Categories
2 SAM

2 SAM 1

Dawuda Ya ji Labarin Rasuwar Saul da Jonatan

1 Bayan rasuwar Saul, sa’ad da Dawuda ya komo daga karkashe Amalekawa, ya yi kwana biyu a Ziklag.

2 Kashegari sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Saul, da tufafinsa a yayyage, da ƙura kuma a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi ƙasa, ya yi gaisuwa.

3 Sai Dawuda ya tambaye shi, ya ce, “Daga ina ka zo?”

Ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ilawa.”

4 Dawuda ya ce masa, “Faɗa mini abin da ya faru.”

Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga bakin dāga, an kuma kashe galibin mutanenmu. Saul da ɗansa Jonatan kuma sun mutu.”

5 Dawuda ya ce wa mutumin, “Ta yaya ka sani Saul da ɗansa, Jonatan, sun mutu?”

6 Mutumin kuwa ya amsa ya ce, “Ya zama fa ina kan dutsen Gilbowa, sai ga Saul ya jingina a māshinsa. Karusai da mahayan dawakan abokan gāba sun rutsa shi.

7 Da ya waiga, ya gan ni, sai ya kira ni, ni kuwa na amsa, na ce, ‘Ga ni.’

8 Ya ce mini, ‘Wane ne kai?’ Na ce masa, ‘Ni Ba’amaleke ne.’

9 Sai ya ce mini, ‘Zo ka kashe ni gama ina cikin azaba, amma raina bai fita ba.’

10 Sai na tafi na kashe shi domin na tabbata ba zai yi rai ba bayan ya fāɗi. Na kuma cire kambin da yake kansa da ƙarau da yake a dantsensa. Ga su, na kawo wa ubangijina.”

11 Sai Dawuda ya yayyage tufafinsa. Dukan mutanen da suke tare da shi kuma suka yayyage nasu.

12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har maraice saboda Saul, da Jonatan ɗansa, da mutanen Ubangiji, da gidan Isra’ila domin an Karkashe su a yaƙi.

13 Dawuda ya ce wa mutumin nan da ya kawo labarin, “Daga ina ka zo?”

Sai ya ce masa, “Ai, ni ɗan wani baƙo ne, Ba’amaleke.”

14 Dawuda ya ce, “Me ya sa ba ka ji tsoro ka miƙa hannunka, ka hallaka wanda Ubangiji ya keɓe ba?”

15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin samarin, ya ce masa, “Ka kashe shi.” Ya dai buge shi, ya mutu.

16 Dawuda kuwa ya ce, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe wanda Ubangiji ya keɓe.’ ”

Dawuda Ya Yi Makoki domin Saul da Jonatan

17 Sai Dawuda ya raira waƙar makoki domin Saul da Jonatan, ɗansa.

18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuza wannan waƙa. (An rubuta ta a littafin Yashar.)

19 “An kashe darajarki, ya Isra’ila, a kan tuddanki!

Jarumawan sojojinmu sun fāɗi!

20 Kada a ba da labarin a Gat,

Ko a titin Ashkelon.

Kada ku sa matan Filistiyawa su yi murna,

Kada ku sa ‘yan matan arna su yi farin ciki.

21 “Kada ruwan sama ko raɓa su zubo kan tuddan Gilbowa.

Da ma gonakinta su zama marasa ba da amfani.

Gama a can ne aka zube garkuwoyin jarumawa a wulakance,

Tsatsa ta rufe garkuwar Saul.

22 Bakan Jonatan mai kisa ne,

Takobin Saul ba shi da jinƙai,

Yana kashe masu iko, yana kuma kashe abokan gāba.

23 “Saul da Jonatan ƙaunatattu ne, suna da bansha’awa,

A raye suna tare, haka kuma a mace suna tare.

Sun fi gaggafa sauri,

Sun fi zaki ƙarfi.

24 “Ku ‘yan matan Isra’ila, ku yi makoki domin Saul!

Ya suturta ku da mulufi mai ƙayatarwa,

Ya yi muku adon lu’ulu’u da zinariya.

25 “Jarumawa sun fāɗi,

An kashe su a bakin dāga.

Jonatan na kwance matacce a tuddai.

26 “Na damu ƙwarai saboda kai, ɗan’uwana Jonatan,

Ƙaunatacce kake a gare ni!

Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce,

Ta fi ƙaunar mace.

27 “Jarumawa sun fāɗi,

Makamansu ba su da sauran amfani.”

Categories
2 SAM

2 SAM 2

An Naɗa Dawuda Sarkin Yahuza

1 Bayan wannan sai Dawuda ya roƙi Ubangiji, ya ce, “Ko in haura in mallaki ɗaya daga cikin garuruwan Yahuza?”

Ubangiji ya ce masa, “Ka haura.”

Dawuda kuma ya ce, “Zuwa wane gari zan haura?”

Sai Ubangiji ya ce masa, “Zuwa Hebron.”

2 Dawuda kuwa ya haura zuwa can tare da matansa biyu, wato Ahinowam Bayezreyeliya, da Abigail matar marigayi Nabal Bakarmele.

3 Ya kuma tafi tare da mutanen da suke tare da shi, kowa da iyalinsa. Suka zauna a garuruwan Hebron.

4 Mutanen Yahuza kuwa suka zo, suka naɗa Dawuda da man naɗawa domin ya zama Sarkin Yahuza.

Da Dawuda ya ji labari mutanen Yabesh-gileyad, sun binne Saul,

5 sai ya aiki manzanni da saƙo wurin mutanen Yabesh-gileyad ya ce, “Ubangiji ya sa muku albarka da yake kun yi wa Saul, ubangijinku, wannan alheri, har kuka binne shi.

