Categories
NAH

NAH 1

Fushin Ubangiji a kan Nineba

1 Jawabi a kan Nineba ke nan, a littafin wahayin Nahum na Elkosh.

2 Ubangiji Allah mai kishi ne, mai

sakayya,

Ubangiji mai sakayya ne, mai

hasala.

Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan

maƙiyansa.

Yana tanada wa maƙiyansa fushi.

3 Ubangiji mai jinkirin fushi ne,

Mai Iko Dukka.

Ubangiji ba zai kuɓutar da mai laifi

ba.

Hanyarsa tana cikin guguwa da cikin

hadiri,

Gizagizai su ne ƙurar ƙafafunsa.

4 Yakan tsauta wa teku, sai teku ta

ƙafe.

Yakan busar da koguna duka.

Bashan da Karmel sukan bushe,

Tohon Lebanon yakan yanƙwane.

5 Duwatsu sukan girgiza a gabansa,

Tuddai kuma su narke.

Duniya ta murtsuke a gabansa,

Da dukan mazauna a cikinta.

6 Wa zai iya tsaya wa fushinsa?

Wa kuma zai iya daurewa da

hasalarsa?

Yana zuba hasalarsa mai kama da

wuta,

Duwatsu sukan farfasu a gabansa.

7 Ubangiji mai alheri ne,

Shi mafaka ne a ranar wahala.

Ya san waɗanda suke fakewa a gare

shi.

8 Zai shafe maƙiyansa da ambaliyar

ruwa,

Zai kuma runtumi maƙiyansa zuwa

cikin duhu.

9 Me kuke ƙullawa game da Ubangiji?

Ubangiji zai wofintar da abin nan da

kuke ƙullawa,

Sau ɗaya kawai zai hallaka ku.

10 Suna maye da abin shansu,

Za su ƙone kamar sarƙaƙƙiyar ƙaya,

Da busasshiyar ciyawa.

11 Daga cikinki wani ya fito,

Wanda ya ƙulla wa Ubangiji

makirci,

Ya ƙulla shawara marar amfani.

12 Ni Ubangiji na ce,

“Ko da yake suna da ƙarfi, suna

kuma da yawa,

Za a datse su, su ƙare.

Ko da yake na wahalar da kai,

Ba zan ƙara wahalar da kai ba.

13 Yanzu zan karya karkiyarsa daga

wuyanka,

Zan kuma tsinke sarƙarta.”

14 Ubangiji ya riga ya yi umarni a

kanka cewa,

“Sunanka ba zai ci gaba ba,

Zan farfashe sassaƙaƙƙun siffofi

Da siffofi na zubi daga gidan

gumakanka.

Zan shirya maka kabari, gama kai

rainanne ne.”

Labarin Fāɗuwar Nineba

15 Duba a kan duwatsu, ƙafafun

wanda yake kawo albishir,

Wanda yake shelar salama!

Ya Yahuza, ka yi bikin idodinka,

Ka kuma cika wa’adodinka.

Gama mugun ba zai sāke zuwa ya yi

gāba da kai ba,

An datse shi ƙaƙaf.

Categories
NAH

NAH 2

1 Wanda yake farfashewa ya auko

maka,

Sai ka sa mutane a kagara, a yi

tsaron hanya,

Ka yi ɗamara, ka tattaro ƙarfinka

duka.

2 Gama Ubangiji zai mayar wa

Yakubu da darajarsa kamar ta

Isra’ila.

Ko da masu washewa sun washe su,

Sun kuma lalatar da rassan inabinsu.

3 Garkuwoyin jarumawansa jajaye ne,

Sojojinsa kuma suna saye da mulufi.

Da ya shirya tafiya,

Karusai suna walƙiya kamar

harshen wuta,

Ana kaɗa mashi da bantsoro.

4 Karusai sun zabura a tituna a

haukace.

Suna kai da kawowa a dandali,

Suna walwal kamar jiniya,

Suna sheƙawa a guje kamar

walƙiya.

5 Sai aka kira shugabanni,

Suka zo a guje suna tuntuɓe,

Suka gaggauta zuwa garu,

Suka kafa kagara.

6 An buɗe ƙofofin kogi,

Fāda ta rikice.

7 An tsiraita sarauniya, an tafi da ita,

‘Yan matanta suna makoki, suna

kuka kamar kurciyoyi,

Suna bugun ƙirjinsu.

