Categories
1 KOR

1 KOR 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, manzo kirayayye na Almasihu Yesu da yardar Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sastanisu,

2 zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Koranti, wato, su waɗanda aka keɓe a cikin Almasihu Yesu, tsarkaka kirayayyu, tare da dukan waɗanda a ko’ina suke addu’a, da sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu, Ubangijinsu da namu duka.

3 Alheri da salama na Allah Ubanmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu su tabbata a gare ku.

Godiya saboda Bayebaye na Ruhu

4 Kullum nakan gode wa Allah dominku, saboda alherin Allah da aka yi muku baiwa ta hanyar Almasihu Yesu,

5 har ta kowace hanya aka wadata ku a cikinsa, a wajen yin magana duka da ilimi duka–

6 domin kuwa an tabbatar da shaida a kan Almasihu a cikinku.

7 Har ma ku ba kāsassu ba ne a wajen samun kowace baiwar Allah, kuna zuba ido ga bayyanar Ubangijinmu Yesu Almasihu.

8 wanda zai tabbatar da ku har ya zuwa ƙarshe, ku kasance marasa abin zargi a ranar Ubangijinmu Yesu Almasihu.

9 Allah mai alkawari ne, shi ne kuma ya kira ku ga tarayya da Ɗansa Yesu Almasihu Ubangijinmu.

Tsattsaguwa a Ikkilisiya

10 Na roƙe ku ‘yan’uwa, saboda sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu, cewa dukanku bakinku yă zama ɗaya, kada wata tsaguwa ta shiga a tsakaninku, sai dai ku haɗa kai, kuna da nufi ɗaya, ra’ayinku ɗaya.

11 Don kuwa, ya ‘yan’uwana, mutanen gidan Kuluwi sun ba ni labari, cewa akwai jayayya a tsakaninku.

12 Abin da nake nufi, shi ne kowannenku yana faɗar abu dabam, “Ni na Bulus ne,” wani kuwa, “Ni na Afolos ne,” wani kuwa, “Ni na Kefas ne,” ko kuwa, “ni na Almasihu ne.”

13 Ashe, Almasihu a rarrabe yake? Ko Bulus ne aka gicciye dominku? Ko kuwa an yi muku baftisma ne da sunan Bulus?

14 Na gode Allah da ban yi wa waninku baftisma ba, banda Kirisbus da Gayus,

15 kada wani ya ce da sunana ne aka yi muku baftisma.

16 Ai, kuwa lalle na yi wa jama’ar gidan Istifanas ma. Amma banda waɗannan ban san ko na yi wa wani baftisma ba.

17 Ai, ba don in yi baftisma Almasihu ya aiko ni ba, sai dai in sanar da bishara, ba kuwa da gwanintar iya magana ba, domin kada a wofinta ƙarfin gicciyen Almasihu.

Almasihu Ikon Allah Ne, da Hikimarsa

18 Maganar gicciye, maganar wauta ce ga waɗanda suke hallaka, amma ƙarfin Allah ce a gare mu, mu da ake ceto.

19 Domin a rubuce yake cewa,

“Zan rushe hikimar mai hikima,

Zan kuma shafe haziƙancin haziƙi.”

20 To, ina masu hikima suke? Ina kuma masana? Ina masu muhawwarar zamanin nan? Ashe, Allah bai fallashi hikimar duniyar nan a kan wauta ce ba?

21 Da yake bisa ga hikimar Allah, duniya ba ta san Allah ta wurin hikimarta ba, sai Allah ya ji daɗin ceton masu ba da gaskiya, ta wurin wautar shelar bishara.

22 Yahudawa kam, mu’ujiza suke nema su gani, Helenawa kuwa hikima suka nema su samu,

23 mu kuwa muna wa’azin Almasihu gicciyeyye, abin sa yin tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga al’ummai,

24 amma ga waɗanda suke kirayayyu, ko Yahudawa ko al’ummai duka biyu, Almasihu ikon Allah ne, da hikimar Allah.

25 Domin abin da aka zata wauta ce ta Allah, ya fi hikimar ɗan adam, abin da kuma aka zata rauni ne na Allah, ya fi duk ƙarfin ɗan adam.

26 Ku dubi kiranku da aka yi, ya ku ‘yan’uwa, a cikinku, ai, ba a kira masu hikima irin ta duniya da yawa ba, masu iko kuma ba su da yawa, haka ma masu asali ma ba yawa.

27 Amma Allah ya zaɓi abin da yake wauta a duniya, domin ya kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abin da yake rarrauna a duniya, domin ya kunyata ƙaƙƙarfa.

28 Allah ya zaɓi abin da yake ƙasƙantacce, wulakantacce a duniya, har ma abubuwan da ba su, domin yă shafe abubuwan da suke akwai.

29 Wannan kuwa duk don kada wani ɗan adam yă yi fariya a gaban Allah ne.

30 Gama Allah ne ya sa kuka zama na Almasihu Yesu, Allah ne kuma ya sa Almasihu ya zama hikima a gare mu. Ta wurin Almasihu ne kuma muka sami adalci, da tsarkakewa da fansa.

