin hallaka dukan

Filistiyawa ya yi.

Za a datse wa Taya da Sidon kowane

taimakon da ya ragu,

Gama Ubangiji zai hallaka

Filistiyawa

Waɗanda suke baƙin teku na Kaftor.

5 Baƙin ciki zalla ya sami Gaza,

Ashkelon ta lalace.

Ya ƙattin mutane, yaushe za ku

daina tsattsage kanku?

6 Ya takobin Ubangiji, yaushe za ka

huta?

Sai ka koma ƙubenka,

Ka huta, ka yi shiru!

7 Ƙaƙa zai huta, tun da ni Ubangiji ne

na umarce shi?

Ni Ubangiji na umarce shi ya yi yaƙi

da Ashkelon

Da mazauna a bakin teku.”

Categories
IRM

IRM 48

Jawabin Ubangiji a kan Mowab

1 Ga abin da Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya faɗa a kan Mowab,

“Kaiton Nebo, gama ta lalace!

An kunyatar da Kiriyatayim, an ci ta

da yaƙi,

An kunyatar da kagararta, an rushe

ta.

2 Darajar Mowab ta ƙare.

Ana shirya mata maƙarƙashiya a

Heshbon,

‘Bari mu je mu ɓata ta daga zaman

al’umma!’

Ke kuma Madmen za ki yi shiru,

Takobi zai runtume ki.

3 Muryar kuka daga Horonayim tana

cewa,

‘Risɓewa da babbar halaka!’

4 “An hallakar da Mowab,

Ƙanananta suna kuka.

5 Gama a hawan Luhit, za su hau da

kuka,

Gama a gangaren Horonayim,

Suna jin kukan wahalar halaka.

6 Ku gudu don ku tserar da

rayukanku,

Ku gudu kamar jakin jeji.

7 “Kun dogara ga ƙarfinku da

wadatarku,

Amma yanzu za a ci ku da yaƙi,

Kemosh zai tafi bauta

Tare da firistocinsa da

shugabanninsa.

8 Mai hallakarwa zai shiga kowane

gari,

Don haka ba garin da zai tsira.

Kwari da tudu za su lalace,

Ni Ubangiji na faɗa.

9 Ku ba Mowab fikafikai,

Gama za ta tashi ta gudu,

Garuruwanta za su zama kango,

Ba mazauna cikinsu.

10 “La’ananne ne shi wanda yake yin

aikin Ubangiji da ha’inci,

La’ananne ne shi kuma wanda ya

hana wa takobinsa jini.

11 “Tun daga ƙuruciya Mowab tana

zama lami lafiya,

Hankali kwance,

Ba a jujjuya ta daga tulu zuwa tulu

ba,

Ba a taɓa kai ta bauta ba,

Domin haka daɗin ɗanɗanonta bai

rabu da ita ba,

Ƙanshinta kuma bai sāke ba.”

12 Ubangiji ya ce, “Domin haka kwanaki suna zuwa, sa’ad da zai aika da mutane su tuntsurar da tuluna, su zubar da ruwan inabi, su farfasa tulunanta.

13 Sa’an nan Kemosh zai kunyatar da Mowab, kamar yadda Betel wadda Isra’ilawa suka dogara gare ta ta kunyatar da su.

14 “Don me kake cewa,

‘Mu jarumawa ne, mayaƙan gaske?’

15 Mai hallaka Mowab da garuruwanta

ya taho,

Zaɓaɓɓun majiya ƙarfinta sun

gangara mayanka,

Ni sarki, mai suna Ubangiji Mai

Runduna, na faɗa.

16 Masifar Mowab ta kusato,

Halakarta kuma tana gaggabtowa.

17 “Ku yi makoki dominta, ku da kuke

kewaye da ita,

Dukanku da kuka san sunanta, ku

ce,

‘Ƙaƙa sandan sarauta mai iko

Da sanda mai daraja ya karye?’

18 Ku da kuke zaune a Dibon,

Ku sauka daga wurin zamanku mai

daraja,

Ku zauna a busasshiyar ƙasa,

Gama mai hallaka Mowab ya zo ya

yi gab da ku.

Ya riga ya rushe kagararku.

19 Ku mazaunan Arower,

Ku tsaya a kan hanya, ku jira,

Ku tambayi wanda yake gudu

Da wanda yake tserewa,

Abin da ya faru.

20 An kunyatar da Mowab, ta rushe.

Ku yi kuka dominta,

Ku faɗa a Arnon, cewa Mowab ta

halaka.

21 “Hukunci ya auka kan garuruwan da suke a ƙasar fili, wato Holon, da Yahaza, da Mefayat,

22 da Dibon, da Nebo, da Bet-diblatayim,

23 da Kiriyatayim, da Bet-gamal, da Ba’almeyon,

24 da Kiriyot, da Bozara. Hukunci ya zo a kan dukan garuruwan Mowab na nesa da na kusa.

25 An karye ikon Mowab da ƙarfinta, ni Ubangiji na faɗa.

26 “Ku sa Mowab ta yi maye domin ta tayar wa Ubangiji. Za ta yi birgima cikin amanta, mutane kuwa za su yi dariya.

27 Kin yi wa mutanen Isra’ila dariya. A kowane lokacin da kika ambaci sunansu, sai ki taɗa kanki da raini kamar an kama su tare da ɓarayi.

28 “Ku mazaunan Mowab, ku bar

garuruwanku,

Ku tafi, ku zauna a kogwanni,

Ku zama kamar kurciya wadda take

yin sheƙarta a bakin kwazazzabo.

29 Mun ji labarin girmankan Mowab,

da ɗaukaka kanta,

Da alfarmarta, da izgilinta,

Tana da girmankai ƙwarai.

30 Ni Ubangiji na san Mowab tana da

girmankai,

Alfarmarta ta banza ce,

Ayyukanta kuma na banza ne.

31 Don haka zan yi kuka saboda

Mowab duka,

Zan kuma yi baƙin ciki saboda

mutanen Kir-heres.

32 Zan yi kuka saboda kurangar inabin

Sibma

Fiye da yadda zan yi kuka saboda

mutanen Yazar.

Rassanku sun haye teku har sun kai

Yazar,

Amma mai hallakarwa ya faɗo a kan

‘ya’yan itatuwanku da damuna

Da kan amfanin inabinku.

33 An ɗauke farin ciki da murna daga

ƙasa mai albarka ta Mowab,

Na hana ruwan inabi malala daga

wurin matsewarsa,

Ba wanda yake matse shi, yana ihu na

murna,

Ihun da ake yi ba na murna ba ne.

34 “Mutanen Heshbon da na Eleyale suna kururuwa ana iya jin kururuwansu a Yahaza. Ana iya jinta kuma a Zowar, da Horonayim, da Eglat-shelishiya. Har ma ruwan Nimra ya ƙafe.

35 Zan hana mutanen Mowab miƙa hadayu na ƙonawa a tuddai, da miƙa wa gumakansu sadaka, ni Ubangiji na faɗa.

36 “Zuciyata tana makoki domin Mowab da Kir-heres kamar wanda yake kukan makoki da sarewa saboda wadatarsu ta ƙare.

37 Gama kowa ya aske kansa da gemunsa, sun tsattsage hannuwansu. Kowa kuma ya sa rigar makoki.

38 Ba abin da ake yi a bisa kan soraye da dandali na Mowab sai baƙin ciki, gama na farfashe Mowab kamar tulun da ba a so, ni Ubangiji na faɗa.