8 Nineba tana kama da tafki wanda

ruwansa yake zurarewa,

Suna cewa, “Tsaya, tsaya,”

Amma ba wanda ya waiga.

9 A washe azurfa!

A washe zinariya!

Dukiyar ba ta da adadi,

Akwai dukiya ta kowane iri.

10 Nineba ta halaka! ta lalace, ta zama

kufai!

Zukata sun narke, gwiwoyi suna

kaɗuwa!

Kwankwaso yana ciwo,

Fuskoki duka sun kwantsare!

11 Ina kogon nan na zakoki,

Inda aka ciyar da ‘ya’yan zaki,

Inda zaki da zakanya da

kwiyakwiyansu sukan tafi,

Su tsere daga fitina?

12 Zaki ya kashe abin da ya ishi

kwiyakwiyansa.

Ya kaso wa zakanyarsa abin da ya

ishe ta.

Ya cika kogonsa da ganima.

Ragargajewar Nineba

13 “Ga shi, ina gāba da ke. Ni Ubangiji

Allah Mai Runduna na faɗa.

Zan ƙone karusanki,

Takobi kuwa zai karkashe sagarun

zakokinki,

Zan hana miki ganima a duniya.

Ba za a ƙara jin muryoyin jakadunki

ba.”

Categories
NAH

NAH 3

1 Kaiton birnin jini,

Wanda yake cike da ƙarairayi da

ganima,

Da waso kuma ba iyaka!

2 Ku ji amon bulala da kwaramniyar

ƙafafu,

Da sukuwar doki da girgizar karusai!

3 Sojojin dawakai suna kai sura,

Takuba suna walƙiya, māsu suna

ƙyalƙyali.

Ga ɗumbun kisassu, da tsibin

gawawwaki,

Matattu ba su ƙidayuwa,

Suna tuntuɓe a kan gawawwaki!

4 Ya faru saboda yawan karuwancin

Nineba kyakkyawa mai daɗin

baki,

Wadda ta ɓad da al’umman duniya

da karuwancinta,

Ta kuma ɓad da mutane da daɗin

bakinta.

5 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ina

gāba da ke,

Zan kware fatarinki a idonki,

Zan sa al’ummai da mulkoki su dubi

tsiraicinki.

6 Zan watsa miki ƙazanta,

In yi miki wulakanci,

In maishe ki abin raini.

7 Dukan waɗanda za su dube ki

Za su ja da baya su ce,

‘Nineba ta lalace, wa zai yi kuka

dominta?’

A ina zan samo miki waɗanda za su

ta’azantar da ke?”

8 Kin fi No ne?

Wadda take a bakin Nilu,

Wadda ruwa ya kewaye ta?

Teku ce kagararta.

Ruwa ne kuma garunta.

9 Habasha da Masar su ne ƙarfinta

marar iyaka,

Fut da Libiya su ne kuma

mataimakanta.

10 Duk da haka an tafi da ita, an kai ta

cikin bauta.

An fyaɗa ƙanananta a ƙasa,

An yi kacakaca da su a kowace

mararraba.

An jefa kuri’a a kan manyan

mutanenta,

Aka ɗaure dukan manyan mutanenta

da sarƙoƙi.

11 Ke Nineba kuma za ki bugu,

Za a ɓoye ki.

Za ki nemi mafaka a wurin maƙiyinki.

12 Dukan kagaranki suna kama da

itatuwan ɓaure,

Waɗanda ‘ya’yansu suka harba.

Da an girgiza sai su faɗo a bakin mai

sha.

13 Sojojinki kamar mata suke a

tsakiyarki!

An buɗe wa maƙiyanki ƙofofin

ƙasarki.

Wuta za ta cinye madogaran

ƙofofinki.

14 Ki tanada ruwa domin za a kewaye

ki da yaƙi!

Ki ƙara ƙarfin kagaranki!

Ki tafi kududdufi, ki kwaɓa laka!

Ki ɗauki abin yin tubali!

15 A can wuta za ta cinye ki,

Takobi zai sare ki,

Zai cinye ki kamar fara.

Ki riɓaɓɓanya kamar fara.

Ki kuma riɓaɓɓanya kamar ɗango.

16 Kin yawaita ‘yan kasuwanki suna da

yawa fiye da taurari,

Amma sun tafi kamar fara waɗanda

sukan buɗe fikafikansu su tashi, su

tafi.

