Categories
1 KOR

1 KOR 11

1 Ku yi koyi da ni kamar yadda nake koyi da Almasihu.

Mata su Rufe Kansu

2 Ina yaba muku ne don kuna tunawa da ni a cikin kowace harka, kuna kuma riƙe ka’idodin nan da kyau, daidai yadda na ba ku.

3 Amma fa ina so ku fahimci cewa, shugaban kowane mutum Almasihu ne, shugaban kowace mace kuwa mijinta ne, shugaban Almasihu kuma Allah ne.

4 Duk mutumin da ya yi addu’a ko ya yi annabci kansa a rufe, ya wulakanta shugabansa ke nan.

5 Amma duk matar da ta yi addu’a, ko ta yi annabci da kanta a buɗe, ta wulakanta shugabanta ke nan, duk ɗaya ne da an aske kanta ma.

6 In mace ta ƙi rufe kanta, to, sai ta sausaye gashinta. In kuwa abin kunya ne a yi wa mace sausaye ko kundumi, to, sai ta rufe kanta.

7 Namiji kam, bai kamata yă rufe kansa ba, tun da yake shi kamannin Allah ne, abin alfahari ga Allah kuma. Amma mace abar taƙamar namiji ce.

8 (Don kuwa namiji ba daga jikin mace yake ba, amma matar daga jikin namiji take.

9 Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.)

10 Shi ya sa ya kamata mace ta rufe kanta, wato, alamar ikon namiji, saboda mala’iku.

11 Duk da haka, a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, haka kuma namiji ba a rabe yake da mace ba.

12 Wato, kamar yadda mace take daga namiji, haka namiji kuma haihuwar mace ne. Amma dukkan abubuwa daga Allah suke.

13 Ku kanku ku duba fa ku gani. Ya dace da mace ke nan ta yi addu’a ga Allah da kanta a buɗe?

14 Ashe, ko ɗabi’a ma ba ta nuna muku cewa namiji ya yi gizo, abin kunya ne ba?

15 In kuwa mace tana da gashi, ba alfarmarta ce ba? Gama don rufin kai ne aka yi mata gashin.

16 In kuwa wani yana da niyyar gardama, to, mu dai ba mu san wata al’ada ba, ikilisiyoyin Allah kuma haka.

Ƙasƙantar da Cin Jibin Ubangiji

17 A game da umarnin nan kuwa, ban yaba muku ba, taruwarku ba ta kirki ba ce, ta rashin kirki ce.

18 To, da farko dai sa’ad da kuka taru, taron ikkilisiya, na ji har akwai rarrabuwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen.

19 Don lalle ne a sami tsattsaguwa a tsakaninku, don a iya rarrabewa da waɗanda suke amintattu a cikinku.

20 Ashe kuwa, in kun taru gu ɗaya, ba jibin Ubangiji kuke ci ba!

21 Domin a wajen cin abinci, kowa yakan dukufa a kan akushinsa, ga wani yana jin yunwa, ga wani kuwa ya sha ya bugu.

22 A! Ba ku da gidajen da za ku ci ku sha a ciki ne? Ko kuwa kuna raina Ikkilisiyar Allah ne, kuna kuma muzanta waɗanda ba su da kome? To, me zan ce muku? Yaba muku zan yi a kan wannan matsala? A’a, ba zan yaba muku ba.

Cin Jibin Ubangiji

23 Abin nan kuwa da na karɓa a gun Ubangiji, shi ne na ba ku, cewa Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki gurasa,

24 bayan da ya yi godiya ga Allah kuma, sai ya gutsuttsura, ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake saboda ku. Ku riƙa yin haka domin tunawa da ni.”

25 Haka kuma bayan jibin, sai ya ɗauki ƙoƙo, ya ce, “Ƙoƙon nan na Sabon Alkawari ne, da aka tabbatar da shi da jinina. Ku yi haka duk a sa’ad da kuke sha, domin tunawa da ni.”