6 Ubangiji ya nuna muku ƙaunarsa da amincinsa. Ni kuwa zan yi muku alheri saboda abin da kuka yi.

7 Yanzu sai ku ƙarfafa, ku yi jaruntaka, gama Saul shugabanku ya rasu, mutanen Yahuza kuwa sun naɗa ni sarkinsu.”

Dawuda ya Yaƙi Gidan Saul

8 Abner kuwa ɗan Ner, sarkin yaƙin Saul, ya tsere da Ish-boshet, ɗan Saul, zuwa Mahanayim.

9 Ya naɗa shi Sarkin Gileyad, da Ashiru, da Yezreyel, da Ifraimu, da ƙasar Biliyaminu, da dukan Isra’ila.

10 Ish-boshet, ɗan Saul, yana da shekara arba’in sa’ad da ya ci sarautar Isra’ila, ya yi shekara biyu yana sarauta. Amma mutanen Yahuza suka bi Dawuda.

11 Dawuda ya yi shekara bakwai da rabi yana sarautar Yahuza a Hebron.

12 Abner, ɗan Ner, tare da fādawan Ish-boshet, ɗan Saul, suka tashi daga Mahanayim zuwa Gibeyon.

13 Sai kuma Yowab, ɗan Zeruya, tare da fādawan Dawuda suka fita suka tafi tarye su a tafkin Gibeyon. Suka zauna, waɗannan a wannan gefe, waɗancan a wancan gefe na tafkin.

14 Sai Abner ya ce wa Yowab, “Bari samarin su tashi su yi kokawa a gabanmu.”

Yowab kuwa ya ce, “To, sai su tashi.”

15 Sai suka tashi, suka haye. Mutum goma sha biyu a madadin mutanen Biliyaminu da Ish-boshet, ɗan Saul, mutum goma sha biyu kuma a madadin mutanen Dawuda.

16 Kowa ya kama abokin kokawarsa a kā, suka soki juna a kwiɓi da takuba. Suka faɗi tare. Aka sa wa wurin suna Helkat-hazzurim, wato filin takuba, wurin yana nan a Gibeyon.

17 Yaƙin kuwa ya yi zafi a ranar. Mutanen Dawuda suka ci Abner da mutanen Isra’ila.

18 ‘Ya’yan Zeruya, maza, su uku suna nan, wato Yowab, da Abishai, da Asahel. Asahel maguji ne kamar barewa.

19 Sai ya tasar wa bin Abner haiƙan, bai kauce ba.

20 Da Abner ya waiga, sai ya ce, “Kai ne Asahel?”

Ya amsa, “Ni ne.”

21 Abner ya ce masa, “Ka daina haye mini, ka runtumi ɗaya daga cikin samarin, ka kama shi, ka karɓe masa makaminsa.” Amma Asahel bai daina binsa ba.

22 Abner kuma ya sāke ce masa, “Ka daina bina, kada ka sa in kashe ka fa! Idan na kashe ka kuwa, yaya zan yi ido biyu da dan’uwanka, Yowab?”

23 Amma Asahel bai daina binsa ba, Abner dai ya nashe shi da gindin māshi a ciki, sai mashin ya fita ta bayansa. Ya fāɗi ya mutu nan take. Duk wanda ya zo inda Asahel ya fāɗi ya mutu, sai ya tsaya cik.

24 Amma Yowab da Abishai suka bi Abner, har faɗuwar rana, suka isa tudun Amma, wanda yake gaban Gaiya, a hanya zuwa jejin Gibeyon.

25 Mutanen Biliyaminu kuma suka haɗa kansu, suka goyi bayan Abner, suka zama ƙungiya guda, suka tsaya kan tudu.

26 Abner kuwa ya kira Yowab, ya ce, “Har abada ne takobi zai hallakar? Ba ka sani ba ƙarshen zai yi ɗaci? Sai yaushe za ka umarci mutanenka su daina runtumar ‘yan’uwansu?”

27 Yowab ya ce, “Na rantse da Ubangiji, hakika da ba domin ka yi magana ba, da mutanena ba za su daina runtumarka ba har gobe da safe.”

28 Sa’an nan Yowab ya busa ƙaho, dukan mutanensa kuwa suka tsaya, ba su ƙara runtumar mutanen Isra’ila ba, ba wanda kuma ya yaƙi wani.

29 Abner da mutanensa suka bi dare farai, suka ratsa Araba, suka haye Urdun. Suka yi ta tafiya dukan safiyan nan, suka shige Bitron, har suka kai Mahanayim.

30 Da Yowab ya komo daga runtumar Abner, ya tattara mutanensa duka, sai ya ga an rasa mutum goma sha tara daga cikin mutanen Dawuda, banda Asahel.

31 Amma barorin Dawuda suka kashe mutanen Biliyaminu mutum ɗari uku da sittin daga cikin waɗanda suke tare da Abner.

32 Suka ɗauki Asahel, suka tafi suka binne shi a kabarin mahaifinsa a Baitalami. Yowab kuwa da mutanensa suka bi dare farai, gari ya waye musu a Hebron.

Categories
2 SAM

2 SAM 3

1 Gidan Saul da gidan Dawuda suka daɗe suna yaƙi da juna. Ƙarfin gidan Dawuda ya yi ta ƙaruwa, amma na gidan Saul ya yi ta raguwa.

‘Ya’ya Maza da aka Haifa wa Dawuda a Hebron

2 ‘Ya’ya maza da aka haifa wa Dawuda a Hebron ke nan, Ahinowam Bayezreyeliya ta haifa masa ɗan farinsa, Amnon.

3 Abigail, matar marigayi, Nabal Bakarmele, ta haifa masa ɗansa na biyu, Kileyab. Ma’aka ‘yar Talmai, Sarkin Geshur, ta haifa masa ɗansa na uku, Absalom.

