Categories
MAR

MAR 14

Shugabanni sun Ƙulla Shawara Gāba da Yesu

1 Sauran kwana biyu a yi Idin Ƙetarewa da idin abinci marar yisti, sai manyan firistoci da malaman Attaura suka nemi hanyar kama Yesu da makirci, su kashe shi,

2 don sun ce, “Ba dai a lokacin idi ba, don kaɗa jama’a su yi hargitsi.”

An Shafi Yesu da Man Ƙanshi a Betanya

3 Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana cin abinci ke nan, sai ga wata mace ta zo da wani ɗan tulu na man ƙanshi na nardi tsantsa, mai tsadar gaske. Sai ta fasa ulun, ta tsiyaye masa man a kā.

4 Waɗansu kuwa da suka ji haushi, suka ce wa juna, “Mene ne na ɓata mai haka?

5 Gama da ma an sayar da shi fiye da dinari ɗari uku, an ba gajiyayyu!” Sai suka hasala da ita, suna gunaguni.

6 Amma Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta. Don me kuke damunta? Ai, alheri ta yi mini, na gaske kuwa.

7 Kullum kuna tare da gajiyayyu, ko yaushe kuma kuke so, kwa iya yi musu alheri, amma ba kullum ne kuke tare da ni ba.

8 Ta yi iyakacin ƙoƙarinta. Ta shafe jikina da mai gabannin jana’izata.

9 Hakika kuwa ina gaya muku, duk inda za a yi bishara a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa domin tunawa da ita.”

Yahuza Ya Yarda Ya Ba da Yesu

10 Sai Yahuza Iskariyoti, ɗaya daga cikin sha biyun nan, ya je wurin manyan firistoci don ya bashe shi a gare su.

11 Da suka ji haka suka yi murna, har suka yi alkawarin su ba shi kuɗi. Shi kuwa ya riƙa neman hanyar bashe shi.

Yesu Ya Ci Idin Ƙetarewa tare da Almajiransa

12 A ranar farko ta idin abinci marar yisti, wato ran da aka saba yanka ɗan ragon Idin Ƙetarewa, sai almajiransa suka ce masa, “Ina kake so mu je mu shirya maka cin Idin Ƙetarewa?”

13 Sai ya aiki almajiransa biyu, ya ce musu, “Ku shiga gari, can za ku gamu da wani mutum ɗauke da tulun ruwa, ku bi shi.

14 Duk gidan da ya shiga, ku ce wa maigidan, ‘In ji Malam, ina masaukin da zai ci Idin Ƙetarewa da almajiransa?’

15 Shi kuwa zai nuna muku wani babban soron bene mai kaya a shirye. A nan za ku shirya mana.”

16 Sai almajiran suka tashi, suka shiga gari, suka kuwa tarar kamar yadda ya faɗa musu, suka shirya Idin Ƙetarewa.

17 Da magariba ta yi, sai ya zo tare da sha biyun nan.

18 Suna cin abinci ke nan, sai Yesu ya ce, “Hakika, ina gaya muku, ɗayanku zai bashe ni, wanda muke ci tare.”

19 Suka fara baƙin ciki, suna ce masa da ɗaya ɗaya, “Ni ne?”

20 Sai ya ce musu, “Ɗaya daga cikin sha biyun nan ne dai, wanda muke ci ƙwarya ɗaya.

21 Ga shi, Ɗan Mutum zai tafi ne, yadda labarinsa yake a rubuce, duk da haka kuwa, kaiton mutumin nan da yake ba da Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da zai fiye masa.”

Cin Jibin Ubangiji

22 Suna cikin cin abinci, sai ya ɗauki gurasa, ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya ba su, ya ce, “Ungo, wannan jikina ne.”

23 Sai ya ɗauki ƙoƙo kuma, bayan ya yi godiya ga Allah, ya ba su, dukkansu kuwa suka shassha.

24 Sa’an nan ya ce musu, “Wannan jinina ne na tabbatar da alkawari, wanda za a bayar saboda mutane da yawa.

25 Hakika, ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabi ba, sai dai a ranan nan da zan sha wani sabo a Mulkin Allah.”

26 Da suka yi waƙar yabon Allah, sai suka fita suka tafi Dutsen Zaitun.

Bitrus Zai Yi Musun Sanin Yesu

27 Yesu ya ce musu, “Duk za ku yi tuntuɓe ne, domin a rubuce yake cewa, ‘Zan bugi makiyayi, tumaki kuwa su fasu.’

28 Amma fa bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa ƙasar Galili.”

29 Bitrus ya ce masa, “Ko duk sun yi tuntuɓe, ni kam, ba zan yi ba.”

30 Sai Yesu ya ce masa, “Hakika, ina gaya maka, ko a wannan dare, kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sanina sau uku.”

31 Amma Bitrus ya yi ta nanatawa da ƙarfi yana cewa, “Ko da za a kashe ni tare da kai, ba zan yi musun saninka ba.” Dukansu ma haka suka ce.

Yesu Ya Yi Addu’a a Gatsemani

32 Sai suka isa wani wuri, wai shi Getsamani. Ya ce wa almajiransa, “Ku zauna nan har in yi addu’a.”

33 Sai ya ɗauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, ya kuma fara jin wahala gaya, yana damuwa ƙwarai.

34 Sai ya ce musu, “Raina na shan wahala matuƙa, har ma kamar na mutu. Ku dakata nan, ku zauna a faɗake.”

35 Da ya ci gaba kaɗan, sai ya faɗi ƙasa, ya yi addu’a ko ya yiwu a ɗauke masa wannan lokaci.

36 Sa’an nan ya ce, “Ya Abba, Uba, kowane abu mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini ƙoƙon wahalan nan. Duk da haka dai ba nufina ba, sai naka.”

37 Ya komo ya samu suna barci, sai ya ce wa Bitrus, “Bitrus, barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a faɗake ko da sa’a ɗaya ba?

38 Ku zauna a faɗake, ku yi addu’a kada ku faɗa ga gwaji. Lalle ruhu ya ɗauka, amma jiki rarrauna ne.”

39 Sai ya sāke komawa, ya yi addu’a, yana maimaita maganar dā.

40 Har wa yau kuma ya sāke dawowa, ya samu suna barci, don duk barci ya cika musu ido ƙwarai, sun kuwa rasa abin da za su ce masa.

41 Ya sāke komowa zuwa na uku, ya ce musu, “Har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka. Lokaci ya yi. An ba da Ɗan Mutum ga masu zunubi.

42 Ku tashi mu tafi. Kun ga, ga mai bashe ni ɗin nan ya matso!”

An Ba da Yesu, an Kama Shi

43 Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, ɗaya daga cikin sha biyun nan, da taron mutane riƙe da takuba da kulake, manyan firistoci, da malaman Attaura, da shugabanni ne suka turosu.

44 To, mai bashe shi ɗin nan ya riga ya ƙulla da su cewa, “Wanda zan yi wa sumba, shi ne mutumin. Ku kama shi, ku tafi da shi a rirriƙe.”

45 Da zuwansa kuwa ya zo wurin Yesu, ya ce masa, “Ya shugaba!” sai ya yi ta sumbantarsa.

46 Su kuwa suka danƙe Yesu, suka kama shi.

47 Amma ɗaya daga cikin na tsaye, ya zaro takobinsa, ya kai wa bawan babban firist sara, ya dauke masa kunne.

48 Sai Yesu ya ce musu, “Kun fito ne da takuba da kulake ku kama ni kamar ɗan fashi?

49 Kowace rana ina tare da ku a Haikalin ina koyarwa, amma ba ku kama ni ba. Amma an yi haka ne fa domin a cika Littattafai.”

50 Daga nan duk almajiran suka yashe shi, suka yi ta kansu.

Saurayin da Ya Gudu

51 Sai wani saurayi, daga shi sai mayafi, ya bi shi. Suka kai masa cafka,

52 shi kuwa ya bar musu mayafin, ya gudu huntu.

Yesu a gaban ‘Yan Majalisa

53 Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. Duk manyan firistoci da shugabanni da malaman Attaura suka taru a wurinsa.

54 Bitrus kuma ya bi shi daga nesa nesa, har cikin gidan babban firist ɗin, ya zauna cikin dogaran Haikali, yana jin wuta.

55 To, manyan firistoci da ‘yan majalisa duka suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi, amma ba su samu ba.

56 Da yawa kam, sun yi masa shaidar zur, amma bakinsu bai zo ɗaya ba.

57 Daga baya kuma waɗansu suka taso, suka yi masa shaidar zur suka ce,

58 “Mun ji ya ce, wai zai rushe Haikalin nan da mutane suka gina, ya gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba.”

59 Duk da haka dai shaida tasu ba ta zo ɗaya ba.

60 Sai babban firist ya miƙe a tsakiyarsu ya tambayi Yesu ya ce, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”

61 Amma yana shiru abinsa, bai amsa kome ba. Sai babban firist ɗin ya sāke tambayarsa, “To, ashe, kai ɗin nan ne Almasihu Ɗan Maɗaukaki?”

62 Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum zaune dama ga Mai Iko, yana kuma zuwa cikin gajimare.”

63 Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa, ya ce, “Wace shaida kuma za mu nema?

64 Kun dai ji saɓon da ya yi! Me kuka gani?” Duk suka yanke masa shari’a a kan ya cancanci kisa.

65 Waɗansu ma suka fara tattofa masa yau, suka ɗaure masa idanu, suka bubbuge shi, suna ce masa, “Yi annabci!” Dogaran Haikali kuma suka yi ta marinsa.