26 Wato, duk sa’ad da kuke cin gurasar nan, kuke kuma sha a ƙoƙon nan, kuma ayyana mutuwar Ubangiji ke nan, har sai ya dawo.

Cin Jibin Ubangiji da Rashin Cancanta

27 Saboda haka duk wanda ya ci gurasar nan, ko ya sha a ƙoƙon nan na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulakanta jikin Ubangiji da jininsa ke nan.

28 Sai dai kowa ya auna kansa, sa’an nan ya ci gurasar, ya kuma sha a ƙoƙon.

29 Kowa ya ci, ya kuma sha, ba tare da faɗaka da jikin Ubangiji ba, ya jawo wa kansa hukunci ke nan, ta wurin ci da sha da ya yi.

30 Shi ya sa da yawa daga cikinku suke da rashin lafiya da rashin ƙarfi, har ma waɗansu da dama suka yi barci.

31 Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za a hukunta mu ba.

32 In kuwa Ubangiji ne yake hukunta mu, to, muna horuwa ke nan, don kada a yanke mana hukunci tare da sauran duniya.

33 Saboda haka, ya ‘yan’uwana, in kuka taru don cin abinci, sai ku jiraci juna.

34 In kuwa wani yana jin yunwa, sai yă ci a gida, kada yă zamana taronku ya jawo muku hukunci. Batun sauran abubuwa kuwa, zan ba da umarni a kai sa’ad da na zo.

Categories
1 KOR

1 KOR 12

Bayebaye na Ruhu

1 A yanzu kuma ‘yan’uwa, a game da baye-baye na ruhu, ba na so ku rasa sani.

2 Kun sani fa a sa’ad da kuke bin al’ummai, an juyar da ku ga bin gumakan nan marasa baki yadda aka ga dama.

3 Don haka nake sanar da ku, cewa ba mai magana ta wurin ikon Ruhun Allah sa’an nan ya ce, “Yesu la’ananne ne!” Haka kuma ba mai iya cewa, “Yesu Ubangiji ne,” sai ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.

4 To, akwai baiwa iri iri, amma Ruhu ɗaya ne.

5 Akwai fanni iri iri na ibada, amma Ubangiji ɗaya ne.

6 Akwai kuma aiki iri iri, amma Allah ɗaya yake iza kowa ga yin kowannensu.

7 An yi wa kowanne baiwa da wani buɗi na Ruhu, don kyautata wa duka.

8 Wani an yi masa baiwa da koyar da hikima ta wurin Ruhu, wani kuma da koyar da sani ta wurin wannan Ruhu.

9 Wani kuwa an yi masa baiwa da bangaskiya ta wurin Ruhun nan, wani kuma baiwar warkarwa ta wurin Ruhun nan,

10 wani kuma yin mu’ujizai, wani kuma annabci, wani kuma baiwar rarrabe ruhu da aljani, wani kuma iya harshe iri iri, wani kuma fassara harsuna.

11 Dukan waɗannan Ruhu ɗaya ne da yake iza su, yake kuma rarraba wa ko wannensu yadda ya nufa.

Dukkanmu Gaɓoɓin Jiki Guda Ne

12 Wato, kamar yadda jiki yake guda, yake kuma da gaɓoɓi da yawa su gaɓoɓin kuwa ko da yake suna da yawa, jiki guda ne, to, haka ga Almasihu.

13 Dukanmu an yi mana baftisma ta wurin Ruhu guda, mu zama jiki guda, Yahudawa ko al’ummai, bayi ko ‘ya’ya, dukanmu kuwa an shayar da mu Ruhu guda.

14 Jiki ba gaba ɗaya ba ne, gaɓoɓi ne da yawa.

15 Da ƙafa za ta ce, “Da yake ni ba hannu ba ce, ai, ni ba gaɓar jiki ba ce,” faɗar haka ba za ta raba ta da zama gaɓar jikin ba.

16 Da kuma kunne zai ce, “Da yake ni ba ido ba ne, ai, ni ba gaɓar jiki ba ne,” faɗar haka ba za ta raba shi da zama gaɓar jikin ba.