4 Haggit ta haifa masa ɗansa na huɗu, Adonaija. Abital ta haifa masa ɗansa na biyar, Shefatiya.

5 Matarsa Egla ta haifa masa ɗansa na shida, Itireyam. Dukan waɗannan a Hebron ne aka haife su.

Abner ya Bi Dawuda

6 Abner ya ƙasaita sosai a gidan Saul a lokacin da ake yaƙi tsakanin jarumawan Saul da na Dawuda.

7 Saul yana da ƙwarƙwara mai suna Rizfa, ‘yar Aiya. Sai Ish-boshet ya ce wa Abner, “Me ya sa ka kwana da ƙwarƙwarar tsohona?”

8 Abner ya husata saboda wannan magana, ya ce, “Kana zato ni maci amanar ƙasa ne? Kana tsammani ina wa ƙasar Yahuza aiki ne? Tun da farko ina ta nuna alheri ga gidan Saul, tsohonka, da ‘yan’uwansa, da abokansa, ban kuwa ba da ka a hannun Dawuda ba. Amma ga shi, yau ka zarge ni da laifin kwartanci game da wannan mata.

9 Allah ya la’anta ni, idan ban yi wa Dawuda abin da Ubangiji ya rantse masa ba,

10 wato in mayar wa Dawuda da sarautar gidan Saul. In kafa kursiyin Dawuda a kan Isra’ila da kan Yahuza tun daga Dan har zuwa Biyer-sheba.”

11 Ish-boshet kuwa bai ce wa Abner uffan ba, don yana jin tsoronsa.

12 Sai Abner ya aiki manzanni zuwa wurin Dawuda a Hebron, ya ce, “Ƙasar ta wane ne? Ka yi mini alkawari, ni kuwa zan goyi bayanka, in sa dukkan Isra’ilawa su bi ka.”

13 Dawuda ya ce, “Da kyau, zan yi maka alkawari a kan wannan sharaɗi, ba za ka ga fuskata ba sai ka kawo mini matata, Mikal, ‘yar Saul, sa’ad da za ka zo wurina.”

14 Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni zuwa wurin Ish-boshet, ɗan Saul, ya ce, “Ka ba ni matata, Mikal, wadda na biya sadakinta da loɓa ɗari ta Filistiyawa.”

15 Sai Ish-boshet ya aika aka ƙwato Mikal daga wurin mijinta, Falti, ɗan Layish.

16 Mijinta ya bi ta yana ta kuka har zuwa Bahurim. Sai Abner ya ce masa ya koma, ya kuwa koma.

17 Abner ya shawarci dattawan Isra’ila, ya ce, “Dā ma can kuna so Dawuda ya sarauce ku.

18 To, yanzu sai ku yarda ya sarauce ku, gama Ubangiji ya yi wa Dawuda alkawari ya ce, ‘Ta hannun bawana, Dawuda, zan ceci jama’ar Isra’ila daga hannun Filistiyawa, da na dukan abokan gābansu.’ ”

19 Abner kuma ya yi magana da mutanen Biliyaminu, sa’an nan ya tafi ya faɗa wa Dawuda a Hebron abin da dukan Isra’ilawa da dukan kabilar Biliyaminu suka ga ya yi kyau, su yi.

20 Abner tare da mutum ashirin suka zo wurin Dawuda a Hebron, Dawuda kuwa ya yi musu liyafa.

21 Sai Abner ya ce wa Dawuda, “Zan tashi in tafi in tattara wa ubangijina sarki dukan Isra’ilawa, domin su yi alkawari da kai, kai kuma ka sarauce su yadda kake so.” Dawuda kuwa ya sallami Abner, ya tafi lafiya.

An Kashe Abner

22 Sai ga barorin Dawuda da Yowab sun komo daga hari. Sun kawo ganima mai yawa. Abner kuwa ya riga ya tafi, gama Dawuda ya riga ya sallame shi, ya tafi lafiya.

23 Da Yowab da sojojin da suke tare da shi suka iso, sai aka faɗa masa cewa, “Abner ɗan Ner ya zo wurin sarki, sarki kuwa ya bar shi ya tafi lafiya.”

24 Sai Yowab ya tafi wurin sarki ya ce, “Me ke nan ka yi? Abner ya zo wurinka, me ya sa ka bar shi ya tafi lafiya?

25 Ka sani Abner ɗan Ner ya zo ya ruɗe ka ne, ya san fitarka da shigarka, ya kuma san dukan abin da kake yi.”

26 Da Yowab ya fita daga wurin Dawuda, sai ya aiki manzanni su bi bayan Abner. Suka komo da shi a rijiyar Sira, amma Dawuda bai sani ba.

27 Sa’ad da Abner ya komo Hebron, sai Yowab ya raɓa da shi wajen ƙofar garin kamar zai gana da shi, sai ya soke shi a ruwan ciki, ya fāɗi ya mutu, saboda alhakin jinin ɗan’uwansa, Asahel.

28 Daga baya sa’ad da Dawuda ya ji, sai ya ce, “Ni da mulkina baratattu ne a gaban Ubangiji daga alhakin jinin Abner ɗan Ner har abada.

29 Allah ya sa alhakin jinin ya faɗa kan Yowab da dukan gidan ubansa. Ya sa kada a rasa mai ɗiga, ko kuturu, ko wanda yake dogara sanda, ko wanda aka kashe da takobi, ko wanda ba shi da abinci, a gidan Yowab.”

30 Ta haka Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka kashe Abner saboda ya kashe ƙanensu, Asahel, a wurin yaƙi a Gibeyon.

31 Dawuda kuwa ya ce wa Yowab da dukan mutanen da suke tare da shi, “Ku kyakketa tufafinku, ku sa tsummoki, ku yi makoki domin Abner.” Sarki Dawuda kuwa ya bi bayan makara.

