Categories
YUSH

YUSH 9

Hukuncin da Za A Yi wa Isra’ila domin Rashin Aminci

1 Kada ku yi farin cikin, ya mutanen Isra’ila!

Kada ku yi murna kamar sauran mutane!

Gama kun yi karuwanci, kun rabu da Allahnku.

Kuna ƙaunar ijarar karuwanci a kowane masussuka.

2 Masussuka da wurin matsa ruwan inabi ba za su ciyar da su ba.

Sabon ruwan inabi kuma ba zai ishe su ba.

3 Ba za su zauna a ƙasar Ubangiji ba,

Amma mutanen Ifraimu za su koma Masar.

Za su ci haramtaccen abinci a Assuriya.

4 Ba za su yi wa Ubangiji hadaya ta sha ba.

Ba za su faranta zuciyarsa da sadakoki ba.

Abincinsu zai zama irin na masu makoki.

Duk wanda ya ci shi zai haramta.

Gama abincinsu zai yi musu maganin yunwa ne kawai,

Ba za su kai shi Haikalin Ubangiji ba.

5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar idi?

Da a ranar idin Ubangiji?

6 Ga shi kuma, suna tafiya zuwa halaka,

Masar za ta tattara su,

Memfis za ta binne su.

Ƙayayuwa za su mallaki abubuwan tamaninsu na azurfa.

Sarƙaƙƙiya za ta tsiro a cikin alfarwansu.

7 Ranar hukunci ta zo, ranar ramako ta iso,

Isra’ila za ta sani!

An ce annabi wawa ne,

Mutumin da yake da ruhu kuwa mahaukaci ne,

Saboda yawan muguntarku da ƙiyayyarku.

8 Ifraimu mai tsaro ne a gaban Allahna, annabi kuwa,

Duk da haka sun zama kamar mai kafa tarkon kama tsuntsu, a farkon kaka.

Akwai ƙiyayya a cikin Haikalin Allahnsu.

9 Sun yi zurfi cikin rashin gaskiya

Kamar a kwanakin Gibeya,

Ubangiji zai tuna da muguntarsu.

Zai hukunta su saboda zunubansu.

10 Ubangiji ya ce, “Na iske Isra’ila a jeji kamar inabi,

Na ga kakanninku kamar nunan fari na ‘ya’yan ɓaure,

Amma da suka zo Ba’al-feyor, sai suka keɓe kansu ga Ba’al.

Suka zama abin ƙyama kamar abin da suke ƙauna.

11 Darajar Ifraimu za ta tashi kamar tsuntsu,

Ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki!

12 Ko sun goyi ‘ya’ya,

Zan sa su mutu tun ba su balaga ba.

Tasu ta ƙare sa’ad da na rabu da su!”

13 Ya Ubangiji, na ga yadda Ifraimu

Ta mai da ‘ya’yanta ganima

Tana fitar da su zuwa wurin yanka.

14 Ya Ubangiji, me zan ce ka ba su?

Me za ka ba su?

Ka ba su cikin da ba ya haihuwa da busassun mama.

15 Ubangiji ya ce, “Kowace irin muguntarsu tana a Gilgal,

A can na ƙi su!

Saboda mugayen ayyukansu, zan kore su daga ƙasata,

Ba kuma zan ƙaunace su ba.

Dukan shugabanninsu ‘yan tayarwa ne.

16 An ka da mutanen Ifraimu, saiwarsu ta bushe.

Ba za su yi ‘ya’ya ba.

Ko ma sun haihu, zan kashe ‘ya’yan nan nasu waɗanda suke ƙauna.”

17 Allahna zai ƙi su

Domin ba su yi masa biyayya ba.

Za su zama masu yawo cikin al’ummai.

Categories
YUSH

YUSH 10

1 Isra’ila kurangar inabi ce mai bansha’awa

Wadda yake ba da ‘ya’ya da yawa.

Ƙara yawan arzikinsu,

Ƙara gina bagadansu.

Ƙara yawan wadatar ƙasarsu.

Ƙara kyautata ginshiƙansu.

2 Zuciyarsu ta munafunci ce,

Yanzu tilas za su ɗauki hakkin laifinsu,

Ubangiji zai farfashe bagadansu da ginshiƙansu.

3 Gama yanzu za su ce,

“Ba mu da sarki,

Domin ba mu ji tsoron Ubangiji ba.

Amma me sarki zai yi mana?”

