Categories
MAR

MAR 4

Misali da Mai Shuka

1 Ya kuma fara koyarwa a bakin teku ke nan, sai babban taro ya haɗu a wurinsa, har ya kai shi ga shiga jirgi a tekun, ya kuwa zauna a ciki. Duk taron kuwa na kan tudu a bakin tekun.

2 Sai ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A cikin koyarwa tasa har ya ce musu,

3 “Ku saurara! Wani mai shuka ya tafi shuka.

4 Yana cikin yafa iri, sai waɗansu ƙwayoyi suka faɗa a hanya, tsuntsaye kuma suka zo suka tsince su.

5 Waɗansu kuma suka faɗa a wuri mai duwatsu inda ba ƙasa da yawa. Nan da nan kuwa suka tsiro saboda rashin zurfin ƙasa.

6 Da rana fa ta ɗaga, sai suka yanƙwane, da yake ba su da saiwa sosai, suka bushe.

7 Waɗansu kuma suka faɗa cikin ƙaya, sai ƙayar ta tashi ta sarƙe su, ba su yi tsaba ba.

8 Waɗansu kuma suka faɗa a ƙasa mai kyau, suka yi yabanya, suka girma, suka yi tsaba, waɗansu riɓi talatin talatin, waɗansu sittin sittin, waɗansu ma har ɗari ɗari.”

9 Sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”

Manufar Misalan

10 Da suka kaɗaita, masu binsa da su sha biyun nan suka tambaye shi ma’anar misalan.

11 Sai ya ce musu, “Ku kam, an yardar muku ku san asirin Mulkin Allah, amma ga waɗanda ba sa cikinku, kome sai a cikin misali,

12 don gani da ido kam, su gani, amma ba da zuci ba. Ji kuma, su ji, amma ba za su fahimta ba, wai don kada su juyo a yafe musu.”

Yesu Ya Ba da Bayanin Misalin Mai Shuka

13 Ya ce musu, “Ashe, ba ku fahimci wannan misali ba? Ƙaƙa za ku fahimci sauran ke nan?

14 Mai shukan nan fa Maganar Allah yake shukawa.

15 Waɗanda suka fāda a hanya kuwa, su ne kwatancin waɗanda aka shuka Maganar a zuciya tasu. Da zarar sun ji, nan da nan sai Shaiɗan ya zo ya ɗauke Maganar da aka shuka a zuciya tasu.

16 Haka kuma waɗanda aka shuka a wuri mai duwatsu, su ne waɗanda da zarar sun ji Maganar sai su karɓa da farin ciki.

17 Su kam, ba su da tushe, rashin ƙarƙo gare su, har in wani ƙunci ko tsanani ya faru domin wannan Magana, nan da nan sai su yi tuntuɓe.

18 Waɗansu kuma su ne kwatancin waɗanda suka fāɗa cikin ƙaya, su ne waɗanda suke jin Maganar,

19 amma taraddadin duniya, da jarabar dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga su sarƙe Maganar, har ta zama marar amfani.

20 Waɗanda aka shuka a ƙasa mai kyau kuwa, su ne kwatancin waɗanda suke jin Maganar, su karɓa, su kuma amfana, waɗansu riɓi talatin talatin, waɗansu sittin sittin, waɗansu ma har ɗari ɗari.”

Fitila a Rufe da Masaki

21 Sai ya ce musu, “Shin, ana kawo fitila don a rufe ta da masaki, ko a ajiye ta a ƙarƙashin gado ne, ba don a ɗora ta a kan maɗorinta ba?

22 Ba abin da yake ɓoye, sai domin a bayyana shi a gaba. Ba kuma wani abin da yake asiri, sai domin a bayyana shi a gaba.

23 In da mai kunnen ji, yă ji.”

24 Sai ya ce musu, “Ku ji. Mudun da ka auna, da shi za a auna maka, har ma a ƙara.

25 Domin mai abu akan ƙara wa. Marar abu kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa.”

Misali na Irin da ya Tsiro

26 Ya ce kuma, “Mulkin Allah kamar mutum yake mai yafa iri a ƙasa.

27 A kwana a tashi har irin ya tsiro, ya girma, bai kuwa san ta yadda aka yi ba.

28 Ƙasa da kanta takan ba da amfani, tsiro shi ne na farko, sa’an nan kai, sai kuma ƙwaƙƙwarar ƙwaya a kan.

29 Sa’ad da amfani ya nuna, sai ya sa lauje ya yanke nan da nan, wato kaka ta yi ke nan.”

Misali na Ƙwayar Mastad

30 Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta Mulkin Allah? Ko kuwa da wane misali za mu misalta shi?

31 Kamar ƙwayar mastad da yake, wadda, in an shuka ta, ko da yake ita ce mafi ƙanƙantar ƙwayoyi a duniya,

32 duk da haka in an shuka ta, sai ta girma ta fi duk sauran ganye, ta yi manyan rassa, har tsuntsaye su iya sauka a inuwarta.”

Yesu Ya Yi Amfani da Misalai

33 Da misalai da yawa irin waɗannan Yesu ya yi musu Maganar Allah, daidai gwargwadon ganewa tasu.

34 Ba ya faɗa musu kome sai da misali, amma a keɓe yakan bayyana wa almajiransa kome.

Yesu Ya Tsawata wa Hadiri

35 A ran nan da maraice ya ce musu, “mu haye can ƙetare.”

36 Da suka bar taron, suka tafi da shi yadda yake a cikin jirgin, waɗansu jirage kuma na tare da shi.

37 Sai babban hadari mai iska ya taso, raƙuman ruwa kuma na ta fantsama cikin jirgin, har jirgin ya tasar wa cika da ruwa.

38 Yesu kuwa na daga ƙarshen baya na jirgin a kan matashi, yana barci. Sai suka tashe shi, suka ce masa, “Malam, za mu hallaka ba ka kula ba ko?”

39 Sai ya farka, ya tsawata wa iskar, ya kuma ce wa ruwan tekun, “Natsu! Ka yi shiru!” Sai iskar ta kwanta, wurin duk ya yi tsit.

40 Ya ce musu, “Don me kuka firgita haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?”

41 Sai suka tsorata, matuƙar tsoro, suka ce wa juna, “Wa ke nan kuma, wanda har iska da ruwan teku ma suke yi masa biyayya?”

Categories
MAR

MAR 5

Warkar da Mai Aljan na Garasinawa

1 Suka iso hayin teku a ƙasar Garasinawa.

2 Da saukarsa daga jirgin, sai ga wani mai baƙin aljan daga makabarta ya tarye shi.

3 Shi kuwa makabarta ce mazauninsa. Ba mai iya ɗaure shi kuma, ko da sarƙa ma.

4 Don dā an sha ɗaure shi da mari da sarƙa, amma ya tsintsinka sarƙar, ya gutsuntsuna marin, har ma ba mai iya bi da shi.

5 Kullum kuwa dare da rana yana cikin makabarta, da kan duwatsu, yana ta ihu, yana kukkuje jikinsa da duwatsu.

6 Da dai ya hango Yesu, sai ya sheƙo a guje ya fāɗi a gabansa,

7 ya ƙwala ihu ya ce, “Ina ruwanka da ni, Yesu Ɗan Allah Maɗaukaki? Na gama ka da Allah, kada ka yi mini azaba.”

8 Ya faɗi haka ne domin Yesu ya ce masa, “Rabu da mutumin nan, kai wannan baƙin aljan!”

9 Yesu ya tambaye shi, “Me sunanka?” Sai ya amsa ya ce, “Sunana Tuli, don muna da yawa.”

10 Sai ya roƙi Yesu da gaske kada ya kore su daga ƙasar.

11 To, wurin nan kuwa da wani babban garken alade na kiwo a gangaren dutsen.

12 Aljannun nan suka roƙe shi suke ce, “Tura mu wajen aladun nan, mu shiga su.”

13 Ya kuwa yardar musu. Sai baƙaƙen aljannun suka fita, suka shiga aladun. Garken kuwa wajen alade dubu biyu, suka rugungunto ta gangaren, suka fāɗa tekun, suka halaka a ruwa.