Bitrus Ya Yi Musun Sanin Yesu

66 Bitrus kuwa na ƙasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo.

67 Da ta ga Bitrus na jin wuta, ta zura masa ido, ta ce, “Kai ma, ai, tare kake da Banazaren nan Yesu!”

68 Amma ya musa ya ce, “Ni ban ma san abin da kike faɗa ba, balle in fahimta.” Sai ya fito zaure. Zakara kuwa ya yi cara.

69 Sai baranyar ta gan shi, ta sāke ce wa waɗanda suke tsaitsaye a wurin, “Wannan ma nasu ne.”

70 Amma ya sāke musawa. Jim kaɗan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus, “Lalle kai ma ɗayansu ne, don Bagalile ne kai.”

71 Sai ya fara la’antar kansa, yana ta rantserantse, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan da kuke faɗa ba.”

72 Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu. Bitrus kuwa ya tuna da maganar da Yesu ya faɗa masa cewa, “Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sanina sau uku.” Ko da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.

Categories
MAR

MAR 15

Yesu a gaban Bilatus

1 Da wayewar gari sai manyan firistoci da shugabanni, da malaman Attaura, da dukkan ‘yan majalisa suka yi shawara. Sai suka ɗaure Yesu, suka tafi da shi, suka ba da shi ga Bilatus.

2 Bilatus ya tambaye shi, “Ashe, kai ɗin nan kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa masa ya ce, “Yadda ka faɗa.”

3 Sai manyan firistoci suka yi ta kai ƙararsa a kan abubuwa da yawa.

4 Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba ka da wata amsa? Dubi yawan maganganu da suke ba da shaida a kanka!”

5 Yesu dai har yanzu bai yi wata magana ba, har Bilatus ya yi mamaki.

An Hukunta wa Yesu Mutuwa

6 To, a lokacin idi kuwa Bilatus ya saba sakar musu kowane ɗan sarƙa guda da suka roƙa.

7 Akwai wani wai shi Barabbas da yake ɗaure, tare da waɗansu ‘yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin tawayen.

8 Jama’a fa suka matso, suka fara roƙon Bilatus ya yi musu abin da ya saba yi.

9 Sai ya amsa musu, ya ce, “Wato kuna so ne in sakar muku Sarkin Yahudawa?”

10 Don ya gane, saboda hassada ne manyan firistoci suka bashe shi.

11 Amma manyan firistocin suka zuga jama’a, gwamma ya sakar musu Barabbas.

12 Sai Bilatus ya sāke ce musu, “To, ƙaƙa zan yi da wanda kuke kira Sarkin Yahudawa?”

13 Sai suka sāke yin ihu suka ce, “A gicciye shi!”

14 Bilatus ya ce musu, “Ta wane hali? Wane mugun abu ne ya yi?” Amma su, sai ƙara ɗaga murya suke yi, suna cewa, “A gicciye shi!”

15 Bilatus kuwa da yake yana son ƙayatar da jama’a, ya sakar musu Barabbas. Bayan ya yi wa Yesu bulala, ya ba da shi a gicciye shi.

Sojoji Sun Yi wa Yesu Ba’a

16 Sai soja suka tafi da shi cikin fada, wato fadar mai mulkin, suka tara dukkan rundunar soja.

17 Suka yafa masa wata alkyabba mai ruwan jar garura, suka kuma yi wani kambi na ƙaya, suka sa masa a kā.

18 Sai suka fara gaishe shi, “Ranka ya daɗe, Sarkin Yahudawa!”

19 Suka riƙa ƙwala masa sanda a ka, suna tattofa masa yau, sa’an nan suka durƙusa, wai suna masa ladabi.

20 Da suka gama yi masa ba’a haka, suka yaye masa alkyabba mai ruwan jar garura, suka sa masa nasa tufafi, suka kai shi waje don su gicciye shi.

An Gicciye Yesu

21 Sai ga wani mai wucewa, wai shi Saminu Bakurane, uban Iskandari da Rufas, yana zuwa daga ƙauye. Suka fa tilasta masa ya ɗauki gicciyen Yesu.

22 Suka kai Yesu wani wuri wai shi Golgota, wato wurin ƙoƙon kai.

23 Suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, amma ya ƙi sha.

24 Sa’an nan suka gicciye shi, suka rarraba tufafinsa a junansu, suna kuri’a a kansu, su ga abin da kowa zai samu.

25 Da ƙarfe tara na safe suka gicciye shi.

26 Aka kuma rubuta sanarwar laifinsa sama da shi, wato “Sarkin Yahudawa.”

27 Suka kuma gicciye ‘yan fashi biyu tare da shi, ɗaya dama da shi, ɗaya kuma a hagun. [

28 Wannan shi ne cikar Nassin nan da ya ce, “An lasafta shi a cikin masu laifi.”]

29 Masu wucewa suka yi ta yi masa baƙar magana, suna kaɗa kai, suna cewa, “Ahaf! kai da za ka rushe Haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku,

30 to, sauko daga gicciyen, ka ceci kanka mana!”

31 Haka kuma manyan firistoci da malaman Attaura suka riƙa yi masa ba’a a junansu suna cewa, “Ya ceci waɗansu, ya kuwa kasa ceton kansa,

32 Almasihun nan, Sarkin Isra’ila, yă sauko mana daga gicciyen yanzu, mu kuwa mu gani mu ba da gaskiya.” Waɗanda aka gicciye tare da shi su ma suka zazzage shi.

Mutuwar Yesu

33 Daidai rana tsaka, sai duhu ya rufe ƙasa duka, har zuwa ƙarfe uku na yamma.

34 Da ƙarfe ukun sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktāna?” wato “Ya Allahna, Ya Allahna, don me ka yashe ni?”

35 Da waɗansu na tsaitsayen suka ji haka, suka ce, “Kun ji yana kiran Iliya.”

36 Sai ɗayansu ya yiwo gudu, ya jiƙo wani soso da ruwan tsami, ya soka a sanda, ya miƙa masa yă sha, yana cewa, “Bari mu gani ko Iliya zai zo ya sauko da shi.”

37 Sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi, kana ya cika.

38 Sa’an nan labulen da yake cikin Haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa.

39 Sa’ad da jarumi ɗin da yake tsaye yana kallon Yesu, ya ga yadda ya mutu haka, sai ya ce, “Hakika mutumin nan Ɗan Allah ne!”

40 Akwai kuma waɗansu mata da suke hange daga nesa, cikinsu da Maryamu Magadaliya, da Maryamu uwar Yakubu ƙarami da Yusufu, da kuma Salome,

41 su ne waɗanda suka biyo shi, sa’ad da yake ƙasar Galili, suna yi masa hidima, da kuma mata da yawa da suka rako shi Urushalima.

Jana’izar Yesu

42 La’asar lis, da yake ranar shiri ce, wato gobe Asabar,

43 Yusufu ya zo, mutumin Arimatiya, wani ɗan majalisa mai mutunci, wanda shi ma yake sauraron bayyanar Mulkin Allah, ya yi ƙarfin hali ya shiga wurin Bilatus, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.

44 Bilatus ya yi mamaki ko ya mutu. Sai ya kira jarumin ɗin, ya tambaye shi ko Yesu ya jima da mutuwa.

45 Da ya san haka daga bakin jarumin ɗin sai ya bai wa Yusufu jikin.

46 Sai Yusufu ya sayi likkafanin lilin. Da ya sauko da Yesu, ya sa shi a likkafanin lilin ɗin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe dutse aka yi, ya kuma mirgina wani dutse a bakin kabarin.

47 Maryamu Magadaliya da Maryamu uwar Yusufu sun ga inda aka sa shi.

Categories
MAR

MAR 16

Tashin Yesu daga Matattu

1 Da Asabar ta wuce, Maryamu Magadaliya, da Maryamu uwar Yakubu, da kuma Salome, suka sayo kayan ƙanshi, domin su je su shafa masa.

2 A ranar farko ta mako, da assussuba suka tafi kabarin, da fitowar rana sai suka isa.

3 Suna ce wa juna, “Wa zai mirgine mana dutsen nan daga bakin kabarin?”

4 Da suka ɗaga kai, suka ga, ashe, an mirgine dutsen waje ɗaya, ga shi kuwa, ƙato ne ƙwarai.

5 Suna shiga kabarin, sai suka ga wani saurayi a zaune daga dama, saye da farar riga. Sai suka firgita.

6 Shi kuwa ya ce musu, “Kada ku firgita. Yesu Banazare kuke nema, wanda aka gicciye. Ai, ya tashi, ba ya nan. Kun ga ma wurin da suka sa shi!

7 Amma ku tafi ku gaya wa almajiransa, duk da Bitrus, cewa zai riga ku zuwa ƙasar Galili, a can ne za ku gan shi, kamar yadda ya faɗa muku.”

8 Sai suka fita, suka ruga a guje daga kabarin, suna rawar jiki a ruɗe. Ba su kuma ce wa kowa kome ba, domin suna tsoro.

Yesu Ya Bayyana ga Maryamu Magadaliya

[

9 Da ya tashi da rai da wuri ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magadaliya, wadda ya fitar wa da aljannu bakwai.