17 Da dukan jiki ido ne, da me za a ji? Da dukan jiki kunne ne, da me za a sansana?

18 Amma ga shi, Allah ya shirya gaɓoɓin jiki, kowaccensu yadda ya nufa.

19 Da dukan jikin gaɓa ɗaya ne, da ina sauran jikin?

20 Amma ga shi, akwai gaɓoɓi da yawa, jiki kuwa ɗaya.

21 Ba dama ido yă ce wa hannu, “Ba ruwana da kai,” ko kuwa kai yă ce wa ƙafafu, “Ba ruwana da ku.”

22 Ba haka yake ba, sai ma gaɓoɓin da ake gani kamar raunana, su ne wajibi,

23 gaɓoɓin jiki kuma da ake gani kamar sun kasa sauran daraja, mukan fi ba su martaba. Ta haka gaɓoɓinmu marasa kyan gani, akan ƙara kyautata ganinsu.

24 Gaɓoɓinmu masu kyan gani kuwa ba sai an yi musu kome ba. Amma Allah ya harhaɗa jiki, yana ba da mafificiyar martaba ga ƙasƙantacciyar gaɓa,

25 kada rashin haɗa kai ya kasance ga jiki, sai dai gaɓoɓin su kula da juna, kula iri ɗaya.

26 Ta haka, in wata gaɓa ta ji ciwo, duk sai su ji ciwo tare, in kuwa an yabi wata, duk sai su yi farin ciki tare.

27 To, ku jikin Almasihu ne, kowannenku kuwa gaɓarsa ne.

28 A cikin ikkilisiya, Allah ya sa waɗansu su zama, na farko manzanni, na biyu annabawa, na uku masu koyarwa, sa’an nan sai masu yin mu’ujizai, sai masu baiwar warkarwa, da mataimaka, da masu tafiyar da Ikkilisiya, da kuma masu magana da harsuna iri iri.

29 Shin, duka manzanni ne? Ko duka annabawa ne? Ko duk masu koyarwa ne? Su duka masu yin mu’ujizai ne?

30 Duka ne suke da baiwar warkarwa? Duka ne suke magana da waɗansu harsuna? Ko kuwa duka ne suke fassara?

31 Sai dai ku himmantu ga neman mafafitan bayebaye.

Har ma zan nuna muku wata hanya mafificiya nesa.

Categories
1 KOR

1 KOR 13

Ƙauna

1 Ko da zan yi magana da harsunan mutane, har da na mala’iku, amma ya zamana ba ni da ƙauna, na zama ƙararrawa mai yawan ƙara ke nan, ko kuwa kuge mai amo.

2 Ko da zan yi annabci, ina kuma fahimtar dukkan asiri, da dukkan ilimi, ko da kuma ina da matuƙar bangaskiya, har yadda zan iya kawar da duwatsu, muddin ba ni da ƙauna, to, ni ba kome ba ne.

3 Ko da zan sadaukar da duk abin da na mallaka, in kuma ba da jikina a ƙone, in har ba ni da ƙauna, to, ban amfana da kome ba.

4 Ƙauna tana sa haƙuri da kirki. Ƙauna ba ta sa kishi, ba ta yin kumbura.

5 Ƙauna ba ta sa ɗaga kai ko rashin kārā, ƙauna ba ta sa sonkai, ba ta jin tsokana, ba ta riƙo.

6 Ƙauna ba ta sa yin farin ciki da mugunta, sai dai da gaskiya.

7 Ƙauna tana sa daurewa a cikin kowane hali, da bangaskiya a cikin kowane hali, haka kuma sa zuciya a cikin kowane hali, da jimiri a cikin kowane hali.

8 Ƙauna ba ta ƙarewa har abada. Annabci zai shuɗe, harsuna za su ɓace, ilimi kuma zai shafe.