4 Surutai kawai suke yi,

Suna yin alkawaran ƙarya,

Don haka hukunci zai zaburo kamar muguwar ciyawa mai dafi a kunyoyin gona.

5 Mazaunan Samariya suna rawar jiki

Domin ɗan maraƙin Bet-awen,

Mutane za su yi makoki dominsa,

Firistoci matsafa, za su yi kururuwa dominsa,

Da kuma darajarsa wadda ta rabu da shi.

6 Za a kai ɗan maraƙin a Assuriya

Don a biya wa sarki haraji.

Za a kunyatar da Ifraimu,

Isra’ila kuwa za ta ji kunya saboda shawararta.

7 Sarakunan Samariya za su ɓace,

Kamar kumfa a bisa ruwa.

8 Za a hallaka masujadan tuddai na Awen inda Isra’ila suke yin zunubi,

Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma a bagadansu.

Za su ce wa manyan duwatsu, “Ku rufe mu!”

Su ce wa tuddai, “Ku faɗo bisa kanmu!”

9 Ubangiji ya ce, “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila!

Tun daga wancan lokaci kuka yi ta ci gaba.

Ashe, yaƙi ba zai tarshe su a Gibeya ba?

10 Zan fāɗa wa waɗannan mutane masu zunubi, in hukunta su.

Za a tattara al’ummai, su yi gāba da su,

Za a hukunta su saboda yawan zunubansu.

11 “Ifraimu horarriyar karsana ce,

Wadda yake jin daɗin yin sussuka,

Amma na sa wa kyakkyawan wuyanta karkiya,

Na sa Yahuza ta ja garmar noma,

Yakubu kuwa za ta ja garmar bajiya.

12 Ku shuka wa kanku adalci,

Ku girbe albarkun ƙauna,

Ku yi kautun saurukanku,

Gama lokacin neman Ubangiji ya yi,

Domin ya zo, ya koya muku adalci.

13 Kun shuka mugunta,

Kun girbe rashin adalci,

Kun ci amfanin ƙarya.

“Da yake dogara ga hanyarku da ɗumbun sojojinku,

14 Domin haka hayaniyar yaƙi za ta tashi a tsakanin jama’arku.

Dukan kagaranku za a hallaka su.

Kamar yadda Shalmanesar ya hallaka Bet-arbel a ranar yaƙi.

An fyaɗa uwaye da ‘ya’yansu a ƙasa.

15 Haka za a yi muku, ya mutanen Betel, saboda yawan muguntarku.

Da asuba za a datse Sarkin Isra’ila.”

Categories
YUSH

YUSH 11

Ƙaunar Allah zuwa ga Mutanensa Masu Tayarwa

1 “A lokacin da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi,

Daga cikin Masar na kirawo ɗana.

2 Yawan kiransu, yawan tayarwar da suke yi mini,

Sai ƙara miƙa wa Ba’al sadaka suke yi,

Suna ƙona turare ga gumaka.

3 Ko da yake ni ne na koya wa Ifraimu tafiya.

Na ɗauke su a hannuna,

Amma ba su sani ni ne na lura da su ba.

4 Na bishe su da linzamin alheri da ragamar ƙauna,

Na zama musu kamar wanda yake ɗauke musu karkiya daga muƙamuƙansu.

Na sunkuya, na ciyar da su.

5 “Ba su koma ƙasar Masar ba,

Amma Assuriya za ta zama sarkinsu

Gama sun ƙi yarda su koma wurina.

6 Takobi zai ragargaje biranensu,

Zai lalatar da sandunan ƙarafan ƙofofinsu,

Zai cinye su domin muguwar shawararsu.

7 Mutanena sun himmantu su rabu da ni,

Ko da yake an kira su ga Ubangiji,

Ba wanda ya girmama shi.

8 “Ƙaƙa zan iya rabuwa da ke, ya Ifraimu?

Ƙaƙa zan miƙa ki, ya Isra’ila?

Ƙaƙa zan maishe ki kamar Adma?

Ƙaƙa zan yi da ke kamar Zeboyim?

Zuciyata tana motsawa a cikina,

Juyayina ya huru.

9 Ba zan aikata fushina mai zafi ba,

Ba zan ƙara hallaka Ifraimu ba,

Gama ni Allah ne, ba mutum ba,

Maitsarki wanda yake tsakiyarku,

Ba zan zo wurinku da hasala ba.