10 Ita kuwa ta tafi ta faɗa wa waɗanda dā suke tare da shi, ta tarar suna baƙin ciki, suna kuka.

11 Amma da suka ji yana da rai, har ma ta gan shi, sai suka ƙi gaskatawa.

Yesu Ya Bayyana ga Almajirai Biyu

12 Bayan haka ya bayyana da wata kama ga waɗansu biyu daga cikinsu, sa’ad da suke tafiya ƙauye.

13 Suka koma suka gaya wa sauran, su ma kuwa ba su gaskata su ba.

Umarnin Yesu ga Goma Sha Ɗayan

14 Daga baya ya bayyana ga sha ɗayan nan, su kansu, sa’ad da suke cin abinci. Sai ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu da taurinkansu, domin ba su gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi ba.

15 Sai ya ce musu, “Ku tafi ko’ina a duniya, ku yi wa dukkan ‘yan adam bishara.

16 Duk wanda ya ba da gaskiya, aka kuma yi masa baftisma, zai sami ceto. Amma wanda ya ƙi ba da gaskiya za a hukunta shi.

17 Za a ga waɗannan mu’ujizai wurin masu ba da gaskiya, wato da sunana za su fitar da aljannu, za su yi magana da waɗansu baƙin harsuna,

18 za su iya ɗaukar maciji, kowace irin guba kuma suka sha, ba za ta cuce su ba ko kaɗan, za su kuma ɗora wa marasa lafiya hannu, su warke.”

An Ɗauke Yesu zuwa Sama

19 To, bayan da Ubangiji Yesu ya yi musu jawabi, aka ɗauke shi aka kai shi Sama, ya zauna dama ga Allah.

20 Su kuwa suka tafi, suka yi ta wa’azi ko’ina, Ubangiji yana taimakonsu, yana kuma tabbatar da maganarsu ta mu’ujizan nan da suke biye da maganar.]

Categories
LUK

LUK 1

Gabatarwa

1 Tun da yake mutane da yawa sun ɗauka su tsara labarin waɗannan al’amura da suka tabbata a cikinmu,

2 daidai yadda waɗanda suke shaidu tun farkon al’amari, masu hidimar Maganar, suka rattaba mana,

3 da yake kuma na bi diddigin kowane abu daidai tun farko, ni ma dai na ga ya kyautu in rubuta maka su bi da bi, ya mafifici Tiyofalas,

4 domin kă san ingancin maganar da aka sanar da kai baki da baki.

An Yi Faɗin Haihuwar Yahaya Maibaftisma

5 A zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na ƙungiyar Abaija. Yana auren wata a cikin zuriyar Haruna, sunanta Alisabatu.

6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna bin umarnin Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.

7 Amma ba su da ɗa, don Alisabatu bakararriya ce, dukansu biyu kuma sun tsufa.

8 Ana nan, wata rana Zakariya na kan hidima tasa ta firist, a sa’ad da hidimar ta kewayo kan ƙungiyarsu,

9 bisa ga al’adar hidimar firistoci, sai kuri’a ta nuna shi ne mai shiga Haikalin Ubangiji, ya ƙona turare.

10 A lokacin ƙona turare kuwa duk taron jama’a suna waje, suna addu’a,

11 sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, yana tsaye a dama da bagadin ƙona turare.

12 Da Zakariya ya gan shi ya firgita, tsoro ya kama shi.

13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro Zakariya, an karɓi addu’arka, matarka Alisabatu za ta haifa maka ɗa, za ka kuma sa masa suna Yahaya.

14 Za ka yi murna da farin ciki,

Mutane da yawa kuma za su yi farin ciki da haihuwa tasa.

15 Domin zai zama mai girma a wurin Ubangiji,

Ba kuwa zai sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba.

Za a cika shi da Ruhu Mai Tsarki

Tun yana cikin uwa tasa.

16 Zai kuma juyo da Isra’ilawa da yawa ga Ubangiji Allahnsu.

17 Zai riga shi gaba cikin ruhu da iko irin na Iliya.

Yă mai da hankalin iyaye a kan ‘ya’yansu,

Yă kuma juyo da marasa biyayya su bi hikimar adalai,

Ya tanada wa Ubangiji jama’a, ya same su a shirye.”

18 Sai Zakariya ya ce wa mala’ikan, “Ta ƙaƙa zan san haka? Ga ni tsoho, maiɗakina kuma ta kwana biyu.”

19 Sai mala’ikan ya amsa ya ce, “Ni ne Jibra’ilu da yake tsaye a gaban Allah. An aiko ni ne in yi maka magana, in kuma yi maka wannan albishir.

20 To, ga shi, za ka bebance, ba za ka iya magana ba, sai a ran da al’amuran nan suka auku, don ba ka gaskata maganata ba, za a kuwa cika ta a lokacinta.”

21 Jama’a suna ta jiran Zakariya, suna mamakin jinkirinsa a Haikali.

22 Da ya fito, ya kāsa yi musu magana. Sai suka gane lalle an yi masa wahayi ne a Haikalin. Sai ya riƙa yi musu nuni, amma ba ya magana.

23 Sa’ad da kuma kwanakin hidimarsa suka cika, ya koma gida.

24 Bayan kwanakin nan mata tasa Alisabatu ta yi ciki. Sai ta riƙa ɓuya har wata biyar, tana cewa,

25 “Haka Ubangiji ya yi mini a kwanakin da ya dube ni da rahama, domin yă kawar mini da wulakanci a wurin mutane.”

An Yi Faɗin Haihuwar Yesu

26 A wata na shida Allah ya aiko mala’ika Jibra’ilu zuwa wani gari a ƙasar Galili, wai shi Nazarat,

27 gun wata budurwa da aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu, na zuriyar Dawuda, sunan budurwar kuwa Maryamu.

28 Sai mala’ikan ya je wurinta, ya ce, “Salama alaikun, yake zaɓaɓɓiya, Ubangiji yana tare da ke!”

29 Amma ta damu ƙwarai da maganar, ta yi ta tunani ko wannan wace irin gaisuwa ce.

30 Mala’ikan kuma ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.

31 Ga shi kuma, za ki yi ciki, ki haifi ɗa, ki kuma sa masa suna Yesu.

32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki.

Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dawuda,

33 Zai kuma mallaki zuriyar Yakubu har abada,

Mulkinsa kuwa ba shi da matuƙa.”

34 Sai Maryamu ta ce wa mala’ikan, “Ƙaƙa wannan zai yiwu, tun da yake ba a kai ni ɗaki ba?”

35 Mala’ikan ya amsa mata ya ce,

“Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki,

Ikon Maɗaukaki kuma zai lulluɓe ki.

Saboda haka Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.

36 Ga shi kuma, ‘yar’uwarki Alisabatu ma ta yi cikin ɗa namiji da tsufanta, wannan kuwa shi ne watanta na shaida, ita da ake ce wa bakararriya.

37 Ba wata faɗar Allah da za ta kasa cika.”

38 Sai Maryamu ta ce, “To, ga shi, ni baiwar Ubangiji ce, yă zama mini yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tashi daga gare ta.

Maryamu ta Ziyarci Alisabatu

39 A kwanakin nan Maryamu ta tashi da hanzari, ta tafi wata ƙasa mai duwatsu, zuwa wani gari na ƙasar Yahuza.

40 Ta shiga gidan Zakariya ta gai da Alisabatu.

41 Sai ya zamana da Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, jariri ya motsa da ƙarfi a cikinta. Aka kuwa cika Alisabatu da Ruhu Mai Tsarki,

42 har ta tā da murya da ƙarfi, ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata, ɗan cikinki kuma mai albarka ne!

43 Ta yaya wannan alheri ya same ni, har da uwar Ubangijina za ta zo gare ni?

44 Domin kuwa da jin muryarki ta gaisuwa a kunnena, sai jaririn ya motsa da ƙarfi a cikina domin farin ciki.

45 Albarka tā tabbata ga wadda ta gaskata, domin za a cika abubuwan da Ubangiji ya aiko a faɗa mata.”

Waƙar Maryamu

46 Sai Maryamu ta ce,

“Zuciyata na ɗaukaka shi, Ubangiji,

47 Allah Mai Cetona, da shi ruhuna yake ta farin ciki,

48 Domin fa shi ya dubi ƙasƙancin baiwa tasa.

Ga shi, jama’a ta dukan zamanai,

Za su ce mini mai albarka ce nan gaba.

49 Domin fa shi da yake Mai Iko,

Manyan al’amura ya yi mini,

Sunansa labudda mai tsarki ne.

50 Daga zamanai ya zuwa wani zamani,

Jinƙansa yana ga waɗanda suke tsoronsa.

51 Manyan ayyuka da ya yi,

Masu girmankai, su da dabarbarunsu ya warwatsa.

52 Ya firfitar da sarakuna a sarauta,

Ya ɗaukaka ƙasƙantattu.

53 Mayunwata ya ƙosar da abubuwan alheri,

Mawadata kuwa ya sallame su hannu wofi.

54 Ya taimaka wa baransa Isra’ila,

Domin yana tunawa da jinƙansa.

55 Ya cika faɗarsa ga kakanninmu,

Ga Ibrahim da zuriyarsa, har abada.”