17 Shugabanninki kamar ɗango suke,

Manyan mutanenki kamar

cincirindon fāra ne,

Suna zaune a kan shinge a kwanakin

sanyi,

Sa’ad da rana ta fito, sukan tashi su

tafi,

Ba wanda ya san inda suke.

18 Ya Sarkin Assuriya, masu tsaronka

suna barci,

Manyan mutanenka suna

kwankwance,

Mutanenka sun watse cikin

duwatsu,

Ba wanda zai tattaro su.

19 Ba abin da zai rage zafin rauninka,

Rauninka ba ya warkuwa.

Duk wanda ya ji labarinka, zai tafa

hannuwansa

Gama wane ne ba ka musguna wa

ba?

Categories
HAB

HAB 1

Damuwar Habakuk a kan Rashin Gaskiya

1 Jawabin da annabi Habakuk ya hurta ke nan.

2 Ya Ubangiji, ina ta kukan neman taimako,

Amma ka ƙi ji, sai yaushe za ka ji?

Ina kuka a gare ka saboda zalunci,

Amma ba ka yi taimako ba.

3 Me ya sa ka sa ni in ga mugunta,

In kuma dubi wahala?

Hallaka da zalunci suna a gabana.

Jayayya da gardama sun tashi.

4 Ba a bin doka,

Shari’a kuma ba ta aiki.

Mugaye sun fi adalai yawa nesa,

Don haka shari’a tana tafe a karkace.

Kaldiyawa Za Su Hori Yahuza

5 Ubangiji ya ce,

“Ka duba cikin al’umman duniya! Ka gani!

Ka yi al’ajabi! Ka yi mamaki!

Gama zan yi aiki a kwanakinka,

Ko an faɗa maka ba za ka gaskata ba.

6 Ga shi, ina tā da Kaldiyawa,

Al’umman nan mai zafi, mai fitina,

Waɗanda suke tafiya ko’ina a duniya,

Sun ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.

7 Suna da bantsoro da firgitarwa.

Adalcinsu da ikonsu sun danganta ga yadda suke so.

8 “Dawakansu sun fi damisa sauri,

Sun fi kyarketan maraice zafin hali,

Sojojin dawakansu suna zuwa a guje.

Sojojin dawakansu suna zuwa daga nesa,

Sukan tashi kamar gaggafa da sauri don su cinye.

9 “Sun zo don su yi kama-karya.

Ana jin tsoronsu tun ma kafin su zo.

Sun tattara bayi kamar yashi.

10 Sukan yi wa sarakuna ba’a,

Sukan mai da masu mulki abin wasa.

Kowace kagara abin dariya ce a wurinsu,

Sukan tsiba ƙasa, su hau, su cinye ta.

11 Sukan wuce da sauri kamar iska,

Su yi tafiyarsu.

Su masu laifi ne,

Ƙarfinsu shi ne gunkinsu.”

Habakuk Ya Ƙara Kuka ga Ubangiji

12 Ba kai ne madawwami ba?

Ya Ubangiji Allahna Mai Tsarki.

Ba za mu mutu ba.

Ya Ubangiji, kai ne ka sa su su yi hukunci,

Ya dutse, kai ne ka kafa su don su yi horo.

13 Kai mai tsarki ne,

Ka fi ƙarfin ka dubi mugunta.

Kai da ba ka duban laifi.

Me ya sa kake duban marasa imani?

Kana iya shiru sa’ad da mugu yake haɗiye

Mutumin da ya fi shi adalci?

14 Gama ka mai da mutane kamar kifaye a cikin teku,

Kamar abubuwa masu rarrafe da ba su da shugaba.

15 Kaldiyawa sukan kama mutane da ƙugiya,

Sukan jawo su waje da tarunsa,

Sa’an nan su tara su cikin ragarsu,

Su yi murna da farin ciki.

16 Domin haka sukan miƙa hadaya ga tarunsa,

Su ƙona turare ga ragarsu,

Domin su ne suka jawo musu wadata, da abinci mai yawa.

17 Za su ci gaba da juye tarunsa ke nan?

Su yi ta karkashe al’umman duniya ba tausayi?

Categories
HAB

HAB 2

Ubangiji Ya Amsa wa Habakuk

1 Zan tsaya a wurin tsayawata,

In zauna kuma a kan hasumiya,

In jira in ji abin da zai ce mini,

Da abin da zai amsa a kan kukata.