9 Ai, hakika iliminmu ba cikakke ba ne, annabcinmu kuma ba cikakke ba ne.

10 Sa’ad da kuwa cikakken ya zo, sai ɗan kiman nan yă shuɗe.

11 Sa’ad da nake yaro, nakan yi magana irin ta ƙuruciya, nakan yi tunani irin na ƙuruciya, nakan ba da hujjojina irin na ƙuruciya. Da na isa mutum kuwa, sai na bar halin ƙuruciya.

12 Gama yanzu kamar a madubi muke gani duhu duhu, a ranar nan kuwa za mu gani ido da ido. A yanzu sanina sama sama ne, a ranar nan kuwa zan fahimta sosai, kamar yadda aka fahimce ni sosai.

13 To, a yanzu abubuwan nan uku sun tabbata, bangaskiya, da bege, da kuma ƙauna, amma duk mafi girma a cikinsu ita ce ƙauna.

Categories
1 KOR

1 KOR 14

Harsuna da Annabci

1 Ku nace wa ƙauna, ku kuma himmantu ga neman bayebaye na ruhu, tun ba ma na yin annabci ba.

2 Duk wanda yake magana da wani harshe, ba da mutane yake magana ba, da Allah yake yi, ba kuwa wanda yake fahimtarsa, domin asirtattun al’amura yake ambato ta wurin Ruhu.

3 Wanda kuwa yake yin annabci, mutane yake yi wa magana domin yă inganta su, ya ƙarfafa su, yă ta’azantar da su.

4 Duk wanda yake magana da wani harshe, kansa yake ingantawa. Mai yin annabci kuwa, ikkilisiya yake ingantawa.

5 To, ina so dukanku ku yi magana da waɗansu harsuna dabam, amma na fi so ku yi annabci. Wanda yake yin annabci, ya fi mai magana da waɗansu harsuna, sai ko in wani ya yi masa fassara, domin a inganta ikkilisiya.

6 To, ‘yan’uwa, in na zo muku ina magana da waɗansu harsuna, amfanin me zan yi muku in ban zo muku da wani bayani, ko ilimi, ko annabci, ko koyar da Maganar Allah ba?

7 In abubuwan nan marasa rai, kamar su sarewa da molo, muryarsu ba ta fita sosai ba, yaya wani zai san abin da ake busawa ko kaɗawa?

8 In ba a busa ƙaho sosai ba, wa zai yi shirin yaƙi?

9 Haka ma yake a gare ku. In kun yi magana da wani harshe, wanda ba a fahimta ba, yaya wani zai san abin da ake faɗa? Kun yi magana a banza ke nan!

10 Hakika akwai harsuna iri iri a duniya, ba kuwa wanda ba shi da ma’ana.

11 In kuwa ba na jin harshen, sai in zama bare ga mai maganar, mai maganar kuma ya zama bare a gare ni.

12 Haka ma yake a gare ku. Tun da yake kun ɗokanta da samun bayebaye na Ruhu, sai ku himmantu ku ba da ƙarfinku ga inganta ikkilisiya.

13 Saboda haka duk mai magana da wani harshe, sai yă yi addu’a a yi masa baiwar fassara.

14 In na yi addu’a da wani harshe, ruhuna ne yake addu’a, amma tunanina bai amfana kowa ba.

15 To, ƙaƙa ke nan? Zan yi addu’a da ruhuna, zan kuma yi a game da tunanina. Zan yi waƙar yabon Allah da ruhuna, zan yi a game da tunanina.

16 In ba haka ba, in ka gode wa Allah da ruhu kawai, ta yaya wanda yake jahili zai ce, “Amin,” a kan godiyar da kake yi, in bai san abin da kake faɗa ba?

17 Ko da yake ka gode wa Allah sosai, ai, ɗan’uwanka bai ƙaru da kome ba.

18 Na gode Allah ina magana da waɗansu harsuna fiye da ku duka.

19 Duk da haka dai a taron ikkilisiya na gwammace in faɗi kalmomi biyar a game da tunanina, domin in karantar da waɗansu, da in faɗi kalmomi dubu goma da wani harshe.

20 Ya ku ‘yan’uwa, kada ku yi hankali irin na yara, sai dai a wajen mugunta, ku yi halin jarirai, amma a wajen hankali ku yi dattako.