56 Maryamu kuma ta zauna tare da Alisabatu wajen wata uku, sa’an nan ta koma gida.

Haihuwar Yahaya Maibaftisma

57 To, lokacin Alisabatu na haihuwa ya yi, ta kuwa haifi ɗa namiji.

58 Sai maƙwabta da ‘yan’uwanta suka ji yadda Ubangiji ya ji ƙanta ƙwarai, har suka taya ta farin ciki.

59 Sai ya zamana a rana ta takwas suka zo yi wa ɗan yaron kaciya. A dā za su sa masa sunan ubansa, Zakariya,

60 amma uwa tasa ta ce, “A’a, Yahaya za a sa masa.”

61 Sai suka ce mata, “Ai kuwa, ba wani ɗan’uwanku mai suna haka.”

62 Sai suka alamta wa ubansa, suna neman sunan da yake so a sa masa.

63 Sai ya nema a ba shi allo, sa’an nan ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Duka suka yi mamaki.

64 Nan da nan ya sami baki, kwaɗon harshensa ya saku, ya fara magana, yana yabon Allah.

65 Sai tsoro ya kama dukan maƙwabtansu. Aka yi ta baza labarin duk waɗannan al’amura ko’ina a dukan ƙasa mai duwatsu ta Yahudiya.

66 Duk waɗanda suka ji kuwa suka riƙe a zuciyarsu, suna cewa, “Me ke nan ɗan yaron nan zai zama?” Gama ikon Ubangiji yana tare da shi.

Waƙar Zakariya

67 Sai aka cika ubansa Zakariya da Ruhu Mai Tsarki, ya yi annabci, ya ce,

68 “Ubangiji Allahn Isra’ila,

A gare shi ne lalle yabo yake tabbata,

Domin ya kula, ya yi wa jama’a tasa fansa.

69 Ya ta da Mai Ceto mai iko dominmu,

Daga zuriyar baransa Dawuda.

70 Yadda tuntuni ya faɗa ta bakunan

Annabawa nasa tsarkakan nan,

71 Yă cece mu daga abokan gābanmu,

Har ma daga dukan maƙiyanmu.

72 Domin nuna jinƙai ne ga kakanninmu,

Ya tuna da alkawarinsa mai tsarkin nan.

73 Shi ne rantsuwan nan wadda ya yi wa ubanmu Ibrahim,

74 Domin yana cetonmu daga abokan gābanmu,

Mu bauta masa ba da jin tsoro ba,

75 Sai dai da tsarki da adalci a gabansa,

Dukan iyakar kwanakin nan namu.

76 Kai kuma, ɗan yarona, za a ce da kai annabin Maɗaukaki,

Gama za ka riga Ubangiji gaba,

Domin ka shisshirya hanyoyinsa,

77 Kă sanar da ceto ga jama’a tasa,

Wato ta samun gafarar zunubansu,

78 Saboda tsananin jinƙai na Allahnmu,

Daga Sama hasken asubahi zai ɓullo mana,

Daga can Sama ne fa zai keto mana,

79 Domin yă haskaka na zaune cikin duhu,

Da waɗanda suke zaune a bakin mutuwa,

Domin ya bishe mu a hanyar salama.”

80 Sai ɗan yaron ya girma, ya ƙarfafa a ruhu. Ya kuwa zauna a jeji har ranar bayyanarsa ga Isra’ila.

Categories
LUK

LUK 2

Haihuwar Yesu

1 A kwanakin nan Kaisar Augustas ya yi shela, cewa a rubuta dukkan mutanen da suke ƙarƙashin mulkinsa.

2 Wannan shi ne ƙirga na fari da aka yi a zamanin Kiriniyas, mai mulkin ƙasar Suriya.

3 Kowa sai ya tafi garinsu a rubuta shi.

4 Yusufu shi ma ya tashi daga birnin Nazarat, a ƙasar Galili, ya tafi ƙasar Yahudiya, ya je birnin Dawuda, da ake kira Baitalami (domin shi daga gidan Dawuda ne, na cikin zuriyarsa),

5 don a rubuta shi, duk da Maryamu tashinsa, wadda take kuma da ciki.

6 Sa’ad da suke can kuwa, sai lokacin haihuwarta ya yi.

7 Sai ta haifi ɗanta na fari, ta rufi shi da zanen goyo, ta kuma kwantar da shi a wani komi dabbobi, don ba su sami ɗaki a masaukin ba.

Makiyaya da Mala’iku

8 A wannan yankin ƙasa kuwa waɗansu makiyaya suna kwana a filin Allah, suna tsaron garken tumakinsu da dad dare.

9 Sai ga wani mala’ikan Ubangiji tsaye kusa da su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewayensu, har suka tsorata gaya,

10 Sai mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ga shi, albishir na kawo muku na farin ciki mai yawa, wanda zai zama na dukan mutane.

11 Domin yau an haifa muku Mai Ceto a birnin Dawuda, wanda yake shi ne Almasihu, Ubangiji.

12 Ga alamar da za ku gani, za ku sami jariri rufe da zanen goyo, kwance a komin dabbobi.”

13 Ba labari sai ga taron rundunar Sama tare da mala’ikan nan, suna yabon Allah, suna cewa,

14 “Ɗaukaka ga Allah ta tabbata, can cikin Sama mafi ɗaukaka.

A duniya salama ta tabbata, ga mutanen da yake murna da su matuƙa.”

15 Da mala’iku suka tafi daga gare su suka koma Sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu tafi Baitalami yanzu, mu ga abin nan da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar da mu.”

16 Sai suka tafi da hanzari, suka sami Maryamu da Yusufu, da kuma jaririn kwance a komin dabbobi.

17 Da suka gan shi, suka bayyana maganar da aka faɗa musu game da wannan ɗan yaro.

18 Duk waɗanda suka ji kuma, suka yi ta al’ajabin abin da makiyayan nan suka faɗa musu.

19 Maryamu kuwa sai ta riƙe duk abubuwan da aka faɗa, tana biya su a zuci.

20 Makiyayan suka koma, suna ta ɗaukaka Allah, suna yabonsa, saboda duk abin da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.

Kaciyar Yesu

21 Da rana ta takwas ta kewayo da za a yi masa kaciya, aka sa masa suna Yesu, wato sunan da mala’ika ya faɗa kafin ya zauna a ciki.

Miƙa Yesu a Haikali

22 Da kwanakin tsarkakewarsu suka cika bisa ga Shari’ar Musa, suka kawo shi Urushalima, su miƙa shi ga Ubangiji

23 (kamar dai yadda yake a rubuce a Shari’ar Ubangiji cewa, “Duk ɗan farin da aka haifa, za a ce da shi tsattsarka ne Ubangiji”),

24 su kuma yi hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Shari’ar Ubangiji cewa, “Kurciyoyi biyu, ko kuwa ‘yan shila biyu.”

25 To, akwai wani mutum a Urushalima, mai suna Saminu, adali, mai bautar Allah, yana kuma ɗokin ganin ta’aziyyar Isra’ila. Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.

26 Ruhu Mai Tsarki kuwa ya riga ya bayyana masa, cewa ba zai mutu ba sai ya ga Almasihun Ubangiji.

27 Ruhu na iza shi, sai ya shiga Haikalin. Da iyayen suka shigo da ɗan yaron nan Yesu, su yi masa yadda ka’idar Shari’ar ta ce,

28 sai Saminu ya rungume shi, ya yi wa Allah godiya, ya ce,

29 “Yanzu kam, ya Mamallaki,

Sai ka sallami bawanka lafiya,

Bisa ga abin da ka faɗa,

30 Don na ga cetonka zahiri,

31 Da ka shirya a gaban kabilai duka,

32 Haske mai bayyana wa alummai hanyarka,

Da kuma ɗaukakar jama’arka Isra’ila.”

33 Uwa tasa da ubansa kuwa suna mamakin abin da aka faɗa game da shi,

34 Sai Saminu ya sa musu albarka, ya ce wa Maryamu uwar Yesu,

“Kin ga wannan yaro, shi aka sa ya zama sanadin faɗuwar waɗansu, tashin waɗansu kuma da yawa cikin Isra’ila,

Zai kuma zama alama wadda ake kushenta,

35 Domin tunanin zukata da yawa su bayyana.

I, ke ma, takobi zai tsaga zuciyarki.”

36 Akwai kuma wata annabiya, mai suna Hannatu, ‘yar Fanuyila, na kabilar Ashiru. Ta kuwa tsufa ƙwarai, ta yi zaman aure shekara bakwai bayan ɗaukanta na budurci,

37 da mijinta ya mutu kuma ta yi zaman gwauranci har shekara tamanin da huɗu. Ba ta rabuwa da Haikalin, tana bauta wa Allah dare da rana ta wurin yin addu’a da azumi.

38 Nan take ita ma ta zo, ta yi wa Allah godiya, ta kuma yi maganar ɗan yaron nan ga dukan masu sauraron fansar Urushalima.

Komawa Nazarat

39 Bayan sun ƙare kome da kome bisa ga Shari’ar Ubangiji, sai suka koma ƙasar Galili suka tafi garinsu Nazarat.

40 Ɗan yaron kuwa ya girma, ya kawo ƙarfi, yana mai matuƙar hikima. Alherin Allah kuwa yana tare da shi.

Yesu, Ɗan Saurayi, ya Shiga Haikali

41 To, iyayensa sukan je Urushalima kowace shekara a lokacin Idin Ƙetarewa.

42 Da ya shekara goma sha biyu, sai suka tafi tare da shi bisa ga al’adarsu a lokacin Idi.

43 Da aka gama idin kuma, suna cikin komowa, sai yaron, wato Yesu, ya tsaya a Urushalima, ba da sanin iyayensa ba.

44 Su kuwa suka yi ta tafiya yini guda, suna zaton yana cikin ayari. Sai suka yi ta cigiyarsa cikin ‘yan’uwansu da idon sani.