39 An farfashe Mowab, ta yi kuka, ta kunyata! Ta zama abin dariya da abin tsoro ga waɗanda suke kewaye da ita.

40 “Ni Ubangiji na ce,

Wani zai yi firiya da sauri kamar

gaggafa,

Zai shimfiɗa fikafikansa a kan

Mowab.

41 Za a ci garuruwa da kagarai da

yaƙi,

A wannan rana zukatan sojojin

Mowab

Za su zama kamar zuciyar macen da

take naƙuda.

42 Za a hallaka Mowab daga zaman

al’umma,

Domin ta tayar wa Ubangiji.

43 Tsoro, da rami, da tarko suna

jiranku,

Ya mazaunan Mowab,

Ni Ubangiji na faɗa.

44 Wanda ya guje wa tsoro,

Zai fāɗa a rami,

Wanda kuma ya fito daga cikin

rami,

Tarko zai kama shi.

Gama na sa wa Mowab lokacin da

zan hukunta ta,

Ni Ubangiji na faɗa.

45 “A ƙarƙashin inuwar Heshbon ‘yan

gudun hijira suna tsaye ba ƙarfi.

Gama wuta ta ɓullo daga Heshbon,

Harshen wuta kuma ya fito daga

Sihon,

Ta ƙone goshin Mowab da

ƙoƙwan kai na ‘yan tayarwa.

46 Kaitonku, ya Mowabawa!

Mutanen Kemosh sun lalace,

An kai ‘ya’yanku mata da maza

cikin bauta.

47 “Amma zan komar da mutanen

Mowab nan gaba,

Ni Ubangiji na faɗa.”

Wannan shi ne hukuncin Mowab.

Categories
IRM

IRM 49

Jawabin Ubangiji a kan Ammonawa

1 Wannan shi ne abin da Ubangiji ya faɗa akan Ammonawa,

“Isra’ila ba shi da ‘ya’ya ne?

Ko kuwa ba shi da māgada ne?

Me ya sa waɗanda suke bautar Milkom

suka mallaki inda Gad take zama,

Suka zauna a garuruwanta?

2 Domin haka lokaci yana zuwa,

Sa’ad da zan sa mutanen garin

Rabba ta Ammon su ji busar

yaƙi.

Rabba za ta zama kufai,

Za a ƙone ƙauyukanta da wuta,

Sa’an nan Isra’ila zai mallaki

waɗanda suka mallake shi.

Ni Ubangiji na faɗa.

3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama Ai ta

zama kufai!

Ku yi kuka, ku mutanen Rabba, ku

sa tufafin makoki.

Ku yi gudu, kuna kai da kawowa a

cikin garuka,

Gama za a kai Milkom bauta tare da

firistocinsa da wakilansa.

4 Me ya sa kuke taƙama da

ƙarfinku,

Ƙarfinku da yake ƙarewa, ku mutane

marasa aminci?

Kun dogara ga dukiyarku,

Kuna cewa, ‘Wane ne zai iya gāba da

mu?’

5 Ga shi, zan kawo muku razana daga

waɗanda suke kewaye da ku,

Za a kore ku, kowane mutum zai

kama gabansa,

Ba wanda zai tattara ‘yan gudun

hijira.

Ni Ubangiji Allah Mai Runduna

na faɗa.

6 “Amma daga baya zan sa

Ammonawa su wadata kuma,

Ni Ubangiji na faɗa.”

Jawabin Ubangiji a kan Edom

7 Ga abin da Ubangiji Mai Runduna

ya faɗa a kan Edom,

“Ba hikima kuma a cikin Teman?

Shawara ta lalace a wurin masu

basira?

Hikima ta lalace ne?

8 Ku mazaunan Dedan, ku juya, ku

gudu,

Ku ɓuya cikin zurfafa,

Gama zan kawo masifa a kan Isuwa

A lokacin da zan hukunta shi,

9 Idan masu tsinkar ‘ya’yan inabi sun

zo wurinka

Ba za su rage abin kala ba?

Idan kuma ɓarayi sun zo da dare,

Za su ɗauki iyakacin abin da suke so

kurum.

10 Amma na tsiraita Isuwa sarai,

Na buɗe wuraren ɓuyarsa,

Har bai iya ɓoye kansa ba,

An hallakar da mutanen Isuwa

Tare da ‘yan’uwansa da

maƙwabtansa,

Ba wanda ya ragu.

11 Ka bar marayunka, ni zan rayar da

su.

Matanka da mazansu sun mutu,

Sai su dogara gare ni.”

12 Ubangiji ya ce, “Ga shi, waɗanda ba a shara’anta su ga shan ƙoƙon hukunci ba, za su sha shi, to, kai za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, amma lalle za ka sha shi!

13 Gama ni Ubangiji na rantse da zatina, cewa Bozara za ta zama abar tsoro, da abar dariya, da kufai, da abar la’ana. Dukan garuruwanta za su zama kufai har abada.”

14 Irmiya ya ce,

“Na karɓi saƙo daga wurin

Ubangiji.

An aiki jakada a cikin al’ummai

cewa,

‘Ku tattara kanku, ku zo ku yi gāba

da ita,

Ku tasar mata da yaƙi!’

15 Gama ga shi, zan maishe ki

ƙanƙanuwa cikin al’ummai,

Abar raini a wurin mutane.

16 Tsoronki da ake ji da girmankanki

sun ruɗe ki,

Ke da kike zaune a kogon dutse, a

kan tsauni,

Ko da yake kin yi gidanki can sama

kamar gaggafa,

Duk da haka zan komar da ke ƙasa,

Ni Ubangiji na faɗa.”

17 Ubangiji ya ce, “Edom za ta lalace, duk wanda ya bi ta wurin zai gigice, ya yi tsaki saboda dukan masifunta.

18 Abin da zai faru ga Edom zai zama daidai da abin da ya faru ga Saduma, da Gwamrata, da biranen da suke kusa da su, a lokacin da aka kaɓantar da su. Ba wanda zai zauna cikinta, ba wanda kuma zai yi zaman baƙunci a cikinta, ni Ubangiji na faɗa.

19 Kamar yadda zaki yakan fito daga cikin kurmin Urdun, garin ya fāda wa babban garken tumaki, haka zan sa nan da nan su gudu daga gare ta. Zan naɗa wani wanda na zaɓa, gama wa yake kama da ni? Wa zai yi ƙarata? Ina makiyayin da ya isa ya yi gāba da ni?

20 Domin haka, ku ji shirin da ni Ubangiji na yi wa Edom, da abin da nake nufin yi wa mazaunan Teman. Hakika za a tafi da su, har da ƙanana na garken tumaki, zan kuma sa wurin kiwonsu ya zama ƙeƙuwa saboda su.

21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza, za a kuma ji muryar kukansu har a Bahar Maliya.

22 Wani zai tashi da sauri, ya yi sama kamar gaggafa. Zai buɗe fikafikansa a kan Bozara. Zukatan sojojin Edom za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.”

Jawabin Ubangiji a kan Dimashƙu

23 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Dimashƙu,

“Hamat da Arfad sun gigice,

Domin sun ji mugun labari,

sun narke saboda yawan damuwa,

Ba za su iya natsuwa ba.

24 Dimashƙu ta yi halin ƙaƙa naka yi,

Ta juya, ta gudu,

Tsoro ya kama ta,

Azaba da baƙin ciki sun kama ta

kamar na naƙuda.

25 Ƙaƙa aka manta da sanannen birni,

Birnin da take cike da murna?

26 A waccan rana samarinta za su fāɗi a

dandalinta.

Za a hallaka sojojinta duka,

Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.

27 Zan kuma sa wuta a garun Dimashƙu,

Za ta kuwa cinye fādodin

Ben-hadad.”