31 Saboda haka, “Duk mai yin alfarma, yă yi da Ubangiji” (abin da yake a rubuce ke nan).

Categories
1 KOR

1 KOR 2

Shelar Almasihu Gicciyeyye

1 Sa’ad da na zo wurinku, ‘yan’uwa, ban zo ina sanar da ku asiran Allah ta wurin iya magana ko gwada hikima ba.

2 Don na ƙudura a raina, sa’ad da nake zaune da ku, ba zan so sanin kome ba, sai dai Yesu Almasihu, shi ma kuwa gicciyeyye.

3 Ina kuma tare da ku ne da rauni, da tsoro, da rawar jiki ƙwarai.

4 Jawabina da wa’azina, ba su danganta ga maganar rarrashi ko ta wayo ba, sai dai ga rinjaye na ikon Ruhu,

5 kada bangaskiyarku ta dogara ga hikimar mutane, sai ga ƙarfin Allah.

Bayani daga Ruhun Allah

6 Duk da haka dai muna sanar da hikima ga waɗanda suka kammala, sai dai ba hikimar wannan zamani ba, ba kuwa ta masu mulkin zamanin nan, waɗanda suke shuɗewa ba.

7 Amma muna maganar asirtacciyar hikima ta Allah, wadda dā ɓoyayyiya ce, wato, hikimar da Allah ya ƙaddara tun gaban farkon zamanai, domin ɗaukakarmu.

8 A cikin masu mulkin zamanin nan, ba wanda ya gane hikimar nan, don da sun gane ta, da ba su gicciye Ubangiji Maɗaukaki ba.

9 Amma kuwa yadda yake a rubuce ke nan cewa,

“Abubuwan da ido bai taɓa gani ba,

Kunne bai taɓa ji ba,

Zuciyar mutum kuma ba ta ko riya ba,

Waɗanda Allah ya tanadar wa masu ƙaunarsa,”

10 mu ne Allah ya bayyana wa, ta wurin Ruhu, domin Ruhu shi yake fayyace kome, har ma zurfafan al’amuran Allah.

11 Wane ne a cikin mutane ya san tunanin wani mutum, in ba ruhun shi mutumin ba? Haka kuma ba wanda ya san tunanin Allah, sai dai Ruhun Allah.

12 Mu kuwa ba ruhun duniya muka samu ba, sai dai Ruhu wanda yake daga wurin Allah, domin mu fahimci abubuwan da Allah ya yi mana baiwa hannu sake.

13 Su ne kuwa muke sanarwa ta maganar da ba hikimar ɗan adam ce ta koyar ba, sai dai wadda Ruhu ya koyar, muna bayyana al’amura masu ruhu ga waɗanda suke na ruhu.

14 Mutumin da ba shi da Ruhu yakan ƙi yin na’am da al’amuran Ruhun Allah, don wauta ne a gare shi, ba kuwa zai iya fahimtarsu ba, domin ta wurin ruhu ne ake rarrabewa da su.

15 Mutumin da yake na ruhu kuwa yakan rarrabe da kome, shi kansa kuma ba mai jarraba shi.

16 “Wa ya taɓa sanin tunanin Ubangiji, har da zai koya masa?” Mu kuwa tunaninmu na Almasihu ne.

Categories
1 KOR

1 KOR 3

Abokan Aiki na Allah

1 Amma ni, ‘yan’uwa, ban iya yi muku jawabi ba, kamar yadda nake yi wa mutanen da suke na ruhu, sai dai kamar yadda nake yi wa masu halin mutuntaka, kamar jarirai a cikin bin Almasihu.

2 Nono ne na shayar da ku, ba abinci mai tauri na ba ku ba, don ba ku isa ci ba a lokacin, ko a yanzu ma ba ku isa ba,

3 don har a yanzu ku masu halin mutuntaka ne. Muddin akwai kishi da jayayya a tsakaninku, ashe, ku ba masu halin mutuntaka ba ne, kuna kuma aikata halin mutuntaka?

4 Don in wani ya ce, “Ni na Bulus ne,” wani kuma ya ce, “Ni na Afolos ne,” ashe, ba aikata halin mutuntaka kuke yi ba?

5 To, wane ne Afolos? wane ne Bulus kuma? Ashe, ba bayi ne kawai ba, waɗanda kuka ba da gaskiya ta wurinsu, ko wannensu kuwa gwargwadon abin da Ubangiji ya ba shi?

6 Ni na yi shuka, Afolos ya yi banruwa, amma Allah ne ya girmar.

7 Don haka da mai shukar, da mai banruwan, ba a bakin kome suke ba, sai dai Allah kaɗai, shi da ya girmar.

8 Da mai shukar, da mai banruwan, duk daidai suke, sai dai ko wanne zai sami tasa ladar gwargwadon wahalarsa,

9 gama mu abokan aiki ne na Allah, ku kuwa gona ce ta Allah, ginin Allah kuma.

10 Kamar gwanin magini, haka na sa harsashin gini, gwargwadon baiwar alherin da Allah ya yi mini, wani kuma yana ɗora gini a kai. Sai dai kowane mutum, yă lura da irin ginin da yake ɗorawa a kai.

11 Harsashin kam, ba wanda yake iya sa wani dabam da wanda aka riga aka sa, wato, Yesu Almasihu.

12 To, kowa ya yi ɗori da zinariya a kan harsashin nan, ko da azurfa, ko da duwatsun alfarma, ko da itace, ko da shuci, ko da kara,

13 ai, aikin kowane mutum zai bayyana, domin ranar nan za ta tona shi, gama za a bayyana ta da wuta, wutar kuwa za ta gwada aikin kowa a san irinsa.