21 A rubuce yake a cikin littattafai masu tsarki cewa, “Zan yi magana da jama’an nan ta wurin mutane masu baƙin harsuna, da kuma ta harshen baƙi, duk da haka kuwa ba za su saurare ni ba, in ji Ubangiji.”

22 Wato, ashe, harsuna a kan alamu suke, ba ga masu ba da gaskiya ba, sai dai ga marasa ba da gaskiya. Annabci kuwa domin masu ba da gaskiya ne, ba don marasa ba da gaskiya ba.

23 Saboda haka, in dukan ikkilisiya ta taru, kowa kuma yana magana da wani harshe dabam, waɗansu jahilai kuma ko marasa ba da gaskiya suka shigo, ashe, ba sai su ce kun ruɗe ba?

24 In kuwa kowa yana yin annabci, wani kuma marar ba da gaskiya ko jahili ya shigo, sai maganar kowa ta ratsa shi, ya kamu a ransa ta maganar kowa,

25 asiran zuciyarsa kuma su tonu. Ta haka sai ya fāɗi ya yi wa Allah sujada, yana cewa lalle Allah na cikinku.

A Yi Kome yadda Ya Dace, a Shirye

26 To, ƙaƙa abin yake ne, ‘yan’uwa? Duk sa’ad da kuka taru, wani yakan yi waƙar yabon Allah, wani kuma koyar da Maganar Allah, wani bayani, wani yin magana da wani harshe, wani kuma fassara. Sai dai a yi kome don ingantawa.

27 In kuwa waɗansu za su yi magana da wani harshe, kada su fi mutum biyu, matuƙa uku, su ma kuwa bi da bi, wani kuma yă yi fassara.

28 In kuwa ba mai fassara, sai kowannensu yă yi shiru a cikin taron Ikkilisiya, yă yi wa Allah magana a zuci.

29 Masu yin annabci kuma, sai dai biyu ko uku su yi magana, saura kuwa su auna maganar.

30 In kuwa an yi wa wani wanda yake zaune wani bayani, sai na farkon nan mai magana yă yi shiru.

31 Dukanku kuna iya yin annabci da ɗaya ɗaya, har kowa yă koya, yă koma sami ƙarfafawa.

32 Annabawa suna sarrafa ruhohinsu na annabci,

33 domin Allah ba Allahn ruɗu ba ne, na salama ne.

Haka yake kuwa a duk ikilisyoyin tsarkaka.

34 Sai mata su yi shiru a cikin taron ikkilisiya, don ba a ba su izinin yin magana ba, sai dai su bi, kamar dai yadda Attaura ma ta ce.

35 In akwai wani abin da suke so su sani, to, sai su tambayi mazansu a gida, don abin kunya ne mace ta yi magana a cikin taron ikkilisiya.

36 A kanku ne maganar Allah ta fara, ko kuwa a gare ku kaɗai ta isa?

37 In wani yana zato shi annabi ne, ko kuwa mai wata baiwa ta ruhu, to, sai yă fahimta, abin nan da nake rubuto muku umarni ne na Ubangiji.

38 In kuwa wani ya ƙi kula da wannan, shi ma sai a ƙi kula da shi.

39 Saboda haka, ‘yan’uwa, sai ku himmantu ga samun baiwar yin annabci, kada kuma ku hana yin magana da waɗansu harsuna.

40 Sai dai a yi kome ta hanyar da ta dace, a shirye kuma.

Categories
1 KOR

1 KOR 15

Tashin Almasihu daga Matattu

1 A yanzu kuma, ‘yan’uwa, zan tuna muku da bisharar da na sanar da ku, wadda kuka karɓa, wadda kuke bi,

2 wadda kuma ake cetonku da ita, muddin kun riƙe maganar da na sanar da ku da kyau, in ba sama sama ne kuka gaskata ba.