10 “Za su bi Ubangiji,

Zai yi ruri kamar zaki, hakika zai yi ruri

‘Ya’yansa za su zo da rawar jiki da yamma.

11 Da sauri za su zo kamar tsuntsaye daga Masar,

Kamar kurciyoyi daga ƙasar Assuriya,

Zan komar da su gidajensu, ni Ubangiji na faɗa.”

An Tsauta wa Ifraimu domin Ƙarya da Zalunci

12 Ubangiji ya ce, “Ifraimu ta kewaye ni da ƙarairayi,

Jama’ar Isra’ila kuwa ta kewaye ni da munafuncinta,

Yahuza kuma ta tayar wa Allah,

Wato tana gāba da Mai Tsarki, mai aminci.

Categories
YUSH

YUSH 12

1 Ifraimu tana kiwon iska,

Tana ta bin iskar gabas dukan yini.

Tana riɓaɓɓanya ƙarya da kamakarya.

Tana ƙulla yarjejeniya da Assuriya,

Tana kai mai a Masar.”

2 Ubangiji yana da magana game da mutanen Yahuza,

Zai hukunta Isra’ila saboda hanyoyinta,

Zai sāka mata gwargwadon ayyukanta.

3 A cikin mahaifa kakansu Yakubu ya kama diddigen ɗan’uwansa,

Sa’ad da ya zama baligi ya yi kokawa da Allah.

4 Ya yi kokawa da mala’ika ya yi rinjaye.

Ya yi kuka, ya roƙi albarka.

Ya sadu da Allah a Betel,

A can Allah ya yi magana da shi.

5 Ubangiji Allah Mai Runduna,

Sunansa Ubangiji,

6 Sai ku koma wurin Allahnku,

Ku yi alheri, ku yi adalci,

Ku saurari Allahnku kullayaumin.

7 Ubangiji ya ce, “Ɗan kasuwa wanda yake da ma’aunin algus a hannunsa.

Yana jin daɗin yin zalunci.

8 Mutanen Ifraimu sun ce, ‘Hakika, mun zama attajirai,

Mun samar wa kanmu dukiya.

A cikin harkokinmu ba za a sami wata mugunta ba.’

9 Ni ne Ubangiji Allahnku tun daga ƙasar Masar,

Zan kuma sa ku zauna cikin alfarwai,

Kamar lokatan ƙayyadaddun idodi.

10 “Na yi magana da annabawa,

Ni ne na ba da wahayi da yawa,

Da misalai kuma ta wurin annabawa.

11 Idan akwai laifi a Gileyad,

Hakika za su zama wofi.

A Gilgal ana sadaka da bijimai,

Bagadansu za su zama kamar tsibin duwatsu

A gyaffan kunyoyin gona.”

12 Kakanmu Yakubu ya gudu zuwa ƙasar Aram,

A can Isra’ila ya yi barantaka saboda mace,

Saboda mace ya yi kiwon tumaki.

13 Ta wurin annabi Ubangiji ya fito da mutanen Isra’ila daga Masar,

Ta wurin annabi kuma ya kiyaye su.

14 Mutanen Ifraimu sun yi muguwar tsokana mai ta da fushi,

Domin haka Ubangiji zai ɗora musu hakkin jini a kansu,

Zai saka musu cin mutuncin da suka yi.

Categories
YUSH

YUSH 13

Za A Hallaka Ifraimu

1 Sa’ad da Ifraimu ta yi magana, mutane suka yi rawar jiki. An ɗaukaka ta cikin Isra’ila,

Amma ta yi laifi ta wurin bauta gunkin nan Ba’al,

Ta kuwa mutu.

2 Har yanzu suna ta ƙara yin zunubi,

Suna yi wa kansu gumaka na zubi,

Da gwaninta sukan yi gumaka da azurfarsu,

Dukansu aikin hannu ne.

Sukan ce, “Ku miƙa wa waɗannan hadayu!”

Mutane sukan sumbaci siffofin maruƙa.

3 Don haka za su zama kamar ƙāsashin da akan yi da safe,

Ko kuwa kamar raɓa mai kakkaɓewa da wuri.

Za su zama kamar ƙaiƙayi wanda ake shiƙarsa cikin iska a masussuka,

Ko kuwa kamar hayaƙin da yake fita ta bututu.

4 Ubangiji ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku

Tun daga ƙasar Masar.