14 In aikin da kowane mutum ya ɗora a kan harsashin nan ya tsira, to, zai sami sakamako.

15 In kuwa aikin wani ya ƙone, to, sai yă yi hasara, ko da yake shi da kansa zai tsira, amma kamar ya bi ta wuta ne.

16 Ashe, ba ku sani ku Haikalin Allah ne ba, Ruhun Allah kuma yana zaune a zuciyarku?

17 In wani ya ɓāta Haikalin Allah, Allah zai ɓāta shi. Gama Haikalin Allah tsattsarka ne, ku kanku Haikalinsa ne.

18 Kada kowa yă ruɗi kansa. In waninku ya zaci shi mai hikima ne, yadda duniya ta ɗauki hikima, sai yă mai da kansa marar hikima, domin ya sami zama mai hikima.

19 Gama hikimar duniyar nan wauta ce a gun Allah, domin a rubuce yake, “Yakan kama masu hikima da makircinsu.”

20 Har wa yau, “Ubangiji ya san tunanin masu hikima banza ne.”

21 Saboda haka kada kowa yă yi fariya da ‘yan adam. Don kuwa kome naku ne,

22 ko Bulus, ko Afolos, ko Kefas, ko duniya, ko rai, ko mutuwa, ko abubuwan yanzu, ko da na gaba, ai, duk naku ne.

23 Ku kuwa na Almasihu ne, Almasihu kuma na Allah ne.

Categories
1 KOR

1 KOR 4

Aikin Manzanni

1 Ta haka ya kamata a san mu da zama ma’aikatan Almasihu, masu riƙon amanar asirtattun al’amuran Allah.

2 Har wa yau dai, abin da ake bukata ga mai riƙon amana, a same shi amintacce.

3 A gare ni kam, sassauƙan abu ne a ce ku ne za ku gwada ni, ko kuwa a gwada ni a gaban kowace mahukunta ta mutane. Ni ma ba na gwada kaina.

4 Ban sani ina da wani laifi ba, amma ba don wannan na kuɓuta ba, ai, Ubangiji shi ne mai gwada ni.

5 Don haka, kada ku yanke wani hukunci tun lokaci bai yi ba, kafin komowar Ubangiji, wanda zai tone al’amuran da suke ɓoye a duhu, ya kuma bayyana nufin zukata. A sa’an nan ne, Allah zai yaɓa wa kowa daidai gwargwado.

6 To, ‘yan’uwa, ga zancen waɗannan abubuwa, na misalta su ne ga kaina, da kuma Afolos saboda ku, don ku yi koyi da mu, cewa, kada ku zarce abin da yake a rubuce, kada kuma waninku ya yi fahariya da wani a kan wani.

7 Wa ya fifita ka da sauran? Me kuma kake da shi, wanda ba karɓa ka yi ba? Da yake karɓa ka yi, don me kake fahariya, kamar ba karɓa ka yi ba?

8 Mhm, wato, har kun riga kun yi hamdala! Har kun wadata! Har ma kun yi sarauta ba tare da mu ba ma! Da ma a ce kun yi mulki mana, har mu ma mu yi tare da ku!

9 Don a ganina, Allah ya bayyana mu, mu manzanni, koma bayan duka ne, kamar waɗanda mutuwa yake jewa a kansu, don mun zama abin nuni ga duniya, da mala’iku duk da mutane.

10 An ɗauke mu marasa azanci saboda Almasihu, wato, ku kuwa masu azanci cikin Almasihu! Wato, mu raunana ne, ku kuwa ƙarfafa! Ku kam, ana ganinku da martaba, mu kuwa a wulakance!

11 Har a yanzu haka, yunwa muke ji, da ƙishirwa, muna huntanci, ana bugunmu, kuma yawo muke yi haka, ba mu da gida.

12 Guminmu muke ci. In an zage mu, mukan sa albarka. In an tsananta mana, mukan daure.

13 In an ci mutuncinmu, mukan ba da haƙuri. Mun zama, har a yanzu ma, mu ne kamar jujin duniya, abin ƙyamar kowa.

14 Ba don in kunyata ku na rubuta wannan ba, sai dai don in gargaɗe ku a kan cewa, ku ‘ya’yana ne, ƙaunatattu.

15 Ko da kuna da malamai masu ɗumbun yawa, amma ba ku da ubanni da yawa, don ni ne ubanku a cikin Almasihu ta wurin bishara.

16 Don haka, ina roƙon ku, ku yi koyi da ni.

17 Saboda haka, na aika muku da Timoti, wanda yake shi ne ɗana ƙaunatacce, amintacce kuma a cikin Ubangiji, zai kuwa tuna muku da ka’idodina na bin Almasihu, kamar yadda nake koyarwa a ko’ina, a kowace ikkilisiya.

18 Waɗansu har suna ɗaga kai, kamar ba zan zo wurinku ba.

19 Amma kuwa zan zo gare ku ba da daɗewa ba, in Ubangiji ya yarda, zan kuma bincika, in ga ƙarfin mutane masu ɗaga kan nan, ba maganganunsu ba.