3 Jawabi mafi muhimmanci da na sanar da ku, shi ne wanda na karɓo, cewa, Almasihu ya mutu domin zunubanmu, kamar yadda Littattafai suka faɗa,

4 cewa an binne shi, an ta da shi a rana ta uku, kamar yadda Littattafai suka faɗa,

5 ya kuma bayyana ga Kefas, sa’an nan ga sha biyun.

6 Sa’an nan ya bayyana ga ‘yan’uwa fiye da ɗari biyar a lokaci guda, yawancinsu kuwa suna nan har zuwa yanzu, amma waɗansu sun yi barci.

7 Sa’an nan ya bayyana ga Yakubu, sa’an nan ga dukan manzanni.

8 Daga ƙarshen duka ya bayyana a gare ni, ni ma da nake kasasshe, marar cancanta.

9 Don ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban ma isa a ce da ni manzo ba, saboda na tsananta wa Ikkilisiyar Allah.

10 Amma saboda alherin Allah na zama yadda nake, alherin da ya yi mini kuwa ba a banza yake ba. Har ma na fi kowannensu aiki, ba kuwa ni ba, alherin Allah ne da yake zuciyata.

11 To, ko ni ne dai, ko kuma su ne, haka muke wa’azi, ta haka kuma kuka gaskata.

Tashin Matattu

12 To, da yake ana wa’azin Almasihu a kan an tashe shi daga matattu, ƙaƙa waɗansunku suke cewa, babu tashin matattu?

13 In dai babu tashin matattu, ashe, ba a ta da Almasihu ba ke nan.

14 In kuwa ba a ta da Almasihu ba, to, ashe, wa’azinmu a banza ne, bangaskiyarku kuma banza ce.

15 Sai ma ya zamana mun yi wa Allah shaidar zur ke nan, domin mun shaida Allah, cewa ya ta da Almasihu, wanda kuwa bai tasar ba, in da gaskiya ne ba a ta da matattu.

16 Don kuwa in ba a ta da matattu, ashe, Almasihu ma ba a ta da shi ba ke nan.

17 In kuwa ba a ta da Almasihu ba, ashe, bangaskiyarku banza ce, har yanzu kuma kuna tare da zunubanku.

18 Ashe, waɗanda suka yi barci a kan su na Almasihu, sun hallaka ke nan.

19 Da begenmu ga Almasihu domin wannan rai ne kaɗai, ai, da mun fi kowa zama abin tausayi.

20 Amma ga hakika an ta da Almasihu daga matattu, shi ne ma nunan fari na waɗanda suka yi barci.

21 Tun da yake mutuwa ta wurin mutum ta faru, haka kuma tashin matattu ta wurin Mutum yake.

22 Kamar yadda duk ake mutuwa saboda Adamu, haka duk za a rayar da su saboda Almasihu.

23 Amma kowanne bi da bi, Almasihu ne nunan fari, sa’an nan a ranar komowarsa, waɗanda suke na Almasihu.

24 Sa’an nan sai ƙarshen, sa’ad da zai mayar wa Allah Uba mulki, bayan ya shafe dukkan sarauta da mulki da iko.

25 Domin kuwa lalle ne ya yi mulki, har ya take dukkan maƙiyansa.

26 Magabciyar ƙarshe da za a shafe, ita ce mutuwa.

27 “Gama Allah ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa.” Amma da aka ce, “An sarayar da kome karƙashin ikonsa” a fili yake shi wannan da ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa ɗin, a keɓe yake.

28 Sa’ad da kuma aka sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa ɗin, sa’an nan ne Ɗan da kansa shi ma zai sarayar da kansa ga wannan da ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa, domin Allah yă tabbata shi ne kome da kome.

29 In ba haka ba, mene ne nufin waɗanda ake yi wa baftisma saboda matattu? In ba a ta da matattu sam, don me ake yi wa waɗansu baftisma saboda su?

30 Don me kuma nake a cikin hatsari a kowane lokaci?

31 Na hakikance ‘yan’uwa, saboda taƙama da ku da nake yi a cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu, a kowace rana sai na sallama raina ga mutuwa!