32 Suka binne Abner a Hebron. Sarki ya ta da murya ya yi kuka a kabarin Abner. Dukan mutane kuma suka yi kuka.

33 Sarki ya yi wannan makoki domin Abner, ya ce,

“Don me Abner zai mutu kamar wawa?

34 Hannuwansa ba a ɗaure suke ba,

Ƙafafunsa kuma ba a dabaibaye suke ba.

Ya mutu kamar wanda mugayen mutane suka kashe.”

Dukan mutane suka yi kuka kuma saboda shi.

35 Mutane kuwa suka zo su ba Dawuda magana, ko ya ci abinci tun rana ba ta faɗi ba. Amma Dawuda ya rantse ya ce, “Allah ya buge ni in mutu nan, idan na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta faɗi.”

36 Da mutanen suka lura, sai suka yarda da abin da sarki ya yi, suka kuma ji daɗin kowane abu da sarki ya yi.

37 A wannan rana dukan mutanen Dawuda da dukan mutanen Isra’ila suka gane, ashe, ba nufin Dawuda ba ne a kashe Abner ɗan Ner.

38 Sarki ya ce wa fādawansa, “Ba ku sani ba, basarake ne, babban mutum ne kuma ya faɗi a cikin Isra’ila yau?

39 Yau na raunana, ko da yake ni sarki ne naɗaɗɗe. Waɗannan mutane, ‘ya’yan Zeruya, sun fi ƙarfina, Ubangiji ya sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata.”

Categories
2 SAM

2 SAM 4

An Kashe Ish-boshet

1 Da Ish-boshet, ɗan Saul, ya ji labari Abner ya mutu a Hebron, sai gabansa ya faɗi. Dukan mutanen Isra’ila kuma suka tsorata.

2 Shi ɗan nan na Saul yana da shugabanni biyu na ‘yan hari, su ne Ba’ana da Rekab, ‘ya’yan Rimmon na ƙasar Biliyaminu daga Biyerot, (gama an lasafta Biyerot cikin yankin ƙasar Biliyaminu.

3 Mutanen Biyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.)

4 Jonatan, ɗan Saul kuwa, yana da ɗa, sunansa Mefiboshet, amma gurgu ne. Yana da shekara biyar sa’ad da aka kawo labarin mutuwar Saul da Jonatan daga Yezreyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi, ta sheƙa a guje. A sa’ad da take gudu sai ya faɗo, sanadin gurguntakar ke nan.

5 Rekab da Ba’ana ‘ya’yan Rimmon suka tafi gidan Ish-boshet da tsakar rana, a lokacin da yake shaƙatawa.

6 Rekab da Ba’ana kuwa, suka laɓaɓa, suka shiga kamar suna neman alkama.

7 Da suka shiga gidan, sai suka iske shi yana kwance a ɗakin kwanansa. Suka buge shi, suka kashe shi, suka datse kansa. Suka ɗauki kansa suka bi ta hanyar Araba, suka yi tafiya dare farai.

8 Suka kai wa Dawuda kan Ish-boshet a Hebron. Suka ce wa sarki Dawuda, “Ga kan Ish-boshet ɗan maƙiyinka, Saul, wanda ya nemi ranka. Ubangiji ya rama wa sarki a kan Saul da zuriyarsa yau.”

9 Amma Dawuda ya ce wa Rekab da Ba’ana, ‘ya’yan Rimmon, mutumin Biyerot, “Na rantse da Ubangiji wanda ya fanshe ni daga kowace masifa,

10 sa’ad da wani ya kawo mini labari cewa, ‘Saul ya mutu,’ mutumin ya yi tsammani albishir ne ya kawo mini, sai na kama shi na kashe shi a Ziklag. Ladan da na ba shi ke nan saboda labarinsa.

11 Balle fa ku da kuke mugayen mutane, da kuka kashe adali a gadonsa, a cikin gidansa, ba sai in nemi hakkin jininsa a hannunku ba, in kawar da ku daga duniya?”

12 Sai Dawuda ya umarci samarinsa su kashe su. Suka datsa hannunsu da ƙafafunsu, suka rataye su a gefen tafkin Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-boshet suka binne a cikin kabarin Abner a Hebron.

Categories
2 SAM

2 SAM 5

Dawuda Ya Zama Sarkin Isra’ilawa da Yahudawa

1 Dukan kabilan Isra’ila kuwa suka zo wurin Dawuda a Hebron, suka ce, “Ga shi, mu ‘yan’uwanka ne.

2 A dā sa’ad da Saul yake sarautarmu, kai kake bi da Isra’ilawa zuwa yaƙi, kai kake komo da su. Ubangiji kuma ya ce maka, ‘Kai za ka lura da jama’ata Isra’ila, za ka zama sarkinsu.’ ”

3 Sai dukan dattawan Isra’ila suka tafi wurin sarki Dawuda a Hebron, shi kuwa ya yi alkawari da su a gaban Ubangiji. Su kuwa suka naɗa shi Sarkin Isra’ila duka.

4 Dawuda ya ci sarauta yana da shekara talatin. Ya yi shekara arba’in yana sarauta.

5 Ya yi sarautar jama’ar Yahuza shekara bakwai da wata shida a Hebron. Ya kuma yi sarautar jama’ar Isra’ila duk da Yahuza shekara talatin da uku a Urushalima.

Dawuda Ya Ci Sihiyona

6 Sarki Dawuda da mutanensa suka tafi Urushalima su yaƙi Yebusiyawa mazaunan ƙasar. Su kuwa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka iya zuwa nan ba, makafi kawai da guragu za su kore ka.” A zatonsu Dawuda ba zai iya zuwa can ba.

7 Duk da haka Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, wato birnin Dawuda.

8 A ran nan Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kashe Yebusiyawa, to, sai kuma ya haura zuwa wuriyar ruwa ya fāɗa wa guragu da makafi waɗanda ran Dawuda yake ƙi.” Don haka a kan ce, “Makafi da guragu ba za su shiga Haikali ba.”