45 Da ba su same shi ba, suka koma Urushalima, suna ta cigiyarsa.

46 Sai kuma a rana uku suka same shi a Haikalin zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu, yana kuma yi musu tambayoyi.

47 Duk waɗanda suka ji shi kuwa suka yi al’ajabin irin fahimtarsa da amsoshinsa.

48 Da suka gan shi suka yi mamaki, sai uwa tasa ta ce masa, “Ya kai ɗana, yaya ka yi mana haka? Ga shi nan, ni da babanka muna ta nemanka duk ranmu a ɓace.”

49 Sai ya ce musu, “Me ya sa kuka yi ta nemana? Ashe, ba ku sani wajibi ne in yi sha’anin Ubana ba?”

50 Amma ba su fahimci maganar da ya yi musu ba.

51 Sai ya koma Nazarat tare da su, yana yi musu biyayya. Uwa tasa kuwa na riƙe da dukan abubuwan nan a ranta.

52 Yesu kuwa ya yi ta ƙaruwa da hikima, da girma, da kuma tagomashi wurin Allah da mutane.

Categories
LUK

LUK 3

Wa’azin Yahaya Maibaftisma

1 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tibariyas, Buntus Bilatus yana mulkin Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarauta Ituriya da Tarakunitas, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiliya,

2 a zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, Maganar Allah ta zaike wa Yahaya ɗan Zakariya a jeji.

3 Sai ya zaga duk lardin bakin Kogin Urdun, yana wa’azi, cewa mutane su tuba a yi musu baftisma, domin a gafarta musu zunubansu,

4 yadda yake a rubuce a Littafin Annabi Ishaya cewa,

“Muryar mai kira a jeji tana cewa,

Ku shirya wa Ubangiji tafarki,

Ku miƙe hanyoyinsa,

5 Za a cike kowane kwari,

Kowane dutse da kowane tsauni za a baje su.

Za a miƙe karkatattun wurare,

Za a bi da hanyoyin da ba su biyu ba.

6 Dukkan ‘yan adam kuma za su ga ceton Allah.”

7 Saboda haka, Yahaya ya ce wa taron jama’ar da yake zuwa domin ya yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku ku guje wa fushin nan mai zuwa?

8 Ku yi aikin da zai nuna tubanku, kada ma ku ko fara cewa a ranku Ibrahim ne ubanku. Ina dai gaya muku Allah yana da iko ya halitta wa Ibrahim ‘ya’ya daga duwatsun nan.

9 Ko yanzu ma an ɗora bakin gatari a gindin itatuwa. Saboda haka duk itacen da bai yi ‘ya’ya masu kyau ba, sai a sare shi, a jefa a wuta.”

10 Sai taron suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi ke nan?”

11 Ya amsa musu ya ce, “Duk mai taguwa biyu, ya raba da marar ita, mai abinci ma haka.”

12 Masu karɓar haraji ma suka zo a yi musu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”

13 Ya ce musu, “Kada ku karɓi fiye da abin da aka umarce ku.”

14 Waɗansu soja ma suka tambaye shi, “To, mu fa, me za mu yi?” Sai ya ce musu, “Kada ku yi wa kowa ƙwace ko ƙazafi. Ku dai dangana da albashinku.”

15 Da yake mutane duk sun zaƙu, kowa yana wuswasi a ransa a game da Yahaya, ko watakila shi ne Almasihu,

16 sai Yahaya ya amsa wa dukansu ya ce, “Ni kam, da ruwa nake yi muku baftisma, amma wani yana zuwa wanda ya fi ni girma, wanda ko maɓallin takalminsa ma ban isa in ɓalle ba. Shi ne zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki, da kuma wuta.

17 Ƙwaryar shiƙarsa tana hannunsa, zai kuwa share masussukarsa sarai sarai, ya taro alkama ya sa a rumbunsa, amma ɓuntun sai ya ƙone shi a wuta marar mutuwa.”

18 Ta haka, da waɗansu gargaɗi masu yawa, Yahaya ya yi wa jama’a bishara.

19 Amma sarki Hirudus, wanda Yahaya ya tsawata wa a kan maganar Hirudiya, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan mugayen ayyukan da ya yi,

20 sai ya ƙara da kulle Yahaya a kurkuku.

An Yi wa Yesu Baftisma

21 To, da aka yi wa dukan mutane baftisma, Yesu ma aka yi masa baftisma, yana addu’a ke nan, sai sama ta dāre,

22 Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa da wata kama, kamar kurciya. Sai aka ji wata murya daga Sama ta ce, “Kai ne Ɗana ƙaunataccena, ina farin ciki da kai ƙwarai,”

Asalin Yesu

23 Yesu kuwa sa’ad da ya fara koyarwa, yana da shekara wajen talatin. An ɗauke shi a kan, wai shi ɗan Yusufu ne, wanda yake ɗan Heli,

24 Heli ɗan Matat, Matat ɗan Lawi, Lawi ɗan Malki, Malki ɗan Yanna, Yanna ɗan Yusufu,

25 Yusufu ɗan Matatiya, Matatiya ɗan Amos, Amos ɗan Nahum, Nahum ɗan Azaliya, Azaliya ɗan Najaya,

26 Najaya ɗan Ma’ata, Ma’ata ɗan Matatiya, Matatiya ɗan Shimeya, Shimeya ɗan Yusufu, Yusufu ɗan Yahuza,

27 Yahuza ɗan Yowana, Yowana ɗan Refaya, Refaya ɗan Zarubabel, Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, Sheyaltiyel ɗan Niri,

28 Niri ɗan Malki, Malki ɗan Addi, Addi ɗan Kosama, Kosama ɗan Almadama, Almadama ɗan Er,

29 Er ɗan Yosi, Yosi ɗan Eliyezer, Eliyezar ɗan Yorima, Yorima ɗan Matat, Matat ɗan Lawi,

30 Lawi ɗan Saminu, Saminu ɗan Yahuza, Yahuza ɗan Yusufu, Yusufu ɗan Yonana, Yonana ɗan Eliyakim,

31 Eliyakim ɗan Malaya, Malaya ɗan Mainana, Mainana ɗan Matata, Matata ɗan Natan, Natan ɗan Dawuda,

32 Dawuda ɗan Yesse, Yesse ɗan Obida, Obida ɗan Bo’aza, Bo’aza ɗan Salmon, Salmon ɗan Nashon,

33 Nashon ɗan Amminadab, Amminadab ɗan Aram, Aram ɗan Hesruna, Hesruna ɗan Feresa, Feresa ɗan Yahuza,

34 Yahuza ɗan Yakubu, Yakubu ɗan Ishaku, Ishaku ɗan Ibrahim, Ibrahim ɗan Tera, Tera ɗan Nahor,

35 Nahor ɗan Serug, Serug ɗan Reyu, Reyu ɗan Feleg, Feleg ɗan Eber, Eber ɗan Shela,

36 Shela ɗan Kenan, Kenan ɗan Arfakshad, Arfakshad ɗan Shem, Shem ɗan Nuhu, Nuhu ɗan Lamek,

37 Lamek ɗan Metusela, Metusela ɗan Anuhu, Anuhu ɗan Yared, Yared ɗan Mahalel, Mahalel ɗan Kenan,

38 Kenan ɗan Enosh, Enosh ɗan Shitu, Shitu ɗan Adamu, Adamu kuma na Allah.

Categories
LUK

LUK 4

Shaiɗan Ya Gwada Yesu

1 Yesu kuma cike da Ruhu Mai Tsarki sai ya dawo daga Kogin Urdun. Ruhu na iza shi zuwa jeji,

2 har kwana arba’in, Iblis yana gwada shi. A kwanakin nan bai ci kome ba. Da suka ƙare kuwa ya ji yunwa.

3 Iblis ya ce masa, “In dai kai Ɗan Allah ne, ka umarci dutsen nan ya zama gurasa,”

4 Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da gurasa kaɗai mutum zai rayu ba.’ ”

5 Sai Iblis ya kai shi wani wuri a bisa, ya nunnuna masa dukkan mulkokin duniya a ƙyiftawar ido.

6 Iblis ya ce masa, “Kai zan bai wa ikon duk waɗannan, da ɗaukakarsu, don ni aka danƙa wa, nakan kuma bayar ga duk wanda na ga dama.

7 In kuwa za ka yi mini sujada, duk su zama naka.”

8 Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake cewa,

‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada,

Shi kaɗai za ka bauta wa.’ ”

9 Sai kuma ya kai shi Urushalima, ya ɗora shi can kan tsororuwar Haikali, ya ce masa, “In dai kai Ɗan Allah ne, to, dira ƙasa daga nan,

10 don a rubuce yake cewa,

‘Zai yi wa mala’ikunsa umarni game da kai, su kiyaye ka,’

11 da kuma

‘Za su tallafe ka,

Don kada ka yi tuntuɓe da dutse.’ ”

12 Sai Yesu ya amsa masa ya ce, “Ai kuwa an ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’ ”

13 Bayan da Iblis ya gama irin dukan gwaje-gwajensa, ya rabu da shi ɗan lokaci tukuna.

Yesu Ya Fara Hidima a Galili

14 Yesu ya koma ƙasar Galili, ikon Ruhu yana tare da shi. Labarinsa ya bazu a dukan kewayen.

15 Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, duk ana girmama shi.