2 Sai Ubangiji ya ce mini,

“Ka rubuta wahayin da kyau a kan alluna,

Yadda kowa zai karanta shi a sawwaƙe.

3 Gama har yanzu wahayin yana jiran lokacinsa,

Yana gaggautawa zuwa cikarsa,

Ba zai zama ƙarya ba.

Ka jira shi, ko da ka ga kamar yana jinkiri,

Hakika zai zo, ba zai makara ba.

4 Wanda zuciyarsa ba daidai take ba, zai fāɗi,

Amma adali zai rayu bisa ga bangaskiyarsa.

5 “Ruwan inabi kuma yana yaudarar mai fariya,

Don haka ba ya zama a gida.

Haɗamarsa tana da fāɗi kamar Lahira,

Kamar kuma mutuwa yake, ba ya ƙoshi.

Ya tattara wa kansa al’ummai duka,

Ya kwaso wa kansa mutane duka.”

Marasa Adalci, Tasu ta Ƙare

6 “Ai, waɗannan duka za su yi ta yi masa zambo,

Su yi masa dariya ta raini,

Su ce, ‘Tasa ta ƙare, shi wanda ya tattara abin da ba nasa ba,

Har yaushe zai riƙa arzuta kansa ta hanyar ba da rance?’

7 Mabartanka za su tasar maka nan da nan,

Waɗanda suke binka bashi za su farka.

Za ka zama ganima a gare su.

8 Saboda ka washe al’umman duniya da yawa,

Sauran mutanen duniya duka za su washe ka,

Saboda jinin mutane, da wulakancin da ka yi wa duniya,

Da birane, da mazauna a cikinsu.

9 “Tasa ta ƙare, shi wanda ya arzuta gidansa da ƙazamar riba,

Ya kuma gina gidansa a bisa don ya tsere wa masifa!

10 Ka jawo wa gidanka kunya,

Saboda ka karkashe mutane da yawa,

Ka hallaka kanka da kanka.

11 Dutse zai yi kuka daga garu,

Katako kuwa zai amsa masa daga aikin da aka yi da itace.

12 “Tasa ta ƙare, shi wanda ya gina gari da jini,

Ya kuma kafa birni da mugunta!

13 Ba Ubangiji Mai Runduna ne ya sa mutanen duniya, su yi wahala, wuta ta cinye ba?

Sun kuma gajiyar da kansu a banza?

14 Duniya za ta cika da sanin ɗaukakar Ubangiji,

Kamar yadda ruwa ya cika teku.

15 “Taka ta ƙare, kai wanda yake sa maƙwabtanka su sha,

Kana zuba musu dafinka har su bugu,

Don ka dubi tsiraicinsu!

16 A maimakon daraja, za ka sha ƙasƙanci.

Ka sha kai da kanka, ka yi tangaɗi.

Ƙoƙon da yake a hannun Ubangiji zai faɗo a kanka,

Kunya za ta rufe darajarka.

17 Ɓarnar da aka yi wa Lebanon za ta komo kanka,

Ka kashe dabbobinta, yanzu dabbobi za su tsorata ka,

Saboda jinin mutanen da ka zubar,

Da wulakancin da ka yi wa duniya,

Da birane, da mazauna a cikinsu.

18 “Ina amfanin gunki sa’ad da mai yinsa ya siffata shi?

Shi siffa ne da aka yi da ƙarfe, mai koyar da ƙarya.

Gama mai yinsa yakan dogara ga abin da ya siffata,

Sa’ad da ya yi bebayen gumaka.

19 Tasa ta ƙare, shi wanda ya ce da abin da aka yi da itace, ‘Farka!’

Ya kuma ce wa dutse wanda ba ya ji, ‘Tashi!’

Wannan zai iya koyarwa?

Ga shi, an dalaye shi da zinariya da azurfa,

Ba ya numfashi ko kaɗan.

20 “Amma Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa,

Bari duniya ta yi tsit a gabansa.”

Categories
HAB

HAB 3

Addu’ar Habakuk

1 Addu’ar nasara wadda annabi Habakuk ya yi.

2 Ya Ubangiji, na ji labarinka,

Sai tsoro ya kama ni.

Ka maimaita manyan ayyukanka a zamaninmu,

Ayyukan da ka saba yi.