Banda ni ba ku san wani Allah ba,

Banda ni kuma ba wani mai ceto.

5 Ni ne wanda ya san ku a cikin jeji,

A ƙasar da take da ƙarancin ruwan sama.

6 Sa’ad da suka sami wurin kiwo, suka ƙoshi,

Sai suka yi girmankai,

Suka manta da ni.

7 Zan zama musu kamar zaki,

Kamar damisa zan yi kwanto a gefen hanya.

8 Zan auka musu kamar beyar,

Wadda aka ƙwace mata ‘ya’ya.

Zan yage ƙirjinsu, in cinye su kamar zaki,

Kamar mugun naman jeji zan yayyage su.

9 “Zan hallaka ku, ya mutanen Isra’ila!

Wane ne zai taimake ku?

10 Yanzu ina sarkinku da zai cece ku?

Ina kuma dukan shugabanninku da za su kāre ku?

Su waɗanda kuka roƙa, kun ce, ‘Ku naɗa mana sarki da shugabanni.’

11 Da fushina na naɗa muku sarki,

Da hasalata kuma na tuɓe shi.

12 “An ƙunshe muguntar Ifraimu,

Zunubinsa kuwa an ajiye shi a rumbu.

13 Naƙudar haihuwarsa ta zo,

Amma shi wawan yaro ne,

Bai fito daga mahaifar ba.

14 Zan fanshe su daga ikon lahira.

Zan fanshe su daga mutuwa.

Ya mutuwa, ina annobanki?

Ya kabari, ina halakarka?

Kan kawar da juyayi daga wurina.

15 Ko da yake Isra’ila tana bunƙasa kamar ciyayi,

Iskar gabas, wato iskar da za ta zo daga jeji,

Za ta busar da maɓuɓɓugarsu da idon ruwansu,

Za ta lalatar da abubuwa masu amfani da yake cikin taskarsu.

16 Samariya za ta ɗauki hakkin zunubinta,

Gama ta tayar wa Allahnta.

Za a kashe mutanenta da takobi.

Za a fyaɗa jariranta a ƙasa,

A kuma tsage matanta masu ciki.”

Categories
YUSH

YUSH 14

Ana Roƙon Isra’ila Ta Komo wurin Ubangiji

1 Ya mutanen Isra’ila, ku komo wurin Ubangiji Allahnku,

Gama zunubinku ya sa kun yi tuntuɓe.

2 Ku komo wurin Ubangiji, ku roƙe shi,

Ku ce, “Ka gafarta mana zunubanmu,

Ka karɓe mu saboda alherinka,

Mu kuwa za mu yabe ka da bakinmu.

3 Assuriya ba za ta cece mu ba,

Ba kuwa za mu hau dawakai ba.

Ba za mu kuma ƙara ce da aikin hannuwanmu,

‘Kai ne Allahnmu,’ ba.

A wurinka ne maraya yakan sami jinƙai.”

Ubangiji Ya Yi wa Isra’ila Alkawarin Sabon Rai

4 Ubangiji ya ce, “Zan warkar musu da riddarsu.

Zan kuma ƙaunace su sosai,

Gama fushina zai huce.

5 Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila,

Isra’ila za ta yi fure kamar lili,

Saiwarta za ta shiga kamar itacen al’ul.

6 Tohonta zai buɗo,

Kyanta zai zama kamar itacen zaitun,

Ƙashinta kuwa kamar itacen al’ul na Lebanon.

7 Waɗanda za su komo, za su zauna a inuwarta,

Za su yi noman hatsi da yawa.

Za su yi fure kamar kurangar inabi.

Ƙanshinsu zai zama kamar ruwan inabi na Lebanon.

8 Ya mutanen Ifraimu, me zan yi da gumaka?

Ni ne wanda yake amsa muku, mai lura da ku kuma.

Ni kamar itacen fir ne mai ganyaye kore shar.

Daga gare ni, kuke samun ‘ya’ya.”

9 Duk wanda yake da hikima, bari ya fahimci abubuwan nan.

Duk wanda yake da ganewa, bari ya san abubuwan nan,

Gama hanyoyin Ubangiji masu gaskiya ne,

Masu adalci kuwa za su yi tafiya a cikinsu,

Amma masu zunubi za su yi tuntuɓe a kansu.