9 Dawuda ya zauna a kagara. Ya ba ta suna Birnin Dawuda. Ya kuma yi gine-gine kewaye da wurin. Ya fara daga Millo zuwa ciki.

10 Dawuda kuwa ya ƙasaita, gama Ubangiji Allah Mai Runduna yana tare da shi.

Hiram Sarkin Taya Ya Yarda da Dawuda

11 Hiram Sarkin Taya ya aiki jakadu zuwa wurin Dawuda. Ya kuma aika masa da katakan itacen al’ul, da kafintoci, da masu yin gini da duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda gida.

12 Dawuda kuwa ya gane lalle Ubangiji ya tabbatar da shi sarki bisa jama’ar Isra’ila, ya kuma ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa, Isra’ila.

‘Ya’yan da aka Haifa wa Dawuda a Urushalima

13 Bayan zuwan Dawuda Urushalima daga Hebron, sai ya ɗauki waɗansu ƙwaraƙwarai, ya kuma auri waɗansu mata. Aka kuma haifa masa waɗansu ‘ya’ya mata da maza.

14 Sunayen ‘ya’yan da aka haifa masa a Urushalima ke nan, Shimeya, da Shobab, da Natan, da Sulemanu,

15 da Ibhar, da Elishuwa, da Nefeg, da Yafiya,

16 da Elishama, da Eliyada, da Elifelet.

Dawuda Ya Ci Nasara a kan Filistiyawa

17 Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra’ila, sai dukansu suka haura zuwa neman ran Dawuda. Da Dawuda ya ji Filistiyawa suna nemansa, sai ya gangara zuwa kagara.

18 Filistiyawa kuwa suka zo suka bazu a kwarin Refayawa.

19 Dawuda kuwa ya yi roƙo ga Ubangiji, ya ce, “Ko in tafi in yi yaƙi da Filistiyawa? Za ka bashe su a hannuna?”

Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka haura, gama hakika, zan ba da Filistiyawa a hannunka.”

20 Sai Dawuda ya zo Ba’al-ferazim, ya ci Filistiyawa a wurin. Sa’an nan ya ce, “Ubangiji ya huda abokan gabana a idona kamar rigyawa.” Saboda haka aka sa wa wurin suna, “Ubangiji Mai Hudawa.”

21 Filistiyawa suka gudu, suka bar gumakansu a nan, Dawuda da mutanensa suka kwashe su.

22 Filistiyawa suka sāke haurawa, suka bazu a kwarin Refayawa.

23 Dawuda ya kuma roƙi Ubangiji. Ubangiji kuwa ya ce masa, “Kada ka haura zuwa wurinsu gaba da gaba, amma ka bi ta bayansu, ka ɓullo musu daura da itatuwan doka.

24 Sa’ad da ka ji motsin rausayawar rassan itatuwan doka, sai ka yi maza, ka faɗa musu, gama Ubangiji zai wuce gaba domin ya bugi rundunar Filistiyawa.”

25 Sai Dawuda ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya yi ta bugun Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.

Categories
2 SAM

2 SAM 6

Dawuda Ya Kawo Akwatin Alkawari a Urushalima

1 Dawuda kuma ya tattara zaɓaɓɓun mutane dubu talatin (30,000) na Isra’ila.

2 Sai ya tafi tare da su duka zuwa Kiriyat-yeyarim domin ya kawo akwatin Alkawarin Allah, wanda ake kira da sunan Ubangiji Mai Runduna wanda yake zaune a tsakanin kerubobin.

3-4 Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Suka sa akwatin alkawari a sabuwar karusa. Uzza da Ahiyo, ‘ya’yan Abinadeb, maza, suka bi da karusar da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo ne yake tafiya a gaban akwatin alkawarin.

5 Sai Dawuda da Isra’ilawa duka suka yi rawa sosai don farin ciki a gaban Ubangiji. Aka yi ta raira waƙoƙi, ana kaɗa molaye, da garayu, da goge, da kacakaura, da kuge.

6 Da suka zo masussukar Kidon, sai Uzza ya miƙa hannunsa ya riƙa akwatin alkawarin Allah, gama takarkaran sun yi kwarangyasa.

7 Ubangiji ya husata da Uzza, ya buge shi, ya mutu nan take kusa da akwatin alkawarin Allah, saboda ya taɓa akwatin alkawari.

8 Sai Dawuda ya ji haushi domin Ubangiji ya fashe haushinsa a kan Uzza. Aka sa wa wurin suna Feresauzza har wa yau.

9 Dawuda kuwa ya ji tsoron Ubangiji a ran nan, ya ce, “Ƙaƙa zan ajiye akwatin alkawarin Ubangiji a wurina?”

10 Domin haka Dawuda bai yarda ya kai akwatin alkawarin Ubangiji cikin Birnin Dawuda ba, sai ya kai shi gidan Obed-edom Bagitte.

11 Akwatin alkawarin Ubangiji yana a gidan Obed-edom Bagitte har wata uku. Ubangiji kuwa ya sa wa Obed-edom da dukan iyalinsa albarka.

An Iso da Akwatin Alkawari a cikin Urushalima

12 Aka faɗa wa Dawuda sarki, cewa, Ubangiji ya sa wa gidan Obed-edom albarka, da dukan abin da yake da shi saboda akwatin alkawarin Allah. Sai Dawuda ya tafi da murna ya kawo akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-edom zuwa Birnin Dawuda.

13 Sa’ad da masu ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai Dawuda ya yi hadaya da sa, da keɓaɓɓiyar tunkiya.