Ka yi jinƙai ko lokacin da kake fushi.

3 Daga Edom Allah ya zo,

Daga dutsen Faran Mai Tsarki yake tahowa.

Ɗaukakarsa ta rufe sammai,

Duniya kuwa ta cika da yabonsa.

4 Walƙiyarsa kamar hasken rana ce,

Haske yana haskakawa daga gare shi,

A nan ne ya lulluɓe ikonsa.

5 Annoba tana tafe a gabansa,

Cuta kuma tana bin bayansa kurkusa.

6 Ya tsaya, ya auna duniya,

Ya duba, sai ya girgiza al’umman duniya.

Sa’an nan madawwaman duwatsu suka farfashe,

Madawwaman tuddai kuma suka zama bai ɗaya.

Haka hanyoyinsa suke tun adun adun.

7 Na ga alfarwan Kushan suna cikin azaba,

Labulen ƙasar Madayana suna rawar jiki.

8 Ya Ubangiji, ka hasala da koguna ne?

Ko kuwa ka yi fushi da koguna?

Ko kuwa ka hasala da teku ne,

Sa’ad da ka hau dawakanka, kana bisa karusarka ta nasara?

9 Ka ja bakanka,

Ka rantsar da sandunan horo.

Ka rarratsa duniya da koguna.

10 Duwatsu sun gan ka, sun ƙame,

Ruwaye masu hauka suka gudu.

Zurfi kuma ya ta da muryarsa,

Raƙuman ruwansa sun tashi.

11 Rana da wata sun tsaya cik a inda suke,

A lokacin da kibanka masu haske suke wucewa fyu,

Da lokacin walƙatawar hasken māshinka.

12 Ka ratsa duniya da hasala,

Ka kuma tattake al’umman duniya da fushi.

13 Ka fito saboda ceton mutanenka,

Saboda ceton shafaffenka kuma.

Ka fasa kan mugu,

Ka kware shi daga cinya zuwa wuya.

14 Ka kuje kan mayaƙansa da sandunansa,

Waɗanda suka zo kamar guguwa don su watsar da mu.

Suna murna kamar waɗanda suke zaluntar matalauci a ɓoye.

15 Ka tattake teku da dawakanka,

Da haukan ruwa mai ƙarfi.

16 Sa’ad da na ji, sai jikina ya yi rawa,

Leɓunana suka raurawa.

Ƙasusuwana suka ruɓe, sai na yi rawar jiki.

Zan yi shiru in jira ranar wahala da za ta zo

A kan waɗanda suka kawo mana yaƙi.

17 Ko da yake itacen ɓaure bai yi toho ba,

Ba kuma ‘ya’ya a kurangar inabi,

Zaitun kuma bai ba da amfani ba,

Gonaki ba su ba da abinci ba,

An kuma raba garken tumaki daga cikin garke,

Ba kuma shanu a turaku,

18 Duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji,

Zan yi murna da Allah Mai Cetona.

19 Ubangiji Allah shi ne ƙarfina,

Ya sa ƙafafuna su zama kamar na bareyi,

Ya kuma sa ni in yi tafiya a cikin maɗaukakan wurare.

Categories
ZAF

ZAF 1

Ranar Hasalar Ubangiji a kan Yahuza

1 Ubangiji ya yi magana da Zafaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon, Sarkin Yahuza.

2 “Ni Ubangiji na ce, zan shafe dukan kome

Da yake a duniya.

3 Zan shafe mutum da dabba,

Zan shafe tsuntsayen sararin sama da kifayen teku,

Zan kuma rushe gumakansu tare da mugaye,

Zan kuma datse ɗan adam daga duniya.

4 “Zan miƙa hannuna gāba da Yahuza

Da dukan mazaunan Urushalima.

A wurin nan zan datse saura waɗanda suke bauta wa Ba’al,

Da kuma sunayen firistocin gumaka tare da firistocina,

5 Da kuma waɗanda suke durƙusa wa rundunan sama a kan bene,

Waɗanda sukan durƙusa, su rantse da Ubangiji,

Duk da haka kuma sai su rantse da Milkom,

6 Da kuma waɗanda suka juya, suka bar bin Ubangiji,

Waɗanda ba su neman Ubangiji, ba su kuma roƙonsa.”