Categories
YOW

YOW 1

Ɓarnar Fāra

1 Maganar Ubangiji zuwa ga Yowel, ɗan Fetuwel.

2 Ku dattawa, ku kasa kunne,

Bari kowa da kowa da yake cikin

Yahuza, ya kasa kunne.

Wani abu mai kamar wannan ya taɓa

faruwa a lokacinku,

Ko a lokacin kakanninku?

3 Ku faɗa wa ‘ya’yanku labarinsa,

‘Ya’yanku kuma su faɗa wa

‘ya’yansu,

‘Ya’yansu kuma su faɗa wa tsara

mai zuwa.

4 Abin da ɗango ya bari fara ta ci,

Abin da fara ta bari burduduwa ta

ci.

5 Ku farka, ku yi ta kuka, ku

bugaggu,

Ku yi kuka, ku mashayan ruwan

inabi,

An lalatar da ‘ya’yan inabin

Da ake yin sabon ruwan inabi da su.

6 Rundunar ta aukar wa ƙasarmu,

Tana da ƙarfi, ba ta kuma

ƙidayuwa,

Haƙoranta suna da kaifi kamar na

zaki.

7 Ta lalatar da kurangar inabinmu,

Ta cinye itatuwan ɓaurenmu.

Ta gaigaye ɓawo duka,

Saboda haka rassan sun zama fari

fat.

8 Ya jama’a, ku yi kuka

Kamar yarinyar da take makokin

rasuwar saurayinta.

9 Ba hatsi ko ruwan inabin

Da za a yi hadaya da su cikin

Haikalin.

Firistoci masu miƙa wa Ubangiji

hadaya suna makoki.

10 Ba kome a gonaki,

Ƙasa tana makoki,

Domin an lalatar da hatsin,

‘Ya’yan inabi sun bushe,

Itatuwan zaitun kuma sun yi yaushi.

11 Ya ku manoma, ku yi baƙin ciki,

Ku yi kuka, ku da kuke lura da

gonakin inabi,

Gama alkama, da sha’ir,

Da dukan amfanin gonaki sun

lalace.

12 Kurangar inabi ta bushe,

Itatuwan ɓaure kuma sun yi yaushi,

Rumman, da dabino, da gawasa,

Da dukan itatuwan gonaki sun

bushe.

Murna ta ƙare a wurin mutane.

13 Ya ku firistoci masu miƙa hadayu a

bagaden Ubangiji,

Ku sa tufafin makoki, ku yi kuka!

Ku shiga Haikali, ku kwana,

Kuna saye da tufafin makoki,

Gama ba hatsi ko ruwan inabi da za

a yi hadaya da su,

A cikin Haikalin Allahnku.

14 Ku sa a yi azumi,

Ku kira muhimmin taro.

Ku tara dattawa da dukan mutanen

ƙasar

A Haikalin Ubangiji Allahnku,

Ku yi kuka ga Ubangiji.

15 Taku ta ƙare a wannan rana!

Gama ranar Ubangiji ta kusa,

Halaka daga wurin Maɗaukaki ta zo.

16 An lalatar da amfanin gonaki a kan

idonmu,

Ba murna a Haikalin Allahnmu.

17 Itatuwa sun mutu a busasshiyar

ƙasa,

Ba hatsin da za a adana a rumbu,

Rumbuna sun lalace domin ba hatsi.

18 Dabbobi suna nishi!

Garkunan shanu sun ruɗe

Domin ba su da makiyaya.

Garkunan tumaki da awaki kuma

suna shan azaba.

19 Ina kuka a gare ka, ya Ubangiji,

Domin ciyayi da itatuwa sun bushe,

Sai ka ce wuta ce ta ƙone su.

20 Har ma namomin jeji suna kuka a

gare ka,

Domin rafuffuka sun bushe,

Ciyayi kuma sun bushe,

Sai ka ce wuta ce ta ƙone su.

Categories
YOW

YOW 2

Fāra ta Zama Musu Alamar Ranar Ubangiji

1 Ku busa ƙaho, ku yi gangami,

A cikin Sihiyona, tsattsarkan

dutsen Allah!

Duk mutanen ƙasar za su yi rawar

jiki,

Domin ranar Ubangiji tana zuwa, ta

yi kusa.

2 Za ta zama rana ce mai duhu

dulum,

Ranar gizagizai ce baƙi ƙirin.

Runduna mai ƙarfi tana tasowa,

Kamar ketowar hasken safiya bisa

tsaunuka.

Faufau ba a taɓa ganin irinta ba,

Ba kuwa za a sāke ganin irinta ba.

3 Tana cinye shuke-shuke kamar wuta,

Ƙasa kamar gonar Adnin take kafin

ta zo,

Amma a bayanta ta zama hamada,

Ba abin da ya tsere mata.

4 Kamar doki take,

Tana gudu kamar dokin yaƙi.

5 Motsin tsallenta a kan duwatsu

kamar Motsin karusa ne.

Kamar kuma amon wutar da take cin

tattaka.

Kamar runduna mai ƙarfi wadda ta

ja dāgar yaƙi.

6 Da zuwanta mutane sukan firgita,

Dukan fuskoki sukan ɓaci.

7 Takan auka kamar mayaƙa,

Takan hau garu kamar sojoji,

Takan yi tafiya,

Kowa ta miƙe sosai inda ta sa

gaba,

Ba ta kaucewa.

8 Ba ta hawan hanyar juna,

Kowa tana bin hanyarta.

Takan kutsa cikin abokan gāba, ba a

iya tsai da ita.

9 Takan ruga cikin birni,

Takan hau garu a guje,

Takan hau gidaje,

Takan shiga ta tagogi kamar ɓarawo.

10 Duniya takan girgiza saboda ita,

Sammai sukan yi rawar jiki.

Rana da wata sukan duhunta,

Taurari kuwa sukan daina

haskakawa.

11 Ubangiji yakan umarci rundunarsa,

Rundunarsa mai cika umarninsa

babba ce, mai ƙarfi,

Gama ranar Ubangiji babba ce mai

banrazana.

Wa zai iya daurewa da ita?

Jinƙan Ubangiji

12 “Koyanzu,” in ji Ubangiji,

“Ku juyo wurina da zuciya ɗaya,

Da azumi, da kuka, da makoki,

13 Ku kyakkece zuciyarku, ba tufafinku

kaɗai ba.”

Ku komo wurin Ubangiji Allahnku.

Gama shi mai alheri ne, mai jinƙai,

Mai jinkirin fushi ne, mai yawan

ƙauna,

Yakan tsai da hukunci.

14 Wa ya sani ko Ubangiji Allahnmu zai

sāke nufinsa,

Ya sa mana albarka,

Har mu miƙa masa hadaya ta gari da

ta sha?

15 Ku busa ƙaho a Sihiyona,

Ku sa a yi azumi,

Ku kira muhimmin taro.

16 Ku tattara jama’a wuri ɗaya,

Ku tsarkake taron jama’a,

Ku tattara dattawa da yara,

Har da jarirai masu shan mama.

Ku sa ango ya fito daga cikin

turakarsa,

Amarya kuma ta fito daga cikin

ɗakinta.

17 Sai firistoci masu hidimar Ubangiji,

Su yi kuka a tsakanin shirayi da

bagade,

Su ce, “Ya Ubangiji, ka ceci

jama’arka,

Kada ka bar gādonka ya zama abin

zargi

Da abin ba’a a tsakiyar al’ummai.

Don kada al’ummai su ce,

‘Ina Allahnsu?’ ”

18 Sai Ubangiji ya ji kishin ƙasarsa,

Ya kuma ji ƙan mutanensa.

19 Sa’an nan ya ce musu,

“Ga shi, zan ba ku hatsi da ruwan

inabi, da mai,

Za ku ƙoshi.

Ba zan sa ku ƙara zama abin zargi ga

al’ummai ba.

20 Zan kawar muku da waɗanda suka

zo daga arewa,

Zan kori waɗansunsu zuwa cikin

hamada.

Zan kori sahunsu na gaba zuwa cikin

Tekun Gishiri,

Zan kori sahunsu na baya, zuwa

cikin Bahar Rum.

Gawawwakinsu za su yi ɗoyi.

Zan yi musu haka saboda dukan abin

da suka yi muku.”

21 Kada ki ji tsoro, ya ƙasa,

Ki yi farin ciki, ki yi murna,

Gama Ubangiji ne ya yi waɗannan

manyan al’amura.

22 Kada ku ji tsoro, ku dabbobin

saura,

Gama wuraren kiwo a jeji sun yi kore

shar.

Itatuwa suna ta yin ‘ya’ya,

Itacen ɓaure da kurangar inabi suna

ta yin ‘ya’ya sosai.

23 Ya ku mutanen Sihiyona, ku yi

murna,

Ku yi farin ciki da Ubangiji

Allahnku,

Gama ya ba ku ruwan farko

Domin shaidar gafarar da ya yi

muku,

Ya kwararo muku da ruwan farko da

na ƙarshe da yawa kamar dā.

24 Masussukai za su cika da hatsi,

Wuraren matse ruwan inabi za su

malala da ruwan inabi.

25 “Zan mayar muku da abin da kuka

yi hasararsa

A shekarun da fara ta cinye

amfaninku,

Wato ɗango da fara mai gaigayewa,

da mai cinyewa,

Su ne babbar rundunata wadda na

aiko muku.

26 Yanzu za ku ci abinci a wadace ku

ƙoshi,

Za ku yabi sunan Ubangiji

Allahnku,

Wanda ya yi muku abubuwa masu

banmamaki,

Ba kuma za a ƙara kunyatar da

mutanena ba.

27 Ku mutanen Isra’ila, za ku sani ina

cikinku,

Ni ne kuwa Ubangiji Allahnku, ba

wani kuma,

Ba kuma za a ƙara kunyatar da

mutanena ba.”

Za a Ba da Ruhun Allah

28 “Bayan wannan zan zubo Ruhuna a

kan jama’a duka,

‘Ya’yanku mata da maza za su iyar

da saƙona,

Tsofaffinku kuwa za su yi mafarkai,

Samarinku za su ga wahayi da yawa.

29 A lokacin zan zubo Ruhuna,

Har a kan barori mata da maza.

30 “Zan yi faɗakarwa a kan wannan

rana

A sararin sama da a duniya.

Za a ga jini, da wuta, da murtukewar

hayaƙi,

31 Rana za ta duhunta,

Wata zai zama ja wur kamar jini,

Kafin isowar babbar ranan nan mai

bantsoro ta Ubangiji.

32 Amma dukan waɗanda suka nemi

Ubangiji za su tsira.

Kamar yadda Ubangiji ya ce,

Akwai waɗanda suke a Dutsen

Sihiyona da Urushalima

Da za su tsira,

Waɗannan da Ubangiji ya zaɓa za su

tsira.”

Categories
YOW

YOW 3

Shari’ar Al’ummai

1 “A wannan lokaci zan mayar wa

Yahuza da Urushalima da

wadatarsu.

2 Zan tattara dukan al’ummai,

In kai su kwarin Yehoshafat.

A can zan yi musu shari’a

A kan dukan abin da suka yi wa

jama’ata.

Sun warwatsa Isra’ilawa a sauran

ƙasashe,

Suka rarraba ƙasata.

3 Sun jefa kuri’a a kan mutanena,

Sun sayar da yara, mata da maza,

zuwa bauta

Don su biya karuwai da ruwan

inabi.

4 “Taya da Sidon, da dukan Filistiya, me kuke so ku yi mini? Kuna ƙoƙari ku rama mini saboda wani abu? Idan haka ne, zan rama muku da gaggawa.

5 Kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe taskata, kun kai cikin haikalinku.

6 Kun kwashe mutanen Yahuza da Urushalima, kun kai su nesa da ƙasarsu, sa’an nan kun sayar da su ga Helenawa.

7 Yanzu zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, zan yi muku abin da kuka yi musu.

8 Zan sa a sayar wa mutanen Yahuza ‘ya’yanku mata da maza, su kuma za su sayar da su ga Sabiyawa, can nesa. Ni Ubangiji na faɗa.”

9 Ku sanar wa al’ummai da wannan,

Su yi shirin yaƙi,

Su kira mayaƙa!

Su tattaro sojoji, su zo!

10 Su bubbuge allunan garmunansu,

Su yi takuba da su.

Su ƙera māsu da wuƙaƙen da ake

yi wa itatuwa aski.

Sai marar ƙarfi ya ce, “Ni jarumi

ne!”

11 Su gaggauta, su zo su al’ummai da

suke kewaye,

Su tattaru a kwarin.

“Ya Ubangiji, ka saukar da

rundunarka mai ƙarfi.”

12 “Sai al’ummai su yi shiri,

Su zo kwarin Yehoshafat,

Gama a can zan zauna in shara’anta

al’umman da suke kewaye,

13 Su sa lauje gama hatsin ya isa girbi.

Su shiga su tattaka,

Gama wurin matsewar ruwan inabi

ya cika.

Manyan randuna sun cika suna

tumbatsa,

Gama muguntarsu da yawa take.”