14 Daga nan sai ‘yan kiwon aladen suka gudu, suka ba da labari birni da ƙauye. Jama’a suka zo su ga abin da ya auku.

15 Da suka zo wurin Yesu suka ga mai aljannun nan a zaune, saye da tufa, cikin hankalinsa kuma, wato mai aljannun nan masu yawa a dā, sai suka tsorata.

16 Waɗanda aka yi abin a kan idonsu kuwa, suka farfaɗi abin da ya gudana ga mai aljannun da kuma aladen.

17 Sai suka fara roƙon Yesu ya bar musu ƙasarsu.

18 Yana shiga jirgi ke nan, sai mai aljannun nan a dā ya roƙe shi izinin zama a gunsa.

19 Amma Yesu bai yardar masa ba, ya ce masa, “Tafi gida wurin ‘yan’uwanka, ka faɗa musu irin manyan abubuwan da Ubangiji ya yi maka, da kuma yadda ya ji tausayinka.”

20 Sai ya tafi, ya shiga baza labari a Dikafolis na irin manyan abubuwan da Yesu ya yi masa. Duk mutane kuwa suka yi al’ajabi.

Warkar da ‘Yar Yayirus da Matar da ta Taɓa Gezar Mayafin Yesu

21 Da Yesu ya sāke haye ƙetare cikin jirgi, sai babban taro ya kewaye shi. Shi kuwa yana bakin tekun.

22 Sai ga wani daga cikin shugabannin majami’a, mai suna Yayirus. Da ganin Yesu kuwa ya fāɗi a gabansa,

23 ya roƙe shi da gaske, yana cewa, “’Yata ƙaramar tana bakin mutuwa. Idan dai a ce ka zo ka ɗora mata hannu, sai ta warke ta rayu.”

24 Sai suka tafi tare. Babban taro kuwa na biye da shi, suna matsa tasa.

25 Sai ga wata mace wadda ta shekara goma sha biyu tana zub da jini,

26 ta kuma sha wahala da gaske a hannun masu magani da yawa, har ta ɓad da duk abin da take da shi, amma duk a banza, sai ma gaba-gaba cutar take yi.

27 Da ta ji labarin Yesu, ta raɓo ta bayansa cikin taron, ta taɓa mayafinsa.

28 Don tā ce a ranta, “Ko da tufarsa ma na taɓa, sai in warke.”

29 Nan take zubar jininta ta tsaya, ta kuma ji a jikinta an warkar da cutarta.

30 Nan da nan kuwa da Yesu ya ji wani iko ya fita daga gare shi, sai ya waiwaya a cikin taron, ya ce, “Wa ya taɓa tufata?”

31 Sai almajiransa suka ce masa, “Kana ganin taro na matsarka, ka ce, wa ya taɓa ka?”

32 Sai Yesu ya juya domin ya ga wadda ta yi haka.

33 Matar kuwa da ta san abin da aka yi mata, sai ta zo a tsorace, tana rawar jiki, ta fāɗi a gabansa, ta faɗa masa ƙashin gaskiya.

34 Sai ya ce mata, “’Yata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya, ki warke daga cutarki.”

35 Yana cikin magana, sai ga waɗansu daga gidan shugaban majami’a suka ce, “Ai, ‘yarka ta rasu, me kuma za ka wahalar da Malamin?”

36 Amma Yesu bai kula da abin da suka faɗa ba, ya ce wa shugaban majami’a, “kada ka ji tsoro, ka ba da gaskiya kawai.”

37 Bai bar kowa ya bi shi ba sai Bitrus, da Yakubu, da kuma Yahaya ɗan’uwan Yakubu.

38 Da suka isa gidan shugaban majami’a, ya ji ana hayaniya, ana kuka, ana kururuwa ba ji ba gani.

39 Da kuma ya shiga, ya ce musu, “Don me kuke hayaniya kuna kuka haka? Ai, yarinyar ba matacciya take ba, barci take yi.”

40 Sai suka yi masa dariyar raini. Shi kuma bayan ya fitar da su duka waje, sai ya ɗauki uban yarinyar, da uwa tata, da kuma waɗanda suke tare da shi, ya shiga inda yarinyar take.

41 Ya kama hannunta, ya ce mata, “Talita ƙumi”, wato, “Ke yarinya, ina ce miki, tashi.”

42 Nan take yarinyar ta tashi ta yi tafiya, domin ‘yar shekara goma sha biyu ce. Nan da nan kuwa mamaki ya kama su.

43 Sai ya kwaɓe su matuƙa kada kowa ya ji wannan labari. Ya kuma yi umarni a ba ta abinci.

Categories
MAR

MAR 6

An Ƙi Yesu a Nazarat

1 Ya tashi daga nan ya koma garinsu, almajiransa kuwa suka bi shi.

2 Da Asabar ta yi, sai ya fara koyarwa a majami’a. Mutane da yawa da suka saurare shi, suka yi mamaki, suna cewa, “Ina mutumin nan ya sami wannan abu duka? Wace hikima ce aka ba shi haka? Dubi irin waɗannan mu’ujizan da ake aikatawa ta hannunsa!

3 Shin, wannan ba shi ne masassaƙin nan ba, ɗan Maryamu, ɗan’uwan su Yakubu, da Yusufu, da Yahuza, da kuma Saminu? ‘Yan’uwansa mata kuma ba ga su tare da mu ba?” Suka yi tuntuɓe sabili da shi.

4 Sai Yesu ya ce musu, “Ai, annabi ba ya rasa girma sai dai a garinsu, da cikin ‘yan’uwansa, da kuma gidansu.”

5 Bai ko iya yin wata mu’ujiza a can ba, sai dai ya ɗora wa marasa lafiya kaɗan hannu ya warkar da su.

6 Ya yi mamakin rashin bangaskiyarsu.

Sai ya zazzaga ƙauyuka yana koyarwa.

Yesu Ya Aiki Sha Biyu Ɗin Nan

7 Sai ya kira goma sha biyun nan, ya fara aikensu biyu-biyu, ya kuma ba su iko a kan baƙaƙen aljannu.

8 Ya umarce su kada su ɗauki guzuri don tafiyar, ko gurasa, ko burgami, ko kuɗi ma a ɗamararsu, sai dai sanda kawai,

9 amma su sa takalmi, kada kuma su haɗa taguwa biyu.

10 Ya ce musu, “Duk gidan da kuka sauka, ku zauna a nan har ku tashi.

11 Duk inda aka ƙi yin na’am da ku, aka kuma ƙi sauraronku, in za ku tashi, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunka don shaida a kansu.”

12 Haka fa, suka fita, suna wa’azi mutane su tuba.

13 Suka fitar da aljannu da yawa, suka kuma shafa wa marasa lafiya da yawa mai, suka warkar da su.

Mutuwar Yahaya Maibaftisma

14 Sai fa sarki Hirudus ya ji labari, domin sunan Yesu ya riga ya shahara, har waɗansu suka ce, “Yahaya Maibaftisma ne aka tasa daga matattu, shi ya sa mu’ujizan nan suke aiki ta wurinsa.”

15 Amma waɗansu kuwa suka ce, “Iliya ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “Ai, annabi ne, kamar ɗaya daga cikin annabawa.”

16 Amma da Hirudus ya ji haka, sai ya ce, “Yahaya, wanda na fille wa kai, shi ne aka tasa.”

17 Don dā Hirudus da kansa ya aika aka kamo Yahaya, ya ɗaure shi a kurkuku saboda Hirudiya matar ɗan’uwansa Filibus, wadda shi Hirudus ya aura.

18 Don dā Yahaya ya ce wa Hirudus, “Bai halatta ka zauna da matar ɗan’uwanka ba.”

19 Hirudiya kuwa na riƙe da Yahaya cikin zuciyarta, har ta so ta kashe shi, amma ba ta sami hanya ba,

20 don Hirudus yana tsoron Yahaya, ya sani shi mutum ne adali, tsattsarka, shi ya sa ya kāre shi. Hirudus yakan damu da yawa sa’ad da yake sauraron Yahaya, ko da yake na murna da jinsa.

21 Amma wani sanadi ya zo, da ranar haihuwar Hirudus ta kewayo, ya yi wa hakimansa, da sarakunan yaƙinsa, da kuma manyan ƙasar Galili biki.