Jawabin Ubangiji a kan Kedar da Hazor

28 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Kedar da sarakunan Hazor, waɗanda sarki Nebukadnezzar ya ci da yaƙi,

“Ku tashi zuwa Kedar,

Ku hallaka mutanen gabas.

29 Za a kwashe alfarwansu da

garkunansu,

Da labulan alfarwansu, da dukan

kayansu.

Za a kuma tafi da raƙumansu,

Za a gaya musu cewa, ‘Razana ta

kewaye ku!’

30 “Ku mazaunan Hazor, ku gudu zuwa

nesa,

Ku ɓuya cikin zurfafa, ni Ubangiji na

faɗa,

Gama Nebukadnezzar, Sarkin

Babila, ya shirya muku

maƙarƙashiya,

Ya ƙulla mugun nufi game da ku.

31 Ku tashi ku fāɗa wa al’ummar da take

zama lami lafiya,

Waɗanda ba su da ƙofofi ko ƙyamare,

Suna zama su kaɗai.

32 “Za a washe raƙumansu da

garkunan shanunsu ganima,

Zan watsar da masu yin kwaskwas

ko’ina,

Zan kuma kawo musu masifu daga

kowace fuska,

Ni Ubangiji na faɗa.

33 Hazor za ta zama kufai har abada,

wurin zaman diloli,

Ba wanda zai zauna a ciki, ba wanda

kuma zai yi zaman baƙunci a wurin.”

Jawabin Ubangiji a kan Elam

34 Maganar da Ubangiji ya yi wa annabi Irmiya a kan Elam a farkon sarautar Zadakiya Sarkin Yahuza.

35 Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Zan karya bakan Elam, inda

ƙarfinta yake.

36 Zan sa iska ta hura a kan Elam daga

kusurwoyi huɗu na samaniya.

Za ta watsar da mutane ko’ina,

Har ba ƙasar da za a rasa mutumin

Elam a ciki.

37 Zan sa mutanen Elam su ji tsoron

maƙiyansu waɗanda suke neman

ransu.

Da zafin fushina zan kawo musu

masifa,

In sa a runtume su da takobi,

Har in ƙare su duka,

Ni Ubangiji na faɗa.

38 Zan kafa gadon sarautata a Elam,

Zan hallaka sarkinta da

shugabanninta.

39 Amma daga baya zan sa Elam kuma

ta wadata.

Ni Ubangiji na faɗa.”

Categories
IRM

IRM 50

Jawabin Ubangiji a kan Babila

1 Jawabin da Ubangiji ya yi wa annabi Irmiya a kan

Babila da ƙasar Kaldiyawa ke nan,

2 “Ku ba da labari ga sauran

al’umma, ku yi shela,

Ku ta da tuta, ku yi shela,

Kada ku ɓuya, amma ku ce,

‘An ci Babila da yaƙi,

An kunyatar da Bel,

An kunyatar da siffofinta,

Merodak ya rushe,

Gumakanta kuma sun ragargaje!’

3 “Wata al’umma za ta taso daga arewa gāba da ita, za ta mai da ƙasar abar ƙyama, ba wanda zai zauna ciki. Mutum da dabba duk sun watse, kowa ya bar ta.”

4 Ubangiji ya ce, “Sa’ad da lokacin nan ya yi, mutanen Isra’ila da na Yahuza za su zo tare, suna kuka, suna nemana, ni Ubangiji Allahnsu.

5 Za su tambayi hanyar Sihiyona, sa’an nan su bi ta, suna cewa, ‘Bari mu haɗa kanmu don mu yi madawwamin alkawari da Ubangiji, alkawari wanda ba za a manta da shi ba.’

6 “Mutanena sun zama kamar ɓatattun

tumaki,

Waɗanda makiyayansu suka bauɗar

da su,

Suka ɓata a cikin tsaunuka,

Suna kai da kawowa daga wannan

dutse zuwa wancan.

Sun manta da shingensu.

7 Duk waɗanda suka same su, sun

cinye su.

Maƙiyansu suka ce, ‘Ba mu yi laifi

ba,’

Gama sun yi wa Ubangiji laifi,

wanda yake tushen gaskiya,

Ubangiji wanda kakanninsu suka

dogara gare shi.

8 “Ku gudu daga cikin Babila,

Ku fita kuma daga cikin ƙasar

Kaldiyawa,

Ku zama kamar bunsurai waɗanda

suke ja gaban garke.

9 Ga shi, zan kuta manyan ƙasashe

daga arewa

Su faɗa wa Babila da yaƙi.

Za su ja dāgar yaƙi gāba da ita, su

cinye ta.

Kibansu kamar na gwanayen

mayaƙa ne

Waɗanda ba su komowa banza.

10 Za a washe Kaldiyawa,

Waɗanda suka washe su kuwa za su

ƙoshi,

Ni Ubangiji na faɗa.

11 “Saboda kuna murna, kuna farin

ciki,

Ku da kuka washe gādona,

Saboda kuma kuna tsalle kamar

karsana a cikin ciyawa,

Kuna haniniya kamar ingarmu,

12 Domin haka za a kunyatar da Babila

sosai, inda kuka fito.

Za ta zama ta baya duka a cikin

sauran al’umma,

Za ta zama hamada, busasshiyar

ƙasa.

13 Saboda fushin Ubangiji, ba wanda

zai zauna a cikinta,

Za ta zama kufai,

Duk wanda ya bi ta wajen Babila, zai

ji tsoro,

Zai kuma yi tsaki saboda

lalacewarta.

14 “Dukanku ‘yan baka, ku ja dāga, ku

kewaye Babila,

Ku harbe ta, kada ku rage kibanku,

Gama ta yi wa Ubangiji zunubi.

15 Ku kewaye ta da kuwwar yaƙi!

Ta ba da gari,

Ginshiƙanta sun fāɗi.

An rushe garunta,

Gama wannan sakayya ce ta

Ubangiji.

Ku sāka mata, ku yi mata kamar

yadda ta yi.

16 Ku datse wa Babila mai shuka,

Da mai yanka da lauje a lokacin

girbi.

Saboda takobin azzalumi,

Kowa zai koma wurin mutanensa,

Kowa kuma zai gudu zuwa

ƙasarsa.”

17 “Isra’ilawa kamar tumaki ne waɗanda zakuna suka bi su suna kora. Da farko dai Sarkin Assuriya ne ya cinye su. Yanzu kuwa Sarkin Babila, wato Nebukadnezzar, shi ne yake gaigayi ƙasusuwansu.

18 Saboda haka ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila na ce, zan yi wa Sarkin Babila da ƙasarsa hukunci, kamar yadda na hukunta Sarkin Assuriya.

19 Zan komar da Isra’ila a makiyayarsa, zai yi kiwo a Karmel da Bashan. Zai sami biyan bukatarsa a tsaunukan Ifraimu da na Gileyad.

20 Ni Ubangiji na ce sa’ad da lokacin nan ya yi za a nemi laifi da zunubi a cikin Isra’ila da Yahuza, amma ba za a samu ba, gama zan gafarta wa sauran da suka ragu.

21 “Ku haura ku fāɗa wa ƙasar

Meratayim da mazaunan Fekod.

Ku kashe, ku hallaka su sarai,

Ku aikata dukan abin da na umarce

ku,

Ni Ubangiji na faɗa.

22 Hargowar yaƙi tana cikin ƙasar,

Da kuma babbar hallakarwa!

23 Ga yadda aka karya gudumar dukan

duniya!

Ga yadda Babila ta zama abar

ƙyama ga sauran al’umma!

