Categories
2 KOR

2 KOR 11

Bulus da Manzannin Ƙarya

1 Da ma a ce ku jure ‘yar wautata. Ku dai yi haƙuri da ni!

2 Ina kishi a kanku saboda Allah. Gama na bashe ku ga Almasihu, domin in miƙa ku kamar amarya tsattsarka ga makaɗaicin mijinta.

3 Amma ina tsoro kada yă zamana, kamar yadda maciji ya yaudari Hawwa’u da makircinsa, ku ma a bauɗar da hankalinku daga sahihiyar biyayya amintacciya ga Almasihu.

4 Don in wani ya zo yana wa’azin wani Yesu dabam da wanda muka yi wa’azi, ko kuma in kun sami wani ruhu dabam da Ruhun da kuka samu, ko wata bishara dabam da wadda kuka yi na’am da ita, ashe, har kuna saurin yin na’am da irinsu ke nan!

5 A ganina ban kasa mafifitan manzannin nan da kome ba.

6 Ko da yake ni bāmi ne a wajen yin magana, a wajen sani kam, ba haka ba ne, mun kuwa bayyana wannan sarai ta kowace hanya a cikin dukan sha’aninmu da ku.

7 Ashe, laifi na yi da na ƙasƙantar da kaina, don a ɗaukaka ku, wato, saboda na yi muku bisharar Allah a kyauta?

8 Waɗansu ikilisiyoyi na biyan hakkina, sai ka ce ina yi musu ƙwace domin in yi muku hidima.

9 Sa’ad da nake a wurinku kuma nake zaman rashi, ban nauyaya wa kowa ba, domin ‘yan’uwan da suka zo daga Makidoniya su ne suka biya mini bukata. Saboda haka, na ƙi nauyaya muku ta kowace hanya, ba kuwa zan nauyaya muku ba.

10 Albarkacin gaskiyar Almasihu da yake tare da ni, ba mai hana ni fahariyar nan tawa a lardin Akaya.

11 To, don me? Domin ba na ƙaunarku ne? Allah dai ya sani ina ƙaunarku.

12 Abin da nake yi kuwa, shi zan riƙa yi, domin in toshe kafar mutanen nan da suke fariya, suna nema mu daidaita da su.

13 Irin waɗannan mutane manzannin ƙarya ne, mayaudaran ma’aikata, suna mai da kansu kamar su manzannin Almasihu ne.

14 Ba abin mamaki ba ne kuwa, domin ko Shaiɗan ma da kansa, yakan mai da kansa kamar shi mala’ikan haske ne.

15 Don haka, ba abin mamaki ba ne in bayinsa ma sun mai da kansu kamar su bayi ne na aikin adalci. A ƙarshe za a saka musu gwargwadon ayyukansu.

Wahalar Bulus saboda Manzanci

16 Ina sāke faɗa, kada wani ya zaci ni wawa ne. In kuwa kun zaci haka nake, to, ku ji ni wawa ne, don ni ma in samu in taɓa ‘yar taƙama kaɗan.

17 Abin nan da nake faɗa fa, ba bisa ga umarnin Ubangiji nake faɗa ba, sai dai magana ce irin ta wawa, wadda yake yi gabagaɗi, yana fariya,

18 da yake mutane da yawa suna fariya irin ta ‘yan adam kawai, ni ma zan yi.

19 Ai, ku kam, hikimarku har ta kai ga jure wa wawaye da murna!

20 Don in wani ya sa ku bauta, kukan jure masa, ko ya yi muku ƙwace, ko ya more ku, ko ya nuna muka isa, ko kuwa ya mare ku.

21 Mu kam, saboda rauninmu, wane mu da yin haka!

Amma ta ko yaya wani yake ƙarfin halin yin fariya, ina magana a kan ni wawa ne fa! to, ni ma sai in yi.

22 In su Ibraniyawa ne, ni ma haka. In su Isra’ilawa ne, ni ma haka. In su zuriyar Ibrahim ne, ni ma haka.

23 In su bayin Almasihu ne, ni na fi su ma, ina magana kamar ruɗaɗɗe ne fa! ai, na fi su shan fama ƙwarai da gaske, da shan ɗauri, na sha dūka marar iyaka, na sha hatsarin mutuwa iri iri.