22 Da ‘yar Hirudiya ta shigo ta yi rawa, sai ta gamshi Hirudus da baƙinsa. Sai fa sarki ya ce wa yarinyar, “Roƙe ni kome, sai in ba ki.”

23 Ya kuma rantse mata, ya ce, “Kome kika roƙe ni zan ba ki, ko da rabin mulkina ne.”

24 Ta fita, ta ce wa uwa tata, “Me zan roƙa?” Uwar ta ce, “Kan Yahaya Maibaftisma.”

25 Nan da nan sai ta shigo wurin sarki da gaggawa, ta roƙe shi, ta ce, “Ina so yanzu yanzu ka ba ni kan Yahaya Maibaftisma a cikin akushi.”

26 Sai sarki ya yi baƙin ciki gaya, amma saboda rantsuwa tasa da kuma baƙinsa, ba ya so ya hana ta.

27 Nan take sai sarki ya aiki dogari, ya yi umarni a kawo kan Yahaya. Ya tafi ya fille wa Yahaya kai a kurkuku,

28 ya kawo kan a cikin akushi, ya ba yarinyar, yarinyar kuwa to ba uwa tata.

29 Da almajiran Yahaya suka ji labari, sai suka zo suka ɗauki gangar jikinsa, suka sa ta a kabari.

Ciyar da Mutum Dubu Biyar

30 Manzannin suka komo wurin Yesu, suka faɗa masa duk iyakar abin da suka yi, da abin da suka koyar.

31 Ya ce musu, “Ku zo mu kaɗaita a wurin da ba kowa, ku ɗan huta.” Domin mutane da yawa suna kaiwa suna kawowa, ko damar cin abinci ma, manzannin ba su samu ba.

32 Sai suka tafi cikin jirgi wurin da ba kowa, su kaɗai.

33 Ashe, mutane da yawa sun ga tafiyarsu, sun kuwa shaida su, suka fa dunguma ta tudu daga garuruwa duka, suka riga su zuwa.

34 Da saukar Yesu sai ya ga taro mai yawa, ya kuma ji tausayinsu, domin kamar tumaki suke ba makiyayi. Ya fara koya musu abubuwa da yawa.

35 Kusan faɗuwar rana sai almajiransa suka zo gare shi, suka ce masa, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuwa, rana ta kusa fāɗuwa.

36 Sai ka sallame su, su shiga karkara da ƙauyuka na kurkusa, su saya wa kansu abinci.”

37 Amma ya amsa musu ya ce, “Ku ku ba su abinci mana.” Sai suka ce masa, “Wato mu je mu sayo gurasa ta dinari metan, mu ba su su ci?”

38 Ya ce musu, “Gurasa nawa gare ku? Ku je ku dubo.” Da suka binciko suka ce, “Ai, biyar ne, da kifi biyu.”

39 Sa’an nan ya yi umarni dukkansu su zazzauna ƙungiya ƙungiya a ɗanyar ciyawa.

40 Haka suka zauna jeri jeri, waɗansu ɗari ɗari, waɗansu hamsin hamsin.

41 Da ya ɗauki gurasa biyar ɗin da kifi biyun, sai ya ɗaga kai sama, ya yi wa Allah godiya, ya gutsuttsura gurasar, ya yi ta ba almajiran, suna kai wa jama’a, duk kuma ya raba musu kifin nan biyu.

42 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi,

43 har suka ɗauki kwando goma sha biyu cike da gutsattsarin gurasar da na kifin.

44 Waɗanda suka ci gurasan nan kuwa maza dubu biyar ne.

Yesu na Tafiya a kan Ruwan Teku

45 Nan da nan ya sa almajiransa su shiga jirgi su riga shi hayewa zuwa Betsaida, kafin ya sallami taron.

46 Bayan ya sallame su, sai ya hau dutse domin ya yi addu’a.

47 Da magariba ta yi, jirgin na tsakiyar teku, Yesu kuwa na nan kan tudu shi kaɗai,

48 da ya ga suna fama da tuƙi, gama iska na gāba da su, misalin ƙarfe uku na dare sai ya nufo su, yana tafe a kan ruwan teku. Ya yi kamar zai wuce su,

49 amma da suka gan shi yana tafiya a kan ruwan, sai suka zaci fatalwa ce, suka yi kururuwa,

50 domin duk sun gan shi, sun kuwa firgita. Sai nan da nan ya yi musu magana ya ce, “Ba kome, ni ne, kada ku ji tsoro.”

51 Sa’an nan ya shiga jirgi wurinsu, iska kuma ta kwanta. Sai mamaki ya kama su ƙwarai,

52 don ba su fahimci al’amarin gurasan nan ba, saboda zuciyarsu ta taurare.

Yesu Ya Warkar da Marasa Lafiya a Janisarata

53 Da suka haye, suka isa ƙasar Janisarata, suka ɗaure jirgin a gaɓa.

54 Da fitarsu daga jirgin sai mutane suka shaida shi.

55 Suka gama ƙasar da gudu, suka fara ɗaɗɗauko marasa lafiya a kan shimfiɗunsu zuwa duk inda suka ji yake.

56 Duk inda ya shiga kuma, birni ko ƙauye ko karkara, sukan kwantar da marasa lafiya a bakin kasuwa, su roƙe shi su taɓa ko ma da gezar mayafinsa ma. Iyakar waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.

Categories
MAR

MAR 7

Al’adun Shugabanni

1 To, da Farisiyawa suka taru a wurinsa tare da waɗansu daga cikin malaman Attaura da suka zo daga Urushalima,

2 suka lura waɗansu almajiransa na cin abinci da hannuwa marasa tsarki, wato marasa wanki.

3 Domin Farisiyawa da dukan Yahudawa ba sa cin abinci sai sun wanke hannu sarai tukuna, saboda bin al’adun shugabanninsu.

4 In sun komo daga kasuwa kuwa, ba sa cin abinci sai sun yi wanka tukuna. Akwai kuma waɗansu al’adu da yawa da suka gada suke kiyayewa, kamar su wankin ƙore, da tuluna, da daruna.

5 Sai Farisiyawa da malaman Attaura suka tambaye shi, “Don me almajiranka ba sa bin al’adun shugabanni, sai su riƙa cin abinci da hannuwa marasa tsarki?”

6 Sai ya ce musu, “Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku, munafukai! Yadda yake a rubuce cewa,

‘Al’umman nan a baka kawai suke girmama ni,

Amma a zuci nesa suke da ni.

7 A banza suke bauta mini,

Domin ƙa’idodin da suke koyarwa umarnin ɗan adam ne.’

8 Kuna yar da umarnin Allah, kuna riƙe da al’adun mutane.”

9 Sai ya ce musu, “Lalle kun iya yar da umarnin Allah don ku bi al’adunku!

10 Domin Musa ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ da kuma, ‘Wanda ya zagi ubansa ko uwa tasa, sai lalle a kashe shi.’

11 Amma ku kukan ce, ‘In mutum ya ce wa ubansa ko uwa tasa, “Duk abin da dā za ku samu a gare ni ya zama Korban,” ’ (wato an sadaukar),

12 shi ke nan fa, ba saura ku bar shi ya yi wa ubansa ko uwa tasa aikin kome.

13 Ta haka kuke banzanta Maganar Allah ta wajen al’adunku na gargajiya. Kun kuwa cika yin irin waɗannan abubuwa.”

Abubuwan da Suke Ƙazantarwa

14 Sai ya sāke kiran jama’a, yă ce musu, “Ku saurare ni dukanku, ku kuma fahimta.

15 Ba abin da yake shiga mutum daga waje yă ƙazanta shi, sai abin da yake fita, yake ƙazanta shi. [

16 Duk mai kunnen ji, yă ji.]”

17 Bayan rabuwarsa da taron, da ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi ma’anar misalin.

18 Ya ce musu, “Ashe, ku ma ba ku da fahimta ne? Ashe, ba ku gane ba, kome ya shiga mutum daga waje, ba yadda zai ƙazanta shi,

19 tun da yake ba zuciya tasa ya shiga ba, cikinsa ne, ta haka kuma zai fita?” Ta haka Yesu ya halatta kowane irin abinci.

20 Ya kuma ce, “Abin da yake fita daga cikin mutum yake ƙazanta shi.

21 Don daga ciki ne, wato daga zuciyar mutum, mugayen tunani yake fitowa, kamar su fasikanci, da sata, da kisankai, da zina,

22 da kwaɗayi, da mugunta, da ha’inci, da fajirci, da kishi, da yanke, da girmankai, da kuma wauta.

23 Duk waɗannan mugayen abubuwa daga ciki suke fitowa, suna kuwa ƙazanta mutum.”

Bangaskiyar Mata Basurofinikiya

24 Daga nan kuma ya tashi ya tafi wajajen Taya da Sidon. Ya shiga wani gida, bai kuwa so kowa ya sani ba, amma ba ya ɓoyuwa.

25 Nan da nan sai wata mace, wadda ‘ya tata ƙarama take da baƙin aljan ta ji labarinsa, ta zo ta fāɗi a gabansa.

26 Matar kuwa Baheleniya ce, asalinta kuma Basurofinikiya ce. Sai ta roƙe shi ya fitar wa ‘ya tata da aljanin.

27 Yesu ya ce mata, “Bari ‘ya’ya su ƙoshi tukuna, domin bai kyautu a bai wa karnuka abincinsu ba.”

28 Amma ta amsa masa ta ce, “I, haka ne, ya Ubangiji, amma ai, karnuka sukan ci suɗin ‘ya’ya.”

29 Sai ya ce mata, “Saboda wannan magana taki, koma gida, aljanin, ai, ya rabu da ‘yarki.”

30 Sai ta koma gida ta iske yarinyar a kwance a gado, aljanin kuwa ya fita.

Yesu Ya Warkar da Bebe

31 Sai ya komo daga wajen Taya, ya bi ta Sidon ya je Tekun Galili ta Dikafolis.

32 Suka kawo masa wani kurma mai i’ina, suka roƙe shi ya ɗora masa hannu.

33 Yesu ya ɗauke shi suka koma waje ɗaya, rabe da taron, ya sa yatsotsinsa a kunnuwansa, ya tofar da yau, ya kuma taɓa harshensa.

34 Ya ɗaga kai sama ya yi ajiyar zuciya, sai ya ce masa, “Iffata!” wato “Buɗu!”

35 Sai aka buɗe kunnuwansa, aka saki kwaɗon harshensa, ya kuma yi magana sosai.

36 Yesu ya kwaɓe su kada su faɗa wa kowa, amma ƙara yawan kwaɓonsu ƙara yawan yaɗa labarin.

37 Suka yi mamaki gaba da kima, suka ce, “Kai, ya yi kome da kyau! Har kurma ma ya sa ya ji, bebe kuma ya yi magana.”

Categories
MAR

MAR 8

Ciyar da Mutum Dubu Huɗu

1 A lokacin nan da wani taro mai yawan gaske ya sāke haɗuwa, ba su kuwa da abinci, sai ya kira almajiransa, ya ce musu,

2 “Ina jin tausayin wannan taro, don yau kwanansu uku ke nan a guna, ba su da wani abinci.

3 In kuwa na sallame su su tafi gida da yunwa haka, ai, za su kasa a hanya, ga shi kuwa, waɗansunsu sun fito nesa.”

4 Sai almajiransa suka amsa masa suka ce, “Ina za a iya samun gurasar da za ta ciyar da mutanen nan a jeji haka?”

5 Sai ya tambaye su, “Gurasa nawa gare ku?” Suka ce, “Bakwai.”

6 Sai ya umarci taron su zauna a ƙasa. Da ya ɗauki gurasan nan bakwai, ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya yi ta ba almajiransa su kai wa taron, suka kuwa kakkai musu.

7 Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan. Da ya yi wa Allah godiya, sai ya ce su ma a kai musu.

8 Suka ci, suka ƙoshi, har suka ɗauki ragowar gutsattsarin, cike da manyan kwanduna bakwai.

9 Mutanen kuwa sun yi wajen dubu huɗu. Sai ya sallame su.

10 Nan da nan kuwa ya shiga jirgi da almajiransa, ya tafi ƙasar Dalmanuta.

Neman Alama

11 Farisiyawa suka zo suka fara muhawara da shi, suna nema ya nuna musu wata alama daga sama, don su gwada shi.

12 Sai ya yi wata doguwar ajiyar zuciya, ya ce, “Don me mutanen zamanin nan suke neman ganin alama? Hakika, ina gaya muku, ba wata alamar da za a nuna wa mutanen wannan zamani.”

13 Daga nan ya bar su, ya sāke shiga jirgi, ya haye wancan ƙetaren.

Yistin Farisiyawa da na Hirudus

14 Sun kuwa manta, ba su kawo gurasa ba, sai guda ɗaya ce kawai gare su a jirgin.

15 Ya gargaɗe su ya ce, “Ku kula, ku yi hankali da yistin Farisiyawa da na Hirudus.”

16 Suka yi magana da juna a kan ba su da gurasa.

17 Da yake Yesu ya gane haka, sai ya ce musu, “Don me kuke zancen ba ku da gurasa? Ashe, har yanzu ba ku gane ba, ba ku kuma fahimta ba? Zuciyarku a taurare take?

18 Kuna da idanu, ba kwa gani ne? Kuna da kunnuwa, ba kwa ji ne? Ba kwa kuma tunawa ne?

19 Da na gutsuttsura wa mutum dubu biyar gurasan nan biyar, kwando nawa kuka ɗauka cike da gutsattsarin?” Suka ce masa, “Sha biyu.”

20 “To, gurasa bakwai da na gutsuttsura wa mutum dubu huɗu fa? Manyan kwanduna nawa kuka ɗauka cike da gutsattsarin?” Suka ce masa, “Bakwai.”

21 Sai ya ce musu, “To, har yanzu ba ku fahimta ba?”

Warkar da Makaho a Betsaida

22 Suka iso Betsaida. Aka kawo masa wani makaho, aka roƙe shi ya taɓa shi.

23 Ya kama hannun makahon, ya kai shi bayan gari. Da ya tofa yau a idanunsa, ya ɗora masa hannu, sai ya tambaye shi cewa, “Kana iya ganin wani abu?”

24 Sai makahon ya ɗaga kai, ya ce, “Ina ganin mutane kam, amma kamar itatuwa nake ganinsu, suna yawo.”

25 Sai ya sāke ɗora hannu a idanunsa. Makahon kuwa ya zura ido ƙwar, ya warke, ya ga kome garau.

26 Sai Yesu ya sallame shi ya koma gida, ya ce, “Ko ƙauyen ma kada ka shiga.”

Hurcin Bitrus a kan Yesu

27 Yesu ya tashi, da shi da almajiransa, ya shiga ƙauyukan Kaisariya Filibi. A hanya kuwa ya tambayi almajiransa, “Wa mutane suke cewa nake?”

28 Suka ce masa, “Yahaya Maibaftisma, waɗansu kuwa, Iliya, waɗansu kuma, wani daga cikin annabawa.”

29 Sai ya tambaye su, “Amma ku fa, wa kuke cewa nake?” Bitrus ya amsa masa ya ce, “Kai ne Almasihu.”

30 Sai ya kwaɓe su kada su gaya wa kowa labarinsa.

Yesu Ya Faɗi irin Mutuwar da Zai Yi

31 Ya fara koya musu, cewa lalle ne Ɗan Mutum ya sha wuya iri iri, shugabanni, da manyan firistoci, da malaman Attaura su ƙi shi, har a kashe shi, bayan kwana uku kuma ya tashi da rai.

32 Ya ko faɗi wannan magana a sarari. Sai Bitrus ya ja shi waje ɗaya, ya fara tsawatar masa.

33 Amma da Yesu ya waiwaya ya ga almajiransa, ya tsawata wa Bitrus ya ce, “Ka yi nesa da ni, Shaiɗan! Ba ka tattalin al’amuran Allah sai na mutane.”

34 Ya kira taron tare da almajiransa, ya ce musu, “Duk mai son bina, sai yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni.

35 Duk mai son tattalin ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa saboda ni, saboda bishara kuma, tattalinsa ya yi.

36 Me mutum ya amfana in ya sami duniya duka a bakin ransa?

37 Me kuma mutum zai iya bayarwa ya fanshi ransa?

38 Duk wanda zai ji kunyar shaida ni da maganata a wannan zamani na rashin amana da yawan zunubi, Ɗan Mutum ma zai ji kunyar shaida shi, sa’ad da ya zo da ɗaukakar Ubansa tare da mala’iku tsarkaka.”

Categories
MAR

MAR 9

1 Sai ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, akwai waɗansu tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba, sai sun ga Mulkin Allah ya bayyana da iko.”

Sākewar Kamanninsa

2 Bayan kwana shida Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai. Sai kamanninsa ya sāke a gabansu,

3 tufafinsa suka yi fari fat suna sheƙi, yadda ba mai wankin da zai iya yinsu haka a duniya.

4 Sai Iliya da Musa sun bayyana a gare su, suna magana da Yesu.

5 Sai Bitrus ya sa baki, ya ce wa Yesu, “Ya Ubangiji, ya kyautu da muke nan wurin, mu kafa bukkoki uku, ɗaya taka, ɗaya ta Musa, ɗaya kuma ta Iliya.”

6 Ya rasa abin da zai faɗa ne, don sun tsorata da gaske.

7 Sai ga wani gajimare ya zo ya rufe su, aka kuma ji wata murya daga cikin gajimaren, ta ce, “Wannan shi ne Ɗana ƙaunataccena. Ku saurare shi.”

8 Farat haka da suka dudduba, ba su ƙara ganin kowa ba, sai Yesu kaɗai tare da su.

9 Suna cikin gangarowa daga dutsen, sai ya kwaɓe su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan Ɗan Mutum ya tashi daga matattu.

10 Sai suka bar maganar yasu-yasu, suna tambayar juna komece ce ma’anar tashi daga matattu.

11 Suka tambaye shi suka ce, “To, yaya kuwa malaman Attaura suke cewa, lalle ne Iliya yă fara zuwa?”

12 Sai ya ce musu, “Lalle ne Iliya ya fara zuwa ya raya dukan abubuwa. Yaya kuwa yake a rubuce a kan Ɗan Mutum, cewa zai sha wuya iri iri, a kuma wulaƙanta shi?

13 Amma ina gaya muku, Iliya ya riga ya zo, sun kuma yi masa abin da suka ga dama, yadda labarinsa yake a rubuce.”

Yesu Ya Warkar da Yaro Mai Beben Aljan

14 To, da suka komo wurin almajiran, sai suka ga babban taro ya kewaye su, malaman Attaura kuma na muhawara da su.

15 Da ganin Yesu sai duk taron suka yi mamaki ƙwarai da gaske, suka ɗungumo wurinsa a guje, suna gaishe shi.

16 Ya tambaye su, “Muhawarar me kuke yi da su?”

17 Sai ɗaya daga cikin taron ya amsa masa ya ce, “Malam, ga shi, na kawo maka ɗana, don yana da beben aljan.

18 Duk inda ya hau shi, sai ya doka shi har ƙasa, bakinsa na kumfa, yana tsukun haƙoransa, yana sandarewa. Na kuma yi wa almajiranka magana su fitar da shi, suka kasa.”

19 Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Ya ku mutanen zamani marar bangaskiya! Har yaushe zan iya zama da ku? Har yaushe kuma zan iya jure muku? Ku dai kawo mini shi.”

20 Suka kawo masa yaron. Da aljanin ya gan shi, nan da nan sai ya buge yaron, jikinsa na rawa, ya fāɗi yana ta birgima, bakinsa na kumfa.

21 Yesu ya tambayi uban yaron, “Tun yaushe wannan abu ya same shi?” Uban ya ce, “Tun yana ƙarami.

22 Ya kuwa sha jefa shi a wuta da ruwa, don ya hallaka shi. Amma in za ka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimake mu.”

23 Sai Yesu ya ce masa, “In zan iya? Ai, dukkan abu mai yiwuwa ne ga mai ba da gaskiya.”

24 Nan da nan sai uban yaron ya ɗaga murya ya ce, “Na ba da gaskiya. A kore mini rashin bangaskiyata!”

25 Da Yesu ya ga taro na ɗungumowa a guje, sai ya tsawata wa baƙin aljanin ya ce masa, “Kai, beben aljan, na umarce ka ka rabu da shi, kada kuma ka ƙara hawansa.”

26 Bayan aljanin nan ya yi ihu, sai ya buge shi da gaske, jikinsa na rawa, ya rabu da shi. Yaron kuma ya zama kamar matacce, har ma yawancin mutane suka ce, “Ai, ya mutu!”

27 Amma Yesu ya kama hannunsa ya tashe shi, ya kuwa tashi tsaye.

28 Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a keɓe suka ce, “Me ya sa mu muka kasa fitar da shi?”

29 Sai ya ce musu, “Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu’a.”

Yesu Ya Sāke Faɗar irin Mutuwar da Zai Yi

30 Sai suka tashi daga nan, suka ratsa ƙasar Galili, bai kuwa so kowa ya sani ba,

31 domin yana koya wa almajiransa ne, yana ce musu, “Za a ba da Ɗan Mutum ga mutane, za su kuwa kashe shi, sa’ad da aka kashe shi kuma, bayan kwana uku zai tashi.”

32 Amma fa ba su fahimci maganar ba, suna kuma jin tsoron tambaya tasa.

Wane ne Mafi Girma?

33 Suka zo Kafarnahum. Da ya shiga gida sai ya tambaye su, “Muhawarar me kuka yi a hanya?”

34 Amma suka yi shiru, don a hanya sun yi muhawarar ko wane ne babbansu.

35 Sai ya zauna, ya kira sha biyun nan, ya ce musu, “Kowa yake son yă zama shugaba, lalle ne yă zama na ƙarshe duka, baran kowa kuma.”

36 Sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa shi a tsakiyarsu, ya rungume shi, ya ce musu,

37 “Duk wanda ya karɓi ƙaramin yaro kamar wannan saboda sunana, ni ya karɓa. Wanda kuma ya karɓe ni, ba ni ya karɓa ba, wanda ya aiko ni ne ya karɓa.”

Wanda ba ya Gāba da Mu, Namu Ne

38 Sai Yahaya ya ce masa, “Malam, mun ga wani na fitar da aljannu da sunanka, mun kuwa hana shi, domin ba ya binmu.”

39 Amma Yesu ya ce, “Kada ku hana shi. Ai, ba wanda zai yi wata mu’ujiza da sunana, sa’an nan, nan da nan ya kushe mini.

40 Ai, duk wanda ba ya gāba da mu, namu ne.

41 Kowa kuma ya ba ku ruwan sha moɗa guda saboda ku na Almasihu ne, hakika ina gaya muku, ba zai rasa ladansa ba ko kaɗan.

Sanadodin Yin Zunubi

42 “Da dai wani yă sa ɗaya daga cikin waɗannan ‘yan yara masu gaskatawa da ni yă yi laifi, zai fiye masa a rataya wani babban dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku.

43 In kuwa hannunka na sa ka laifi, to, yanke shi. Zai fiye maka ka shiga rai dungu, da ka shiga Gidan Wuta da hannu biyu, wuta marar kasuwa kuwa. [

44 A wurin tsutsotsi masu cinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a kashe ta.]

45 In kuwa ƙafarka na sa ka laifi, to, yanke ta. Zai fiye maka ka shiga rai da gurguntaka, da a jefa ka Gidan Wuta da ƙafa biyu. [

46 A wurin tsutsotsi masu cinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a kashe ta.]

47 In kuma idonka na sa ka laifi, to, ƙwaƙule shi. Zai fiye maka ka shiga Mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka Gidan Wuta da ido biyu.

48 A wurin tsutsotsi masu cinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a kashe ta.

49 Da wuta za a tsarkake kowa, kamar yadda ake tsarkake abu da gishiri.

50 Gishiri abu ne mai kyau, amma in gishiri ya sane, dame za a daɗaɗa shi? Sai ku kasance da gishiri a zuciyarku, ku yi zaman lafiya da juna.”

Categories
MAR

MAR 10

Koyarwar Yesu a kan Kisan Aure

1 Sai Yesu ya tashi daga nan, ya tafi ƙasar Yahudiya, da kuma hayin Kogin Urdun. Taro kuma ya sāke haɗuwa wurinsa, ya kuma sāke koya musu kamar yadda ya saba.