24 Na kafa miki tarko, ya kuwa kama

ki, ya Babila,

Ke kuwa ba ki sani ba.

An same ki, an kama,

Domin kin yi gāba da ni.”

25 Ubangiji ya buɗe taskar

makamansa,

Ya fito da makaman hasalarsa,

Gama Ubangiji Allah Mai Runduna

yana da aikin da zai yi a ƙasar

Kaldiyawa.

26 Ku zo, ku fāɗa mata daga kowane

sashi.

Ku buɗe rumbunanta,

Ku tsittsiba ta kamar tsibin hatsi,

Ku hallakar da ita ɗungum,

Kada wani abu nata ya ragu.

27 Ku kashe dukan bijimanta, a kai su

mayanka!

Kaitonsu, gama kwanansu ya ƙare,

Lokacin hukuncinsu ya yi.

28 Ku ji, sun gudu sun tsere daga ƙasar

Babila,

Don su faɗa cikin Sihiyona,

Sakayyar Ubangiji Allahnmu domin

Haikalinsa.

29 “Ku kirawo ‘yan baka, dukan

waɗanda sukan ja baka, su faɗa

wa Babila.

Ku kafa sansani kewaye da ita, kada

ku bar kowa ya tsira.

Ku sāka mata bisa ga dukan

ayyukanta, gama ta raina Ubangiji

Mai Tsarki na Isra’ila.

30 Domin haka samarinta za su fāɗi a

tituna.

Za a hallaka sojojinta duka a wannan

rana,

Ni Ubangiji na faɗa.

31 “Ga shi, ina gāba da ke, ke Babila,

mai girmankai.

Gama ranar da zan hukunta ki, ta zo,

Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.

32 Mai girmankai za ta yi tuntuɓe ta

fāɗi,

Ba kuwa wanda zai tashe ta,

Zan ƙone garuruwanta da wuta,

Zan kuma hallaka dukan abin da yake

kewaye da ita.

33 “Ni Ubangiji Mai Runduna na ce,

An danne mutanen Isra’ila da na

Yahuza,

Duk waɗanda suka kama su bayi sun

riƙe su da ƙarfi.

Sun ƙi su sake su.

34 Mai fansarsu mai ƙarfi ne,

Ubangiji Mai Runduna ne sunansa.

Hakika zai tsaya musu don ya kawo

wa duniya salama,

Amma zai kawo wa mazaunan Babila

fitina.

35 Ni Ubangiji na ce,

Akwai takobi a kan Kaldiyawa,

Da a kan mazaunan Babila,

Da a kan ma’aikatanta da masu

hikimarta,

36 Akwai takobi a kan masu sihiri

Don su zama wawaye.

Akwai takobi a kan jarumawanta

Don a hallaka su.

37 Akwai takobi a kan mahayan

dawakanta, da a kan karusanta,

Da a kan sojojin da ta yi ijara da su

Don su zama kamar mata,

Akwai takobi a kan dukan dukiyarta

domin a washe ta.

38 Fari zai sa ruwanta ya ƙafe,

Gama ƙasa tana cike da gumaka

waɗanda suka ɗauke hankalin

mutane.

39 “Domin haka namomin jeji da diloli

za su zauna a Babila,

Haka kuma jiminai.

Ba za a ƙara samun mazauna a

cikinta ba har dukan zamanai.

40 Abin da ya faru da Saduma da

Gwamrata,

Da biranen da suke kewaye da su,

Shi ne zai faru da Babila.

Ba mutumin da zai zauna cikinta.

41 “Ga mutane suna zuwa daga arewa,

Babbar al’umma da sarakuna

Suna tahowa daga wurare masu nisa

na duniya.

42 Suna riƙe da baka da māshi,

Mugaye ne marasa tausayi.

Amonsu yana kama da rurin teku,

Suna shirya don yin yaƙi da ke, ya

Babila.

43 Sarkin Babila ya ji labarinsu,

Hannuwansa suka yi suwu.

Wahala da azaba sun kama shi

kamar mace mai naƙuda.

44 “Ni Ubangiji ina zuwa kamar zakin da yake fitowa daga kurmin Urdun zuwa makiyaya. Nan da nan zan sa su gudu daga gare ta. Sa’an nan zan naɗa mata wanda na zaɓa. Wa yake kama da ni? Wa zai yi ƙarata? Wane shugaba zai yi gāba da ni?

45 Saboda haka ku ji shirin da Ubangiji ya yi gāba da Babila, da nufin ya yi gaba da ƙasar Kaldiyawa. Hakika za a tafi da ƙananansu, garke zai zama kango.

46 Duniya za ta girgiza sa’ad da ta ji an ci Babila da yaƙi. Za a ji kukanta cikin sauran al’umma.”

Categories
IRM

IRM 51

Hukuncin Ubangiji a kan Babila

1 Ubangiji ya ce,

“Ga shi, zan kawo iskar ɓarna a

kan Babila

Da mazaunan Kaldiya.

2 Zan aika da masu casawa zuwa

Babila, za su casa ta,

Su bar ƙasarta kango.

Za su kewaye ta a kowane sashi

A wannan ranar masifa.

3 Kada ku bar maharbi ya yi harbi da

bakansa,

Kada kuma ya sa kayan yaƙinsa,

Kada ku rage samarinta,

Ku hallaka dukan sojojinta.

4 Za su fāɗi matattu a ƙasar

Kaldiyawa,

Za a sassoke su a titunansu.”

5 Allah na Isra’ila da Yahuza,

Ubangiji Mai Runduna, bai yashe

su ba,

Ko da yake sun yi wa Mai Tsarki na

Isra’ila zunubi.

6 Ku gudu daga cikin Babila,

Bari kowa ya ceci ransa,

Kada a hallaka ku tare da ita,

Gama a wannan lokaci Ubangiji zai

sāka mata,

Zai sāka mata bisa ga alhakinta.

7 Babila ta zama ƙoƙon zinariya a

hannun Ubangiji,

Ta sa dukan duniya ta yi maye.

Ƙasashen duniya sun sha ruwan

inabinta, suka haukace.

8 Farat ɗaya, Babila ta fāɗi, ta

kakkarye,

Ku yi kuka dominta!

Ku samo mata magani domin azabar

da take sha, watakila ta warke.

9 Mun ba Babila magani, amma ba ta

warke ba.

Bari mu ƙyale ta, kowannenmu ya

koma garinsu,

Gama hukuncinta ya kai sammai, ya

yi tsawo har samaniya.

10 Ubangiji ya baratar da mu a fili,

Bari mu tafi mu yi shelar aikin

Ubangiji Allahnmu a cikin

Sihiyona.

11 Ku wasa kibau, ku cika

kwaruruwanku!

Ubangiji ya ta da ruhun sarakunan

Mediyawa,

Domin yana niyyar hallaka Babila.

Gama Ubangiji zai yi ramuwa

saboda Haikalinsa.

12 Ku ta da tuta don a faɗa wa garun

Babila,

Ku ƙarfafa matsara,

Ku sa su su yi tsaro,

Ku kuma sa ‘yan kwanto!

Ga shi, Ubangiji ya yi niyya, ya kuwa

aikata

Abin da ya faɗa a kan mazaunan

Babila.

13 Ƙarshenki ya zo,

Ke mai zama kusa da ruwa mai yawa,

Mai yawan dukiya.

Ajalinki ya auka.

14 Ubangiji Mai Runduna ya rantse da

zatinsa, ya ce,

“Hakika zan cika Babila da mutane

kamar fāra,

Za su kuwa raira waƙar nasara a

kanta.”