7 Ku yi tsit a gaban Ubangiji Allah!

Gama ranar Ubangiji ta gabato.

Ubangiji ya shirya ranar shari’a,

Ya kuma keɓe waɗanda za su aikata hukuncinsa.

8 “A ranar shari’a, ni Ubangiji zan hukunta shugabanni da hakimai,

Da dukan waɗanda suke bin al’adun ƙasashen waje.

9 A wannan rana zan hukunta duk wanda yake tsalle a bakin ƙofa,

Da waɗanda suke cika gidan maigidansu da zalunci da ha’inci.

10 “Ni Ubangiji na ce, a wannan rana, za a ji kuka a Ƙofar Kifi,

Za a ji kururuwa kuma daga unguwa ta biyu,

Da amon ragargajewa daga kan tuddai.

11 Ku yi kururuwa, ku mazaunan Maktesh,

Gama ‘yan kasuwa sun ƙare,

An kuma datse dukan waɗanda suke awon azurfa.

12 “A lokacin nan,

Zan bincike Urushalima da fitilu,

Zan kuwa hukunta marasa kulawa

Waɗanda suke zaman annashuwa,

Waɗanda suke cewa a zukatansu,

‘Ubangiji ba zai yi alheri ba,

Ba kuma zai yi mugunta ba!’

13 Za a washe dukiyarsu,

Za a kuwa rurrushe gidajensu,

Ko da yake sun gina gidaje, ba za su zauna a ciki ba,

Ko da yake sun dasa inabi, ba za su sha ruwansa ba.”

14 Babbar ranar Ubangiji ta gabato,

Tana gabatowa da sauri.

Ku ji muryar ranar Ubangiji!

Jarumi zai yi kuka mai zafi.

15 Wannan rana ta hasala ce,

Ranar azaba da wahala,

Ranar lalatarwa da hallakarwa,

Ranar duhu baƙi ƙirin,

Ranar gizagizai da baƙin duhu,

16 Ranar busar ƙaho da yin kururuwar yaƙi

Gāba da birane masu garu da hasumiyai masu tsawo.

17 “Zan aukar wa mutane da wahala,

Za su kuwa yi tafiya kamar makafi,

Domin sun yi wa Ubangiji zunubi.

Za a zubar da jininsu kamar ƙura,

Namansu kuwa kamar taroso.”

18 Azurfarsu da zinariyarsu ba za su cece su

A ranar hasalar Ubangiji ba,

A cikin zafin kishinsa

Dukan duniya za ta hallaka.

Zai kawo ƙarshen duniya duka nan da nan.

Categories
ZAF

ZAF 2

Za a Hallaka Al’umman da Suke Kewaye da Su

1 Ya ke al’umma marar kunya, ku tattaru, ku yi taro,

2 Kafin a zartar da umarni,

Kafin a kore ku kamar ƙaiƙayi,

Kafin kuma zafin fushin Ubangiji ya auko muku,

Kafin ranar hasalar Ubangiji ta auko muku.

3 Ku nemi Ubangiji,

Dukanku masu tawali’u na duniya,

Ku waɗanda kuke bin umarninsa.

Ku nemi adalci da tawali’u.

Watakila za a ɓoye ku a ranar hasalar Ubangiji.

4 Za a bar Gaza ba kowa,

Ashkelon za ta zama kufai,

Za a kori mutanen Ashdod da tsakar rana,

Ekron kuwa za a tumɓuke ta.

5 Taku ta ƙare, ku mazaunan gaɓar teku, ke al’ummar Keretiyawa!

Ya Kan’ana, ƙasar Filistiyawa,

Maganar Ubangiji tana gāba da ke,

Za a hallaka ki har ba wanda zai ragu.

6 Gāɓar teku za ta zama makiyaya, da wurin zaman masu kiwo,

Da kuma garakan tumaki.

7 Gaɓar teku za ta zama ta mutanen Yahuza waɗanda suka ragu,

Wurin da za su yi kiwo.

Za su kwanta da maraice a gidajen Ashkelon,

Gama Ubangiji Allahnsu zai kula da su,

Zai kuwa mayar musu da albarkarsu ta dā.

8 “Na ji ba’ar da Mowab ta yi, da zagin Ammonawa,

Yadda suka yi wa mutanena ba’a,

Sun yi alwashi, cewa za su cinye ƙasarsu.