An Ƙi Yesu a Nazarat

16 Ya zo Nazarat inda aka rene shi. Ya shiga majami’a a ran Asabar kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe domin ya yi karatu.

17 Aka miƙa masa Littafin Annabi Ishaya, ya buɗe littafin, ya sami inda aka rubuta cewa,

18 “Ruhun Ubangiji yana tare da ni,

Domin yā shafe ni in yi wa matalauta bishara.

Ya aiko ni in yi shelar saki ga ɗaurarru,

In kuma buɗe wa makafi ido,

In kuma ‘yanta waɗanda suke a danne,

19 In yi shelar zamanin samun karɓuwa ga Ubangiji.”

20 Ya rufe littafin ya mayar wa mai hidima, ya zauna. Duk waɗanda suke cikin majami’a suka zuba masa ido.

21 Sai ya fara ce musu, “Yau Nassin nan ya cika a kunnenku.”

22 Duk suka yabe shi, suna mamakin maganarsa ta alheri da ya faɗa, har suka ce, “Ashe, wannan ba ɗan Yusufu ba ne?”

23 Yesu ya ce musu, “Lalle za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka.’ Za ku kuma ce mini, ‘Duk abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, ka yi a nan garinku mana.’ ”

24 Ya ce kuma, “Hakika, ina gaya muku, ba annabin da yake yardajje a garinsu.

25 Amma gaskiya nake gaya muku, a zamanin Iliya akwai mata gwauraye da yawa a Isra’ila, wato a lokacin da aka hana ruwan sama har shekara uku da wata shida, sa’ad da babbar yunwa ta game dukan ƙasar.

26 Duk da haka ba a aiki Iliya gun ko ɗaya daga cikinsu ba, sai ga wata mace kaɗai a Zarifat ta ƙasar Sidon wadda mijinta ya mutu.

27 A zamanin Annabi Elisha kuma akwai kutare da yawa a Isra’ila, ba kuwa ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman, mutumin Suriya, kaɗai.”

28 Da suka ji haka, duk waɗanda suke a majami’a suka husata ƙwarai.

29 Sai suka tashi suka fitar da shi bayan gari, har suka kai shi goshin dutsen da aka gina garinsu a kai, don su jefa shi ƙasa.

30 Amma ya ratsa ta tsakiyarsu, ya yi tafiyarsa.

Mai Baƙin Aljan

31 Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a ƙasar Galili, yana koya musu ran Asabar.

32 Suka yi mamakin koyarwarsa domin magana tasa da hakikancewa take.

33 A majami’ar kuwa akwai wani mutum mai baƙin aljan. Sai ya ta da murya da ƙarfi ya ce,

34 “Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne ka hallaka mu? Na san ko wane ne kai, Mai Tsarkin nan ne kai na Allah.”

35 Sai Yesu ya kwaɓe shi ya ce, “Shiru! Rabu da shi!” Bayan da aljanin ya fyaɗa shi ƙasa a tsakiyarsu, ya rabu da shi, bai kuwa cuce shi ba.

36 Sai mamaki ya kama su duka, suna ce wa juna, “Wannan wace irin magana ce? Ga shi, da tabbatarwa, da gabagaɗi kuma yake umartar baƙaƙen aljannu, suna kuwa fita.”

37 Labarinsa duk ya bazu ko’ina a kewayen ƙasar.

Yesu Ya Warkar da Surukar Bitrus

38 Sai ya tashi daga majami’a, ya shiga gidan Bitrus. Surukar Bitrus kuwa tana fama da mugun zazzaɓi, sai suka roƙe shi saboda ita.

39 Sai ya tsaya a kanta, ya tsawata wa zazzaɓin, ya kuwa sake ta. Nan take ta tashi ta yi musu hidima.

Yesu Ya Warkar da Mutane da yawa da Maraice

40 A daidai fāɗuwar rana, duk waɗanda suke da marasa lafiya, masu cuta iri iri, suka kakkawo su wurinsa. Sai ya ɗaɗɗora wa kowannensu hannu, ya warkar da su.

41 Aljannu kuma suka fita daga mutane da yawa, suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya tsawata musu, ya hana su magana, don sun sani shi ne Almasihu.

Yesu Ya Tafi Yin Wa’azi

42 Da gari ya waye ya fita, ya tafi wani wurin inda ba kowa. Sai taro masu yawa suka yi ta nemansa, suka je wurinsa. Sonsu ne su tsaishe shi, don kada ya tashi daga gare su,

43 amma ya ce musu, “Lalle ne in yi wa sauran garuruwa bisharar Mulkin Allah, domin saboda wannan nufi ne aka aiko ni.”

44 Sai ya yi ta yin wa’azi a majami’un ƙasar Galili.

Categories
LUK

LUK 5

An Kama Kifi Jingim

1 Wata rana taro suna matsarsa domin su ji Maganar Allah, shi kuwa yana tsaye a bakin Tekun Janisarata,

2 sai ya hangi ƙananan jirage biyu a bakin tekun, masuntan kuwa sun fita daga cikinsu, suna wankin tarunansu.

3 Sai ya shiga ɗaya jirgin, wanda yake na Bitrus, ya roƙe shi ya ɗan zakuɗa da jirgin daga bakin gaci. Sai ya zauna ya yi ta koya wa taro masu yawa daga jirgin.

4 Da ya gama magana, ya ce wa Bitrus, “Zakuɗa da jirgin zuwa wuri mai zurfi, ku saki tarunanku, ku janyo kifi.”

5 Bitrus ya amsa masa ya ce, “Ya Maigida, dare farai muna wahala, ba mu kama kome ba, amma tun da ka yi magana zan saki tarunan.”

6 Da suka yi haka kuwa, suka kamo kifi jingim, har ma tarunansu suka fara kecewa.

7 Sai suka yafato abokan aikinsu a ɗaya jirgin su zo su taimake su. Suka kuwa zo, suka ciccika jiragen nan duka biyu kamar sa nutse.

8 Da Bitrus ya ga haka, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce. “Ya Ubangiji, wane ni da za ka tsaya kusa da ni, domin ni mutum ne mai zunubi.”

9 Domin shi da waɗanda suke tare da shi duka, mamaki ya kama su saboda kifin nan da suka janyo,

10 haka ma Yakubu da Yahaya ‘ya’yan Zabadi, abokan sabgar Bitrus. Sai Yesu ya ce wa Bitrus, “Kada ka ji tsoro. Nan gaba mutane za ka riƙa kamowa.”

11 Da suka kawo jiragensu gaci, suka bar kome duka suka bi shi.

Yesu Ya Warkar da Kuturu

12 Wata rana Yesu na ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa ya zo. Da ya ga Yesu ya fāɗi a gabansa, ya roƙe shi ya ce, “Ya Ubangiji, in dai ka yarda kana da ikon tsarkake ni.”

13 Sai Yesu ya miƙa hannu, ya taɓa shi, ya ce, “Na yarda, ka tsarkaka.” Nan take sai kuturtar ta rabu da shi.

14 Yesu ya kwaɓe shi kada ya gaya wa kowa, ya ce, “Sai dai ka je wurin firist ya gan ka, ka kuma yi hadaya saboda tsarkakewarka, domin tabbatarwa a gare su, kamar yadda Musa ya umarta.”

15 Amma duk da haka labarinsa sai ƙara yaɗuwa yake yi, har taro masu yawan gaske suka yi ta zuwa domin su saurare shi, a kuma warkar da su daga rashin lafiyarsu.

16 Amma shi, sai ya riƙa keɓanta a wuraren da ba kowa, yana addu’a.

Yesu ya Warkar da Shanyayye

17 Wata rana na koyarwa, waɗansu Farisiyawa kuwa da masanan Attaura da suka fito daga kowane gari na ƙasar Galili, da na ƙasar Yahudiya, daga kuma Urushalima, suna nan a zaune. Ikon Ubangiji na warkarwa kuwa yana nan.

18 Sai ga waɗansu mutane ɗauke da wani shanyayye a kan shimfiɗa, suna ƙoƙari su shigar da shi su ajiye shi a gaban Yesu.

19 Da suka kasa samun hanyar shigar da shi saboda taro, suka hau a kan soron, suka zura shi ta tsakanin rufin soron duk da shimfiɗarsa, suka ajiye shi a tsakiyar jama’a a gaban Yesu.

20 Da Yesu ya ga bangaskiyarsu sai ya ce, “Malam, an gafarta maka zunubanka.”

21 Sai malaman Attaura da Farisiyawa suka fara wuswasi cewa, “Wane ne wannan da yake maganar saɓo? Wa yake iya gafarta zunubi banda Allah shi kaɗai?”

22 Da Yesu ya gane wuswasinsu, ya amsa musu ya ce, “Don me kuke wuswasi haka a zuciyarku?

23 Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuwa a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?

24 Amma domin ku sakankance Ɗan Mutum na da ikon gafarta zunubi a duniya”, sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ka ɗauki shimfiɗarka, ka tafi gida.”

25 Nan take ya tashi a gaban idonsu, ya ɗauki abin kwanciyarsa, ya tafi gida, yana ɗaukaka Allah.

26 Sai suka yi mamaki matuƙa, su duka, suka yi ta ɗaukaka Allah, tsoro kuma ya kama su, suka ce, “Yau mun ga al’ajabai!”

Kiran Lawi

27 Bayan haka ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, a zaune, yana aiki a wurin karɓar haraji. Ya ce masa, “Bi ni.”