15 Ubangiji ne ya halicci ƙasa da

ikonsa,

Ya kafa duniya da hikimarsa,

Ya kuma shimfiɗa sammai da

fahiminsa.

16 Bisa ga umarninsa ruwan da yake

samaniya yakan yi ruri,

Yakan sa gajimare su tashi daga

ƙarshen duniya,

Yakan sa walƙiya ta walƙata cikin

ruwan sama,

Yakan sa iska ta haura daga cikin

taskokinsa.

17 Kowane ɗan adam wawa ne, marar

ilimi,

Kowane maƙerin zinariya kuma zai

sha kunya daga wurin gumakansa,

Gama siffofinsa na ƙarya ne, ba

numfashi a cikinsu.

18 Su marasa amfani ne, aikin ruɗarwa

ne kawai,

Za su lalace a lokacin da za a

hukunta su.

19 Amma wanda yake wajen Yakubu ba

haka yake ba,

Domin shi ne ya halicci dukan

abu,

Isra’ila kuwa abin mallakarsa ne,

Ubangiji Mai Runduna ne sunansa.

20 Ubangiji ya ce,

“Kai ne guduma da kayan yaƙina,

Da kai ne na farfasa ƙasashen

duniya,

Da kai ne na hallaka mulkoki.

21 Da kai ne na karya doki da

mahayinsa,

22 Da kai ne na farfasa karusa da

mahayinsa.

Da kai ne na kakkarya mace da

namiji,

Da kai ne na kakkarya tsoho da

saurayi,

Da kai ne na kakkarya saurayi da

budurwa,

23 Da kai ne na kakkarya makiyayi da

garkensa,

Da kai ne na kakkarya manoma da

dawakan nomansa,

Da kai ne na kakkarya masu mulki

da shugabanni.”

24 Ubangiji ya ce, “Zan sāka wa Babila da dukan mazaunan Kaldiya a ganin idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona.

25 Ga shi, ina gaba da kai, ya dutse mai

hallakarwa,

Wanda ya hallaka duniya duka.

Zan miƙa hannuna gāba da kai,

Zan mirgino da ƙasa daga

ƙwanƙolin dutse,

Zan maishe ka ƙonannen dutse.

26 Ba za a sami dutsen yin kusurwa, ko

na kafa harsashen gini a cikinka

ba,

Amma za ka zama marar amfani har

abada.”

27 Ku ta da tuta a duniya,

Ku busa wa ƙasashen duniya ƙaho,

Ku shirya ƙasashe don su yi yaƙi

da ita,

Ku kirawo mulkokin Ararat, da na

Minni, da na Ashkenaz, su yi yaƙi

da ita.

Ku naɗa sarkin yaƙi wanda zai

shugabanci yaƙin da za a yi da ita,

Ku kawo dawakai kamar fāra.

28 Ku shirya ƙasashe su yi yaƙi da ita,

Sarakunan Mediyawa, da masu

mulkinsu, da shugabanninsu,

Da kowace ƙasar da take ƙarƙashin

mulkinsu.

29 Duniya ta girgiza, tana makyarkyata

saboda azaba,

Gama nufin Ubangiji na gāba da

Babila ya tabbata,

Nufinsa na mai da ƙasar Babila

kufai, inda ba kowa.

30 Sojojin Babila sun daina yaƙi, suna

zaune a cikin kagaransu.

Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata,

An sa wa wuraren zamanta wuta,

An karya ƙyamaren ƙofofin

garinta.

31 Maguji yana biye da maguji a guje,

Jakada yana biye da jakada,

Don su faɗa wa Sarkin Babila, cewa

an ci birninsa a kowane gefe.

32 An ƙwace mashigai

An ƙone fadamu da wuta,

Sojoji sun gigice.

33 Ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na

Isra’ila na ce,

“Mutanen Babila sun zama kamar

daɓen masussuka

A lokacin da ake sussuka,

Ba kuwa da daɗewa ba lokacin girbe

ta zai zo.”

34 Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya

cinye Urushalima,

Ya ragargaza ta,

Ya maishe ta kufai,

Ya haɗiye ta kamar yadda dodon

ruwa yakan yi,

Ya cika cikinsa da kayan

marmarinta,

Ya tatse ta sarai.

35 Bari mutanen Sihiyona su ce,

“Allah ya sa muguntar da mutanen

Babila suka yi mana ta koma

kansu!”

Bari kuma mutanen Urushalima su

ce,

“Allah ya sa hakkin jininmu ya koma

kan Kaldiyawa!”

36 Ubangiji ya ce,

“Zan tsaya muku,

Zan ɗaukar muku fansa,

Zan sa tekunsu da maɓuɓɓugarsu su

ƙafe.

37 Babila za ta zama tarin juji, wurin

zaman diloli,

Abar ƙyama da abar ba’a, inda ba

kowa.

38 Mutanen Babila za su yi ruri kamar

zakuna,

Su yi gurnani kamar ‘ya’yan zaki.

39 Sa’ad da suke cike da haɗama zan yi

musu biki,

In sa su sha, su yi maye, su yi

murna.

Za su shiga barcin da ba za su farka

ba.

40 Zan kai su mayanka kamar ‘yan

raguna, da raguna, da bunsurai.

41 “An ci Babila,

Ita wadda duniya duka take yabo an

cinye ta da yaƙi,

Ta zama abar ƙyama ga sauran

al’umma!

42 Teku ta malalo a kan Babila,

Raƙuman ruwa masu hauka sun

rufe ta.

43 Garuruwanta sun zama abin

ƙyama,

Ta zama hamada, inda ba ruwa,

Ƙasar da ba mazauna,

Ba kuma mutumin da zai ratsa ta

cikinta.

44 Zan hukunta Bel, gunkin Babila,

Zan sa ya yi aman abin da ya

haɗiye,

Ƙasashen duniya ba za su ƙara

bumbuntowa wurinsa ba.

Garun Babila ya rushe!”

45 “Ku fito daga cikinta, ya jama’ata,

Kowa ya tsere da ransa daga zafin

fushin Ubangiji.

46 Kada zuciyarku ta yi suwu,

Kada kuma ku ji tsoro saboda

labarin da ake ji a ƙasar,

Labari na wannan shekara dabam,

na wancan kuma dabam,

A kan hargitsin da yake a ƙasar,

Mai mulki ya tasar wa mai mulki.

47 Saboda haka kwanaki suna zuwa,

Sa’ad da zan hukunta gumakan

Babila,

Za a kunyatar da dukan ƙasar

Babila,

Dukan matattunta za su faɗi a

tsakiyarta.

48 Sa’an nan sama da duniya, da dukan

abin da take cikinsu,

Za su raira waƙar farin ciki,

Domin masu hallakarwa daga arewa

da za su auko mata,

Ni Ubangiji na faɗa.”

49 Babila za ta fāɗi,

Saboda mutanen Isra’ila da dukan

mutanen duniya waɗanda ta

kashe.

50 Ku waɗanda kuka tsere wa takobi!

Ku gudu! Kada ku tsaya!

Ku tuna da Ubangiji a can nesa inda

kuke,

Ku kuma yi ta tunawa da

Urushalima.

51 Mun sha kunya saboda zargin da ake

yi mana,

Kunya ta rufe mu,

Gama baƙi sun shiga tsarkakan

wurare na Haikalin Ubangiji.

52 “Domin haka kwanaki suna zuwa,”

in ji Ubangiji,

“Sa’ad da zan hukunta gumakan

Babila, da dukan ƙasarta,

Waɗanda aka yi wa rauni, za su yi

nishi.

53 Ko da Babila za ta hau samaniya,

Ta gina kagara mai ƙarfi a can,

Duk da haka zan aiki masu

hallakarwa a kanta,

Ni Ubangiji na faɗa.”

54 Ku ji muryar kuka daga Babila,

Da hargowar babbar hallakarwa

daga ƙasar Kaldiyawa!

55 Gama Ubangiji yana lalatar da

Babila,

Yana kuma sa ta kame bakinta na

alfarma,

Sojoji suna kutsawa kamar raƙuman

ruwa,

Suna ta da muryoyinsu.

56 Gama mai hallakarwa ya auka wa

Babila,

An kama sojojinta,

An kuma kakkarya bakunansu,

Gama Ubangiji shi Allah ne, mai

sakayya,

Zai yi sakayya sosai.

57 “Zan sa mahukuntanta, da masu

hikimarta,

Da masu mulkinta, da

shugabanninta,

Da sojojinta su sha su yi maye.

Za su dinga yin barcin da ba za su

farka ba,”

In ji Sarkin, mai suna Ubangiji Mai

Runduna.

58 “Ni Ubangiji Mai Runduna, na ce,

Za a baje garun nan na Babila mai

fāɗi

Za a kuma ƙone dogayen

ƙyamarenta da wuta.

Mutane sun wahalar da kansu a

banza.

Sauran al’umma sun yi wahala kawai

domin wutar lalata.”

59 Jawabin da annabi Irmiya ya ba Seraiya, ɗan Neriya, wato jikan Ma’aseya, lokacin da ya tafi tare da Zadakiya, Sarkin Yahuza, zuwa Babila a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Seraiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.

60 Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babila, wato dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babila.

61 Irmiya kuwa ya ce wa Seraiya, “Lokacin da ka kai Babila, sai ka karanta dukan maganan nan.

62 Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’

63 Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yufiretis.

64 Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babila za ta nutse, ba za ta ƙara tashi ba saboda masifar da Ubangiji zai kawo mata.’ ”

Wannan shi ne ƙarshen maganar Irmiya.

Categories
IRM

IRM 52

Mulkin Zadakiya

1 Zadakiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal, ‘yar Irmiya, wanda yake zaune a Libna.

2 Sarki Zadakiya ya aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehoyakim ya yi.

3 Al’amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra’ila da Yahuza, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala.

Faɗuwar Urushalima

Zadakiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babila.

4 A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zadakiya, Sarkin Yahuza, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina garu kewaye da ita.

5 An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zadakiya.

6 A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci.

7 Sai aka huda garun birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa’ad da Kaldiyawan take kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba.

8 Amma sojojin Kaldiyawa suka runtumi sarki Zadakiya, suka ci masa a filayen Yariko. Dukan sojoji suka yashe shi.

9 Da aka kama Zadakiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babila a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babila ya yanke masa shari’a.

10 Ya kuwa kashe ‘ya’yan Zadakiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuza a Ribla.

11 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zadakiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babila inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.

Yahuza ya Je Zaman Talala

12 A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babila, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima.

13 Sai ya ƙone Haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan manyan gidajen da suke Urushalima.

14 Sojojin Kaldiyawa da suke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan garun Urushalima.

15 Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babila, da sauran masu sana’a, ya kai su bautar talala a Babila.

16 Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki.

17 Kaldiyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda suke a Haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babila.

18 Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar Haikali.

19 Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe.

20 Tagullar da sarki Sulemanu ya yi waɗannan abubuwa da ita, wato ginshiƙai biyu, da kwatarniyar tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda suke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.

21 Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma taƙi huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki.

22 A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman.

23 Akwai siffofin rumman tasa’in da shida da ake gani a gyaffan. Dukan siffofin rumman da suke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne.

24 Shugaban matsara kuma ya ɗauki Seraiya babban firist, da Zafaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar Haikali, ya tafi da su.

25 Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai ‘yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su.

26 Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babila a Ribla,

27 Sarkin Babila kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat.

Haka aka tafi da mutanen Yahuza bautar talala.

28 Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa dubu uku da ashirin da uku (3,023).

29 A shekara ta goma sha takwas ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima ɗari takwas da talatin da biyu.

30 A shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa kuma, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa ɗari bakwai da arba’in da biyar. Jimillarsu duka kuwa dubu huɗu da ɗari shida ne (4.600).

An saki Yekoniya an ba shi Girma a Babila

31 A shekarar da Ewil-merodak ya zama Sarkin Babila, sai ya nuna wa Yekoniya Sarkin Yahuza alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yekoniya bauta.

32 Ewil-merodak ya nuna wa Yekoniya alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babila tare da shi.

33 Yekoniya ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa.

34 Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarki, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.

Categories
MAK

MAK 1

Baƙin Cikin Sihiyona

1 Urushalima wadda take cike da mutane a dā,

Yanzu tana zaman kaɗaici!

Tana zama kamar mace wadda mijinta ya rasu,

Ita wadda dā ta zama babba a cikin sauran al’ummai!

Ita wadda take a dā sarauniya a cikin larduna,

Ta zama mai biyan gandu!

2 Da dare tana kuka mai zafi,

Hawaye suna zuba sharaf-sharaf a kumatunta.

Dukan masoyanta ba wanda yake ta’azantar da ita.

Dukan abokanta sun ci amanarta, sun zama maƙiyanta.

3 Yahuza ta tafi bauta tana shan azaba,

Da bauta mai tsanani.

Tana zaune a tsakiyar sauran al’umma,

Amma ba ta sami hutawa ba,

Gama masu runtumarta sun ci mata, ba hanyar tsira.

4 Hanyoyin Sihiyona suna baƙin ciki

Domin ba mai halartar ƙayyadaddun idodi.

Dukan ƙofofinta sun zama kufai,

Firistocinta suna nishi,

Budurwanta kuma suna wahala,

Ita kanta ma tana shan wuya ƙwarai.

5 Maƙiyanta sun zama shugabanninta,

Abokan gābanta kuma sun zama iyayengijinta.

Gama Ubangiji ne ya sa ta sha wahala

Saboda yawan zunubanta.

‘Ya’yanta sun tafi bauta wurin maƙiyanta.

6 Dukan darajar Sihiyona ta rabu da ita,

Shugabanninta sun zama kamar bareyin

Da ba su sami wurin kiwo ba,

Suna gudu ba ƙarfi a gaban wanda yake korarsu.

7 A kwanakin wahalarta na rashin wurin zama,

Urushalima ta tuna da dukan abubuwanta masu daraja a dā.

A lokacin da mutanenta suka fāɗa a hannun maƙiyi,

Ba wanda ya taimake ta,

Maƙiyanta sun gan ta,

Sun yi mata ba’a saboda fāɗuwarta.

8 Urushalima ta yi zunubi ƙwarai da gaske,

Saboda haka ta ƙazantu,

Dukan waɗanda suka girmama ta sun raina ta

Domin sun ga tsiraicinta,

Ita kanta ma tana nishi, ta ba da baya.

9 Ƙazantarta tana cikin tufafinta,

Ba ta tuna da ƙarshenta ba,

Domin haka faɗuwarta abar tsoro ce,

Ba ta da mai yi mata ta’aziyya.

“Ya Ubangiji, ka dubi wahalata,

Gama maƙiyi ya ɗaukaka kansa!”

10 Maƙiyi ya miƙa hannunsa

A kan dukan kayanta masu daraja,

Gama ta ga al’ummai sun shiga Haikali,

Su waɗanda ka hana su shiga cikin jama’arka.

11 Dukan jama’arta suna nishi don neman abinci,

Sun ba da kayansu masu daraja saboda abinci

Don su rayu.

“Ya Ubangiji ka duba, ka gani,

Gama an raina ni.”

12 “Dukanku masu wucewa, ba wani abu ba ne a gare ku?

Ku duba, ku gani, ko akwai baƙin ciki irin nawa,

Wanda Ubangiji ya ɗora mini,

A ranar fushinsa mai zafi.

13 “Daga sama ya aukar da wuta a cikin ƙasusuwana.

Ya kuma kafa wa ƙafafuna ashibta,

Ya komar da ni baya,

Ya bar ni a yashe, sumamme dukan yini.

14 “Ubangiji ya tattara laifofina

Ya yi karkiya da su,

Ya ɗaura su a wuyana,

Ya sa ƙarfina ya kāsa.

Ya kuma bashe ni a hannun

Waɗanda ban iya kome da su ba.

15 “Ubangiji ya yi watsi da majiya ƙarfina,

Ya kirawo taron jama’a a kaina

Don su murƙushe samarina.

Ya kuma tattake Urushalima, zaɓaɓɓiyarsa,

Kamar ‘ya’yan inabi a wurin matsewa.

16 “Ina kuka saboda waɗannan abubuwa,

Hawaye suna zuba sharaf-sharaf daga idanuna.

Gama mai ta’azantar da ni,

Wanda zai sa in murmure yana nesa da ni.

‘Ya’yana sun lalace,

Gama maƙiyi ya yi nasara!”

17 Sihiyona tana miƙa hannuwanta,

Amma ba wanda zai ta’azantar da ita.

Gama Ubangiji ya umarci maƙwabtan Yakubu su zama maƙiyansa.

Urushalima kuma ta zama ƙazantacciya a tsakaninsu.

18 “Abin da Ubangiji ya yi daidai ne,

Gama ni na ƙi bin maganarsa,

Ku ji, ya ku jama’a duka,

Ku dubi wahalata,

‘Yan matana da samarina,

An kai su bauta!

19 “Na kira masoyana, amma suka yaudare ni,

Firistocina da dattawana a cikin birni sun hallaka

Saboda neman abincin da za su ci su rayu.

20 “Ka duba, ya Ubangiji, ina shan wahala,

Raina yana cikin damuwa,

Zuciyata tana makyarkyata saboda tayarwata.

A titi takobi yana karkashewa,

A gida kuma ga mutuwa.

21 “Sun ji yadda nake nishi,

Ba mai ta’azantar da ni.

Dukan maƙiyana sun ji labarin wahalar da nake ciki,

Suna kuwa murna da ka yi haka.

Ka kawo ranan nan da ka ambata,

Domin su ma su zama kamar yadda nake.

22 “Ka sa mugayen ayyukansu su bayyana a gabanka,

Sa’an nan ka hukunta su kamar yadda ka hukunta ni saboda dukan laifofina.

Gama nishe-nishena sun yi yawa.

Zuciyata kuma ta karai.”

Categories
MAK

MAK 2

Hukuncin Ubangiji a kan Urushalima

1 Ubangiji ya duhunta Sihiyona saboda fushinsa!

Daga Sama kuma ya jefar da darajar Isra’ila a ƙasa.

Bai kuma tuna da matashin sawayensa ba

A ranar fushinsa.

2 Dukan wuraren zaman Yakubu,

Ubangiji ya hallakar ba tausayi,

Da fushinsa kuma ya rurrushe kagaran Sihiyona.

Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulkin.

3 Da zafin fushinsa, ya karya ƙarfin Isra’ila,

Ya kuma bar yi musu taimako

A lokacin da abokan gāba suka zo.

Kamar harshen wuta, ya ƙone dukan abin da yake na Yakubu.

4 Ya ja bakansa kamar abokan gāba,

Ya kuma nuna ikonsa kamar maƙiyi.

Ya hallaka dukan abin da yake da bansha’awa.

A alfarwar Sihiyona, ya zubo da hasalarsa kamar wuta.

5 Ubangiji ya zama kamar maƙiyi, ya hallaka Isra’ila.

Ya hallaka fādodinta duka,

Ya mai da kagaranta kango.

Ya aukar wa Yahuza da makoki da baƙin ciki mai yawa.

6 Ya rushe Haikalinsa kamar bukka cikin gona,

Ya mai da wurin yin ƙayyadaddun idodinsa kufai.

Ubangiji ya sa ƙayyadadden idi da kiyaye Asabar

Su ƙare a Sihiyona,

Da zafin fushinsa kuma ya wofinta sarki da firist.

7 Ubangiji ya wulakanta bagadensa,

Ya kuma wofinta tsattsarkan Haikalinsa.

Ya ba da garun fādodinta a hannun abokan gāba,

Suka yi sowa a Haikalin Ubangiji

Kamar a ranar idi.

8 Ubangiji ya yi niyya

Ya mai da garun Sihiyona kufai,

Ya auna ta da igiyar awo,

Bai janye dantsensa daga hallaka ta ba.

Ya sa kagara da garu su zozaye, su lalace tare.

9 Ƙofofinta sun nutse ƙasa,

Ya lalatar, ya kakkarya ƙyamarenta,

An kai sarkinta da mahukuntanta cikin al’ummai,

Inda ba a bin dokokin annabawanta,

Ba su kuma samun wahayi daga wurin Ubangiji.

10 Dattawan Sihiyona suna zaune a ƙasa shiru,

Sun yi hurwa, suna saye da tufafin makoki.

‘Yan matan Urushalima kuma sun sunkuyar da kansu ƙasa.

11 Idanuna sun dushe saboda kuka,

Raina yana cikin damuwa.

Zuciyata ta karai saboda halakar mutanena,

Gama ‘yan yara da masu shan mama

Sun suma a titunan birnin.

12 Suna yi wa uwayensu kuka, suna cewa,

“Ina abinci da ruwan inabi?”

Suna suma kamar mutanen da aka yi wa rauni

A titunan birnin,

Suna mutuwa a ƙirjin uwayensu.

13 Me zan ce miki?

Da me zan kwatanta ki, ya Urushalima?

Da me zan misalta wahalarki

Don in ta’azantar da ke, ya Sihiyona?

Masifar da ta same ki tana da fāɗi kamar teku,

Wa zai iya warkar da ke?

14 Annabawanki sun gano miki wahayan ƙarya,

Ba su tone asirin muguntarki,

Har da za a komo da ke daga bauta ba.

Amma suka yi miki annabcin ƙarya na banza.

15 Dukan masu wucewa suna yin miki tafin raini.

Suna yi wa Urushalima tsāki,

Suna kaɗa mata kai, suna cewa,

“Ai, Urushalima ke nan,

Birnin nan da ake cewa mai cikakken jamali,

Wanda ya ƙayatar da dukan duniya?”

16 Maƙiyanki duka sun wage bakinsu gāba da ke,

Suna tsāki, suna cizon bakinsu,

Suna ihu, suna cewa, “Mun hallaka ta!

Ai, wannan ita ce ranar da muke fata!

Ga shi kuwa, ta zo, mun gan ta!”

17 Ubangiji ya aikata abin da ya yi niyya,

Ya cika maganarsa wadda ya faɗa tun dā,

Ya hallakar, ba tausayi,

Ya sa maƙiyi ya yi murna a kanki,

Ya ƙarfafa ƙarfin maƙiyanki.

18 Ya Sihiyona, ki yi kuka ga Ubangiji,

Bari hawayenki su gudana dare da rana kamar ruwan rafi,

Kada ki huta, kada kuma idanunki su huta!

19 Ki tashi, ki ya ta kuka dukan dare,

Ki bulbule abin da yake cikin zuciyarki

Kamar ruwa gaban Ubangiji.

Ki miƙa hannuwanki zuwa gare shi,

Saboda rayukan ‘ya’yanki,

Waɗanda suke suma da yunwa

A magamin kowane titi!

20 Ya Ubangiji, ka duba, ka gani!

Wane ne ka yi wa haka?

Mata za su cinye ‘ya’yansu da suke reno?

Ko kuwa za a kashe firist da annabi

A cikin Haikalin Ubangiji?

21 Yara da tsofaffi suna kwance cikin ƙurar tituna,

An kashe ‘ya’yana, ‘yan mata da samari, da takobi.

Ka kashe su a ranar fushinka, ba tausayi.

22 Ka gayyato mini tsoro

Kamar yadda akan gayyato taro a ranar idi.

A ranar fushin Ubangiji

Ba wanda ya tsere, ko wanda ya tsira.

‘Ya’yan da na yi renonsu, na goye su,

Maƙiyina ya hallaka su.

Categories
MAK

MAK 3

Sa Zuciya ga Samun Taimako daga Wurin Ubangiji

1 Ni ne mutumin da ya sha wuyar horon Ubangiji.

2 Ya kore ni zuwa cikin duhu baƙi ƙirin.

3 Hakika ikonsa ya yi ta gāba da ni dukan yini.

4 Ya sa naman jikina da fatar jikina su lalace,

Ya kuma kakkarya ƙasusuwana.

5 Ya kewaye ni da yaƙi,

Ya rufe ni da baƙin ciki mai tsanani da wahala.

6 Ya zaunar da ni cikin duhu,

Kamar waɗanda suka daɗe da mutuwa.

7 Ya kewaye ni da garu don kada in tsere,

Ya ɗaure ni da sarƙa mai nauyi.

8 Ko da yake ina kira, ina kukan neman taimako,

Ya yi watsi da addu’ata.

9 Ya toshe hanyata da sassaƙaƙƙun duwatsu,

Ya karkatar da hanyoyina.

10 Ya zamar mini kamar beyar wanda yake fako,

Kamar zaki a ɓoye cikin ruƙuƙi.

11 Ya bauɗar da ni daga hanyata, ya yayyage ni,

Ya maishe ni, ba ni a kowa.

12 Ya ja bakansa, ya sa in zama abin baratarsa.

13 Ya harbe zuciyata da kiban kwarinsa.

14 Na zama abin dariya ga dukan mutane,

Dukan yini suna yi mini waƙar zambo.

15 Ya shayar da ni da ruwan ɗaci,

Ya ƙosar da ni da abinci mai ɗaci.

16 Ya sa in tauna tsakuwa da haƙorana,

Ya zaunar da ni cikin ƙura.

17 An raba ni da salama,

Na manta da abar da ake ce da ita wadata.

18 Sai na ce, “Darajata ta ƙare,

Ba ni kuma da sa zuciya wurin Ubangiji.”

19 Ka tuna da azabata, da galabaitata,

Da ɗacin raina, da kumallon da nake fama da shi.

20 Kullum raina yana tunanin azabaina,

Raina kuwa ya karai.

21 Da na tuna da wannan, sai na sa zuciya ga gaba.

22 Ƙaunar Ubangiji ba ta ƙarewa,

Haka kuma jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.

23 Su sababbi ne kowace safiya,

Amincinka kuma mai girma ne.

24 Na ce, “Ubangiji shi ne nawa,

Saboda haka zan sa zuciya gare shi.”

25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke sauraronsa,

Da wanda suke nemansa kuma.

26 Yana da kyau a jira ceton Ubangiji da natsuwa,

27 Yana da kyau mutum ya hori kansa tun yana yaro.

28 Bari ya zauna a kaɗaice, ya yi shiru

Sa’ad da yake da damuwa.

29 Bari ya kwanta cikin ƙura,

Watakila akwai sauran sa zuciya.

30 Bari ya yarda a mari kumatunsa,

Ya haƙura da cin mutunci.

31 Gama Ubangiji ba zai yashe mu har abada ba.

32 Ko da ya sa ɓacin rai,

Zai ji tausayi kuma,

Saboda tabbatacciyar ƙaunarsa mai yawa.

33 Gama ba da gangan ba ne yakan wahalar da ‘yan adam

Ko ya sa su baƙin ciki.

34 Ubangiji bai yarda a danne

‘Yan kurkuku na duniya ba.

35 Bai kuma yarda a hana wa mutum hakkinsa

A gaban Maɗaukaki ba,

36 Ko kuwa a karkatar wa mutum da shari’arsa.

37 Wa ya umarta, abin kuwa ya faru,

In ba Ubangiji ne ya umarta ba?

38 Ba daga bakin Maɗaukaki

Alheri da mugunta suke fitowa ne ba?

39 Don me ɗan adam

Zai yi gunaguni a kan hukuncin zunubansa?

40 Bari mu jarraba, mu bincika hanyoyinmu,

Sa’an nan mu komo wurin Ubangiji.

41 Bari mu roƙi Allah na Sama,

Muna miƙa hannuwanmu sama, mu ce,

42 “Mun yi zunubi, mun tayar,

Kai kuwa ba ka gafarta ba.

43 “Ka yafa fushi, ka runtume mu,

Kana karkashe mu ba tausayi.

44 Ka kuma rufe kanka da gajimare

Don kada addu’a ta kai wurinka.

45 Ka maishe mu shara da juji a cikin mutane.

46 “Dukan maƙiyanmu suna yi mana ba’a.

47 Tsoro, da wushefe,

Da lalatarwa, da hallakarwa sun auka mana.

48 Hawaye suna gangarawa daga idanuna kamar ruwan koguna,

Saboda an hallaka mutanena.

49 “Hawayena suna ta gangarawa, ba tsayawa, ba hutawa,

50 Har lokacin da Ubangiji daga Sama ya duba, ya gani.

51 Ganin azabar ‘yan matan birnina

Ya sa ni baƙin ciki.

52 “Waɗanda suke maƙiyana ba dalili

Sun farauce ni kamar tsuntsu.

53 Sun jefa ni da rai a cikin rami,

Suka rufe ni da duwatsu.

54 Ruwa ya sha kaina,

Sai na ce, ‘Na halaka.’

55 “Ya Ubangiji, na yi kira ga sunanka

Daga cikin rami mai zurfi.

56 Ka kuwa ji muryata.

Kada ka rufe kunnenka ga jin kukana na neman taimako.

57 Sa’ad da na yi kira gare ka, ka zo kusa.

Sa’an nan ka ce mini kada in ji tsoro.

58 “Ka karɓi da’awata, ya Ubangiji,

Ka kuwa fanshi raina.

59 Ka ga laifin da aka yi mini,

Sai ka shara’anta da’awata, ya Ubangiji.

60 Ka ga dukan irin sakayyarsu,

Da dukan dabarun da suke yi mini.

61 “Ya Ubangiji, ka ji zargi

Da dukan dabarun da suke yi mini.

62 Leɓunan maƙiyana da tunaninsu

Suna gāba da ni dukan yini.

63 Suna raira mini waƙar zambo sa’ad da suke zaune,

Da lokacin da suka tashi.

64 “Ya Ubangiji, za ka sāka musu bisa ga ayyukansu,

65 Za ka ba su tattaurar zuciya,

La’anarka kuwa za ta zauna a kansu!

66 Da fushi za ka runtume su

Har ka hallaka su a duniya, ya Ubangiji!”