32 Idan bisa ga ra’ayin mutum ne, na yi kokawa da namomin jeji a Afisa, mece ce ribata in dai har ba a ta da matattu? “Ba sai mu yi ta ci da sha ba, da yake gobe za mu mutu?”

33 Kada fa a yaudare ku! “Zama da mugaye yakan ɓata halayen kirki.”

34 Ku farka daga magagi, ku kama aikin adalci, ku daina yin zunubi. Waɗansu kam, ba su da sanin Allah. Na faɗi wannan ne don ku kunyata.

Tashin Jiki

35 Watakila wani zai yi tambaya, “Ta yaya ake ta da matattu? Da wace irin kama kuma suke fitowa?”

36 Kai, marar azanci! Abin da ka shuka, ai, ba zai tsiro ba sai ya mutu.

37 Abin da ka shuka kuma, ba shi ne ainihin abin da zai kasance ba, ƙwaya ce ƙawai, ko ta alkama ce, ko kuma, wata iri dabam.

38 Amma Allah yakan ba ta kama, yadda ya nufa, kowace ƙwaya da irin tata kama.

39 Don ba dukan tsoka ce iri ɗaya ba, mutane da irin tasu, dabbobi ma da irin tasu, tsuntsaye da irin tasu, kifaye kuma da irin tasu.

40 Akwai halitta irin ta Sama, akwai kuma irin ta ƙasa. Amma ɗaukakar irin ta Sama dabam, ɗaukakar irin ta ƙasa kuma dabam.

41 Ɗaukakar rana dabam, ta wata dabam, ta taurari kuma dabam. Wani tauraro kuwa yakan bambanta da wani a wajen ɗaukaka.

42 Haka kuma yake ga tashin matattu. Akan shuka su da halin ruɓa, akan kuma ta da su da halin rashin ruɓa.

43 Akan shuka da wulakanci, akan tasa da ɗaukaka, akan shuka da rashin ƙarfi, akan tasa da ƙarfi.

44 Akan shuka da jikin mutuntaka, akan tasa da jiki na ruhu. Da yake akwai jiki na mutuntaka, lalle kuma akwai jiki na ruhu.

45 Haka kuma yake a rubuce, “Mutumin farko, Adamu, ya zama rayayyen taliki,” Adamun ƙarshe kuwa Ruhu ne mai rayarwa.

46 Amma ba shi na Ruhun nan ne ya fara bayyana ba, na mutuntaka ne, daga baya kuma sai na Ruhu.

47 Mutumin farko daga ƙasa yake, na turɓaya ne. Na biyun kuwa daga Sama yake.

48 Kamar yadda shi na turɓayar nan yake, haka kuma waɗanda suke na turɓaya suke. Kamar yadda shi na Saman nan yake, haka kuma waɗanda suke na Sama suke.

49 Kamar yadda muka ɗauki siffar na turɓayar nan, haka kuma za mu ɗauki siffar na Saman nan.

50 Ina dai gaya muku wannan ‘yan’uwa, ba shi yiwuwa jiki mai tsoka da jini ya sami gādo a Mulkin Allah, haka kuma mai ruɓa ba ya gādon marar ruɓa.

51 Ga shi, zan sanar da ku wani asiri! Ba dukanmu ne za mu yi barci ba, amma dukanmu za a sauya kamanninmu,

52 farat ɗaya da ƙyiftawar ido, da jin busar ƙaho na ƙarshe, domin za a busa ƙaho, za a kuma ta da matattu da halin rashin ruɓa, za a kuma sauya kamanninmu.

53 Domin lalle ne, marar ruɓa ya maye mai ruɓar nan, marar mutuwa kuma ya maye mai mutuwar nan.

54 Sa’ad da kuma marar ruɓa ya maye mai ruɓar nan, marar mutuwa kuma ya maye mai mutuwar nan, a sa’an nan ne fa maganar nan da take a rubuce za a cika ta, cewa,

“An shafe mutuwa da aka ci nasararta.”

55 “Ke mutuwa, ina nasararki?

Ke mutuwa, ina ƙarinki?”

56 Ai, zunubi shi ne ƙarin mutuwa, Shari’a kuwa ita ce sanadin ƙarfin zunubi.

57 Godiya tā tabbata ga Allah wanda yake ba mu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu.

58 Don haka, ya ‘yan’uwana, ƙaunatattu, ku tsaya a kafe, kullum kuna himmantuwa ga aikin Ubangiji, domin kuwa kun san famar da kuke yi saboda Ubangiji ba a banza take ba.

Categories
1 KOR

1 KOR 16

Gudunmawa ga Tsarkaka

1 To, a yanzu kuma ga zancen ba da gudunmawa ga tsarkaka, kamar yadda na umarci ikilisiyoyin Galatiya, haka ku ma za ku yi.

2 A kowace ranar farko ta mako, kowannenku ya riƙa tanada wani abu, yana ajiyewa gwargwadon samunsa, kada sai na zo tukuna, a tara gudunmawa.

3 Sa’ad da na iso, sai in aiki waɗanda kuka amince da su da wasiƙa, su kai taimakonku Urushalima.

4 In ya kyautu ni ma in tafi, to, sai su raka ni.

Shirye-shiryen Tafiya

5 Zan zo gare ku bayan na zazzaga ƙasar Makidoniya, don kuwa ta Makidoniya zan bi.

6 Watakila zan jima a wurinku, ko ma in ci damina, don ku yi mini rakiya duk in da za ni.

7 Ba sona ne in gan ku a yanzu in wuce kawai ba, a’a, ina sa zuciya ma in yi kwanaki a wurinku, in Ubangiji ya yarda.

8 Amma zan dakata a Afisa har ranar Fentikos.

9 Don kuwa, an buɗe mini wata hanya mai fāɗi ta yin aiki mai amfani, akwai kuma magabta da yawa.

10 In Timoti ya zo, ku tabbata ya sami sakewa a cikinku, domin aikin Ubangiji yake yi kamar yadda nake yi.

11 Kada fa kowa yă raina shi. Ku raka shi lafiya, ya komo a gare ni, domin ina duban hanyarsa tare da ‘yan’uwa.

12 Ga zancen ɗan’uwanmu Afolos kuwa, na roƙe shi ƙwarai, don yă zo wurinku, tare da saurar ‘yan’uwa, amma ko kusa bai yi nufin zuwa a yanzu ba. Zai zo dai sa’ad da ya ga ya dace.

Gargaɗi da Gaisuwa

13 Ku zauna a faɗake, ku dāge ga bangaskiyarku, ku yi ƙwazo, ku yi ƙarfi.

14 Duk abin da za ku yi, ku yi shi da ƙauna.

15 To, ‘yan’uwa, kun sani fa jama’ar gidan Istifanas su ne nunan fari a ƙasar Akaya, sun kuwa ba da kansu ga yi wa tsarkaka hidima.

16 Ina roƙonku ku yi wa irin waɗannan mutane biyayya, har ma ga duk waɗanda suke abokan aikinmu da wahalarmu.

17 Na yi farin ciki da zuwan Istifanas, da Fartunatas, da Akaikas, domin sun ɗebe mini kewarku.

18 Sun dai wartsakar da ni da kuma ku. Sai ku kula da irin waɗannan mutane.

19 Ikilisiyoyin ƙasar Asiya suna gaishe ku. Akila da Bilkisu, tare da ikkilisiyar da take taruwa a gidansu, suna gaishe ku da kyau da kyau saboda Ubangiji.

20 Dukan ‘yan’uwa suna gaishe ku. Ku gaggai da juna da tsattsarkar sumba.

21 Ni Bulus, ni nake rubuta gaisuwar nan da hannuna.

22 Duk wanda ba ya ƙaunar Ubangiji yă zama la’ananne. Ubangijinmu fa yana zuwa!

23 Alherin Ubangijinmu Yesu yă tabbata a gare ku.

24 Ina gaishe ku duka, gaisuwar ƙauna, albarkar Almasihu Yesu.