28 Sai ya bar kome duka, ya tashi ya bi shi.

29 Sai Lawi ya yi masa ƙasaitacciyar liyafa a gidansa, akwai kuwa taron masu karɓar haraji da waɗansu mutane suna ci tare da su.

30 Sai Farisiyawa da malamansu na Attaura suka yi wa almajiransa gunaguni suka ce, “Don me kuke ci kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”

31 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, lafiyayyu ba ruwansu da magani, sai dai marasa lafiya.

32 Ba domin in kira masu adalci na zo ba, sai dai masu zunubi, su tuba.”

Tambaya a kan Azumi

33 Sai suka ce masa, “Almajiran Yahaya suna azumi a kai a kai, suna kuma addu’a, haka kuma almajiran Farisiyawa, amma naka suna ci suna sha.”

34 Sai Yesu ya ce musu, “Wato kwa iya sa abokan ango su yi azumi tun angon yana tare da su?

35 Ai, lokaci na zuwa da za a ɗauke musu angon. A sa’an nan ne fa za su yi azumi.”

36 Ya kuma yi musu misali, ya ce, “Ba mai tsage ƙyalle a jikin sabuwar tufa ya yi maho a tsohuwar tufa da shi. In ma an yi, ai, sai ya kece sabuwar tufar, sabon ƙyallen kuma ba zai dace da tsohuwar tufar ba.

37 Ba kuma mai ɗura sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. In ma an ɗura, sai sabon ruwan inabin ya fasa salkunan, ya zube, salkunan kuma su lalace.

38 Sabon ruwan inabi, ai, sai sababbin salkuna.

39 Ba wanda zai so shan sabon ruwan inabin bayan ya sha tsohon, don ya ce, ‘Ai, tsohon yana da kyau.’ ”

Categories
LUK

LUK 6

Almajirai suna Zagar Alkama a Ran Asabar

1 Wata rana ran Asabar, yana ratsa gonakin alkama, sai almajiransa suka zāgi alkamar, suna murtsukewa suna ci.

2 Sai waɗansu Farisiyawa suka ce, “Don me kuke yin abin da bai halatta a yi ba a ran Asabar?”

3 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba sa’ad da ya ji yunwa, shi da abokan tafiyarsa?

4 Yadda ya shiga masujadar Allah, ya ɗauki keɓaɓɓiyar gurasan nan ya ci, har ma ya ba abokan tafiyarsa, wadda ba ta halatta kowa ya ci ba, sai firistoci kaɗai?”

5 Sai ya ce musu, “Ai, Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabar.”

Mai Shanyayyen Hannu

6 A wata Asabar kuma ya shiga majami’a, yana koyarwa. Akwai kuwa wani mutum a ciki wanda hannunsa na dama ya shanye.

7 Sai malaman Attaura da Farisiyawa suka yi haƙwansa su ga ko yā warkar a ran Asabar, don su samu su kai ƙararsa.

8 Shi kuwa ya san tunaninsu. Sai ya ce wa mai shanyayyen hannun, “Taso, ka tsaya nan tsakiya.” Sai ya tashi, ya tsaya a wurin.

9 Yesu ya ce musu, “Ina yi muku tambaya. Ya halatta ran Asabar a yi alheri ko mugunta? A ceci rai, ko a hallaka shi?”

10 Sai ya duddube su duke, ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Ya miƙa, hannunsa kuwa sai ya koma lafiyayye.

11 Sai suka husata ƙwarai, suka yi shawarar abin da za su yi wa Yesu.

Yesu Ya Zaɓi Almajirai Sha Biyu

12 A kwanakin nan Yesu ya fita ya hau dutse domin yin addu’a. Dare farai yana addu’a ga Allah.

13 Da gari ya waye ya kira almajiransa, ya zaɓi goma sha biyu a cikinsu, ya ce da su manzanni.

14 Su ne Bitrus, da ɗan’uwansa Andarawas, da Yakubu, da Yahaya, da Filibus, da Bartalamawas,

15 da Matiyu, da Toma, da Yakubu ɗan Halfa, da Saminu, wanda ake ce da shi Zaloti,

16 da Yahuza ɗan Yakubu, da kuma Yahuza Iskariyoti, wanda ya zama maci amana.

Yesu Ya Hidimta wa Mutane Masu Yawa

17 Sai ya gangaro tare da su, ya tsaya a wani sarari. Ga kuwa babban taro masu binsa, da kuma taro masu yawan gaske daga duk ƙasar Yahudiya da Urushalima, da kuma yankin ƙasar Taya da Sidon da yake bakin bahar, waɗanda suka zo su saurare shi, a kuma warkar da cuce-cucensu.

18 Waɗanda kuma baƙaƙen aljannu suke wahalshe su, aka warkar da su.

19 Duk taron suka nema su taɓa shi, domin iko yana fitowa daga gare shi, ya kuwa warkar da su duka.

Albarka da La’ana

20 Sai ya ɗaga kai, ya dubi almajiransa, ya ce,

“Albarka tā tabbata gare ku, ku matalauta, domin Mulkin Allah naku ne.

21 “Albarka tā tabbata gare ku, ku da kuke mayunwata a yanzu, domin za a ƙosar da kuke.

“Albarka tā tabbata gare ku, ku da kuke kuka a yanzu domin za ku yi dariya.

22 “Albarka tā tabbata a gare ku sa’ad da mutane suka ƙi ku, suka kuma ware ku, suka zage ku, suka yi ƙyamar sunanku saboda Ɗan Mutum.

23 Ku yi farin ciki a wannan rana, ku yi tsalle don murna, domin ga shi, sakamakonku mai yawa ne a Sama. Haka kakanninsu ma suka yi wa annabawa.

24 “Amma kaitonku, ku masu arziki domin kun riga kun sami taku ta’aziyya.

25 “Kaitonku, ku da kuke ƙosassu a yanzu, don za ku ji yunwa. “Kaitonku, ku masu dariya a yanzu, don za ku yi baƙin ciki, ku yi kuka.

26 “Kaitonku in kowa na yabonku. Haka kakanninsu ma suka yi wa annabawan ƙarya.”

Ƙaunar Magabta

27 “Amma ina gaya muku, ku masu sauraro, ku ƙaunaci magabtanku, ku yi wa maƙiyanku alheri.

28 Ku sa wa masu zaginku albarka. Masu wulakanta ku kuma, ku yi musu addu’a.

29 Wanda ya mare ka a kunci ɗaya, juya masa ɗaya kuncin kuma. Wanda ya ƙwace maka mayafi, kada ka hana masa taguwarka ma.

30 Duk wanda ya roƙe ka, ka ba shi. Wanda kuma ya ƙwace maka kaya, kada ka neme shi.

31 Yadda kuke so mutane su yi muku, to, ku yi musu haka.

32 In masoyanku kawai kuke ƙauna wane lada ne da ku? Ai, ko masu zunubi ma suna ƙaunar masoyansu.

33 In kuma sai waɗanda suke muku alheri kawai kuke yi wa alheri, wane lada ne da ku? Ai, ko masu zunubi ma haka suke yi.

34 In kuma sai ga waɗanda kuke tsammani za su biya ku ne kuke ba da rance, wane lada ne da ku? Ai, ko masu zunubi ma, sukan ba masu zunubi rance, don a biya su daidai.

35 Amma ku ƙaunaci magabtanku, kuna yi musu alheri. Ku ba da rance, kada kuwa ku tsammaci biya. Ladanku kuma zai yi yawa, za ku kuma zama ‘ya’yan Maɗaukaki, domin shi mai alheri ne ga masu butulci da kuma mugaye.

36 Ku kasance masu tausayi kamar yadda Ubanku yake mai tausayi.”

Kada ku Ɗora wa Kowa Laifi

37 “Kada ku ɗora wa kowa laifi, ku ma ba za a ɗora muku ba. Kada ku yi wa kowa mugun zato, ku ma ba za a yi muku ba. Ku yafe, ku ma sai a yafe muku.

38 Ku bayar, ku ma sai a ba ku mudu a cike, a danƙare, har ya yi tozo, har yana zuba, za a juye muku a hannun riga. Mudun da kuka auna, da shi za a auna muku.”

39 Ya kuma ba su wani misali ya ce, “Makaho yana iya yi wa makaho jagora? Ashe, dukansu biyu ba sai su fāɗa a rami ba?

40 Almajiri ba ya fin malaminsa. Amma kowa aka karantar da shi sosai, sai ya zama kamar malaminsa.

41 Don me kake duban ɗan hakin da yake a idon ɗan’uwanka, amma gungumen da yake a naka ido ba ka kula ba?

42 Ƙaƙa kuma za ka iya ce wa ɗan’uwanka, ‘Ya ɗan’uwana, bari in cire maka ɗan hakin da yake a idonka,’ alhali kuwa kai kanka ba ka ga gungumen da yake a naka ido ba? Kai munafuki! Sai ka fara cire gungumen da yake a idonka tukuna sa’an nan ka gani sosai yadda za ka cire ɗan hakin da yake a idon ɗan’uwanka.”

Akan Gane Itace ta ‘Ya’yansa

43 “Ba kyakkyawan itace da yake haifar munanan ‘ya’ya, ba kuma mummunan itace da yake haifar kyawawan ‘ya’ya.