2 Sai waɗansu Farisiyawa suka zo wajensa don su gwada shi, suka tambaye shi suka ce, “Halal ne mutum ya saki mata tasa?”

3 Sai ya amsa musu ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”

4 Suka ce, “Musa ya ba da izini a rubuta takardar kisan aure, a kuma saki matar.”

5 Yesu ya ce musu, “Don taurinkanku ne Musa ya rubuta muku wannan umarni.

6 Amma tun farkon halitta ‘Allah ya halicce su, namiji da tamata.’

7 ‘Don haka fa sai mutum yă bar uwa tasa da ubansa, yă manne wa mata tasa.

8 Haka su biyun nan su zama jiki guda.’ Har nan gaba su zama ba jiki biyu ba ne, ɗaya ne.

9 Abin da Allah fa ya gama, kada mutum ya raba.”

10 A cikin gida kuma sai almajiransa suka sāke tambayarsa wannan magana.

11 Sai ya ce musu, “Kowa ya saki mata tasa, ya auri wata, zina yake yi da ta biyun.

12 In kuma matar ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”

Yesu Ya Sa wa ‘Yan Yara Albarka

13 Suna kawo masa waɗansu yara ƙanana domin ya taɓa su, sai almajiransa suka kwaɓe su.

14 Da Yesu ya ga haka, sai ya ji haushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai, Mulkin Allah na irinsu ne.

15 Hakika, ina gaya muku, duk wanda bai yi na’am da Mulkin Allah kamar yadda ƙaramin yaro yake yi ba, ba zai shiga Mulkin ba har abada.”

16 Sai Yesu ya rugume su, yana ɗora musu hannu, yana sa musu albarka.

Saurayi Mai Dukiya

17 Ya fara tafiya ke nan, sai ga wani ya sheƙo a guje, ya durƙusa a gabansa, ya tambaye shi ya ce, “Malam managarci, me zan yi in gaji rai madawwami?”

18 Sai Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Ai, ba wani Managarci sai Allah kaɗai.

19 Ka dai san umarnan nan, ‘Kada ka yi kisankai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi shaidar zur. Kada ka yi zamba. Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’ ”

20 Sai ya ce masa, “Malam, ai, duk na kiyaye waɗannan tun ƙuruciyata.”

21 Yesu ya dube shi duban ƙauna, ya ce masa, “Abu guda ne kawai ya rage maka. Sai ka je, ka sayar da duk mallakarka, ka ba gajiyayyu, za ka sami wadata a Sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”

22 Da jin wannan magana gabansa ya fāɗi, ya tafi yana baƙin ciki, don yana da arziki ƙwarai.

23 Daga nan sai Yesu ya duddubi almajiransa, ya ce musu, “Da ƙyar kamar me masu dukiya su shiga Mulkin Allah!”

24 Almajiran kuwa suka yi mamakin maganarsa. Sai Yesu ya sāke ce musu, “Ya ku ‘ya’yana, da ƙyar ne kamar me a shiga Mulkin Allah!

25 Zai fiye wa raƙumi sauƙi ya bi ta kafar allura, da mai arziki ya shiga Mulkin Allah.”

26 Sai suka yi mamaki ƙwarai da gaske, suka ce masa, “To, in haka ne, wa zai sami ceto ke nan?”

27 Yesu ya dube su, ya ce, “Ga mutane kam ba mai yiwuwa ba ne, amma fa ba ga Allah ba. Domin kowane abu mai yiwuwa ne a gun Allah.”

28 Sai Bitrus ya fara ce masa, “To, ai, ga shi, mu mun bar kome, mun bi ka.”

29 Yesu ya ce, “Hakika, ina gaya muku, ba wanda zai bar gida, ko ‘yan’uwansa mata, ko ‘yan’uwansa maza, ko uwa tasa, ko ubansa, ko ‘ya’yansa, ko gonakinsa, sabili da ni da kuma bishara,

30 sa’an nan ya kasa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu, na gidaje, da ‘yan’uwa mata, da ‘yan’uwa maza, da iyaye mata, da ‘ya’ya, da gonaki, amma game da tsanani, a lahira kuma ya sami rai madawwami.

31 Da yawa na farko za su koma na ƙarshe, na ƙarshe kuma za su zama na farko.”

Yesu kuma Ya Sāke Faɗar Irin Mutuwar da Zai Yi

32 Suna tafiya Urushalima, Yesu kuwa na tafe gabansu, sai suka yi mamaki, mutanen da suke biye kuma suka tsorata. Ya sāke keɓe sha biyun nan, ya fara shaida musu abin da zai same shi.

33 Ya ce, “Ga shi, za mu Urushalima, za a ba da Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman Attaura, za su kuwa yi masa hukuncin kisa, su bāshe shi ga al’ummai.

34 Za su yi masa ba’a, su tofa masa yau, su yi masa bulala, su kashe shi, bayan kwana uku kuma ya tashi.”

Roƙon Yakubu da Yahaya

35 Yakubu da Yahaya, ‘ya’yan Zabadi, suka kusato shi, suka ce masa, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙe ka.”

36 Sai ya ce musu, “Me kuke so in yi muku?”

37 Suka ce masa, “Ka yardar mana, ranar ɗaukakarka, mu zauna ɗaya a damanka, ɗaya a hagun.”

38 Amma Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Kwa iya sha da ƙoƙon da ni zan sha? Ko kwa iya a yi muku baftisma da baftismar da za a yi mini?”

39 Suka ce masa, “Ma iya.” Sai Yesu ya ce musu, “Ƙoƙon da ni zan sha, da shi za ku sha, baftismar da za a yi mini kuwa, da ita za a yi muku.

40 Amma zama a damana, ko a haguna, ba nawa ba ne da zan bayar, ai, na waɗanda aka riga aka shirya wa ne.”

41 Da almajiran nan goma suka ji haka, suka fara jin haushin Yakubu da Yahaya.

42 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.

43 Ba haka zai zama a tsakaninku ba. Amma duk wanda yake son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku.

44 Wanda duk kuma yake so ya shugabance ku, lalle ne ya zama bawan kowa.

45 Domin Ɗan Mutum ma ya zo ba domin a bauta masa ba, sai dai domin shi ya yi bautar, ya kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”

Bartimawas Makaho Ya Sami Ganin Gari

46 Sai suka iso Yariko. Yana fita daga Yariko ke nan, da shi, da almajiransa, da wani ƙasaitaccen taro, sai ga wani makaho mai bara, wai shi Bartimawas, ɗan Timawas, yana zaune a gefen hanya.

47 Da ya ji dai Yesu Banazare ne, sai ya fara ɗaga murya yana cewa, “Ya Yesu, Ɗan Dawuda, ka ji tausayina!”

48 Waɗansu da yawa suka kwaɓe shi, cewa ya yi shiru. Amma sai ƙara ɗaga murya yake yi ƙwarai da gaske, yana cewa, “Ya Ɗan Dawuda, ka ji tausayina!”

49 Sai Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kirawo shi.” Sai suka kirawo makahon suka ce masa, “Albishirinka! Taso, yana kiranka.”

50 Sai ya yar da mayafinsa, ya zaburo wurin Yesu.

51 Yesu ya ce masa, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce masa, “Malam, in sami gani!”

52 Sai Yesu ya ce masa, “Yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan take ya gani, ya bi Yesu, suka tafi.

Categories
MAR

MAR 11

Mutanen Urushalima Sun Marabci Yesu

1 Da suka kusato Urushalima, da Betafaji, da Betanya, wajen Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa biyu,

2 ya ce musu, “Ku shiga ƙauyen can da yake gabanku. Da shigarku za ku ga wani aholaki a ɗaure, wanda ba a taɓa hawa ba. Ku kwanto shi.

3 Kowa ya ce muku, ‘Don me kuke haka?’ ku ce, ‘Ubangiji ne yake bukatarsa, Zai kuma komo da shi nan da nan.’ ”

4 Sai suka tafi, suka tarar da aholakin a ɗaure a ƙofar gida a bakin hanya, suka kwance shi.

5 Sai waɗanda suke tsaitsaye a gun suka ce musu, “Don me kuke kwance aholakin nan?”

6 Suka faɗa musu abin da Yesu ya ce. Su kuwa suka ƙyale su suka tafi.

7 Suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfiɗa mayafansu a kai, ya hau.

8 Sai mutane da yawa suka shisshimfiɗa mayafansu a hanya, waɗansu kuma suka baza ganyen da suka kakkaryo a saura.

9 Da na gaba da na baya suka riƙa sowa suna cewa, “Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji!

10 Albarka ta tabbata ga mulkin nan mai zuwa na ubanmu Dawuda! Hosanna ga Allah!”

11 Sai ya shiga Urushalima, ya shiga Haikalin. Da dai ya dudduba kome, da yake magariba ta yi, ya fita ya tafi Betanya tare da goma sha biyun nan.