14 Dawuda ya sa falmaran ta lilin. Ya kuwa yi rawa da dukan ƙarfinsa a gaban Ubangiji.

15 Shi da mutanen Isra’ila duka suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da busar ƙaho.

16 Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal, ‘yar Saul, ta leƙa ta taga, ta ga sarki Dawuda yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta raina shi a zuci.

17 Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, suka ajiye shi a wurinsa a cikin alfarwar da Dawuda ya kafa dominsa. Dawuda ya miƙa hadayun ƙonawa da na salama a gaban Ubangiji.

18 Sa’ad da ya gama miƙa hadayun ƙonawa da na salama, sai ya sa wa mutanen albarka da sunan Ubangiji Mai Runduna.

19 Ya kuma rarraba wa dukan taron jama’ar Isra’ila, mata da maza, ƙosai, da nama, da zabibi, sa’an nan dukan mutane suka watse, kowa ya tafi gidansa.

20 Da Dawuda ya komo gida domin ya sa wa iyalinsa albarka, Mikal, ‘yar Saul, ta fito domin ta tarye shi, ta ce masa, “Ƙaƙa Sarkin Isra’ila ya ɗauki kansa yau? Ya kware darajarsa a gaban barorinsa mata kamar yadda shakiyyai suke yi.”

21 Sai Dawuda ya ce wa Mikal, “Ai, na yi wannan a gaban Ubangiji wanda ya zaɓe ni a madadin mahaifinki da iyalinsa, ya naɗa ni in zama Sarkin Isra’ila, wato jama’ar Ubangiji. Lalle zan yi rawar farin ciki a gaban Ubangiji.

22 Zan mai da kaina abin raini fiye da haka, zan kuma zama abin raini gare ki, amma barori mata da kika ambata, za su girmama ni.”

23 Mikal, ‘yar Saul fa, ba ta haihu ba har ta rasu.

Categories
2 SAM

2 SAM 7

Alkawarin Allah da Dawuda

1 Sa’ad da sarki yake zaune a gidansa, Ubangiji kuma ya hutasshe shi daga fitinar abokan gābansa da suke kewaye da shi,

2 sai sarki ya ce wa annabi Natan, “Duba, ga shi, ina zaune a gidan katakon al’ul, amma akwatin alkawarin Ubangiji yana a alfarwa.”

3 Natan kuwa ya ce wa sarki, “Sai ka yi abin da yake a zuciyarka, gama Ubangiji yana tare da kai.”

4 Amma a daren nan Ubangiji ya yi magana da Natan.

5 Ya ce, “Tafi, ka faɗa wa bawana Dawuda, ka ce, in ji Ubangiji, ‘Ɗakin zama za ka gina mini?

6 Har wa yau ban taɓa zama a ɗaki ba, tun lokacin da na fito da Isra’ilawa daga Masar, amma a alfarwa nake kai da kawowa daga wannan wuri zuwa wancan.

7 A cikin kai da kawowata tare da dukan jama’ar Isra’ila ban taɓa ce wa wani daga cikin shugabannin Isra’ila waɗanda na sa su lura da jama’ata Isra’ila, ya gina mini ɗaki na katakon al’ul ba.’

8 Abin da za ka faɗa wa bawana Dawuda ke nan, in ji Ubangiji Mai Runduna, ‘Na ɗauko ka daga makiyaya inda kake kiwon tumaki domin ka zama sarkin jama’ata Isra’ila.

9 Ban kuwa rabu da kai ba duk inda ka tafi, na kuma kawar da abokan gābanka duka. Zan sa ka shahara kamar shahararrun mutane na duniya.

10-11 Zan nuna wa jama’ata Isra’ila wuri na kansu inda zan kafa su su zauna. Ba wanda zai sāke damunsu. Mugayen mutane kuma ba za su ƙara wahalshe su kamar dā ba, tun lokacin da na naɗa wa jama’ata Isra’ila mahukunta. Zan hutar da kai daga fitinar abokan gābanka duka. Banda wannan kuma ina shaida maka, cewa, zan sa gidanka ya kahu.

12 Sa’ad da kwanakinka suka ƙare, za ka rasu tare da kakanninka. A bayanka, zan ta da ɗanka, na cikinka. Zan sa mulkinsa ya kahu.

13 Shi ne zai gina mini ɗaki. Ni kuwa zan tabbatar da kursiyin sarautarsa har abada.

14 Zan zama uba gare shi, zai kuma zama ɗa a gare ni. Sa’ad da ya yi laifi zan hukunta shi da sanda kamar yadda mutane suke yi. Zan yi masa bulala kamar yadda ‘yan adam suke yi.

15 Amma ba zan daina nuna masa madawwamiyar ƙaunata ba, kamar yadda na yi wa Saul wanda na kawar daga fuskata.

16 Gidanka kuwa da mulkinka za su dawwama a gabana har abada. Gadon sarautarka kuma zai kahu har abada.’ ”

17 Haka kuwa Natan ya faɗa wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.

Addu’ar Dawuda ta Godiya

18 Sarki Dawuda ya tafi ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allah, ko ni ko iyalina ba mu cancanci dukan abin da ka yi mana ba.

19 Ga shi, ka ƙara fiye da haka, ya Ubangiji Allah, gama ka yi magana, cewa, gidan bawanka zai kai kwanaki masu tsawo. Wannan ka’ida ce ta ‘yan adam!

20 Me kuma zan ƙara ce maka, gama ka san bawanka, ya Ubangiji Allah.

21 Bisa ga alkawarinka da yardar zuciyarka ne ka aikata waɗannan manyan al’amura domin ka sa in san su.

22 Bisa ga dukan abin da muka ji, kai mai girma ne, ya Ubangiji Allah. Ba kamarka, in banda kai kuma babu wani Allah.

23 Ba wata al’umma kuma a duniya wadda take kama da jama’arka Isra’ila, wadda kai Allah ka fansa ta zama jama’arka. Ka mai da kanka sananne. Ka yi wa jama’arka manyan abubuwa masu banmamaki. Ka kori al’ummai da gumakansu a gaban jama’arka, waɗanda ka fansa daga Masar.