44 Domin kowane itace da irin ‘ya’yansa ake saninsa. Ai, ba a ɗiban ɓaure a jikin ƙaya, ko kuwa inabi a jikin sarƙaƙƙiya.

45 Mutumin kirki kam ta kyakkyawar taskar zuciyarsa yakan yi abin kirki, mugu kuwa ta mummunar taskar zuciyarsa yakan yi mugun abu. Ai, abin da ya ci rai, shi mutum yake faɗa.”

Kafa Harsashin Gini Iri Biyu

46 “Don me kuke kirana, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ ba kwa kuwa yin abin da na faɗa muku?

47 Duk mai zuwa wurina, yake jin maganata, yake kuma aikata ta, zan nuna muku kwatancinsa.

48 Kamar mutum yake mai gina gida, wanda ya yi haƙa mai zurfi, har ya sa harsashin ginin a kan fā. Da aka yi rigyawa, sai ruwan kogi ya bugi gidan, amma bai iya girgiza shi ba, saboda an gina shi da aminci.

49 Amma wanda ya ji maganata, bai kuwa aikata ba, kamar mutum yake wanda ya gina gida a kan turɓaya, ba harsashi. Ruwan kogi ya buge shi, nan da nan ya rushe. Wannan gida ya yi mummunar ragargajewa!”

Categories
LUK

LUK 7

Yesu Ya Warkar da Bawan Wani Jarumi

1 Bayan da Yesu ya ƙare jawabinsa duka a gaban jama’a, ya shiga Kafarnahum.

2 To, sai bawan wani jarumi, wanda Ubangijinsa yake jin daɗinsa, ya yi rashin lafiya, har ya kai ga bakin mutuwa.

3 Da jarumin ɗin ya ji labarin Yesu, sai ya aiki waɗansu shugabannin Yahudawa wurinsa, su roƙe shi ya zo ya warkar da bawa nasa.

4 Da suka isa wurin Yesu sai suka roƙe shi ƙwarai suka ce, “Ai, ya cancanci a yi masa haka,

5 don yana ƙaunar jama’armu, shi ne ma ya gina mana majami’armu.”

6 Sai Yesu ya tafi tare da su. Da ya matso kusa da gidan, sai jarumin ɗin ya aiki aminansa wurinsa su ce masa, “Ya Ubangiji, kada ka wahalar da kanka. Ban ma isa har ka zo gidana ba.

7 Shi ya sa ban ga ma na isa in zo wurinka ba, amma kă yi magana kawai, yarona kuwa sai ya warke.

8 Don ni ma a hannun wani nake, da kuma soja a hannuna, in ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai ya je, wani kuwa in ce masa, ‘Zo,’ sai ya zo, in ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai ya yi.”

9 Da Yesu ya ji haka, ya yi mamakinsa, ya kuma juya ya ce wa taron da suke biye da shi, “Ina gaya muku, ko a cikin Isra’ila ban taɓa samun bangaskiya mai ƙarfi irin wannan ba.”

10 Da waɗanda aka aika suka koma gidan, suka sami bawan garau.

Yesu Ya Tā da Ɗan Mace wadda Mijinta Ya Mutu

11 Ba da daɗewa ba, Yesu ya tafi wani gari, wai shi Nayin, almajiransa da kuma babban taro suka tafi da shi.

12 Ya kusaci ƙofar garin ke nan, sai ga wani mamaci ana ɗauke da shi, shi kaɗai ne wajen uwa tasa, mijinta kuwa ya mutu. Mutanen gari da yawa sun rako ta.

13 Da Ubangiji ya gan ta, ya ji tausayinta, ya kuma ce mata, “Daina kuka.”

14 Sa’an nan ya matso, ya taɓa makarar, masu ɗauka kuma suka tsaya cik. Sai Yesu ya ce, “Samari, na ce maka ka tashi.”

15 Mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuwa ya ba da shi ga uwa tasa.

16 Sai tsoro ya kama su duka, suka ɗaukaka Allah suna cewa, “Lalle, wani annabi mai girma ya bayyana a cikinmu,” da kuma, “Allah ya kula da jama’arsa.”

17 Wannan labarin nasa kuwa ya bazu a dukan ƙasar Yahudiya da kewayenta.

‘Yan Saƙo daga Yahaya Maibaftisma

18 Sai almajiran Yahaya suka gaya masa dukan abubuwan nan.

19 Sai Yahaya ya kira almajiransa biyu, ya aike su gun Ubangiji yana tambaya, “Kai ne mai zuwan nan, ko kuwa mu sa ido ga wani?”

20 Da mutanen nan suka isa wurinsa, suka ce, “Yahaya Maibaftisma ne ya aiko mu gare ka, yana tambaya, ‘Kai ne mai zuwan nan, ko kuwa mu sa ido ga wani?’ ”

21 Nan take Yesu ya warkar da mutane da yawa daga rashin lafiyarsu da cuce-cucensu da kuma baƙaƙen aljannu. Makafi da yawa kuma ya yi musu baiwar gani.

22 Sai ya amsa musu ya ce, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da kuka ji da abin da kuka gani. Makafi na samun gani, guragu na tafiya, ana tsarkake kutare, kurame na ji, ana ta da matattu, ana kuma yi wa matalauta bishara.

23 Albarka tā tabbata ga wanda ba ya tuntuɓe sabili da ni.”

24 Baya jakadun Yahaya sun tafi, sai Yesu ya fara yi wa taro maganar Yahaya, ya ce, “Kallon me kuka je yi a jeji? Kyauron da iska take kaɗawa?

25 To, kallon me kuka je yi? Wani mai adon alharini? Ai kuwa, masu adon gaske, masu zaman annashuwa, a fāda suke.

26 To, kallon me kuka je yi? Annabi? Hakika, ina gaya muku, har ya fi annabi nesa.

27 Wannan shi ne wanda labarinsa yake rubuce cewa,

‘Ga shi, na aiko manzona ya riga ka gaba,

Wanda zai shirya maka hanya gabaninka.’

28 Ina gaya muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.”

29 Da duk jama’a da masu karɓar haraji suka ji haka, suka tabbata Allah mai adalci ne, aka yi musu baftisma da baftismar Yahaya.

30 Amma Farisiyawa da masanan Attaura suka shure abin da Allah yake nufinsu da shi, da yake sun ƙi ya yi musu baftisma.

31 “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Waɗanne iri ne su?

32 Kamar yara suke da suke zaune a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa,

‘Mun busa muku sarewa, ba ku yi rawa ba,

Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.’

33 Ga shi, Yahaya Maibaftisma ya zo, ba ya cin gurasa, ba ya shan ruwan inabi, amma kuna cewa, ‘Ai, yana da iska.’

34 Ga Ɗan Mutum ya zo, yana ci yana sha, kuna kuma cewa, ‘Ga mai haɗama, mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi!’

35 Duk da haka hikimar Allah, ta dukkan aikinta ne ake tabbatar da gaskiya tata.”

Yesu a Gidan Saminu Bafarisiye

36 Wani Bafarisiye ya kira shi cin abinci. Sai ya shiga gidan Bafarisiyen, ya ƙishingiɗa wurin cin abincin.

37 Sai ga wata matar garin, mai zunubi, da ta ji Yesu na cin abinci a gidan Bafarisiyen, ta kawo wani ɗan tandu na man ƙanshi,

38 ta tsaya a bayansa a wajen ƙafafunsa, tana kuka. Sai hawayenta ya fara zuba a ƙafafunsa, ta goge su da gashinta, ta yi ta sumbantarsu, ta shafa musu man ƙanshin.

39 To, da Bafarisiyen da ya kira shi ya ga haka, sai ya ce a ransa, “Da mutumin nan annabi ne, da ya san ko wace ce, da kuma ko wace irin mace ce wannan da yake taɓa shi, don mai zunubi ce.”

40 Yesu ya amsa ya ce, “Saminu, ina da magana da kai.” Sai shi kuma ya ce, “Malam, sai ka faɗa.”

41 Yesu ya ce, “Wani yana bin mutum biyu bashi, ɗaya dinari ɗari biyar, ɗayan kuma hamsin.

42 Da suka gagara biya, sai ya yafe musu dukansu biyu. To, a cikinsu wa zai fi ƙaunarsa?”

43 Saminu ya amsa masa ya ce, “A ganina, wanda ya yafe wa mai yawa.” Sai ya ce masa “Ka faɗa daidai.”

44 Da ya waiwaya wajen matar, ya ce wa Saminu. “Ka ga matan nan? Na shigo gidanka, ba ka ba ni ruwan wanke ƙafa ba, amma ita ta zub da hawayenta a ƙafafuna, ta kuma goge su da gashinta.

45 Kai ba ka sumbance ni ba, ita kuwa, tun shigowata nan ba ta daina sumbantar ƙafafuna ba.

46 Ba ka shafa mini mai a ka ba, amma ita ta shafa man ƙanshi a ƙafafuna.

47 Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawan nan duk an gafarta mata, domin ta yi ƙauna mai yawa. Wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, ƙauna kaɗan yake yi.”

48 Sai ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.”

49 Masu ci tare da shi kuwa suka fara ce wa juna, “Wannan kuwa wane ne wanda har yake gafarta zunubai?”

50 Sai Yesu ya ce wa matar, “Bangaskiyarki ta cece ki. Ki sauka lafiya.”