24 Sau biyar Yahudawa suka yi mini bulala arba’in ɗaya babu.

25 Sau uku aka bulale ni da tsumagu, sau ɗaya har aka jejjefe ni da dutse. Sau uku jirgi ya ragargaje ina ciki, na kwana na yini ruwan bahar yana tafiya da ni.

26 Na yi tafifiya da yawa, na sha hatsari a koguna , na sha hatsarin ‘yan fashi, na sha hatsari a hannun kabilarmu, na sha hatsari a hannun al’ummai, na sha hatsari a birane, na sha hatsari a jeji, na sha hatsari a bahar, na kuma sha hatsarin ‘yan’uwa na ƙarya.

27 Na sha fama, na sha wuya, na sha rashin barci, na sha yunwa da ƙishirwa, sau da yawa na rasa abinci, na sha sanyi da huntanci.

28 Banda waɗansu abubuwa dabam kuma, kowace rana ina a matse da matsananciyar kula saboda dukan ikilisiyoyi.

29 Wane ne ya raunana da ban raunana ba? Wane ne aka sa tuntuɓe, ban ji zafin ba?

30 In ma lalle ne in yi gadara, to, sai in yi taƙama da abubuwan da suke nuna raunanata.

31 Allahn Ubangiji Yesu, wato Ubansa, wanda ya yabo ya tabbata a gare shi har abada, ya sani ba ƙarya nake yi ba.

32 A Dimashƙu gwamnan da yake ƙarƙashin sarki Aretis ya tsare ƙofofin birnin Dimashƙu don ya kama ni,

33 amma sai aka zura ni a cikin babban kwando ta tagar garu, na kuɓuce masa.

Categories
2 KOR

2 KOR 12

Wahayan Bulus da Bayani Iri Iri

1 An tilasta mini ne in yi gadara, ko da yake ba ta amfane ni da kome ba. Amma zan ci gaba da zancen ruya da wahayi da Ubangiji ya yi mini.

2 Na san wani mutum wanda yau shekara goma sha huɗu ke nan, aka ɗauke shi zuwa Sama ta uku bisa ga ikon Almasihu, ko yana a cikin jiki ne, ko ba a cikin jiki ba, ban sani ba, Allah ne masani.

3 Na kuma san mutumin nan, an ɗauke shi zuwa Firdausi, ko yana a cikin jiki ne, ko ba a cikin jiki ba, ban sani ba, Allah ne masani,

4 ya kuma ji waɗansu maganganu, waɗanda ba dama a faɗa, irin ma waɗanda ɗan adam ba shi da izinin faɗa.

5 Zan yi gadara da mutumin nan kam, amma ba zan yi gadara da kaina ba, sai dai ko da raunanata.

6 Ko da zan so yin gadara ma, ba zan zama wawa ba, gama gaskiya zan faɗa. Amma na bar zancen haka, don kada wani ya ɗauke ni fiye da yadda yake ganina, ko yadda yake jin maganata.

7 Don kada kaina yă kumbura kuma saboda mafifitan wahayan da aka yi mini, sai aka saka mini wata cuta, wadda ta zama mini ƙaya, jakadan Shaiɗan, don yă riƙa wahalshe ni, don kada kaina ya kumbura.

8 Sau uku nake roƙon Ubangiji a kan wannan abu ya rabu da ni,

9 amma ya ce mini, “Alherina yā isa, domin ta wajen rashin ƙarfi ake ganin cikar ikona.” Saboda haka sai ma in ƙara yin alfarma da raunanata da farinciki fiye da na da, domin ikon Almasihu ya zauna a tare da ni.

10 Saboda haka, ina murna da raunanata, da cin mutuncin da ake yi mini, da shan wuya, da shan tsanani, da masifu saboda Almasihu, don sa’ad da nake rarrauna, a sa’an nan ne nake da ƙarfi.

Alhinin Bulus a kan Ikkilisiyar Koranti

11 Na yi wauta kam, amma ku ne kuke tilasta mini, ku ne kuwa ya kamata ku yaba mini, domin ba inda na kasa waɗannan mafifitan manzanni, ko da yake ni ba kome ba ne.

12 An gudanar da tabbatattun alamun manzo a cikinku ta matuƙar jimiri, da alamu da abubuwan al’ajabi da mu’ujizai.

13 Ta wace hanya ce kuka kasa sauran ikkilisiyoyi? Ko kuwa domin dai ni ban nauyaya muku ba? To, ku yafe mini wannan laifi!

14 Ga shi, na yi shirin zuwa wurinku, zuwa na uku, ba kuwa zan nauyaya muku ba, don ba abinku nake nema ba, ku nake nema, domin ba yara ne da ɗaukar nauyin iyayensu ba, sai dai iyaye ne da ɗaukar nauyin yaran.

15 Ni kam, zan kashe dukan abin hannuna da dukan zarafina da matuƙar farin ciki saboda ranku. In na ƙara ƙaunarku, ashe, sai a rage ƙaunata?

16 To, a ce ban nauyaya muku ba ɗin, ashe, sai ku ce dabara na yi muku, na shawo kanku ta hanyar yaudara!

17 Na cuce ku ne ta wurin wani daga cikin waɗanda na aiko a gare ku?

18 Na roƙi Titus ya je, na kuma aiko ɗan’uwan nan tare da shi. To, Titus ya cuce ku ne? Ashe, ba Ruhu ɗaya yake bi da mu ba, ni da shi? Ba kuma hanya ɗaya muke bi ba?

19 Ashe, tun dā tsammani kuke yi muna kawo hanzarinmu a gare ku ne? A’a, a gaban Allah muke magana, muna na Almasihu, wannan kuwa duk domin inganta ku ne, ya ku ƙaunatattu.

20 Ina tsoro kada watakila in na zo in same ku ba a yadda nake so ba, ku kuma ku gan ni ba a yadda kuke so ba, ko ma a tarar da jayayya, da kishi, da fushi, da sonkai, da yanke, da tsegunguma, da girmankai, da tashin hankali.

21 Ina tsoro kada in na sāke zuwa, Allahna ya ƙasƙanta ni a gabanku, in kuma yi baƙin ciki saboda waɗansu da yawa da suka yi zunubi a dā, ba su kuwa tuba da aikinsu na lalata ba, da fasikancinsu, da fajircinsu da suka aikata.

Categories
2 KOR

2 KOR 13

Kashedi da Gaisuwa

1 Wannan shi ne zai zama zuwana na uku a gare ku. Lalle ne kuwa a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku.

2 Na gargaɗi waɗanda suka yi zunubi a dā, da kuma saura duka, a yanzu kuma da ba na nan ina yi musu gargaɗi, kamar yadda na yi sa’ad da nake nan a zuwana na biyu, cewa in na sāke zuwa ba zan sawwaƙe musu ba.

3 In dai nema kuke yi ku tabbata, cewa da izinin Almasihu nake magana, to, ai, shi ba rarrauna ba ne a gare ku, amma ƙaƙƙarfa ne a cikinku.

4 Ko da yake an gicciye shi ne da rashin ƙarfi, duk da haka a raye yake ta ikon Allah. Mu ma marasa ƙarfi ne kamarsa, amma a game da al’amuranku da za mu zartar, a raye muke tare da shi, ta ikon Allah.

5 Ku jarraba kanku ku gani, ko har yanzu kuna a raye da bangaskiya. Ku riƙa auna kanku. Ashe, ba ku tabbata Almasihu yana a cikinku ba? Sai ko in kun kasa ga gwajin!

6 Muna fata ku gane, mu ba mu kāsa ba.

7 Amma muna roƙon Allah kada ku yi wani mugun abu, ba don mu mu zama kamar mun ci gwajin kawai ba, sai dai domin ku yi abin da yake daidai, ko da yake za ku ga kamar mun kāsa.

8 Domin ba dama mu sāɓa wa gaskiya, sai dai mu bi bayan gaskiyar.

9 Gama farin ciki muke yi in muna raunana, ku kuna ƙarfafa. Addu’armu ita ce ku kammala.

10 Ina rubuta wannan ne sa’ad da ba na tare da ku, domin sa’ad da na zo, kada ya zama mini tilas in yi muku tsanani a game da nuna ikon nan da Ubangiji ya ba ni saboda ingantawa, ba saboda rushewa ba.

11 Daga ƙarshe kuma, ‘yan’uwa, sai wata rana. Ku kammala halinku. Ku kula da roƙona, ku yi zaman lafiya da juna, ku yi zaman salama, Allah mai zartar da ƙauna da salama kuwa zai kasance a tare da ku.

12 Ku gaggai da juna da tsattsarkar sumba.

13 Dukan tsarkaka suna gaishe ku.

14 Alherin Ubangiji Yesu Almasihu, da ƙaunar Allah, da zumuntar Ruhu Mai Tsarki su tabbata a gare ku duka.