La’antar da Itacen Ɓaure

12 Kashegari da suka tashi daga Betanya, ya ji yunwa.

13 Da ya hango wani itacen ɓaure mai ganye kore shar, sai ya je ya ga ko ya sami ‘ya’ya. Da ya isa wurinsa bai ga kome ba sai ganye, don ba lokacin ‘ya’yan ɓaure ba ne.

14 Sai ya ce wa ɓauren, “Kada kowa ya ƙara cin ‘ya’yanka har abada!” Almajiransa kuwa suna ji.

Yesu Ya Tsabtace Haikalin

15 Suka iso Urushalima. Ya shiga Haikalin ya fara korar masu saye da sayarwa daga ciki, ya kuma birkice teburorin ‘yan canjin kuɗi da kujerun masu sayar da tattabarai,

16 ya kuma hana kowa ratsa Haikalin ɗauke da wani abu.

17 Sai ya yi musu gargaɗi ya ce, “Ashe, ba a rubuce yake ba cewa, ‘Za a kira masujadata ɗakin addu’a na dukkan al’ummai’? Amma ku kun maishe shi kogon ‘yan fashi.”

18 Da manyan firistoci da malaman Attaura suka ji wannan magana suka kuma nemi hanyar hallaka shi, saboda sun tsorata da shi, don duk jama’a na mamaki da koyarwa tasa.

19 Kowace yamma kuwa Yesu yakan fita gari.

Aya a kan Bushewar Itacen Ɓaure

20 Suna wucewa da safe, sai suka ga ɓauren nan ya bushe har saiwarsa.

21 Bitrus kuwa ya tuna, sai ya ce masa, “Ya Shugaba, dubi! Ɓauren nan da ka la’anta ya bushe!”

22 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku gaskata da Allah.

23 Hakika, ina gaya muku, kowa ya ce wa dutsen nan, ‘Ka ciru, ka faɗa teku’, bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata abin da ya faɗa zai auku, sai a yi masa shi.

24 Don haka ina dai gaya muku, kome kuka roƙa da addu’a, ku gaskata cewa samamme ne, za ku kuwa samu.

25 Koyaushe kuka tsaya yin addu’a, in akwai wanda kuke jin haushinsa, ku yafe masa, domin Ubanku da yake Sama shi ma yă yafe muku laifofinku. [

26 Amma in ba kwa yafewa, haka Ubanku da yake Sama ma ba zai yafe muku laifofinku ba.]”

Ana Shakkar Iznin Yesu

27 Suka koma Urushalima. Yana zaga cikin Haikalin sai manyan firistoci, da malaman Attaura, da shugabannin jama’a suka zo wurinsa,

28 suka ce masa, “Da wane izni kake yin waɗannan abubuwa, ko kuwa wa ya ba ka iznin yin haka?”

29 Sai Yesu ya ce musu, “Zan yi muku wata tambaya. Ku ba ni amsa, ni kuwa in gaya muku ko da wane izni nake yin abubuwan nan.

30 To, baftismar da Yahaya ya yi, daga Sama take, ko kuwa ta mutum ce? Ku ba ni amsa.”

31 Sai suka yi muhawara da juna, suka ce, “In muka ce, ‘Daga Sama take,’ sai ya ce, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’

32 Ma kuwa ce, ‘Ta mutum ce’?” Suna kuwa jin tsoron jama’a, don duk kowa ya tabbata, cewa Yahaya annabi ne.

33 Sai suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Yesu ya ce musu, “Haka ni kuma ba zan faɗa muku ko da wane izni nake yin abubuwan nan ba.”

Categories
MAR

MAR 12

Misali na Manoman da Suka Yi Sufurin Garkar Inabi

1 Sai Yesu ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ne ya yi garkar inabi, ya shinge ta, ya haƙa ramin matse inabin, ya kuma gina wata ‘yar hasumiyar tsaro. Ya ba waɗansu manoma sufurin garkar, sa’an nan ya tafi wata ƙasa.

2 Da kakar inabin ta yi, sai ya aiki wani bawansa wurin manoman nan ya karɓo masa gallar garkar.

3 Manoman kuwa suka kama shi, suka yi masa dūka, suka kore shi hanu banza.

4 Sai ya sāke aika musu wani bawa. Shi kuma suka yi masa rotsi, suka wulakanta shi.

5 Ya sāke aiken wani, shi kam, sai suka kashe shi. Haka fa aka yi ta yi da waɗansu da yawa, ana dūkan waɗansu, ana kashe waɗansu.

6 Har yanzu dai yana da sauran ɗaya tak, shi ne makaɗaicin ɗansa. Daga ƙarshe ya aike shi wurinsu, yana cewa, ‘Sā ga girman ɗana.’

7 Amma manoman nan suka ce wa juna, ‘Ai, wannan shi ne magajin. Ku zo mu kashe shi, gādon yă zama namu.’

8 Sai suka kama shi, suka kashe shi, suka jefar da shi bayan shinge.

9 To, me ubangijin garkan nan zai yi? Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba waɗansu garkar.

10 Ashe, ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba? cewa,

‘Dutsen da magina suka ƙi,

Shi ne ya zama mafificin dutsen gini.

11 Wannan aikin Ubangiji ne,

A gare mu kuwa abin al’ajabi ne.’ ”

12 Sai suka nemi su kama shi, don sun lura a kansu ne ya yi misalin, amma suna jin tsoron jama’a. Don haka suka ƙyale shi, suka tafi.

Biyan Haraji ga Kaisar

13 Suka aiko masa da waɗansu Farisiyawa da mutanen Hirudus, don su burma shi cikin magana tasa.

14 Da suka zo, suka ce masa, “Malam, ai, mun sani kai mai gaskiya ne, ba ka kuma zaɓen kowa, domin ka ɗauki kowa da kowa daidai, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi. Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa?

15 Mu biya, ko kada mu biya?” Shi kuwa da ya gane makircinsu, ya ce musu, “Don me kuke jarraba ni? Ku kawo mini dinari in gani.”

16 Suka kawo masa. Ya ce musu, “Suran nan da sunan nan na wane ne?” Suka ce masa, “Na Kaisar ne.”

17 Sai Yesu ya ce musu, “To, ku ba Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah.” Sai suka yi mamakinsa ƙwarai.

Tambaya a kan Tashin Matattu

18 Sai Sadukiyawa (su da suke cewa, wai ba tashin matattu) suka zo wurinsa, suka tambaye shi suka ce,

19 “Malam, Musa dai ya rubuta mana, cewa idan ɗan’uwan mutum ya mutu, ya bar mata tasa ba ɗa, sai lalle mutumin ya auri matar, ya haifa wa ɗan’uwansa ‘ya’ya.

20 To, an yi waɗansu ‘yan’uwa maza guda bakwai. Na farkon ya yi aure, ya mutu bai bar baya ba.

21 Na biyun kuma ya aure ta, shi ma ya mutu, ba ɗa. Na ukun ma haka.

22 Haka dai duk bakwai ɗin, ba wanda ya bar ɗa. Daga ƙarshe kuma ita matar ta mutu.

23 To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu? Don duk bakwai ɗin sun aure ta.”

24 Sai Yesu ya ce musu, “Ba saboda wannan ne ya sa kuka ɓata ba? Wato don ba ku san Littattafai ba, ba ku kuma san ikon Allah ba.

25 Domin in an tashi daga matattu, ba a aure, ba a aurarwa, amma kamar mala’ikun da suke Sama ake.

26 Game da tashin matattu kuma, ashe, ba ku taɓa karantawa a Littafin Musa ba, yadda Allah ya ce masa, ‘Ni ne Allahn Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu’?

27 Ai, waɗanda Allah shi ne Allahnsu rayayyu ne, ba matattu ba. Kun ɓata da gaske.”

Umarni Mafi Girma

28 Sai wani malamin Attaura ya zo ya ji suna muhawara da juna. Da dai ya ga Yesu ya ba su kyakkyawar amsa, sai ya tambaye shi, “Wane umarni ne mafi girma duka?”

29 Yesu ya amsa masa ya ce, “Mafi girma shi ne, ‘Ku saurara, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.

30 Sai ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka, da kuma dukkan ƙarfinka.’

31 Mabiyinsa shi ne, ‘Ka ƙaunaci ɗan’uwanka kamar kanka.’ Ba fa sauran wani umarni da ya fi waɗannan girma.”

32 Sai malamin Attaura ya ce masa, “Hakika gaskiyarka Malam, Ubangiji ɗaya ne, ba kuwa wani sai shi.

33 A ƙaunace shi kuma da dukkan zuciya, da dukan hankali, da dukkan ƙarfi, a kuma ƙaunaci ɗan’uwa kamar kai, ai, ya fi dukkan hadayar ƙone-ƙone da yanke-yanke nesa.”

34 Da Yesu ya ga ya yi masa magana da fasaha, sai ya ce masa, “Ba ka nesa da Mulkin Allah.” Bayan wannan kuma ba wanda ya yi ƙarfin halin sāke tambayarsa wani abu.

Tambaya a kan Ɗan Dawuda

35 Sa’ad da Yesu yake koyarwa a Haikalin sai ya ce, “Ƙaƙa malaman Attaura za su ce Almasihu ɗan Dawuda ne?

36 Domin Dawuda kansa, ta ikon Ruhu Mai Tsarki ya ce,

‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,

Zauna a damana,

Sai na ɗora ka a kan maƙiyanka.’

37 Dawuda da kansa ya kira shi Ubangiji. To, ƙaƙa zai zama ɗansa?” Babban taron mutane kuwa sun saurare shi da murna.

Yesu Ya Fallashi Malaman Attaura

38 A koyarwa tasa har ya ce, “Ku yi hankali da malaman Attaura, masu son yawo da manyan riguna, suna so a gaishe su a kasuwa,

39 da kuma mafifitan mazaunai a majami’u, da mazaunan alfarma a wurin biki.

40 Su ne masu cin kayan matan da mazansu suka mutu, da yin doguwar addu’a don ɓad da sawu. Su za a yi wa hukunci mafi tsanani.”

Baiko Wadda aka Zuba

41 Sai ya zauna gaban baitulmalin Haikalin, yana duban yadda jama’a suke zuba kuɗi a ciki. Waɗansu masu arziki da yawa suna zuba kuɗi masu tsoka.

42 Sai ga wata gajiyayyiya da mijinta ya mutu ta zo, ta zuba rabin kobo biyu a ciki, wato kobo ke nan.

43 Sai ya kira almajiransa, ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, abin da gajiyayyiya gwauruwan nan ta zuba cikin baitulmalin nan ya fi na sauran duka.

44 Su duk sun bayar daga yalwa tasu ne, ita kuwa daga cikin rashinta ta ba da duk abin da take da shi, duk ma da kuɗinta na abinci.”

Categories
MAR

MAR 13

Yesu Ya Faɗi irin Rushewar da za Ta Sami Haikalin

1 Yesu na fita daga Haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam, dubi irin duwatsun nan da gine-ginen nan!”

2 Sai Yesu ya ce masa, “Ka ga manyan gine-ginen nan? Ba wani dutsen da za a bari nan a kan ɗan’uwansa, da ba za a baje shi ba.”

Farkon Azaba

3 Yana zaune a kan Dutsen Zaitun wanda yake kallon Haikalin sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawas suka tambaye shi a keɓe suka ce.

4 “Gaya mana yaushe za a yi waɗannan abubuwa? Wace alama kuma za a gani sa’ad da suke shirin aukuwa?”

5 Sai Yesu ya fara ce musu, “Ku kula fa kada kowa ya ɓad da ku.

6 Mutane da yawa za su zo da sunana, suna cewa su ne ni, har su ɓad da mutane da yawa.

7 In kuma kun jin labarin yaƙe-yaƙe da jita-jitarsu, kada hankalinku ya tashi. Lalle ne wannan ya auku, amma ƙarshen tukuna.

8 Al’umma za ta tasar wa al’umma, mulki ya tasar wa mulki. Za a yi ta raurawar ƙasa a wurare dabam dabam, da kuma yunwa. Amma fa duk wannan masomin azaba ne tukuna.

9 “Amma ku kula da kanku, don za su kai ku gaban majalisa, a kuma yi muku dūka a majami’u. Za a kuma kai ku gaban mahukunta da sarakuna saboda sunana, domin ku ba da shaida a gabansu.

10 Amma lalle sai an fara yi wa dukan al’ummai bishara.

11 Sa’ad da suka kai ku gaban shari’a suka miƙa ku, kada ku damu kan abin da za ku faɗa. Amma duk abin da aka yi muku baiwa da shi a lokacin nan, shi za ku faɗa, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne.

12 Ɗan’uwa zai ba da ɗan’uwansa a kashe shi, uba kuwa ɗansa. ‘Ya’ya kuma za su tayar wa iyayensu har su sa a kashe su.

13 Kowa kuma zai ƙi ku saboda sunana. Amma duk wanda ya jure har ƙarshe zai cetu.”

Matsananciyar Wahala

14 “Sa’ad da kuka ga an kafa mummunan aikin saɓo mai banƙyama a wurin da bai kamata ba (mai karatu fa yă fahimta), to, sai waɗanda suke ƙasar Yahudiya su gudu su shiga duwatsu.

15 Wanda yake kan soro kuma kada yă sauko yă shiga gida garin ɗaukar wani abu.

16 Wanda yake gona kuma kada ya koma garin ɗaukar mayafinsa.

17 Kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokaci!

18 Ku yi addu’a kada abin nan ya auku da damuna.

19 A lokacin nan za a yi wata matsananciyar wahala, irin wadda ba a taɓa yi ba tun farkon halittar da Allah ya yi, har ya zuwa yanzu, ba kuwa za a ƙara yi ba har abada.

20 Da ba don Ubangiji ya taƙaita kwanakin nan ba, da ba ɗan adam ɗin da zai tsira. Amma sabili da zaɓaɓɓun nan da ya zaɓa, sai ya taƙaita kwanakin.

21 To, a lokacin nan kowa ya ce muku, ‘Kun ga, ga Almasihu nan!’ ko, ‘Kun ga, ga shi can!’ kada ku yarda.

22 Don almasihan ƙarya da annabawan ƙarya za su firfito, su nuna alamu da abubuwan al’ajabi, don su ɓad da ko da zaɓaɓɓu ma, in zai yiwu.

23 Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.”

Komowar Ɗan Mutum

24 “Amma lokacin nan, wato bayan tsabar wahalan nan, za a duhunta rana, wata kuma ba zai yi haske ba.

25 Taurari za su riƙa faɗawa daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.

26 A sa’an nan ne za a ga Ɗan Mutum na zuwa cikin gajimare, da iko mai girma da ɗaukaka.

27 Sa’an nan zai aiko mala’ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga gabas da yamma, kudu da arewa, wato daga iyakar duniya har ya zuwa iyakar sama.”

Aya a kan Itacen Ɓaure

28 “Ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa sun fara sakuwa, suna toho, kun san damuna ta yi kusa ke nan.

29 Haka kuma sa’ad da kuka ga waɗannan abubuwa na aukuwa, ku sani ya kusato, a bakin ƙofa ma yake,

30 Hakika, ina gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun auku.

31 Sararin sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za ta shuɗe ba.”

Ba Wanda Ya San Ranar ko Sa’ar

32 “Amma fa wannan rana ko wannan sa’a ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke Sama, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.

33 Ku kula, ku zauna a faɗake, kuna addu’a, domin ba ku san sa’ar da lokacin zai yi ba.

34 Kamar mutum ne mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta yaransa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai jiran ƙofa ya zauna a faɗake.

35 To, ku zauna a faɗake fa, don ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne,

36 kada ya zo kwaram, ya samu kuna barci.

37 Abin kuwa da na gaya muku, ina gaya wa kowa ne, shi ne ku zauna a faɗake.”