24 Ka zaɓar wa kanka jama’ar Isra’ila su zama mutanenka har abada. Kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.

25 “Ya Ubangiji Allah, yanzu ka tabbatar da maganar da ka yi da bawanka da gidansa har abada. Ka aikata bisa ga faɗarka.

26 Za a kuwa ɗaukaka sunanka da cewa, ‘Ubangiji Mai Runduna shi ne Allah na Isra’ila har abada.’ Gidan bawanka Dawuda kuma zai kahu a gabanka.

27 Gama kai, ya Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, kai ne ka sanar wa ni bawanka, cewa, za ka sa gidana ya kahu, saboda haka ni bawanka na sami ƙarfin halin yin wannan addu’a a gare ka.

28 “Yanzu kuwa, ya Ubangiji Allah, kai ne Allah, kana cika alkawarinka ko yaushe. Ka kuwa yi wa bawanka alkawari mai girma.

29 Ka yarda da farin ciki ka sa wa gidan bawanka albarka domin gidansa ya dawwama a gabanka har abada, gama kai ne ka faɗa, ya Ubangiji Allah. Ka sa albarkarka ta tabbata a gidan bawanka har abada.”

Categories
2 SAM

2 SAM 8

Yaƙe-Yaƙen Dawuda

1 Bayan haka kuma sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar.

2 Sa’an nan ya ci Mowabawa da yaƙi. Ya sa su su kwanta a ƙasa sa’an nan ya riƙa auna su da igiya, kowane awo biyu ya sa a kashe su, awo na uku kuwa sai ya sa a bar su da rai. Mowabawa suka zama talakawansa, suka riƙa kawo haraji.

3 Dawuda kuma ya ci Hadadezer ɗan Rehob, Sarkin Zoba, da yaƙi lokacin da shi Hadadezer yake kan tafiya zuwa Kogin Yufiretis don ya tabbatar da ikonsa a wurin.

4 Dawuda ya ƙwace masa mahayan dawakai dubu ɗaya da ɗari bakwai (1,700), da sojojin ƙafa dubu ashirin (20,000). Dawuda ya yanyanke agarar dawakan, sai dai doki ɗari ne ya bari.

5 Suriyawan Dimashƙu kuwa, suka zo don su taimaki Hadadezer, Sarkin Zoba, Dawuda kuwa ya kashe Suriyawa dubu ashirin da dubu biyu (22,000).

6 Sa’an nan ya ajiye ƙungiyoyin sojojinsa a Suriya ta Dimashƙu. Suriyawa suka zama talakawan Dawuda, suka riƙa kawo masa haraji. Duk inda Dawuda ya tafi, Ubangiji yakan taimake shi.

7 Dawuda ya kwashe garkuwoyi na zinariya waɗanda shugabannin sojojin Hadadezer suka riƙe, ya kawo su Urushalima.

8 Ya kuma kwashe tagulla da yawa daga Beta da Berotayi biranen Hadadezer.

9 Sa’ad da Toyi Sarkin Hamat ya ji labari Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer da yaƙi,

10 sai ya aiki Adoniram ɗansa wurin sarki Dawuda don ya gaishe shi, ya kuma yaba masa saboda ya ci Hadadezer da yaƙi, gama Hadadezer yakan yi yaƙi da Toyi kullum. Adoniram kuwa ya kawo wa Dawuda kyautar kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.

11 Dawuda ya keɓe wa Ubangiji kayayyakin nan tare da azurfa da zinariya da ya karɓe daga dukan al’umman da ya mallaka,

12 wato azurfa da zinariya na Edomawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, Sarkin Zoba.

13 Dawuda kuwa ya yi suna. Ya kashe Edomawa dubu goma sha takwas (18,000) a kwarin Gishiri sa’ad da yake komowa.

14 Sai ya sa ƙungiyoyin sojoji a ƙasar Edom duka. Edomawa suka zama talakawan Dawuda. Ubangiji ya ba Dawuda nasara duk inda ya tafi.

Sarakunan Yaƙi na Dawuda

15 Dawuda ya mallaki Isra’ila duka. Ya yi wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.

16 Yowab ɗan Zeruya, shi ne shugaban sojojin. Yehoshafat ɗan Ahilud, shi ne marubuci.

17 Zadok ɗan Ahitub, da Ahimelek ɗan Abiyata, su ne firistoci. Seraiya shi ne magatakarda.

18 Benaiya ɗan Yehoyada, shi ne shugaban Keretiyawa da Feletiyawa, wato matsara. ‘Yan’yan Dawuda, maza, suka zama mataimakansa.

Categories
2 SAM

2 SAM 9

Dawuda ya Nuna wa Mefiboshet Alheri

1 Dawuda ya yi tambaya, ko akwai wani da ya ragu daga gidan Saul, wanda zai nuna wa alheri saboda Jonatan.

2 Akwai wani bara na gidan Saul, sunansa Ziba. Sai aka kirawo shi wurin sarki Dawuda. Sarki ya tambaye shi, “Kai ne Ziba?”

Sai ya amsa, “Ranka ya daɗe, ni ne.”

3 Sa’an nan sarki ya tambaye shi ko akwai wani wanda ya ragu daga gidan Saul, wanda zai nuna masa alherin Allah.

Ziba ya ce wa sarki, “Akwai ɗan Jonatan, gurgu ne kuwa.”

4 Sai sarki ya tambaye shi, “Ina yake?”

Ziba ya ce, “Yana gidan Makir, ɗan Ammiyel a Lodebar.”