9 Domin haka, ni Ubangiji Mai Runduna Allah na Isra’ila,

Na rantse cewa,

Mowab za ta zama kamar Saduma,

Ammonawa kuma za su zama kamar Gwamrata.

Za su zama ƙasar ƙayayuwa

Da kwazazzaban gishiri marar amfani har abada.

Mutanena waɗanda suka ragu za su washe su, su mallake su.”

10 Wannan shi ne hakkin girmankansu,

Saboda sun raina jama’ar Ubangiji Mai Runduna,

Sun yi musu alfarma.

11 Ubangiji zai tsananta musu,

Zai kawo wa dukan gumakan da yake a duniya yunwa.

Kowane mutum a duniya zai yi masa sujada a inda yake,

Har da ƙasar sauran al’umma.

12 “Ku kuma, Habashawa, za a kashe ku da takobina.”

13 Zai miƙa hannunsa gāba da arewa,

Zai hallaka Assuriya,

Zai mai da Nineba busasshen kufai

Marar amfani kamar hamada.

14 Tumaki za su kwanta a tsakiyarta,

Da kuma kowace irin dabba ta kowace ƙasa.

Mujiya da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta,

Ga muryar kuka a taga.

Ga risɓewa a bakin ƙofa,

Gama za a kware rufin katakan itacen al’ul.

15 Wannan shi ne birnin da yake da harka, mai zaman lafiya,

Wanda yake ce wa kansa, “Ba wani sai ni.”

Ga shi, ya zama kufai,

Wurin zaman dabbobi!

Duk wanda ya wuce ta wurin,

Zai yi tsaki, ya kaɗa kai.

Categories
ZAF

ZAF 3

Zunubin Urushalima da Fansarta

1 Taka ta ƙare, kai mai tayarwa,

Ƙazantaccen birni mai zalunci!

2 Ba ya kasa kunne ga muryar kowa,

Ba ya karɓar horo.

Bai dogara ga Ubangiji ba,

Bai kuma kusaci Allahnsa ba.

3 Shugabanninsa zakoki ne masu ruri,

Alƙalansa kuma kyarketai ne da sukan fito da maraice,

Waɗanda ba su rage kome kafin wayewar gari.

4 Annabawansa sakarkari ne, maciya amana.

Firistocinsa sun ƙazantar da abin da yake mai tsarki.

Sun kuma keta dokoki.

5 Ubangiji wanda yake cikinsa mai adalci ne,

Ba ya kuskure.

Yakan nuna adalcinsa kowace safiya,

Kowace safiya kuwa bai taɓa fāsawa ba.

Amma mugu bai san kunya ba.

6 Ubangiji ya ce,

“Na datse al’umman duniya,

Hasumiyansu sun lalace.

Na kuma lalatar da hanyoyinsu,

Ba mai tafiya a kansu.

An mai da biranensu kufai,

Ba mutumin da yake zaune ciki.

7 Na ce, hakika za ka ji tsorona,

Ka kuma karɓi horo.

Ba za a rushe wurin zamanta ba

Bisa ga hukuncin da na yi mata.

Amma suka ɗokanta su lalatar da ayyukansu.

8 “Domin haka ni Ubangiji na ce,

Ku jira ni zuwa ranar da zan tashi in yi tuhuma.

Gama na ƙudura zan tattara al’umman duniya, da mulkoki,

Don in kwarara musu hasalata

Da zafin fushina,

Gama zafin kishina

Zai ƙone dukan duniya.

9 “Sa’an nan zan sauye harshen mutane da harshe mai tsabta,

Domin dukansu su yi kira ga sunan Ubangiji,

Su kuma bauta masa da zuciya ɗaya.

10 Gama daga hayin kogunan Habasha,

Masu yi mini sujada,

Mutanena da yake warwatse,

Za su kawo mini hadaya.

11 A wannan rana ba za a kunyatar da kai ba,

Saboda tayarwar da ka yi mini ta wurin ayyukanka.

Gama a sa’an nan zan fitar da masu girmankai

Da masu fankama daga cikinka,

Ba za ka ƙara yin alfarma ba

A dutsena tsattsarka.

12 Zan kuwa bar mutane masu tawali’u,

Da masu ladabi a cikinka,

Su kuwa za su nemi mafaka a wurin Ubangiji.