20 Domin Mulkin Allah ba ga maganar baka yake ba, sai dai ga ƙarfi.

21 To, me kuka zaɓa, in zo muku da sanda, ko kuwa da fuskar ƙauna da lumana?

Categories
1 KOR

1 KOR 5

Hukunci a kan Fasikanci

1 Ana ta cewa akwai fasikanci a tsakaninku, irin wanda ba a yi ko a cikin al’ummai, har wani yana zama da matar ubansa.

2 A! Har kuwa alfarma kuke yi! Ashe, ba gwamma ku yi baƙin ciki ba, har a fitar da wanda ya yi wannan mugun aiki daga cikin jama’arku?

3 Ko da yake a jiki ba na nan, ai, ruhuna yana nan, kamar ma ina nan ne, har ma na riga na yanke wa mutumin da ya yi abin nan hukunci da sunan Ubangijinmu Yesu.

4 Sa’ad da kuka hallara, ruhuna kuma yana nan, da kuma ikon Ubangijinmu Yesu,

5 sai ku miƙa irin wannan mutum ga Shaiɗan, don yă hallaka jikinsa, ruhunsa kuma ya tsira a ranar Ubangiji Yesu.

6 Fāriyarku ba shi da kyau. Ashe, ba ku sani ba, ɗan yisti kaɗan yake game dukkan curin gurasa?

7 Ku fitar da tsohon yistin nan, don ku zama sabon curi, domin hakika an raba ku da yistin, da yake an riga an yanka Ɗan Ragonmu na Idin Ƙetarewa, wato, Almasihu.

8 Saboda haka, sai mu riƙa yin idinmu, ba da gurasa mai tsohon yisti ba, ba kuwa gauraye da yisti na ƙeta da na mugunta ba, sai dai da gurasa marar yisti ta sahihanci da ta gaskiya.

9 Na rubuta muku a cikin wasiƙata, cewa kada ku yi cuɗanya da fasikai.

10 Ko kusa, ba na nufin fasikai marasa bi, ko makwaɗaita, da mazambata, ko matsafa, don in haka ne, sai yă zama dole ku fita daga duniya.

11 Sai dai na rubuta muku ne, don kada ku yi cuɗanya da duk wanda ake kira ɗan’uwa, mai bi, in yana fasikanci, ko makwaɗaici, ko matsafi, ko mai zage-zage, ko mashayi, ko mazambaci, kada ku ko ci abinci da irin waɗannan.

12 Ina ruwana da hukunta waɗanda ba namu ba? Ba waɗanda suke a cikin Ikkilisiya za ku hukunta ba?

13 Allah ne yake hukunta waɗanda ba namu ba. Ku kori mugun nan daga cikinku.

Categories
1 KOR

1 KOR 6

Kada a Kai Ƙara Gaban Marasa Bi

1 In waninku yana da wata ƙara a game da ɗan’uwansa, ashe, zai yi ƙurun kai maganar a gaban marasa adalci, ba a gaban tsarkaka ba?

2 Ashe, ba ku sani ba, tsarkaka ne za su yi wa duniya shari’a? In kuwa ku ne za ku yi wa duniya shari’a, ashe, ba za ku iya shari’ar ƙananan al’amura ba?

3 Ba ku sani ba, za mu yi wa mala’iku shari’a, balle al’amuran da suka shafi zaman duniyar nan?

4 In kuwa kuna da irin waɗannan ƙararraki, don me kuma kuke kai su gaban waɗanda su ba kome ba ne, a game da Ikkilisiya?

5 Na faɗi wannan ne don ku kunyata. Ashe, wato, ba ko mutum ɗaya mai hikima a cikinku, da zai iya sasanta tsakanin ‘yan’uwa?

6 Amma ɗan’uwa yakan kai ƙarar ɗan’uwa, gaban marasa ba da gaskiya kuma?

7 Ku yi ƙarar juna ma, ai, hasara ce a gare ku. Ba gara ku haƙura a cuce ku ba? Ku kuma haƙura a zambace ku?

8 Amma, ga shi, ku da kanku kuna cuta, kuna zamba, har ma ‘yan’uwanku kuke yi wa!

9 Ashe, ba ku sani ba, marasa adalci ba za su sami gādo a cikin Mulkin Allah ba? Kada fa a yaudare ku! Ba fasikai, ko matsafa, ko mazinata, ko masu luɗu da maɗugo,

10 ko ɓarayi, ko makwaɗaita, ko mashaya, ko masu zage-zage, ko mazambata, da za su sami gādo a cikin Mulkin Allah.

11 Waɗansunku ma dā haka suke, amma an wanke ku, an tsarkake ku, an kuma kuɓutar da ku, da sunan Ubangiji Yesu Almasihu, da kuma Ruhun Allahnmu.

Ku Ɗaukaka Allah da Jikinku

12 “Dukan abubuwa halal ne a gare ni,” amma ba dukan abubuwa ne masu amfani ba. “Abu duka halal na a gare ni,” amma ba zan zama bawan kome ba.

13 “Abinci don ciki aka yi shi, ciki kuma don abinci”–Allah kuma zai hallaka duka biyu, wannan da wancan. Jiki kam, ba don fasikanci yake ba, sai dai domin Ubangiji, Ubangiji kuma domin jiki.

14 Allah ya ta da Ubangiji daga matattu, haka mu ma zai ta da mu da ikonsa.

15 Ashe, ba ku sani ba jikinku gaɓoɓin Almasihu ne? Ashe kuma, sai in ɗauki gaɓoɓin Almasihu in mai da su gaɓoɓin karuwa? Faufau!

16 Ashe, ba ku sani ba, duk wanda ya tara da karuwa, sun zama jiki ɗaya ke nan? Domin a rubuce yake cewa, “Su biyun za su zama jiki ɗaya.”

17 Duk wanda kuwa yake haɗe da Ubangiji, sun zama ɗaya a ruhu ke nan.

18 Ku guji fasikanci. Duk sauran zunubin da mutum yake yi bai shafi jikinsa ba, amma mai yin fasikanci, yana ɗaukar alhalin jikinsa ne.

19 Ashe, ba ku sani ba, jikinku Haikali ne na Ruhu Mai Tsarki wanda yake a zuciyarku, wanda kuka kuma samu a gun Allah? Ai, ku ba mallakar kanku ba ne.

20 Sayenku aka yi da tamani. To, sai ku ɗaukaka Allah da jikinku.

Categories
1 KOR

1 KOR 7

Damuwar da take a cikin Aure

1 To, a yanzu, a game da abin da kuka rubuto, yana da kyau mutum ya zauna ba aure.

2 Amma don gudun fasikanci sai kowane mutum ya kasance da matarsa, kowace mace kuma da mijinta.

3 Miji yă ba matarsa hakkinta na aure, haka kuma matar ga mijinta.

4 Matar kuwa ba ta da iko da jikinta, sai dai mijin, haka kuma mijin ba shi da iko da jikinsa, sai dai matar.

5 Kada ɗayanku yă ƙaurace wa ɗaya, sai ko da yardar juna zuwa wani ɗan lokaci kaza, don ku himmantu ga addu’a, sa’an nan ku sāke haɗuwa, kada Shaiɗan yă zuga ku ta wajen rashin kamewa.

6 Na fadi wannan ne bisa ga shawara, ba bisa ga umarni ba.

7 Da ma a ce kowa kamar ni yake mana! Sai dai kowa da irin baiwar da Allah ya yi masa, wani iri kaza, wani kuma iri kaza.

8 Abin da na gani ga waɗanda ba su yi aure ba, da kuma mata gwauraye, ya kyautu a gare su su zauna ba aure kamar yadda nake.

9 In kuwa ba za su iya kamewa ba, to, sai su yi aure. Ai, gwamma dai a yi aure da sha’awa ta ci rai.

10 Masu aure kuwa ina yi musu umarni, ba kuwa ni ba, Ubangiji ne, cewa kada mace ta rabu da mijinta

11 (in kuwa ta rabu da shi, sai ta zauna haka ba aure, ko kuwa ta sāke shiryawa da mijinta), miji kuma kada ya saki matarsa.

12 Ga sauran, ni nake faɗa, ba Ubangiji ba, in wani ɗan’uwa yana da mace marar ba da gaskiya, ta kuma yarda su zauna tare, to, kada yă rabu da ita.

13 Mace kuma mai miji marar ba da gaskiya, ya kuwa yarda su zauna tare, to, kada ta rabu da shi.

14 Don miji marar ba da gaskiya, a tsarkake yake a wajen matarsa. Mace marar ba da gaskiya kuma, a tsarkake take a wajen mijinta. In ba haka ba, zai zamana ‘ya’yanku ba masu tsarki ba ne, amma ga hakika masu tsarki ne.

15 In kuwa shi, ko ita, marar ba da gaskiya ɗin yana son rabuwa, to, sai su rabu. A wannan hali, ɗan’uwa ko ‘yar’uwa mai bi, ba tilas a kansu, domin Allah ya kira mu ga zaman lafiya.

16 Ke mace, ina kika sani ko za ki ceci mijinki? Kai miji, ina ka sani ko za ka ceci matarka?

Zaman da Ubangiji Ya Nufa

17 Sai dai kowa yă yi zaman da Ubangiji ya sa masa, wanda kuma Allah ya kira shi a kai. Haka nake umarni a dukan Ikilisiyoyi.

18 Duk wanda Allah ya kira, wanda dā ma yake da kaciya, to, kada yă nemi zama marar kaciya. Wanda kuwa ya kira yana marar kaciya, to, kada yă nema a yi masa kaciya.

19 Don kaciya da rashin kaciya ba sa hassala kome, sai dai kiyaye umarnin Allah.

20 Kowa yă zauna a maƙamin da Allah ya kiraye shi.

21 In ya kira ka kana bawa, kada ka damu. In kuwa kana iya samun ‘yanci, ai, sai ka samu.

22 Wanda aka kiraye shi ga tafarkin Ubangiji yana bawa, ai, ‘yantacce ne na Ubangiji. Kuma, wanda aka kira shi yana ɗa, bawa ne na Almasihu.

23 Da tamani aka saye ku. Kada fa ku zama bayin mutane.

24 To, ‘yan’uwa, duk halin da aka kira mutum a ciki, sai yă zauna a kai, yana zama tare da Allah.

Marasa Aure da Mata Gwauraye

25 A game da matan da ba su yi aure ba kuwa, ba ni da wani umarnin Ubangiji, amma ina ba da ra’ayina ne a kan ni amintacce ne, bisa ga jinƙan Ubangiji.

26 Na dai ga ya yi kyau mutum yă zauna yadda yake, saboda ƙuncin nan da yake gabatowa.

27 In da igiyar aure a wuyanka, to, kada ka nemi tsinkewa. In kuwa ba igiyar aure a wuyanka, to, kada ka nemi aure.

28 Amma kuwa in ka yi aure, ba ka yi zunubi ba, ko budurwa ma ta yi aure, ba ta yi zunubi ba. Duk da haka dai, duk masu yin aure za su ji jiki, niyyata kuwa in sawwaƙe muku.

29 Abin da nake nufi ‘yan’uwa, lokacin da aka ƙayyade ya ƙure. A nan gaba masu mata su zauna kamar ba su da su,

30 masu kuka kamar ba kuka suke yi ba, masu farin ciki ma kamar ba farin ciki suke yi ba, masu saye kuma kamar ba su riƙe da kome,

31 masu moron duniya kuma, kada su ba da ƙarfi ga moronta. Don yayin duniyar nan mai shuɗewa ne.

32 Ina so ku ‘yantu daga damuwa. Mutum marar aure yakan tsananta kula da sha’anin Ubangiji, yadda zai faranta wa Ubangiji rai.

33 Mutum mai aure kuwa, yakan tsananta kula da sha’anin duniya, yadda zai faranta wa matarsa rai.

34 Hankalinsa ya rabu biyu ke nan. Mace marar aure, ko budurwa, takan tsananta kula da sha’anin Ubangiji, yadda za ta kasance tsattsarka a jiki, da kuma a rai. Mace mai aure kuwa takan tsananta kula da sha’anin duniya, yadda za ta faranta wa mijinta rai.

35 Na faɗi haka ne, don in taimake ku, ba don in ƙuntata muku ba, sai dai don in kyautata zamanku, da nufin ku himmantu ga bautar Ubangiji ba da raba hankali ba.

36 Ga zancen ‘ya budurwa, wadda ta zarce lokacin aure, idan mahaifinta ya ga bai kyauta mata ba, in kuwa hali ya yi, sai yă yi abin da ya nufa, wato, a yi mata aure, bai yi zunubi ba.

37 In kuwa ya zamana ba lalle ne yă yi wa ‘yar tasa budurwa aure ba, amma ya tsai da shawara bisa ga yadda ya nufa, ya kuma ƙudura sosai a ransa, a kan tsare ta, to, haka daidai ne.

38 Wato, wanda ya yi wa ‘yar tasa budurwa aure, ya yi daidai, amma wanda bai aurar da ita ba, ya fi shi.

39 Igiyar aure tana wuyan mace, muddin mijinta yana da rai. In kuwa mijinta ya mutu, to, tana da dama ta auri wanda take so, amma fa, sai mai bin Ubangiji.

40 Amma a nawa ra’ayi, za ta fi farin ciki, in ta zauna a yadda take. A ganina kuwa ina da Ruhun Allah.

Categories
1 KOR

1 KOR 8

Abincin da aka Miƙa wa Gumaka

1 To, yanzu a game da abubuwan da aka yanka wa gumaka, mun sani dukanmu muna da ilimi. Ilimi yakan kumbura mutum, ƙauna kuwa takan inganta shi.

2 Duk mai gani ya san wani abu, ai, har a yanzu, bai san yadda ya kamata ya sani ba.

3 In kuwa wani na ƙaunar Allah, to, Allah ya san shi.

4 A game da cin abin da aka yanka wa gumaka kuwa, mun sani, duk duniyar nan gunki yana a matsayin abin da babu ne, da kuma, babu wani Allah sai ɗaya.

5 Ko da yake, akwai waɗanda ake kira alloli a sama ko a ƙasa, don kuwa akwai “alloli” da “iyayengiji” da yawa,

6 duk da haka dai, a gare mu kam, Allah ɗaya ne, wato Uba, wanda dukkan abubuwa suke daga gare shi, wanda mu kuma zamansa muke yi, Ubangiji kuma ɗaya ta gare shi muka kasance.

7 Amma dai ba kowa ne yake da wannan sani ba. Amma waɗansu ta wurin sabawarsu da al’amuran gunki har yanzu, sukan ci naman da suka ɗauka kamar an yanka wa gunki ne. Saboda haka lamirinsu, da yake rarrauna ne, ya ƙazantu.

8 Abinci ba zai ƙare mu a game da Allah ba. In mun ci, ba mu ƙaru ba, in kuma ba mu ci ba, ba mu ragu ba.

9 Sai dai ku lura, kada ‘yancin nan naku ya zama abin sa tuntuɓe ga waɗanda ba su tsai da zuciyarsu ba.

10 Amma in wani mutum, wanda yake da rarraunan lamiri, ya gan ka, kai da kake da sani, kana ci a ɗakin gunki, ashe, wannan ba zai ƙarfafa lamirinsa har ya ci abincin da aka miƙa wa gunki ba?

11 Wato, ta sanin nan naka, sai a rushe rarraunan nan, ɗan’uwa ne kuwa wanda Almasihu ya mutu dominsa!

12 Ta haka ne kuke yi wa Almasihu laifi, wato ta wurin yi wa ‘yan’uwanku laifi, kuna rushe rarraunan lamirinsu.

13 Saboda haka in dai cin nama ya sa ɗan’uwana tuntuɓe, har abada ba zan ƙara cin nama ba, don kada in sa ɗan’uwana tuntuɓe.

Categories
1 KOR

1 KOR 9

Hakkokin Manzo

1 Ni ba ɗa ba ne? Ba kuma manzo ba ne? Ban ga Yesu Ubangijinmu ba ne? Ku ba aikina ba ne a cikin Ubangiji?

2 Ai, ko waɗansu ba su ɗauke ni a kan manzo ba, lalle ku kam, ni manzo ne a gare ku, domin kuwa ku ne tabbatar manzancina a gaban Ubangiji.

3 Wannan ita ce kariyata ga masu son tuhumata.

4 Ashe, ba mu da iko a ba mu ci da sha?

5 Ba mu da ikon tafiya da matarmu ta aure mai bi, kamar yadda sauran manzanni, da ‘yan’uwan Ubangiji, da kuma Kefas suke yi?

6 Ko kuwa dai ni da Barnaba ne kawai, ba mu da iko a ɗauke mana aikin ci da kai?

7 Wa yake yin aikin soja, sa’an nan yă ci da kansa? Wa zai shuka garkar inabi, yă kasa cin ‘ya’yan? Wa zai yi kiwon garke, yă kasa shan nonon?

8 Wato, ina faɗar haka bisa ga ra’ayin mutum kawai ne? Ba haka ma Attaura ta faɗa ba?

9 Ai, haka yake a rubuce a Shari’ar Musa cewa, “Kada ka sa wa takarkari takunkumi a sa’ad da yake sussuka.” Da shanu ne kawai Allah yake kula?

10 Ba saboda mu musamman yake magana ba? Hakika saboda mu ne aka rubuta. Ai, ya kamata mai noma yă yi noma da sa zuciya, mai sussuka kuma yă yi sussuka da sa zuciya ga samun rabo daga amfanin gonar.

11 Da yake mun shuka iri na ruhu a zuciyarku, to, wani ƙasaitaccen abu ne, in mun mori amfaninku irin na duniya?

12 Da yake waɗansu sun mori halaliyarsu a game da ku, ashe ba mu muka fi cancanta ba?

Duk da haka ba mu mori wannan halaliya ba, sai dai muna jure wa kome, don ta koƙaƙa kada mu hana bisharar Almasihu yaɗuwa.

13 Ashe, ba ku sani ba, masu hidima a Haikali daga nan suke samun abincinsu? Masu hidimar bagadi kuma, a nan suke samun rabo daga hadayar da aka yanka?

14 Haka nan kuma Ubangiji ya yi umarni, cewa, ya kamata masu sanar da bishara, a cishe su albarkacin bishara.

15 Amma ni kam, ban mori ko ɗaya daga cikin halaliyan nan ba, ba kuma ina rubuta wannan ne, don a yi mini haka ba. Ai, gara in mutu a kan wani ya banzanta mini fahariyata.

16 Don ko da yake ina yin bishara, ba na fahariya da haka, gama tilas ne a gare ni. Kaitona in ba na yin bishara!

17 Da da ra’ina nake yi, da sai a biya ni. Amma da yake ba da ra’ina ba ne, an danƙa mini amana ke nan.

18 Ina kuma hakkina? To, ga shi. A duk lokacin da nake yin bishara, sona in yi ta a kyauta, kada in ƙurashe halaliyata a game da bishara.

19 Ko da yake ni ba bawan kowa ba ne, na mai da kaina bawan kowa, domin in rinjayi mutane masu yawa.

20 Ga Yahudawa, sai na zama kamar Bayahude, domin in rinjayi Yahudawa. Ga waɗanda Shari’a take iko da su, sai na zama kamar wanda Shari’a take iko da shi, ko da yake ba Shari’a take iko da ni ba, domin in rinjayi waɗanda Shari’a take iko da su ne.

21 Ga marasa Shari’a kuwa, sai na zama kamar marar Shari’a, ba cewa ba wata shari’ar Allah da take iko da ni ba, a’a, shari’ar Almasihu na iko da ni, domin in rinjayi marasa Shari’a ne.

22 Ga raunana, sai na zama kamar rarrauna domin in rinjayi raunana. Na zama kowane irin abu ga ko waɗanne irin mutane, domin ta ko ƙaƙa in ceci waɗansu.

23 Na yi wannan ne duk saboda bishara, domin in sami rabo a cikin albarkarta.

24 Ashe, ba ku sani ba, a wajen tsere dukan masu gudu suna ƙoƙarin tsere wa juna, amma ɗaya ne kaɗai yake samun kyautar ci? To, sai ku yi ta gudu haka nan, don ku ci.

25 Duk masu wasan gasa, sukan hori kansu ta kowane hali. Su kam, suna yin haka ne, don su sami lada mai lalacewa, mu kuwa marar lalacewa.

26 To, ni ba gudu nake yi ba wurin zuwa ba, dambena kuwa ba naushin iska nake yi ba.

27 Amma ina azabta jikina ne, don in bautar da shi, kada bayan da na yi wa waɗansu wa’azi, ni da kaina a yar da ni.

Categories
1 KOR

1 KOR 10

Kashedi a kan Bautar Gumaka

1 To, ina so ku sani, ‘yan’uwa, dukan kakanninmu an kāre su ne a ƙarƙashin gajimare, dukansu kuma sun ratsa ta cikin bahar.

2 Dukansu kuwa an yi musu baftisma ga bin Musa a cikin gajimaren, da kuma bahar ɗin.

3 Duka kuwa sun ci abincin nan na ruhu,

4 duk kuma sun sha ruwan nan na ruhu. Domin sun sha ruwa daga Dutsen nan na ruhu, wanda ya yi tafiya tare da su. Dutsen nan kuwa Almasihu ne.

5 Duk da haka Allah bai yi murna da yawancinsu ba, har aka karkashe su a jeji.

6 To, ai, waɗannan abubuwa gargaɗi ne a gare mu, kada mu yi marmarin mugayen abubuwa, kamar yadda suka yi.

7 Kada fa ku zama matsafa kamar yadda waɗansunsu suke. A rubuce yake cewa, “Jama’a sun zauna garin ci da sha, suka kuma tashi suka yi ta rawa.”

8 Kada fa mu yi fasikanci yadda waɗansunsu suka yi, har mutum dubu ashirin da uku suka zuba a rana ɗaya tak.

9 Kada kuma mu gwada Ubangiji yadda waɗansu suka yi, har macizai suka hallaka su.

10 Kada kuma mu yi gunaguni yadda waɗansu suka yi, har mai hallakarwa ya hallaka su.

11 To, duk wannan ya same su ne a kan misali, an kuma rubuta shi ne don a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana.

12 Don haka duk wanda yake tsammani ya kahu, ya mai da hankali kada ya fāɗi.

13 Ba wani gwajin da ya taɓa samunku, wanda ba a saba yi wa ɗan adam ba. Allah mai alkawari ne, ba zai kuwa yarda a gwada ku fin ƙarfinku ba, amma a game da gwajin sai ya ba da mafita, yadda za ku iya jure shi.

14 Saboda haka, ya ƙaunatattuna, ku guji bautar gumaka.

15 Ina magana da ku a kan ku mahankalta ne fa, ku duba da kanku ku ga abin da nake faɗa.

16 Ƙoƙon nan na yin godiya, wanda muke gode wa Allah saboda shi, ashe, ba tarayya ne ga jinin Almasihu ba? Gurasar nan da muke gutsuttsurawa kuma, ashe, ba tarayya ce ga jikin Almasihu ba?

17 Da yake gurasar nan ɗaya ce, ashe kuwa, mu da muke da yawa jiki ɗaya ne, gama mu duk gurasa ɗaya muke ci.

18 Ku dubi ɗabi’ar Isra’ila. Ashe, waɗanda suke ci daga hadayu, ba tarayya suke yi da bagadin hadaya ba?

19 Me nake nufi ke nan? Abin da aka yanka wa gumakan ne ainihin wani abu, ko kuwa gunkin ne ainihin wani abu?

20 A’a! Na nuna ne kawai cewa abin da al’ummai suke yankawa, ga aljannu suke yanka wa, ba Allah ba. Ba na fa so ku zama abokan tarayya da aljannu.

21 Ba dama ku sha a ƙoƙon Ubangiji, ku kuma sha a na aljannu. Ba dama ku ci abinci a teburin Ubangiji, ku kuma ci a na aljannu.

22 Ashe, har mā tsokani Ubangiji ya yi kishi? Mun fi shi ƙarfi ne?

Yi Kome saboda Ɗaukakar Allah

23 “Dukan abubuwa halal ne,” amma ba dukan abubuwa ne masu amfani ba. “Dukan abubuwa halal ne,” amma ba dukan abubuwa ne suke ingantawa ba.

24 Kada kowa ya nemi ya kyautata wa kansa, sai dai ya kyautata wa ɗan’uwansa.

25 Ku ci kowane irin abu da ake sayarwa a mahauta, ba tare da tambaya ba saboda lamiri.

26 Don an rubuta, “Duniya ta Ubangiji ce, da duk abin da yake cikinta.”

27 In wani a cikin marasa ba da gaskiya ya kira ku cin abinci, kuka kuwa yarda ku tafi, sai ku ci duk irin da aka sa a gabanku, ba tare da tambaya ba saboda lamiri.

28 In kuwa wani ya ce muku, “An yanka wannan saboda gunki ne fa,” to, kada ku ci, saboda duban mutuncin wannan mai gaya muku, da kuma saboda lamiri,

29 nasa lamiri fa na ce, ba naka ba. Don me fa lamirin wani zai soki ‘yancina?

30 In na yi godiya ga Allah a kan abincina, saboda me za a zarge ni a kan abin da na ci da godiya ga Allah?

31 To, duk abin da kuke yi, ko ci, ko sha, ku yi kome saboda ɗaukakar Allah.

32 Kada ku zama abin tuntuɓe ga Yahudawa ko al’ummai ko ikkilisiyar Allah,

33 kamar dai yadda nake ƙoƙarin kyautata wa dukan mutane a cikin duk abin da nake yi, ba nema wa kaina amfani nake yi ba, sai dai in amfani mutane da yawa, don su sami ceto.