Categories
DAN

DAN 11

1 A shekara ta fari ta sarautar Dariyus Bamediye, na tashi na tabbatar da shi, na kuma ƙarfafa shi.”

Sarkin Kudu da Sarkin Arewa

2 “Yanzu zan faɗa maka gaskiya. Za a ƙara samun sarakuna uku a Farisa, amma na huɗun zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da ya ƙasaita saboda dukiyarsa, zai kuta dukan daularsa ta yi gaba da mulkin Hellas.

3 “Sa’an nan wani sarki babba zai taso wanda zai yi mulki da babban iko yadda ya ga dama.

4 Sa’ad da ya ƙasaita mulkinsa zai faɗi, a rarraba shi kashi huɗu a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, amma ba za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki mulkinsa saboda waɗansu.

5 “Sarkin kudu zai yi ƙarfi, amma ɗaya daga cikin jarumawansa zai ƙasaita fiye da shi, mulkinsa kuma zai zama babba.

6 Bayan waɗansu shekaru za su ƙulla zumunci. Sarkin kudu zai aurar wa sarkin arewa da ‘yarsa don sāda zumunci, amma ba za ta sami iko ba. Shi da zuriyarsa ba za su amince da ita ba. Za a yi watsi da ita, ita da masu yi mata hidima, da mahaifinta, da waliyyinta.

7 Ba za a daɗe ba, wani daga cikin danginta zai tasar wa sojojin sarkin arewa da yaƙi, ya shiga kagararsu, ya ci su da yaƙi.

8 Zai kwashe gumakansu ganima, da siffofinsu na zubi, ya kai Masar, tare da tasoshinsu na azurfa da na zinariya masu daraja. Zai yi shekaru bai kai wa sarkin arewa yaƙi ba.

9 Bayan wannan sarkin arewa zai kai wa sarkin kudu yaƙi, amma tilas zai janye, ya koma ƙasarsa.

10 “’Ya’yansa maza za su tara babbar rundunar yaƙi. Ɗayansu zai mamaye kamar rigyawa, har ya kai kagara wurin da abokan gāba suke.

11 Sarkin kudu zai husata ya kai wa sarkin arewa yaƙi, za a ba da rundunar sojojin sarkin arewa a hannunsa.

12 Ganin ya kashe sojoji masu ɗumbun yawa, sai ya yi girmankai, amma nasararsa ba mai ɗorewa ba ce.

13 Sarkin arewa kuwa zai tara babbar rundunar soja fiye da ta dā. Bayan waɗansu shekaru kuwa zai kama hanya da babbar rundunar soja, da kayan faɗa masu yawan gaske.

14 “A waɗannan kwanaki mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin kudu. Amma waɗansu ‘yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattaka su.

15 Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin garun birni don ya ci birnin da yaƙi. Sojojin kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansa ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.

16 Amma wanda ya kawo masa yaƙin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai tsaya a ƙasa mai albarka, ya mallake ta duka.

17 Zai yunƙuro da dukan ƙarfin mulkinsa, zai zo ya gabatar da shawarar salama, ya aikata ta. Zai aurar masa da ‘yarsa don ta lalatar da mulkin abokin gabansa, amma wannan dabara ba za ta ci ba.

18 Daga nan zai yunƙura zuwa ƙasashen gaɓar teku, ya ci da yawa daga cikinsu, amma wani jarumi zai kawo ƙarshen fāɗin ransa. Zai sa fāɗin ransa ya koma masa.

19 Sa’an nan zai juya, ya nufi kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe, ya fāɗi, ba za a ƙara ganinsa ba.”

Mugun Sarki

20 “Wani sarki zai ɗauki matsayinsa, zai aiki mai karɓar haraji cikin daularsa, amma ba da daɗewa ba za a kashe shi, ba cikin hargitsin yaƙi ba.

21 “Wani kuma rainanne zai maye gurbin wancan, shi kuwa ba ɗan jinin sarauta ba ne. Zai taso ba zato ba tsammani, ya ƙwace sarautar ta hanyar zamba.

22 Zai shafe rundunonin sojoji har da rantsattsen shugaba.

23 Daga lokacin da aka ƙulla yarjejeniya da shi, zai yi munafunci. Zai sami iko ta wurin goyon bayan mutane kima.

24 Ba zato ba tsammani zai kai wa lardi mafi arziki hari. Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba wa mabiyansa kwason yaƙi, da ganima, da dukiya. Zai kuma yi shiri ya kai wa kagara hari amma domin ɗan lokaci ne kawai.

25 “Zai iza kansa ya yi ƙarfin hali ya kai wa sarkin kudu yaƙi da babbar rundunar soja. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.

26 Waɗanda suke na jikinsa, su ne za su zama sanadin faɗuwarsa. Za a kashe rundunar sojojinsa, a shafe su duk.

27 Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.

28 “Sarkin arewa zai koma gida da dukiya mai ɗumbun yawa. Zuciyarsa za ta yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai yi yadda ya ga dama sa’an nan ya koma ƙasarsa.

29 “A ƙayyadadden lokaci kuma zai koma kudu, amma a wannan karo abin ba zai zama kamar dā ba,

30 gama jiragen ruwa na Kittim za su tasar masa, shi kuwa zai ji tsoro, ya janye.

“Zai koma ya huce fushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai kula da waɗanda suka yi banza da tsattsarkan alkawarin.

31 Sojojinsa za su ɓata tsattsarkan wuri da kagararsa. Za su kuma hana yin hadayu na yau da kullum, su kafa abin banƙyama da suke lalatarwa.

32 Waɗanda suka ta da alkawarin kuma, sarki zai ƙara dulmuyar da su ta wurin daɗin bakinsa. Amma waɗanda suka san Allahnsu za su tsaya da ƙarfi su yi wani abu.

33 Waɗansu daga cikin mutane waɗanda suke da hikima, za su wayar da kan mutane da yawa. Amma duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.

34 Sa’ad da suka fāɗi ba za su sami wani taimakon kirki ba, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.

35 Waɗanda suke da hikima, za a kāshe su, don a tsabtace su, a tsarkake su, su yi tsab tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.

36 “Sa’an nan sarki zai yi yadda ya ga dama. Zai ɗaukaka kansa, ya aza ya fi kowane allah. Zai kuma yi maganganu na saɓo a kan Allahn alloli, zai yi nasara, sai lokacin da aka huce haushi, gama abin da aka ƙaddara zai cika.

37 Ba zai kula da gumakan kakanninsa ba, ko begen da mata suke yi. Ba kuwa zai kula da kowane irin gunki ba, domin zai aza kansa ya fi su duka.

38 A maimakon haka zai girmama gunkin kagarai, gunkin da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tamani.

39 Zai tasar wa kagara mafi ƙarfi da taimakon baƙon gunki. Waɗanda suka yarda da shi, zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.

40 “A lokaci na ƙarshe sarkin kudu zai tasar masa, sarkin arewa kuwa zai tunzura, ya tasar masa da karusai da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, ya ci su da yaƙi, ya wuce.

41 Zai shiga kyakkyawar ƙasa ya kashe dubban mutane. Amma ƙasar Edom, da ta Mowab, da yawancin ƙasar Ammonawa za su kuɓuta daga hannunsa.

42 Zai kai wa waɗansu ƙasashe yaƙi, ƙasar Masar kuwa ba za ta kuɓuta ba.

43 Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tamani na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Habasha da yaƙi.

44 Labarin da zai zo masa daga gabas da arewa zai firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, ya karkashe mutane da yawa, ya shafe su.

45 Zai kafa manyan alfarwai na sarauta a tsakanin teku da tsattsarkan dutse. Amma zai mutu ba kuwa wanda zai taimake shi.”

Categories
DAN

DAN 12

Lokaci na Ƙarshe

1 “A wannan lokaci Mika’ilu babban shugaba wanda yake lura da jama’arka zai bayyana. A lokacin za a yi tashin hankali irin wanda ba a taɓa yi ba, tun da aka yi duniya. Amma a lokacin za a ceci jama’arka waɗanda aka rubuta sunayensu cikin littafi.

2 Waɗanda suka rasu za su tashi, waɗansu zuwa rai madawwami, waɗansu kuwa zuwa kunya da madawwamin ƙasƙanci.

3 Waɗanda suke da hikima za su haskaka kamar sararin sama, waɗanda kuma suka juyar da mutane da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin.

4 “Amma kai, Daniyel, sai ka rufe maganar, ka kuma kulle littafin, har zuwa ƙarshen lokaci. Mutane da yawa za su yi ta kai da kawowa, ilimi kuma zai ƙaru.”

5 Sa’an nan ni Daniyel na duba, sai ga waɗansu biyu a tsaye, ɗaya a wannan gāɓa ɗayan kuma a waccan gāɓar kogin.

6 Dayansu ya ce wa mutumin da yake sāye da rigar lilin, wanda yake tsaye a gaɓar kogin, “Sai yaushe waɗannan abubuwan banmamaki za su ƙare?”

7 Sai mutumin da yake sāye da rigar lilin ɗin, wanda yake tsaye a gaɓar kogin ya ɗaga hannuwansa sama, sa’an nan ya rantse da wanda yake rayayye har abada, ya ce, “Za a yi shekara uku da rabi. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa’ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.”

8 Na ji, amma ban gane ba. Sai na ce, “Ya shugabana, mene ne ƙarshen waɗannan abubuwa?”

9 Sai ya ce, “Yi tafiyarka, Daniyel, gama an rufe wannan magana, an kuma kulle ta har ƙarshen lokaci.

10 Mutane da yawa za su tsarkake kansu, su zama masu tsabta tsab tsab, amma mugaye ba za su gane ba, za su yi ta muguntarsu, amma masu hikima za su gane.

11 “Tun daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kafa abin banƙyama, wanda yake lalatarwa, za a yi kwana dubu da ɗari biyu da tasa’in.

12 Masu farin ciki ne waɗanda suka daure, har suka kai ƙarshen kwana dubu da ɗari uku da talatin da biyar.

13 “Ka yi tafiyarka ka huta, a ƙarshen kwanaki za ka tashi ka karɓi naka rabo.”

Categories
YUSH

YUSH 1

Matar Yusha’u wadda Ta Ci Amanarsa da ‘Ya’yanta

1 Ubangiji kuwa ya yi magana da Yusha’u ɗan Beyeri a zamanin mulkin Azariya, da Yotam, da Ahaz, da Hezekiya, sarakunan Yahuza, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yehowash, Sarkin Isra’ila.

2 Sa’ad da Ubangiji ya fara yin magana da Yusha’u ya ce masa, “Tafi ka auro karuwa, ka haifi ‘ya’yan karuwanci, gama ƙasar tana yin fasikanci sosai, wato ta bar bin Ubangiji.”

3 Sai ya tafi ya auri Gomer, ‘yar Diblayim. Ta yi ciki, ta haifi masa ɗa namiji.

4 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka raɗa masa suna, Yezreyel, gama ba da daɗewa ba zan ziyarci gidan Yehu da hukunci saboda jinin da ya zubar a Yezreyel. Zan sa mulkin Isra’ila ya ƙare.

5 A wannan rana zan karya bakan Isra’ila a kwarin Yezreyel.”

6 Gomer ta kuma ɗauki ciki, ta haifi ‘ya mace. Ubangiji kuma ya ce wa Yusha’u, “Ka raɗa mata suna Bajinƙai, gama ba zan ƙara yi wa jama’ar Isra’ila jinƙai ba, har da zan gafarta mata.

7 Amma zan yi wa mutanen Yahuza jinƙai. Ni kaina zan cece su ba da baka ba, ba kuwa da takobi, ko da yaƙi, ka da dawakai, ko da sojojin dawakai ba.”

8 Sa’ad da ta yaye Ba-jinƙai, ta sāke ɗaukar ciki, ta haifi ɗa namiji.

9 Ubangiji kuma ya ce masa, “Ka raɗa masa suna, Ba-mutanena-ba-ne, gama ku ba mutanena ba ne,ni kuma ba Allahnku ba ne.

10 “Duk da haka yawan mutanen Isra’ila

Zai zama kamar yashi a bakin teku,

Wanda ba za a iya aunawa ko ƙidayawa ba.

Maimakon kuma a ce, ‘Ku ba mutanena ba ne,’

Za a ce, ‘Ku mutanen Allah ne mai rai.’

11 Mutanen Yahuza da mutanen Isra’ila za su haɗu su zama ɗaya,

Za su zaɓa wa kansu shugaba ɗaya.

Za su shugabanci ƙasar

Gama ranar Yezreyel babba ce.”

Categories
YUSH

YUSH 2

Ubangiji Yana Ƙaunar Mutanensa Marasa Aminci

1 “Ka ce wa ‘yan’uwanka maza, ‘Ku mutanena ne,’ ka kuma ce wa ‘yar’uwarka, ‘Kin sami jinƙai!’

2 Ku roƙi uwarku,

Gama ita ba matata ba ce,

Ni kuma ba mijinta ba ne.

Ku roƙe ta ta daina karuwancinta,

Ta rabu da masu rungumar mamanta.

3 In ba haka ba, sai in yi mata tsiraici,

In bar ta kamar ran da aka haife ta.

In maishe ta kamar jeji,

In bar ta kamar busasshiyar ƙasa,

In kashe ta da ƙishi.

4 Ba zan yi wa ‘ya’yanta jinƙai ba,

Domin su ‘ya’yan karuwanci ne

5 Gama uwarsu ta yi karuwanci.

Ita wadda ta haife su ta yi abin kunya.

Gama ta ce, ‘Zan bi samarina

Waɗanda suke ba ni ci da sha,

Da ulu, da lilin, da mai, da ruwan inabi.’

6 “Don haka zan shinge hanyarta da ƙaya,

Zan gina mata garu don kada ta sami hanyar fita.

7 Za ta bi samarinta, amma ba za ta tarar da su ba.

Za ta neme su, amma ba za ta same su ba.

Sa’an nan za ta ce, ‘Zan koma wurin mijina na fari,

Gama zamana na dā ya fi na yanzu!’

8 “Amma ba ta sani ni nake ba ta hatsi, da ruwan inabi, da mai,

Da azurfa, da zinariya da yawa

Waɗanda suka bauta wa gunkin nan Ba’al da su ba.

9 Don haka zan hana mata hatsi a kakarsa,

Da ruwan inabi a kakarsa, da kuma ulu da lilin

Waɗanda suka zama abin rufe tsiraicinta.

10 Yanzu zan buɗe tsiraicinta

A idon samarinta,

Ba kuwa wanda zai cece ta daga hannuna.

11 Zan sa ta daina farin cikinta,

Da idodinta, da kiyaye lokatan amaryar wata,

Da hutawar ranar Asabar,

Da ƙayyadaddun idodinta.

12 Zan ɓata inabinta da itatuwan ɓaure

Waɗanda take cewa, ‘Waɗannan su ne hakkina

Wanda samarina suka ba ni.’

Zan sa su zama kurmi,

Namomin jeji su cinye su.

13 Zan hukunta ta saboda kwanakin idodin gunkin nan Ba’al.

A kwanakin nan takan ƙona musu turare,

Ta yi ado da zobe da lu’ulu’ai,

Ta bi samarinta, amma ta manta da ni.”

In ji Ubangiji.

14 “Don haka, ga shi, zan rarrashe ta,

In kai ta cikin jeji,

In ba ta magana.

15 Can zan ba ta gonar inabi,

In mai da kwarin Akor, wato wahala, ƙofar bege.

A can za ta amsa mini kamar a kwanakin ƙuruciyarta,

Kamar lokacin da ta fito daga ƙasar Masar.

16 Ni Ubangiji na ce, a waccan rana

Za ta ce da ni,

‘Mijina,’ ba za ta ƙara ce da ni Ba’al ba.

17 Zan kawar da sunayen Ba’al daga bakinta.

Ba za a ƙara kiransu da sunayensu ba.

18 “A waccan rana zan yi alkawari

Da namomin jeji, da tsuntsaye,

Da abubuwa masu rarrafe saboda Isra’ila.

Zan kuma kakkarya baka da takobi,

In kuma sa yaƙi ya ƙare a ƙasar,

Sa’an nan za su yi zamansu lami lafiya.

19 Zan ɗaura auren da yake cikin adalci,

Da bisa kan ka’ida, da ƙauna.

20 Zan ɗaura auren da yake cikin aminci,

Za ki kuwa sani, ni ne Ubangiji.

21 “A waccan rana, zan amsa wa sammai,

Su kuma za su amsa wa ƙasa.

22 Ƙasa kuma za ta amsa wa hatsi, da ruwan inabi, da mai,

Su ma za su amsa wa Yezreyel.

23 Zan dasa ta a ƙasa domin kaina.

Zan kuma yi wa ‘Ba-jinƙai,’ jinƙai,

In kuma ce wa ‘Ba-mutanena ba,’ ‘Mutanena!’

Su ma za su ce, ‘Kai ne Allahna!’ ”

Categories
YUSH

YUSH 3

Yusha’u da Karuwa

1 Ubangiji kuma ya ce mini, “Ka sāke tafiya, ka ƙaunaci karuwa wadda take tare da kwartonta. Ka ƙaunace ta kamar yadda ni Ubangiji nake ƙaunar mutanen Isra’ila, ko da yake suna bin gumaka, suna ƙaunar wainar zabibi da aka miƙa wa gumaka.”

2 Sai na ba da sadakinta a bakin tsabar azurfa goma sha biyar, da buhu biyu na sha’ir.

3 Sa’an nan na ce mata, “Ki keɓe kanki kwanaki da yawa domina, kada ki yi kwartanci, ki kwana da wani, ni kuma ba zan shiga wurinki ba.”

4 Gama mutanen Isra’ila za su zauna kwanaki da yawa ba sarki, ba shugaba, ba sadaka, ba al’amudi, ba falmaran, ba kan gida.

5 Bayan wannan mutanen Isra’ila za su komo su nemi Ubangiji Allahnsu, da Dawuda, sarkinsu. Da tsoro za su komo zuwa wurin Ubangiji domin alheransa a kwanaki na ƙarshe.

Categories
YUSH

YUSH 4

Ubangiji Ya Soki Mutanen Isra’ila

1 Ya ku mutanen Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji,

Gama Ubangiji yana da shari’a da ku, ku mazaunan ƙasar.

“Gama ba gaskiya, ko ƙauna,

Ko sanin Ubangiji a ƙasar.

2 Akwai rantsuwa, da ƙarya, da kisankai, da sata, da zina,

Da kama-karya, da zub da jini a kai a kai.

3 Saboda haka ƙasar za ta yi makoki,

Dukan waɗanda yake zaune a cikinta za su yi yaushi.

Namomin jeji kuma, da tsuntsaye, da kifaye za su ƙare.

4 “Duk da haka kada wani ya sa wa mutum laifi,

Kada wani kuma ya tsautar.

Da ku nake magana, ku firistoci.

5 Za ku yi tuntuɓe da rana,

Annabi kuma zai yi tuntuɓe tare da kai da dare,

Ni kuwa zan hallaka mahaifiyarku.

6 Mutanena sun lalace saboda jahilci.

Tun da yake sun ƙi ilimi,

Ni ma na ƙi ku da zaman firist ɗina.

Tun da yake kun manta da umarnan Allahnka,

Ni ma zan manta da ‘ya’yanku.

7 “Yawan ƙaruwar firistoci, yawan ƙaruwar zunubi.

Zan sāke darajarsu ta zama kunya.

8 Suna ciyar da kansu da zunubin mutanena,

Suna haɗamar ribar muguntarsu.

9 Kamar yadda mutane suke, haka firistocin suke,

Zan hukunta su saboda al’amuransu,

Zan sāka musu gwargwadon ayyukansu.

10 Za su ci, amma ba za su ƙoshi ba.

Za su yi karuwanci, amma ba za su ƙaru ba.

Gama sun rabu da Ubangiji don su bauta wa gumaka.

11 “Karuwanci, da ruwan inabi,

Da ruwan inabin da bai sa hauka ba sukan kawar da hankali.

12 Mutanena sukan yi tambaya a wurin abin da aka yi da itace,

Sandansu yakan faɗa musu gaiɓu,

Gama ruhun karuwanci ya ɓad da su,

Sun rabu da Allahnsu don su yi karuwanci.

13 Suna miƙa sadaka a bisa ƙwanƙolin duwatsu.

Suna yin hadaya a bisa tuddai,

Da kuma a gindin itacen oak, da aduruku, da katambiri,

Domin suna da inuwa mai kyau.

Don haka ‘ya’yanku mata suke karuwanci,

Surukanku mata suke yin zina.

14 Ba zan hukunta ‘ya’yanku mata sa’ad da suka yi karuwanci ba,

Ko kuwa surukanku mata sa’ad da suka yi zina ba,

Gama mazan da kansu sukan shiga wurin karuwai.

Sukan miƙa sadaka tare da karuwai a Haikali,

Mutane marasa fahimi za su lalace.

15 “Ko da yake mutanen Isra’ila suna karuwanci,

Kada kuma mutanen Yahuza su yi laifi.

Kada ku tafi Gilgal,

Ko ku haura zuwa Bet-awen.

Kada ku yi rantsuwa da cewa,

‘Har da zatin Ubangiji!’

16 Mutanen Isra’ila masu taurinkai ne kamar alfadari.

Ta yaya Ubangiji zai yi kiwonsu

Kamar ‘ya’yan tumaki a makiyaya mai fāɗi?

17 Mutanen Ifraimu sun haɗa kai da gumaka,

Sai a rabu da su.

18 Su taron mashaya ne kawai,

Karuwai ne kuma.

Suna ƙaunar abin kunya.

19 Iska ta ƙunshe su cikin fikafikanta.

Za su ji kunyar bagadansu.”

Categories
YUSH

YUSH 5

Hukunci a kan Riddar Isra’ilawa

1 “Ku ji wannan, ya ku firistoci!

Ku saurara, ya mutanen Isra’ila!

Ku kasa kunne, ya gidan sarki!

Gama za a yi muku hukunci,

Domin kun zama tarko a Mizfa,

Da ragar da aka shimfiɗa a bisa Tabor.

2 Sun tayar, sun yi zurfi cikin zunubi,

Zan hore su duka.

3 Na san Ifraimu, Isra’ila kuma ba a ɓoye take a gare ni ba.

Gama Ifraimu ta yi aikin karuwanci,

Isra’ila kuma ta ƙazantu.

4 “Ayyukansu ba su bar su

Su koma wurin Allahnsu ba,

Gama halin karuwanci yana cikinsu,

Don haka kuma ba su san Ubangiji ba.

5 Girmankan mutanen Isra’ila yana ba da shaida a kansu.

Mutanen Ifraimu za su yi tuntuɓe cikin laifinsu.

Mutanen Yahuza kuma za su yi tuntuɓe tare da su.

6 Da garkunan tumaki da na awaki, da na shanunsu

Za su tafi neman Ubangiji,

Amma ba za su same shi ba,

Gama ya rabu da su.

7 Sun ci amanar Ubangiji.

Su haifi shegu.

Yanzu amaryar wata za ta cinye su da gonakinsu.

Yaƙi tsakanin Mutanen Yahuza da na Isra’ila

8 “Ku busa ƙaho cikin Gibeya,

Ku busa kakaki cikin Rama,

Ku yi gangami cikin Bet-awen,

Ku yi rawar yaƙi, ya ku Biliyaminu!

9 Ifraimu za ta zama kango a ranar hukunci.

A kabilan Isra’ila na sanar da abin da zai faru, ba makawa.

10 “Shugabannin Yahuza sun zama kamar masu cin iyaka,

Zan zubo musu da fushina kamar ruwa.

11 An danne Ifraimu, shari’a ta murƙushe ta,

Domin ta ƙudura ta bi banza.

12 Domin haka na zama kamar asu ga Ifraimu,

Kamar ruɓa ga mutanen Yahuza.

13 “Sa’ad da Ifraimu ta ga ciwonta,

Yahuza kuma ta ga rauninta,

Sai Ifraimu ta aika zuwa Assuriya,

Wurin babban sarki.

Amman ba zai iya warkar da ciwonki, ko rauninki ba.

14 Zan zama kamar zaki ga Ifraimu,

Kamar sagarin zaki ga mutanen Yahuza.

Ni kaina zan yayyage, in yi tafiyata.

Zan ɗauka, in tafi, ba wanda zai yi ceto.

Isra’ila Ta Yi Tuban Muzuru

15 “Zan koma wurin zamana

Sai lokacin da suka yarda sun yi zunubi, su neme ni.

A cikin ƙuncinsu za su neme ni.”

Categories
YUSH

YUSH 6

1 Mutane sun ce, “Zo, mu koma wurin Ubangiji,

Gama shi ne ya yayyaga,

Shi ne kuma zai warkar.

Shi ne ya yi mana rauni,

Shi ne kuma zai ɗaure raunin da maɗauri.

2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu.

A rana ta uku kuwa zai tashe mu

Mu yi zammanmu a gabansa.

3 Mu nace domin mu san Ubangiji

Zuwansa tabbatacce ne kamar wayewar gari.

Zai zo wurinmu kamar ruwan sama,

Kamar ruwan bazara da yake shayar da ƙasa.”

Amsar Ubangiji

4 Ubangiji ya ce, “Me zan yi da ke, ya Ifraimu?

Me zan yi da ke, ya Yahuza?

Ƙaunarku tana kama da ƙāsashi,

Kamar kuma raɓar da take watsewa da wuri.

5 Domin haka na sassare su ta wurin annabawansu,

Na karkashe su da maganar bakina.

Hukuntaina suna kama da hasken da yake ketowa.

6 Gama ƙauna nake so, ba sadaka ba,

Sanin Allah kuma fiye da hadayu na ƙonawa.

7 “Amma sun ta da alkawarina kamar Adamu,

Sun ci amanata.

8 Gileyad gari ne na masu aikata mugunta.

Tana da tabban jini.

9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum,

Haka nan firistoci suka haɗa kansu

Don su yi kisankai a hanyar Shekem,

Ai, sun aikata mugayen abubuwa.

10 Na ga abin banƙyama a cikin Isra’ila,

Karuwancin Ifraimu yana wurin,

Isra’ila ta ƙazantar da kanta.

11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuza, an shirya muku ranar girbi,

A lokacin da zan mayar wa mutanena da dukiyarsu.”

Categories
YUSH

YUSH 7

Zunubin Isra’ila da Tayarwarta

1 “Sa’ad da zan warkar da mutanen Isra’ila,

Sai zunubin Ifraimu da muguntar Samariya su bayyana,

Gama suna cin amana.

Ɓarawo yakan fasa, ya shiga,

‘Yan fashi suna fashi a fili,

2 Amma ba su tunani,

Cewa zan tuna da dukan muguntarsu.

Yanzu ayyukansu sun kewaye su,

Ina ganinsu.

3 “Suna faranta zuciyar sarki da muguntarsu,

Na shugabanni kuma da ƙarairayinsu.

4 Dukansu mazinata ne,

Suna kama da tanda da aka zafafa,

Wadda matoyi ya daina iza mata wuta,

Tun daga lokacin cuɗe kullu

Har zuwa lokacin da yisti ya tasar da shi.

5 A ranar bikin sarki,

Sukan sa sarki da shugabanni su bugu da ruwan inabi.

Yakan yi cuɗanya da shakiyai.

6 Zukatansu suna ƙuna da ƙullaƙulle kamar tanderu.

Fushinsu na ci dare farai,

Da safe fushinsu yana ci bal-bal kamar harshen wuta.

7 “Dukansu suna da zafi kamar tanderu.

Suna kashe masu mulkinsu.

Dukan sarakunansu sun faɗi.

Ba wanda ya kawo mini kuka.”

Ifraimu ta Haɗu da Al’ummai

8 Ubangiji ya ce, “Mutanen Ifraimu sun haɗa kansu da al’ummai,

Sun zama kamar wainar da ba a juya ba.

9 Baƙi sun cinye ƙarfinsu, su kuwa ba su sani ba,

Furfura ta faso musu, amma ba su sani ba.

10 Girmankan mutanen Isra’ila ya kai ƙararsu,

Duk da haka ba wanda ya komo wurin Ubangiji Allahnsu,

Ba su kuwa neme shi ba.

11 Ifraimu kamar kurciya take, marar wayo, marar hankali,

Takan tafi Masar da Assuriya neman taimako.

12 Lokacin da suke tafiya, zan shimfiɗa musu ragata,

Zan saukar da su ƙasa kamar yadda akan yi wa tsuntsun da yake tashi sama.

Zan hukunta su saboda mugayen ayyukansu.

13 “Tasu ta ƙare, gama sun ratse, sun rabu da ni.

Halaka za ta auka musu domin sun tayar mini.

Ko da yake zan cece su, duk da haka suna faɗar karya a kaina.

14 Ba su yi kuka gare ni da zuciya ɗaya ba,

Sa’ad da suke kuka a gadajensu,

Sun tsattsaga jikinsu domin abinci da ruwan inabi.

Sun yi mini tawaye.

15 Ko da yake na horar da su, na ƙarfafa damatsansu,

Duk da haka suna shirya mini maƙarƙashiya.

16 Sun juya mini baya, suna bin gunkin nan Ba’al.

Suna kama da tankwararren baka.

Za a kashe shugabanninsu da takobi

Saboda maganganunsu na fariya.

Za su zama abin ba’a a ƙasar Masar.”

Categories
YUSH

YUSH 8

An Tsauta wa Isra’ila domin Tsafi

1 Ubangiji ya ce, “Ki sa ƙaho a bakinki,

Kamar gaggafa, haka maƙiyi ya kawo sura a kan ƙasar Ubangiji,

Domin mutanena sun ta da alkawarina,

Sun kuma keta dokokina.

2 Sun yi kuka a wurina,

Suna cewa, ‘Ya Allah, mu Isra’ila mun san ka!’

3 Isra’ila ta ƙi abin da yake mai kyau,

Don haka abokan gāba sun fafare ta.

4 “Suna naɗa sarakuna, amma ba da iznina ba.

Suna naɗa shugabanni amma ba da yardata ba.

Suna ƙera gumaka da azurfarsu da zinariyarsu,

Wannan kuwa zai zama sanadin halakarsu.

5 Ya mutanen Samariya, ina ƙin maraƙinku na siffa.

Ina jin haushinsu ƙwarai!

Sai yaushe za su rabu da gumaka?

6 Ai, mai aikin hannu ne ya yi shi a Isra’ila!

Gunki ne ba Allah ba ne.

Za a farfashe siffar maraƙin Samariya.

7 Gama sun shuka iska

Don haka zu su girbe guguwa.

Hatsin da yake tsaye ba shi da zangarniya,

Ba zai yi tsaba ba.

Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci,

8 Isra’ila kamar kowace al’umma ce.

Suna cikin al’ummai

Kamar kaskon da ba shi da amfani,

9 Gama sun haura zuwa Assuriya,

Kamar jakin jeji da yake yawo shi kaɗai.

Mutanen Ifraimu sun yi ijara da abokan tsafinsu.

10 Ko da yake sun yi ijara da abokai daga cikin al’ummai,

Yanzu zan tattara su, in hukunta su.

Sa’an nan za su fara ragowa,

Ta wurin tunanin nawayar Sarkin sarakuna.

11 “Da yake Ilfraimu ta yawaita bagadan zunubi,

Sun zama mata bagadai na yin zunubi.

12 Ko da na rubuta mata dokokina sau da yawo,

Za ta ɗauke su wani baƙon abu ne kawai.

13 Suna jin daɗin miƙa hadayu don cin naman,

Amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu.

Ubangiji zai tuna da muguntarsu,

Zai hukunta su saboda zunubansu.

Za su koma Masar.

14 “Gama mutanen Isra’ila sun manta da Mahaliccinsu,

Sai sun gina manyan gidaje masu daraja.

Mutanen Yahuza kuma sun yawaita biranensu masu garu,

Amma ni Ubangiji, zan aika da wuta a kan biranensu,

Ta ƙone fādodinsu.”