14 Dubun dubbai suna cikin kwarin da

za a yanke shari’a!

Gama ranar Ubangiji ta kusa zuwa a

kwarin yanke shari’a.

15 Rana da wata sun yi duhu,

Taurari kuma ba su haskakawa.

Ceton Yahuza

16 Ubangiji yana magana da ƙarfi daga

Sihiyona,

Yana tsawa daga Urushalima,

Sammai da duniya sun girgiza.

Amma Ubangiji shi ne mafakar

jama’arsa, Shi ne kagarar mutanen Isra’ila.

17 “Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji

Allahnku,

Wanda yake zaune a Sihiyona, tuduna

tsattsarka.

Urushalima kuma za ta tsarkaka,

Sojojin abokan gāba ba za su ƙara

ratsawa ta cikinta ba.

18 “A wannan lokaci tsaunuka za su rufu

da kurangar inabi,

Tuddai za su cika da shanu,

Dukan rafuffukan Yahuza za su

gudano da ruwa,

Maɓuɓɓuga za ta gudano daga

Haikalin Ubangiji,

Ta shayar da kwarin Shittim.

19 “Masar za ta zama hamada,

Edom kuma za ta zama kufai,

Saboda kama-karya da suka yi wa

mutanen Yahuza,

Saboda sun zubar da jinin marasa

laifi a ƙasarsu,

20 Za a zauna a Yahuza da Urushalima

dukan tsararraki har abada.

21 Zan sāka alhakin jininsu,

Ba zan kuɓutar da mai laifi ba,

Gama Ubangiji yana zaune a Sihiyona.”

Sihiyona.”

Categories
AMOS

AMOS 1

Horon Allah a kan Maƙwabtan Isra’ila

1 Ga zantuttukan Amos, ɗaya daga cikin makiyayan ƙauyen Tekowa. Allah ya bayyana wa Amos wannan saƙo, tun shekara biyu kafin girgizar duniya, a lokacin da Azariya yake sarautar Yahuza, Yerobowam ɗan Yehowash kuwa yake sarautar Isra’ila.

2 Amos ya ce,

“Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona,

Muryarsa za ta yi tsawa daga

Urushalima.

Da jin wannan, sai wuraren kiwo za

su bushe,

Ƙwanƙolin Dutsen Karmel, da yake

kore zai yi yaushi.”

Suriya

3 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Dimashƙu sun ci gaba da

yin zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun zalunci mutanen Gileyad da

zalunci mai tsanani.

4 Don haka zan aukar da wuta a kan

fādar Sarkin Suriya.

Za ta ƙone kagarar Ben-hadad,

sarki.

5 Zan ragargaje ƙyamaren ƙofofin

birnin Dimashƙu,

In kawar da masu sarautar Bet-eden

da na kwarin Awen.

Za a kwashe mutanen Suriya ganima

zuwa ƙasar Kir.”

Filistiya

6 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Gaza sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun kwashe al’umma duka, sun

sayar wa mutanen Edom.

7 Saboda haka zan aukar da wuta a

kan garun Gaza ta ƙone kagarar

birnin.

8 Zan kawar da masu sarautar biranen

Ashdod da Ashkelon,

Zan karɓe sandan mulkin Ekron.

Sauran Filistiyawa da suka ragu

kuma,

Za su mutu duka.”

Taya

9 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Taya sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun kwashe mutanen sun kai

ƙasar Edom.

Suka karya yarjejeniyar abuta wadda

suka yi.

10 Saboda haka zan aukar da wuta a

kan garun Taya,

Ta ƙone kagarar birnin.”

Edom

11 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Edom sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun farauci ‘yan’uwansu,

Isra’ilawa,

Suka ƙi su nuna musu jinƙai.

Ba su yarda su huce daga fushinsu

ba.

12 Saboda haka zan aukar da wuta a

kan Teman,

Ta ƙone kagarar Bozara.”

Ammon

13 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Ammon sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don haɗamarsu ta ƙasa,

Suka tsaga mata masu ciki a

Gileyad.

14 Saboda haka zan aukar da wuta a

kan garun Rabba,

Ta ƙone kagarar birnin.

Za a yi kururuwa a ranar yaƙi,

Faɗan kuwa zai yi rugugi kamar

hadiri.

15 Sarkinsu da manyan mutanensu za a

kai su wata ƙasa dabam.”