13 Waɗanda suka ragu cikin Isra’ila,

Ba za su aikata mugunta ba,

Ba kuma za su faɗi ƙarya ba,

Gama harshen ƙarya ba zai kasance a bakinsu ba.

Za su yi kiwo, su kwanta,

Ba wanda zai tsorata su.”

Waƙar Murna

14 Ki raira waƙa da ƙarfi, ya ke Sihiyona!

Ki ta da murya, ya Isra’ila!

Ki yi murna, ki yi farin ciki,

Ya ke Urushalima!

15 Ubangiji ya kawar miki da hukuncinsa,

Ya kuma kori abokan gābanki.

Ubangiji Sarkin Isra’ila, yana a tsakiyarki,

Ba za ki ji tsoro ba.

16 A wannan rana za a ce wa Urushalima,

“Kada ki ji tsoro, ke Sihiyona,

Kada ki bar hannuwanki su raunana.

17 Ubangiji Allahnki yana tsakiyarki,

Mayaƙi mai cin nasara ne.

Zai yi murna, ya yi farin ciki da ke.

Zai sabunta ki da ƙaunarsa.

Zai kuma yi murna da ke ta wurin raira waƙa da ƙarfi.

18 Zan tara waɗanda suka yi makoki domin idi,

Waɗanda suke tare da ke,

Wato waɗanda nawayar zaman talala

Ta zamar musu abin zargi.

19 Ga shi kuwa, a wannan lokaci

Zan hukunta masu zaluntarki,

Zan kuma ceci gurgu,

Zan tattara korarru,

Zan mai da kunyarsu ta zama yabo,

Za su yi suna a duniya duka.

20 A wannan lokaci zan komo da ku gida,

In tattara ku wuri ɗaya.

Zan sa ku yi suna,

Ku sami yabo a wurin mutanen duniya duka,

A sa’ad da na mayar muku da arzikinku,

Ni Ubangiji na faɗa.”

Categories
HAG

HAG 1

An Zuga Mutane Su Gina Haikali

1 A rana ta fari ga watan shida a shekara ta biyu ta sarautar sarki Dariyus, Ubangiji ya yi magana da annabi Haggai, cewa ya yi magana da Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, mai mulkin Yahuza, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.

2 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Mutanen nan suna cewa lokaci bai yi ba tukuna da za a sāke gina Haikalin Ubangiji.”

3 Ubangiji kuwa ya yi magana da annabi Haggai ya ce,

4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi wa rufin katako, amma Haikalin nan yana zaman kufai?

5 Yanzu, ni Ubangiji Mai Runduna na ce, ku lura da al’amuranku!

6 Kun yi shuka da yawa, kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha ruwa, amma bai kashe muku ƙishi ba. Kun sa tufafi, amma ba wanda ya ji ɗumi. Wanda yake karɓar albashi kuwa, sai ka ce yana sawa a huɗajjen aljihu.”

7 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ku lura da al’amuranku!

8 Ku haura zuwa kan tuddai, ku kawo itace don ku gina Haikalina, in ji daɗinsa, a kuma ɗaukaka ni.

9 “Kun sa zuciya za ku sami da yawa, sai kuka sami kaɗan. Sa’ad da kuma kuka kawo shi gida, sai na hurar da shi. Me ya sa haka? Saboda Haikalina da yake zaman kufai, amma ko wannenku yana fama da ginin gidansa.

10 Domin haka sama ta ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.

11 Na kawo fari a kan ƙasa, da kan tuddai, da kan hatsi, da kan ‘ya’yan inabi, da kan ‘ya’yan zaitun, da kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da kan mutane, da kan dabbobi, da kan ayyukansu.”

12 Zarubabel ɗan Sheyaltiyel kuwa, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da dukan sauran mutane, suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu, suka kuma yi biyayya da maganar annabi Haggai, kamar yadda Ubangiji Allahnsu ya faɗa masa. Mutane kuwa suka yi tsoron Ubangiji.

13 Sai Haggai, manzon Ubangiji, ya faɗa wa mutane maganar Ubangiji, ya ce, “Ubangiji ya ce, ‘Ni Ubangiji ina tare da ku.’ ”

14 Ubangiji kuwa ya zuga zuciyar Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, mai mulkin Yahuza, da zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da zuciyar dukan sauran mutane. Suka zo, suka fara aikin Haikalin Ubangiji Allahnsu Mai Runduna

15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida a shekara ta biyu ta sarautar Dariyus.