5 Sarki kuwa ya aika aka zo da shi daga gidan Makir, ɗan Ammiyel, daga Lodebar.

6 Da aka zo da Mefiboshet, ɗan Jonatan, wato jikan Saul, sai ya rusuna har ƙasa, ya yi gaisuwa. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!”

Ya amsa, “Ranka ya daɗe, ga baranka.”

7 Dawuda ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, gama zan yi maka alheri ne saboda mahaifinka, Jonatan. Zan mayar maka da dukan gonakin kakanka, Saul. Kullum kuma za ka riƙa cin abinci a teburina.”

8 Mefiboshet kuwa ya rusuna, ya ce, “Ni wane ne har da za ka kula da ni, ni da ban fi mataccen kare daraja ba?”

9 Sa’an nan sarki ya kira Ziba, baran Saul, ya ce masa, “Dukan abin da yake na Saul, da dukan abin da yake na iyalinsa, na ba ɗan maigidanka.

10 Kai, da ‘ya’yanka maza, da barorinka za ku riƙa yi wa iyalin Saul noma, ku kawo musu amfanin domin su sami abinci, amma Mefiboshet kansa, zai riƙa cin abinci a teburina kullum.” (Ziba kuwa yana da ‘ya’ya maza goma sha biyar, da barori ashirin.)

11 Ziba ya amsa wa sarki, ya ce, “Baranka zai yi dukan abin da sarki ya umarta.”

Mefiboshet kuwa ya riƙa cin abinci a teburin sarki kamar ɗaya daga cikin ‘ya’yan sarkin.

12 Mefiboshet yana da ɗa sunansa Mika. Dukan waɗanda suke zaune a gidan Ziba kuma suka zama barorin Mefiboshet.

13 Mefiboshet kuwa ya zauna a Urushalima ya riƙa cin abinci a teburin sarki kullum. Dukan ƙafafunsa kuwa sun naƙasa.

Categories
2 SAM

2 SAM 10

Dawuda ya ci Ammonawa da Suriyawa

1 Sa’ad da Sarkin Ammonawa, wato Nahash, ya rasu, sai Hanun ɗansa ya gāje shi.

2 Dawuda ya ce, “Zan yi wa Hanun alheri kamar yadda tsohonsa ya yi mini.” Dawuda kuwa ya aiki manzanni su yi masa ta’aziyya.

Amma da suka isa can,

3 sai hakiman Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama tsohonka ne, da ya aiko manzanninsa su yi maka ta’aziyya? Ai, manzannin nan da ya aiko ‘yan leƙen asirin ƙasa ne. Sun zo ne su bincika don su san yadda za a ci birnin.”

4 Sai Hanun ya sa aka aske wa manzannin nan na Dawuda rabin gyammansu suka kuma yanyanke rigunansu daidai ɗuwawu, sa’an nan suka sallame su.

5 Da aka faɗa wa Dawuda sai ya aika a tarye su, gama mutanen sun sha kunya ƙwarai. Sarki Dawuda ya ce musu su zauna a Yariko har gyammansu su toho, sa’an nan su komo.

6 Da Ammonawa suka ga sun sa Dawuda ya yi gāba da su, suka yi sufurin Suriyawan Bet-rehob da na Zoba, mutum dubu ashirin (20,000), suka kuma yi sufurin Sarkin Ma’aka da mutanensa dubu ɗaya, da mutanen Ish-tobi dubu goma sha biyu (12,000).

7 Da Dawuda ya ji labari, sai ya aiki Yowab da dukan rundunar jarumawan.

8 Ammonawa suka fita suka ja dāgar yaƙi a ƙofar garin, amma Suriyawan Zoba da na Rehob, da mutanen Ish-tobi da na Ma’aka suka ja tasu dāgar a karkara.

9 Da Yowab ya ga an ja masa dāgar yaƙi gaba da baya, sai ya zaɓi waɗansu Isra’ilawa, ya sa su gabza da Suriyawa.

10 Sauran mutane kuwa ya sa su a hannun Abishai, ƙanensa. Ya sa su gabza da Ammonawa.

11 Ya ce musu, “Idan Suriyawa sun fi ƙarfina, ku kawo mini gudunmawa, amma idan Ammonawa sun fi ƙarfinku, sai in kai muku gudunmawa.

12 Mu yi ƙarfin hali, mu yi jaruntaka saboda jama’armu da biranen Allahnmu. Ubangiji ya yi abin da ya gamshe shi.”

13 Sa’an nan Yowab da mutanensa suka matsa, su gabza da Suriyawa. Suriyawa kuwa suka gudu.

14 Da Ammonawa suka ga Suriyawa sun gudu, su ma suka gudu daga gaban Abishai suka shiga birnin. Sa’an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙi da Ammonawa.

15 Sa’ad da Suriyawa suka ga Isra’ilawa sun ci su, suka tattara kansu.

16 Hadadezer ya aika aka kawo Suriyawan da suke a hayin Kogin Yufiretis. Suka taru a Helam. Shobak shugaban rundunar Hadadezer shi ne ya shugabance su.

17 Sa’ad da Dawuda ya ji labari, ya tara Isra’ilawa duka, ya haye Urdun zuwa Helam. Suriyawa kuwa suka ja dāgar yaƙi, suka yi yaƙi da Dawuda.

18 Amma Suriyawa suka gudu daga gaban Isra’ilawa. Dawuda kuwa ya kashe Suriyawa, mahayan karusai ɗari bakwai, da mahayan dawakai dubu arba’in (40,000). Aka yi wa Shobak shugaban rundunarsu rauni wanda ya zama ajalinsa, a can ya rasu.

19 Sa’ad da dukan hakiman Hadadezer suka ga Isra’ilawa sun ci su, sai suka yi sulhu da Isra’ilawa. Suka zama talakawansu. Wannan ya sa Suriyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudunmawa.