Categories
2 SAR

2 SAR 1

Rasuwar Ahaziya

1 Bayan rasuwar Ahab, Sarkin Isra’ila, sai Mowabawa suka tayar wa Isra’ilawa.

2 Ahaziya ya faɗo daga tagar benensa a Samariya, ya kuwa ji ciwo ƙwarai. Sai ya aiki manzanni, ya ce musu, “Ku tafi, ku tambayi Ba’alzabul, gunkin Ekron, ko zan warke daga wannan ciwo.”

3 Sai mala’ikan Ubangiji ya yi magana da Iliya Batishbe, ya ce, “Tashi, ka tafi, ka sadu da manzannin Sarkin Samariya, ka ce musu, ‘Ba Allah a Isra’ila da za ku tafi ku tambayi Ba’alzabul, gunkin Ekron?’

4 Ku faɗa wa sarki, Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga kan gadon da kake kwance ba, amma lalle za ka mutu.’ ”

Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.

5 Manzannin kuwa suka koma wurin sarki. Sarki ya ce, “Me ya sa kuka komo?”

6 Suka ce masa, “Wani mutum ya sadu da mu, ya ce mana, mu koma wurinka mu shaida maka, ‘Ubangiji ya ce, ba Allah a Isra’ila, har aka aike ku ku tambayi Ba’alzabul, gunkin Ekron? Domin haka ba za ka tashi daga kan gadon da kake kwance ba, amma lalle za ka mutu.’ ”

7 Sarki ya tambaye su, “Yaya mutumin yake, shi wanda ya sadu da ku, ya faɗa muku irin wannan magana?”

8 Suka ce masa, “Ai, wani gargasa ne mai ɗamara ta fata.”

Sarki ya ce, “Ai, Iliya ne Batishbe.”

9 Sa’an nan sarki ya aiki shugaba tare da mutum hamsin su taho da Iliya. Mutumin kuwa ya haura wurin Iliya a kan dutse, ya ce masa, “Ya mutumin Allah, sarki ya umarta ka sauko.”

10 Iliya ya ce wa shugaban da mutum hamsin ɗin, “Idan ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da mutane naka hamsin.” Wuta kuwa ta sauko daga sama, ta cinye shugaban tare da mutanensa hamsin.

11 Sarki kuma ya sāke aiken wani shugaba tare da mutum hamsin. Suka tafi, shugaban ya ce wa Iliya, “Ya mutumin Allah, sarki ya umarta ka sauko da sauri.”

12 Iliya kuwa ya ce musu, “Idan ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da mutane naka guda hamsin.” Wuta kuwa daga wurin Allah ta sauko daga sama ta cinye shugaban da mutanensa hamsin.

13 Sarki kuma ya sāke aiken wani shugaba, na uku ke nan, tare da mutanensa hamsin. Sai shugaba na uku ya tafi ya rusuna a gaban Iliya, ya roƙe shi, ya ce, “Ya mutumin Allah, ina roƙonka ka ga darajar raina da na barorinka, su hamsin.

14 Gama wuta ta sauko daga sama ta cinye shugabanni biyu tare da mutanensu hamsin hamsin, amma ka dubi darajar raina.”

15 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Ka sauka, ka tafi tare da shi, kada ka ji tsoronsa.” Iliya kuwa ya tashi, ya tafi tare da shi har gaban sarki.

16 Ya ce wa sarki, “Ubangiji ya ce, ‘Domin ka aiki manzanni su yi tambaya wurin Ba’alzabul, gunkin Ekron, ba Allah a Isra’ila ne wanda za ka yi tambaya a wurinsa? Domin haka ba za ka sauko daga kan gadon da kake kwance ba, amma za ka mutu lalle.’ ”

17 Ahaziya kuwa ya mutu bisa ga maganar Ubangiji, daidai yadda Iliya ya faɗa. Sai ɗan’uwansa Yehoram ya gāji gadon sarautarsa a shekara ta biyu ta Yoram ɗan Yehoshafat Sarkin Yahuza, gama Ahaziya ba shi da ɗa.

18 Sauran ayyukan da Ahaziya ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra’ila.

Categories
2 SAR

2 SAR 2

An Ɗauki Iliya zuwa Sama

1 Sa’ad da Ubangiji zai ɗauki Iliya zuwa Sama cikin guguwa, Iliya da Elisha suka kama hanya daga Gilgal.

2 Sai Iliya ya ce wa Elisha, “Ina roƙonka, ka dakata a nan, gama Ubangiji ya aike ni har zuwa Betel.”

Amma Elisha ya ce, “Na rantse da Ubangiji da kuma kai kanka, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka tafi Betel.

3 Akwai wata ƙungiyar annabawa da take a Betel suka zo, suka ce wa Elisha, “Ko ka sani, yau Ubangiji zai ɗauke maigidanka?”

Elisha ya ce, “I, na sani, amma mu bar zancen tukuna.”

4 Sa’an nan Iliya ya ce masa, “Elisha, ina roƙonka ka dakata a nan gama Ubangiji ya aike ni Yariko.”

Amma Elisha ya ce, “Na rantse da Ubangiji da kuma kai kanka, ba zan rabu da kai ba.” Sai suka tafi Yariko.

5 Ƙungiyar annabawa da take Yariko suka zo wurin Elisha suka ce masa, “Ko ka sani yau Ubangiji zai ɗauke maigidanka?”

Ya ce, “Na sani, amma mu bar zancen tukuna.”

6 Sa’an nan Iliya ya ce masa, “Ina roƙonka, ka dakata a nan, gama Ubangiji ya aike ni zuwa Kogin Urdun.”

Amma Elisha ya ce, “Na rantse da Ubangiji da kuma kai kanka, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka tafi tare.

7 Waɗansu annabawa hamsin kuma suka tafi tare da su. Iliya da Elisha suka tsaya kusa da kogi, annabawa hamsin ɗin suka tsaya da ɗan nisa.

8 Sa’an nan Iliya ya tuɓe alkyabbarsa, ya naɗe ta, ya bugi ruwa da ita, sai ruwan ya dāre, ya rabu biyu, dukansu biyu fa suka taka sandararriyar ƙasa suka haye.

9 Sa’ad da suka haye, sai Iliya ya ce wa Elisha, “Ka faɗa mini abin da kake so in yi maka kafin a ɗauke ni daga wurinka.”

Elisha ya ce, “Bari in sami rabo daga cikin ikonka domin in gaje ka.”

10 Iliya kuwa ya ce, “Ka roƙi abu mai wuya, duk da haka, idan ka gan ni lokacin da za a ɗauke ni, to, abin da ka roƙa za ka samu, amma idan ba ka gan ni ba, to, ba za ka samu ba ke nan.”

11 Da suka ci gaba da tafiya suna taɗi, sai ga karusar wuta da dawakan wuta suka raba su. Aka ɗauke Iliya zuwa Sama cikin guguwa.

12 Elisha kuwa ya gani, ya yi kuka yana cewa, “Ubana, ubana! Mai ikon tsaron Isra’ila! Ka tafi ke nan!” Bai kuwa ƙara ganin Iliya ba.

Elisha Ya Gāji Iliya

Da baƙin ciki Elisha ya kama tufafinsa ya kece.

13 Sa’an nan ya ɗauki alkyabbar Iliya wadda ta faɗo daga wurinsa, ya tafi ya tsaya a gaɓar Kogin Urdun.

14 Sai ya ɗauki alkyabban nan da ta faɗo daga wurin Iliya, ya bugi ruwan, yana cewa, “Ina Ubangiji, Allah na Iliya?” Sa’ad da ya bugi ruwan, sai ruwan ya dāre, ya rabu biyu, Elisha kuwa ya haye.

15 Sa’ad da annabawa hamsin da suke Yariko suka ga ya haye ya nufo su, sai suka ce, “Ai, ruhun Iliya yana kan Elisha.” Sai suka tafi su tarye shi, suka rusuna har ƙasa a gabansa,

16 suka kuma ce masa, “Yanzu fa, ga mu mu hamsin ƙarfafa. Bari mu tafi mu nemo maigidanka, mai yiwuwa ne Ruhun Ubangiji ya ɗauke shi, ya jefa shi kan wani dutse, ko cikin wani kwari.”

Elisha ya ce, “Kada ku tafi.”

17 Amma suka matsa masa har suka i masa, sai ya yardar musu su tafi. Su kuwa suka tafi su hamsin. Suka yi ta neman Iliya, har kwana uku, amma ba su same shi ba.

18 Sa’an nan suka komo wurinsa a Yariko. Sai ya ce musu, “Ai, dā ma na ce muku kada ku tafi.”

Mu’ujizan Elisha

19 Waɗansu mutanen gari suka ce wa Elisha, “Ga shi, garin yana da kyan gani, amma ruwan ba kyau, yana sa ana yin ɓari.”

20 Elisha kuwa ya ce, “Ku kawo mini gishiri a sabuwar ƙwarya.” Su kuwa suka kawo masa,

21 sai ya tafi maɓuɓɓugar ruwa yana barbaɗa gishirin, ya ce, “Haka Ubangiji ya ce, ‘Na warkar da wannan ruwa, ba zai ƙara sa a mutu ko a yi ɓari ba.’ ”

22 Ruwan kuwa ya gyaru bisa ga maganar Elisha, har wa yau.

23 Daga nan Elisha ya haura zuwa Betel. A hanya sai ga waɗansu samari sun fito daga cikin gari, suna yi masa eho, suna cewa, “Ka bar wurin nan, kai mai saiƙo.”

24 Elisha ya waiga, ya gan su, ya la’anta su da sunan Ubangiji. Sai waɗansu namomin jeji guda biyu suka fito daga cikin kurmi suka yayyage arba’in da biyu daga cikin samarin.

25 Daga nan Elisha ya tafi har Dutsen Karmel, sa’an nan ya koma Samariya.

Categories
2 SAR

2 SAR 3

Yaƙi tsakanin Isra’ila da Mowab

1 A shekara ta goma sha takwas ta sarautar Yehoshafat Sarkin Yahuza, Yehoram ɗan Ahab ya zama Sarkin Isra’ila a Samariya. Ya yi mulki shekara goma sha biyu.

2 Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji, amma bai kai na tsohonsa da tsohuwarsa ba, gama ya kawar da ginshiƙin gunkin nan Ba’al wanda tsohonsa ya yi.

3 Duk da haka, bai rabu da zunubin Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra’ila su yi zunubi.

4 Mesha Sarkin Mowab kuwa makiyayin tumaki ni. Yakan ba Sarkin Isra’ila ‘yan tumaki dubu ɗari (100,000), da raguna dubu ɗari (100,000) duk da ulunsu, gandu a shekara.

5 Amma da Ahab ya rasu, Sarkin Mowab kuwa ya tayar wa Sarkin Isra’ila.

6 Sai sarki Yehoram ya fita daga Samariya a lokacin, ya tattara Isra’ila duka.

7 Ya kuma aika wa Yehoshafat Sarkin Yahuza, ya ce, “Sarkin Mowab ya tayar mini, ko za ka yarda ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowabawa?”

Yehoshafat ya ce, “Zan tafi, ni kamarka ne, mutanena kuma kamar mutanenka, dawakaina kuma kamar naka.

8 Wace hanya za mu bi?”

Yehoram kuwa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”

9 Yehoram Sarkin Isra’ila ya tafi tare da Sarkin Yahuza da Sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.

10 Sa’an nan Sarkin Isra’ila ya ce, “Kaito! Ubangiji ya kirawo mu sarakunan nan uku don ya bashe mu a hannun Mowabawa.”

11 Yehoshafat ya ce, “Ba wani annabin Ubangiji ne a nan, wanda zai tambayar mana Ubangiji?”

Sai ɗaya daga cikin fādawan Sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, na’ibin Iliya.”

12 Yehoshafat kuwa ya ce, “Gaskiya ne, maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sai sarakunan nan uku suka ɗunguma zuwa wurin Elisha.

13 Elisha kuwa ya ce wa Sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan tsohonka da na tsohuwarka.”

Amma Sarkin Isra’ila ya ce masa, “A’a, ai, Ubangiji ya kirawo mu, mu sarakunan nan uku, domin ya bashe mu a hannun Mowabawa.”

14 Elisha ya amsa ya ce, “Na rantse da Ubangiji Mai Runduna, wanda nake bautarsa, da ba domin ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuza ba, da ba zan kula da kai har ma in dube ka ba.

15 Amma yanzu ku kawo mini makaɗin garaya.”

Da makaɗin garaya ya kaɗa, sai ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha.

16 Sai ya ce, “Ubangiji ya ce, ‘Ku haƙa kududdufai a kwarin nan.

17 Ko da yake ba ku ga iska, ko ruwan sama ba, duk da haka kwarin zai cika da ruwa domin ku sha, ku da dabbobinku.’

18 Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji, zai kuma ba da Mowabawa a hannunku.

19 Za ku ci kowane birni mai garu da kowane birni na musamman. Za ku sassare kowane kyakkyawan itace, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku lalatar da gonaki masu kyau da duwatsu.”

20 Kashegari, da safe a lokacin miƙa hadaya, sai ga ruwa ya malalo daga wajen Edom har ƙasar ta cika da ruwa.

21 Da Mowabawa suka ji labari, sarakuna sun kawo musu yaƙi, sai dukan waɗanda suka isa ɗaukar makamai, daga ƙarami zuwa babba, aka kirawo su, suka ja dāga a kan iyaka.

22 Sa’ad da suka tashi da sassafe, rana tana haskaka ruwa, sai suka ga ruwan a gabansu ja wur kamar jini.

23 Sai suka ce, “Wannan jini ne, hakika sarakunan sun yi yaƙi da juna, sun karkashe juna. Bari mu tafi mu kwashi ganima!”

24 Da suka kai sansanin Isra’ilawa, sai Isra’ilawa suka tashi, suka fāɗa musu, har suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka bi su, suna ta karkashe su,

25 suka lalatar da biranensu, a kowace kyakkyawar gona kuma, kowannensu ya jefa dutse a cikinta, har aka cika ta da duwatsu, suka kuma tattoshe kowace maɓuɓɓugar ruwa, suka sassare kyawawan itatuwa. Babban birnin Kir-hareset kaɗai ya ragu, Isra’ilawa suka kewaye shi suka fāɗa shi da yaƙi.

26 Da Sarkin Mowab ya ga yaƙin ya juya masa baya, sai ya zaɓi masu takobi ɗari bakwai ya kutsa kai a wajen ɓayar Sarkin Edom, amma suka kāsa.

27 Sai Sarkin Mowab ya kama babban ɗansa, wanda zai gāji sarautarsa, ya miƙa shi hadayar ƙonawa a kan garu. Isra’ilawa kuwa suka tsorata ko allahn abokan gāba zai cuce su, don haka suka janye, suka koma ƙasarsu.

Categories
2 SAR

2 SAR 4

Mai na Macen da Mijinta Ya Rasu

1 Matar wani daga cikin ƙungiyar annabawa da ya rasu, ta kai kuka wurin Elisha, ta ce, “Maigidana, baranka, wato mijina, ya rasu, ka kuwa sani shi mai tsoron Ubangiji ne, amma wanda yake binsa bashi ya zo zai kwashe ‘ya’yana biyu su zama bayinsa.”

2 Sai Elisha ya ce mata, “Me zan yi miki? Ki faɗa mini abin da kike da shi a gida.”

Ta ce, “Ni dai ba ni da kome a cikin gidan, sai dai kurtun mai.”

3 Sa’an nan ya ce mata, “Ki tafi ki yi aron tandaye da yawa daga maƙwabtanki waɗanda ba kome a ciki.

4 Sa’an nan ki shiga ɗaki, ke da ‘ya’yanki, ku rufe ƙofa. Ki ɗura mai cikin tandayen nan duka, bi da bi.”

5 Sai ta tashi daga wurinsa, ta tafi ta shiga ɗaki tare da ‘ya’yanta, ta rufe ƙofar. ‘Ya’yan suna kawo tandaye tana ɗurawa.

6 Da tandayen suka cika ta ce wa ɗanta, “Kawo mini wani tandu.”

Ɗan kuwa ya ce mata, “Ai, ba saura.” Sai man ya janye.

7 Sai ta koma ta faɗa wa annabi Elisha, shi kuwa ya ce mata, “Ki je ki sayar da man, ki biya bashin, abin da ya ragu kuwa ki ci, ke da ‘ya’yanki.”

Elisha da Attajira a Shunem

8 Wata rana Elisha ya wuce zuwa Shunem inda wata mace take da zama, sai ta gayyace shi cin abinci. Don haka duk lokacin da ya bi ta wannan hanya, sai ya ratsa ta gidanta, ya ci abinci.

9 Sai ta ce wa mijinta, “Na gane wannan mutum adali ne, mutumin Allah, wanda kullum yakan wuce ta hanyan nan.

10 Bari mu gina masa ɗan ɗaki a kan bene, mu sa masa gado, da tebur, da kujera, da fitila, don duk sa’ad da ya zo ya sauka a wurin.”

11 Wata rana da Elisha ya zo, ya shiga ɗakin, ya huta.

12 Sai ya ce wa baransa, Gehazi, “Kirawo matan nan.” Da ya kirawo ta, sai ta zo ta tsaya a gabansa.

13 Ya ce wa Gehazi, “Ka tambaye ta me take so in yi mata saboda dukan wannan wahala da ta yi dominmu? Tana so in yi mata magana da sarki ko da shugaban sojoji?”

Sai ta ce, “Ai, ina da dukan abin da nake bukata a cikin jama’ata.”

14 Elisha ya ce, “To, me za a yi mata?”

Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Ai, ba ta da ɗa, mijinta kuwa tsoho ne.”

15 Sai ya ce, “Kirawo ta.” Da ya kirawo ta, sai ta zo ta tsaya a ƙofar ɗakin.

16 Elisha kuwa ya ce mata, “Baɗi war haka za ki rungumi ɗa na kanki.”

Sai ta ce, “A’a, ya shugabana, mutumin Allah, kada fa ka yi mini ƙarya.”

17 Amma macen ta sami juna biyu, ta kuwa haifi ɗa a daidai lokacin da Elisha ya faɗa mata.

18 Da yaron ya yi girma, sai wata rana ya bi mahaifinsa gona zuwa wurin masu girbi.

19 Sai ya ce wa mahaifinsa, “Wayyo, kaina, kaina.”

Uban kuwa ya ce wa baransa, “Ka ɗauke shi, ka kai shi wurin uwar.”

20 Da aka ɗauke shi, aka kai wa uwar, sai ya zauna a cinyar uwar har rana tsaka, sa’an nan ya rasu.

21 Sai ta hau, ta kwantar da shi a gadon annabi Elisha, sa’an nan ta rufe ƙofa, ta fita.

22 Sa’an nan ta aika a faɗa wa mijinta, ta ce, “Ka aiko mini ɗaya daga cikin barori da jaki domin in tafi wurin annabi Elisha, zan komo da sauri.”

23 Sai ya ce, “Me ya sa za ki tafi wurinsa yau? Ai, yau ba amaryar wata ba ce, ba kuwa ranar Asabar ba ce.”

Ita kuwa ta ce, “Ba kome, kada ka damu.”

24 Amma ta yi wa jakin shimfiɗa, ta kuma ce wa baranta, “Yi ta kora mini jakin, kada ka sassauta, sai na faɗa maka.”

25 Sai ta kama hanya, ta tafi wurin annabi Elisha a Dutsen Karmel.

Sa’ad da annabi Elisha ya gan ta zuwa, sai ya ce wa Gehazi, wato baransa, “Duba, ga Bashunemiya can.

26 Ruga ka tarye ta, ka tambayi lafiyarta, da ta mijinta, da ta ɗanta.”

Ta amsa, ta ce, “Lafiya ƙalau.”

27 Sa’ad da ta isa wurin annabi Elisha a kan dutsen, sai ta kama ƙafafunsa. Sai Gehazi ya zo zai ture ta. Amma mutumin Allah ya ce masa, “Ƙyale ta kurum, gama tana da baƙin ciki ƙwarai, Ubangiji kuwa ya ɓoye mini abin.”

28 Matar ta ce masa, “Na roƙe ka ka ba ni ɗa ne? Ashe, ban ce maka kada ka ruɗe ni ba?”

29 Elisha ya ce wa Gehazi, “Yi ɗamara, ka ɗauki sandana ka tafi. Duk wanda ka gamu da shi, kada ka gaishe shi, duk kuma wanda ya gaishe ka kada ka amsa, ka tafi ka ɗora sandana a fuskar yaron.”

30 Sai macen ta ce, “Na rantse da Ubangiji da kai kuma, ba zan bar ka ba.” Sai Elisha ya tashi, ya bi ta.

31 Gehazi kuma ya yi gaba, ya ɗora sandan a fuskar yaron, amma ba motsi ko alamar rai. Saboda haka ya koma, ya taryi Elisha, ya faɗa masa yaron bai farka ba.

32 Da Elisha ya kai ɗakin, ya ga yaron yana kwance matacce a gadonsa.

33 Sai ya shiga ya rufe ƙofa, daga shi sai yaron, ya yi addu’a ga Ubangiji.

34 Sa’an nan ya kwanta a kan yaron, ya sa bakinsa a bakin yaron, ya sa idanunsa a idanun yaron, hannuwansa kuma a kan na yaron, ya miƙe jikinsa akan yaron, sai jikin yaron ya yi ɗumi.

35 Elisha ya tashi, ya yi ta kai da komowa a cikin gidan, sa’an nan ya sāke hawan ɗakin, ya miƙe a kan yaron, sai yaron ya yi atishawa har sau bakwai, yaron kuma ya buɗe idanu.

36 Sai ya kira Gehazi ya ce, “Kirawo Bashunemiyar.” Sai ya kirawo ta. Da ta zo wurinsa, ya ce, “Ki ɗauki ɗanki.”

37 Ta kuwa zo, ta faɗi a gaban Elisha har ƙasa, sa’an nan ta ɗauki ɗanta, ta fita.

Mu’ujizai Biyu domin Annabawa

38 Elisha kuwa ya koma Gilgal sa’ad da ake fama da yunwa a ƙasar. Sa’ad da ƙungiyar annabawa suke zaune a gabansa, sai ya ce wa baransa, “Dora babbar tukunya, ka dafa wa annabawan nan fate-fate.”

39 Ɗaya daga cikinsu ya tafi saura don ya samo ganyayen ci. Sai ya ga yaɗon inabin jeji, ya ɗebo ‘ya’yan ya rungumo cike da hannu, ya zo ya yanyanka ya zuba a tukunyar abinci, ba tare da sanin ko mene ne ba.

40 Amma da suka ɗanɗana, sai suka ta da murya suka ce, “Ya mutumin Allah, akwai dafi a cikin tukunyar nan!” Ba su iya cin abincin ba.

41 Sai Elisha ya ce, “To, ku kawo gari.” Aka kawo masa, ya kuwa zuba garin a tukunyar, sa’an nan ya ce, “Ku kwaso wa mutanen. Yanzu dai kome lafiya.”

42 Wani mutum ya zo daga Ba’alshalisha ya kawo wa annabi Elisha abinci na ‘ya’yan fari, da dunƙule ashirin na sha’ir, da ɗanyun zangarkun hatsi. Sai Elisha ya ce wa baransa, ya ba ƙungiyar annabawa su ci,

43 amma baran ya ce, “Ƙaka zan raba wa mutum ɗari wannan abinci?”

Elisha ya sāke cewa, “Ka ba mutane su ci, gama Ubangiji ya ce za su ci har su bar saura.”

44 Sai ya ajiye shi a gabansu. Suka ci, suka kuwa bar saura kamar yadda Ubangiji ya faɗa.

Categories
2 SAR

2 SAR 5

Na’aman Ya Warke daga Kuturta

1 Na’aman kuwa, shugaban sojojin Sarkin Suriya, shi babba ne mai farin jini ƙwarai a wurin ubangidansa, domin ta wurinsa ne Ubangiji ya ba Suriyawa nasara. Shi mutum ne ƙaƙƙarfan jarumi, amma kuma kuturu ne.

2 Daga cikin hare-haren da Suriyawa suke kaiwa, sai suka kama wata yarinya daga ƙasar Isra’ila, aka sa ta zama mai yi wa matar Na’aman aiki.

3 Wata rana sai ta ce wa uwargijyarta, “Da a ce ubangijina yana tare da annabin nan wanda yake Samariya, da ya warkar da shi daga kuturtarsa!”

4 Na’aman kuwa ya tafi, ya faɗa wa ubangidansa, ya ce, “Ka ji abin da yarinyan nan ta ƙasar Isra’ila ta ce?”

5 Sai Sarkin Suriya ya ce, “Ka tafi yanzu, zan aika wa Sarkin Isra’ila da takarda.”

Na’aman kuwa ya ɗauki azurfa na talanti goma, zinariya kuma na shekel dubu shida (6,000), da rigunan ado guda goma, ya kama hanya.

6 Ya kai wa Sarkin Isra’ila tarkardar, wadda ta ce, “Sa’ad da wannan takarda ta sadu da kai, ka sani fa, ni ne na aiko barana, Na’aman, wurinka domin ka warkar da shi daga kuturtarsa.”

7 Da Sarkin Isra’ila ya karanta takardar, sai ya keta tufafinsa, ya ce, “Ni Allah ne, da zan kashe in rayar, har mutumin nan zai aiko mini da cewa in warkar da mutum daga kuturtarsa? Ku duba fa, ku ga yadda yake nemana da faɗa.”

8 Amma sa’ad da Elisha, annabin Allah, ya ji cewa Sarkin Isra’ila ya keta tufafinsa, sai ya aika wa sarki ya ce, “Me ya sa ka keta tufafinka? Bari ya zo wurina, zai sani akwai annabi a Isra’ila.”

9 Na’aman kuwa da dawakansa da karusansa suka tafi suka tsaya a ƙofar gidan Elisha.

10 Sai Elisha ya aiki manzo ya faɗa wa Na’aman ya tafi, ya yi wanka a Kogin Urdun har sau bakwai, naman jikinsa zai warke, zai tsarkaka.

11 Amma Na’aman ya husata, ya yi tafiyarsa, yana cewa, “Na yi tsammani zai fito ya zo wurina ne, ya tsaya, ya yi kira sunan Ubangiji Allahnsa ya kaɗa hannunsa a wurin kuturtar, ya warkar da ni.

12 Ashe, kogin Abana da na Farfar, wato kogunan Dimashƙu, ba su fi dukan ruwayen Isra’ila ba? Da ban yi wanka a cikinsu na tsarkaka ba?” Ya juya, ya yi tafiyarsa da fushi.

13 Amma barorinsa suka je wurinsa, suka ce masa, “Ranka ya daɗe, da a ce annabin ya umarce ka ka yi wani babban abu ne, ashe, da ba ka yi ba, balle wannan, da ya ce ka tafi ka yi wanka, ka tsarkaka?”

14 Sai ya tafi ya yi wanka har sau bakwai a Kogin Urdun bisa ga maganar annabin Allah, sai naman jikinsa ya warke ya zama kamar na ƙaramin yaro, ya tsarkaka.

15 Ya kuwa komo wurin annabi Elisha shi da jama’arsa duka, ya zo ya tsaya a gabansa, ya ce, “Yanzu na sani a duniya duka ba wani Allah banda na Isra’ila, saboda haka, sai ka karɓi kyauta daga wurina.”

16 Amma Elisha ya ce, “Na rantse da Ubangiji, wanda nake bauta masa, ba zan karɓi kome ba.”

Ya yi ta roƙonsa ya karɓa, amma ya ƙi.

17 Na’aman kuwa ya ce, “Da yake ka ƙi ka karɓa, ina roƙonka, ka ba baranka labtun alfadari biyu na ƙasa, gama nan gaba baranka ba zai ƙara miƙa hadaya ta ƙonawa ko baiko ga wani gunki ba, sai dai Ubangiji.

18 Sai dai Ubangiji ya gafarta mini lokacin da na bi sarki zuwa cikin haikalin Rimmon, gunkin Suriya, don ya yi sujada. Na gaskata Ubangiji zai gafarta mini.”

19 Elisha kuwa ya ce masa, “Ka sauka lafiya.” Na’aman ya tafi.

Amma tun Na’aman bai yi nisa ba,

20 sai Gehazi, baran annabi Elisha, ya ce, “Duba, maigidana ya bar Na’aman Basuriyen nan ya tafi, bai karɓi kome daga cikin abin da ya kawo masa ba. Na rantse da Ubangiji, zan sheƙa a guje, in bi shi, in karɓi wani abu daga gare shi.”

21 Gehazi kuwa ya bi bayan Na’aman.

Da Na’aman ya ga wani yana biye da shi a guje, sai ya sauka daga karusarsa, ya juya ya tarye shi, ya ce, “In ce ko lafiya?”

22 Gehazi ya ce, “Lafiya ƙalau, maigidana ne ya aiko ni in faɗa maka, yanzu yanzu waɗansu samari biyu daga ƙungiyar annabawa suka zo wurinsa daga ƙasar tudu ta Ifraimu, yana roƙonka, ka ba ni talanti ɗaya na azurfa da rigunan ado guda biyu in kai masa.”

23 Na’aman kuwa ya ce, “In ka yarda ka karɓi talanti biyu na azurfa.” Ya ƙirga su ya ɗaure kashi biyu, da kuma rigunan ado masu kyau ya ɗora wa barorinsa biyu, ya umarce su su kai wa Gehazi har gida.

24 Sa’ad da Gehazi ya kai tudu, sai ya karɓi kayan daga hannunsu, ya ajiye a gida, sa’an nan ya sallame su, suka tafi.

25 Sai ya shiga, ya tsaya a gaban Elisha, Elisha kuwa ya tambaye shi, “Ina ka tafi, Gehazi?”

Sai ya ce, “Ranka ya daɗe ban tafi ko’ina ba.”

26 Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba, sa’ad da mutumin ya juyo daga karusarsa don ya tarye ka? Wannan shi ne lokacin karɓar kuɗi, da riguna, da gonaki na zaitun, da na inabi, da tumaki, da shanu, da barori mata da maza?

27 Saboda haka kuturtar Na’aman za ta kama ka, kai da zuriyarka har abada.”

Haka kuwa ya fita a wurinsa kuturu, fari fat kamar auduga.

Categories
2 SAR

2 SAR 6

An Tsamo Ruwan Gatari

1 Ƙungiyar annabawa da suke a hannun Elisha suka kawo masa kuka, suka ce, “Ga shi, wurin da muke zaune ya yi mana kaɗan.

2 Ka ba mu izini mu tafi Kogin Urdun, domin mu saro gumagumai a can, mu ƙara wa kanmu wurin zama.”

Sai ya ce, “Ku tafi.”

3 Ɗaya daga cikinsu kuwa ya ce, “In ka yarda, ka tafi tare da mu.”

Elisha kuwa ya yarda, ya ce, “To, mu tafi.”

4 Ya kuwa tafi tare da su.

Sa’ad da suka isa Urdun, suka sassari itatuwa.

5 Amma sa’ad da ɗaya daga cikinsu yake saran wani gungume, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe ya fāɗa a ruwa. Sai ya yi ihu, ya ce, “Wayyo, maigida, me zan yi? Abin aro ne.”

6 Sa’an nan Elisha ya ce, “Daidai ina ya fāɗa?”

Da ya nuna masa wurin, sai ya karyi tsumagiya, ya jefa a wurin, ya sa ruwan gatarin ya taso bisa kan ruwan.

7 Sa’an nan ya ce, “Ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu, ya ɗauka.

Elisha da Suriyawa

8 Wata rana, sa’ad da Sarkin Suriya yake yaƙi da Isra’ila, sai ya shawarci fādawansa, suka zaɓi wurin da za su kafa sansani.

9 Amma Elisha ya aika wa Sarkin Isra’ila, ya ce, “Ka yi hankali, kada ka wuce wuri kaza, gama Suriyawa suna gangarawa zuwa can.”

10 Sarkin Isra’ila kuwa ya aika zuwa wurin da Elisha ya faɗa masa. Da haka ya riƙa faɗakar da shi, har ya ceci kansa ba sau ɗaya, ba sau biyu ba.

11 Zuciyar Sarkin Suriya kuwa ta ɓaci ƙwarai a kan wannan al’amari, don haka ya kirawo fādawansa, ya ce musu, “Wane ne wannan da yake cikinmu, yana goyon bayan Sarkin Isra’ila?”

12 Ɗaya daga cikin fādawan ya ce, “A’a, ranka ya daɗe, sarki, ai, annabi Elisha ne wanda yake cikin Isra’ila, yake faɗa wa Sarkin Isra’ila maganar da kake faɗa a ɗakin kwananka.”

13 Sai ya ce, “Ku tafi, ku ga inda yake don in aika a kamo shi.” Aka faɗa masa, cewa a Dotan yake.

14 Sai ya aika da dawakai, da karusai, da sojoji da yawa. Suka tafi da dare suka kewaye garin.

15 Da baran annabi Elisha ya tashi da sassafe, ya fita waje, sai ga sojoji, da dawakai, da karusai sun kewaye gari. Sai baran ya ce, “Wayyo, maigidana! Me za mu yi?”

16 Elisha kuwa ya ce masa, “Kada ka ji tsoro gama waɗanda suke tare da mu, sun fi waɗanda suke tare da su yawa.”

17 Sa’an nan Elisha ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa ya gani.” Ubangiji kuwa ya buɗe idanun saurayin, sai ga dutsen cike da dawakai da karusan wuta kewaye da Elisha.

18 Da Suriyawa suka gangaro wurinsa, sai Elisha ya yi addu’a ga Ubangiji, ya ce, “Ina roƙonka, ka bugi mutanen nan da makanta.” Ubangiji kuwa ya buge su da makanta bisa ga addu’ar Elisha.

19 Sa’an nan Elisha ya ce musu, “Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma gari ke nan ba, ku bi ni, ni kuwa in kai ku wurin mutumin da kuke nema.” Sai ya kai su Samariya.

20 Da shigarsu Samariya, sai Elisha, ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanun mutanen nan su gani.” Ubangiji kuwa ya buɗe idanunsu, suka gani, ashe, suna tsakiyar Samariya ne.

21 Da Sarkin Isra’ila ya gan su, sai ya ce wa Elisha, “Ya mai girma, in karkashe su? In karkashe su?”

22 Amma Elisha ya ce, “Ba za ka karkashe su ba. Ba za ka karkashe waɗanda ba kai ka kama su ta wurin takobinka ko bakanka ba. Ka ba su abinci da ruwa su ci su sha, su koma wurin shugabansu.”

23 Sai ya shirya musu babbar liyafa. Sa’ad da suka ci suka sha, sai ya sallame su, suka koma wurin shugabansu. Suriyawa kuwa ba su ƙara kai wa ƙasar Isra’ila hari ba.

Elisha da Yaƙi a Samariya

24 Bayan wannan kuwa Ben-hadad, Sarkin Suriya, ya tattara sojojinsa duka, ya haura ya kewaye Samariya da yaƙi.

25 Aka yi yunwa mai tsanani a Samariya a lokacin da aka kewaye ta da yaƙin, har aka riƙa sayar da kan jaki a bakin shekel tamanin, an kuma sayar da rubu’in mudu na kashin kurciya a bakin shekel biyar.

26 Sa’ad da Sarkin Isra’ila yake wucewa ta kan garun birni, sai wata mace ta yi masa kuka, ta ce, “Ka yi taimako, ran sarki ya daɗe.”

27 Shi kuwa ya ce, “Idan Ubangiji bai taimake ki ba, ƙaƙa zan yi, ni in taimake ki? Ina da alkama ne ko kuwa ina da ruwan inabi?

28 Me yake damunki?”

Sai ta amsa, ta ce, “Wannan mace ta ce mini, in kawo ɗana mu ci yau, gobe kuma mu ci nata.

29 Sai muka dafa ɗana muka cinye. Kashegari kuwa na ce mata ta kawo ɗanta mu ci, amma sai ta ɓoye shi.”

30 Da sarki ya ji maganar macen, sai ya keta tufafinsa, sa’ad da yake wucewa ta kan garun birni. Sai mutane suka gani, ashe, yana saye da rigar makoki a ciki.

31 Ya ce, “Allah ya yi mini hukunci mai tsanani, idan ban fille kan Elisha ɗan Shafat yau ba.”

32 Elisha kuwa yana zaune a gidansa, dattawa kuma suna zaune tare da shi. Sai sarki ya aiki mutum, amma kafin mutumin ya isa, sai Elisha ya ce wa dattawan, “Kun ga yadda mai kisankan nan ya aiko don a fille mini kai? Idan mutumin ya zo, sai ku rufe ƙofar, ku riƙe ta da ƙarfi. Ba da jimawa ba sarki zai bi bayansa.”

33 Yana magana da su ke nan, sai sarki ya iso, ya ce, “Wannan masifa daga wurin Ubangiji ta fito, don me zan ƙara jiran Ubangiji kuma?”

Categories
2 SAR

2 SAR 7

1 Amma Elisha ya ce, “Kasa kunne ga abin da Ubangiji ya ce! Gobe war haka za a sayar da mudu na lallausan gari a bakin shekel guda, da mudu biyu na sha’ir a bakin shekel guda a ƙofar garin Samariya.”

2 Amma dogarin da yake tare da sarki ya ce wa Elisha, “Ko da Ubangiji kansa zai buɗe tagogin sama, wannan abu ba zai yiwu ba.”

Elisha kuwa ya ce, “Za ka gani da idanunka, zai faru, amma ba za ka ci ba.”

Sojan Suriyawa sun Tafi

3 Akwai mutum huɗu, kutare, waɗanda suke zaune a bakin ƙofar gari, sai suka ce wa junansu, “Me ya sa muke zaune nan har mu mutu?

4 Idan mun ce, ‘Bari mu shiga birni,’ yunwa tana birnin, za mu mutu a wurin. Idan kuma mun zauna a nan za mu mutu. Saboda haka bari mu tafi sansanin Suriyawa, idan sun bar mu da rai, za mu rayu, idan kuwa sun kashe mu, za mu mutu.”

5 Sai suka tashi da magariba, suka tafi sansanin Suriyawa. Da suka isa gefen sansanin Suriyawa, sai suka tarar ba kowa a wurin,

6 gama Ubangiji ya sa sojojin Suriyawa suka ji amon karusai, da na dawakai, da na babbar rundunar soja. Sai suka ce wa junansu, “Ai, Sarkin Isra’ila, ya yi ijara da sarakunan Hittiyawa, da na Masarawa, su zo su fāɗa mana.”

7 Saboda haka suka gudu da almuru, suka bar alfarwansu, da dawakansu, da jakunansu, suka bar sansanin yadda yake, suka tsira da rayukansu.

8 Sa’ad da kutaren nan suka zo sansanin, sai suka shiga wata alfarwa, suka ci suka sha. Suka kwashe azurfa, da zinariya, da tufafi, suka tafi suka ɓoye. Suka koma suka shiga wata alfarwa kuma, suka kwashe abubuwan da suke cikinta. Suka tafi suka ɓoye su.

9 Sa’an nan suka ce wa junansu, “Ba mu kyauta ba. Yau ranar albishir ce, idan mun yi shiru, mun jira har safe, wani mugun abu zai same mu. Domin haka bari mu tafi mu faɗa a gidan sarki.”

10 Sai suka tafi wurin masu gadin ƙofar birnin, suka ce musu, “Mun tafi sansanin Suriyawa ba mu ga kowa ba, ba mu kuma ji motsin kowa a wurin ba, ba kowa a wurin sai dawakai da jakai, a ɗaure, alfarwai kuma suna nan yadda suke.”

11 Sa’an nan masu tsaron ƙofar birnin suka aika a faɗa a gidan sarki.

12 Sai sarki ya tashi da dare ya ce wa fādawansa, “Bari in faɗa muku irin shirin da Suriyawa suka yi a kanmu. Sun sani muna fama da yunwa, domin haka suka fita daga sansanin suka ɓuya a karkara, suna nufin sa’ad da muka fita daga birnin, sai su kama mu da rai, sa’an nan su shiga birnin.”

13 Ɗaya daga cikin fādawan sarki ya ce, “A sa waɗansu mutane su ɗauki dawakai biyar da suka ragu cikin birnin, idan ba su tsira ba, za su zama kamar sauran Isra’ilawan da suka riga suka mutu. Bari mu aika, mu gani.”

14 Aka ɗibi mahayan dawakai biyu, sarki kuwa ya aike su, su bi bayan sojojin Suriyawa, ya ce musu, “Ku tafi, ku gani.”

15 Sai suka bi bayansu har zuwa Kogin Urdun, suka ga tufafi da makamai barjat ko’ina a hanya, waɗanda Suriyawa suka zubar lokacin da suke gudu. Sai manzannin suka komo suka faɗa wa sarki.

16 Sa’an nan mutane suka fita, suka washe sansanin Suriyawa. Aka kuwa sayar da mudu na lallausan gari da mudu biyu na sha’ir a bakin shekel ɗaya ɗaya kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa.

17 Sarki kuwa ya sa dogari wanda ya raka shi wajen Elisha ya tsare ƙofar birnin. Sai mutane suka tattake shi a ƙofar har ya mutu, kamar yadda annabi Elisha ya faɗa sa’ad da sarki ya tafi wurinsa.

18 Ya faru daidai yadda annabi Elisha ya ce wa sarki, “Za a sayar da mudu biyu na sha’ir, da mudu na lallausan gari a bakin shekel ɗaya ɗaya gobe war haka a ƙofar birnin Samariya.”

19 Dogarin ya ce wa Elisha, “Ko da Ubangiji da kansa zai buɗe tagogin sama, wannan abu zai yiwu ke nan?”

Elisha kuwa ya ce, “Za ka gani da idanunka amma ba za ka ci ba.”

20 Haka kuwa ya zama gama mutane suka tattake shi a ƙofar har ya mutu.

Categories
2 SAR

2 SAR 8

An Mayar da Gonakin Mata daga Shunem

1 Elisha kuwa ya ce wa matar da ya ta da ɗanta daga matattu, “Ki tashi, ke da gidanki, ki zauna duk inda kika samu, gama Ubangiji ya sa a yi yunwa a ƙasar har shekara bakwai.”

2 Sai matar ta tashi, ta yi kamar yadda annabi Elisha ya faɗa mata. Ta tafi, ita da iyalinta suka zauna a ƙasar Filistiyawa har shekara bakwai.

3 A ƙarshen shekara bakwai ɗin, matar ta komo daga ƙasar Filistiyawa, ta tafi wurin sarki, ta roƙe shi a mayar mata da gidanta da gonarta.

4 A lokacin kuwa sarki yana tare da Gehazi, wato baran annabi Elisha, ya ce, “Ka faɗa mini dukan mu’ujizan da Elisha ya yi.”

5 A sa’ad da yake faɗa wa sarki yadda Elisha ya ta da matacce, sai ga matar da ya ta da ɗanta daga matattu, ta zo ta roƙi sarki ya mayar mata da gidanta da gonarta. Sai Gehazi ya ce, “Ran sarki ya daɗe, ai, ga matar, ga kuma yaronta wanda Elisha ya tashe shi daga matattu.”

6 Da sarki ya tambayi matar sai ta faɗa masa dukan labarin. Sarki kuwa ya sa wani bafade ya mayar mata da dukan abin da yake nata da dukan amfanin gonakin, tun daga ran da ta bar ƙasar har ranar da ta komo.

Hazayel Ya Ci Sarautar Suriya

7 Elisha kuwa ya tafi Dimashƙu. A lokacin kuwa Ben-hadad, Sarkin Suriya, yana ciwo. Aka faɗa masa cewa, annabi Elisha ya zo, yana nan,

8 sai sarki ya ce wa Hazayel, ɗaya daga cikin fādawansa, “Ka ɗauki kyauta, ka tafi wurin annabin Allah ka sa ya roƙar mini Ubangiji ko zan warke daga wannan cuta.”

9 Hazayel kuwa ya tafi wurin Elisha tare da kyauta iri iri na kayan Dimashƙu. Raƙuma arba’in ne suka ɗauko kayan. Da ya tafi ya tsaya a gabansa, ya ce, “Danka, Ben-hadad Sarkin Suriyawa, ya aiko ni wurinka don yana so ya ji ko zai warke daga wannan cuta.”

10 Elisha kuwa ya ce masa, “Tafi ka faɗa masa zai warke, amma Ubangiji ya nuna mini lalle zai mutu.”

11 Sai Elisha ya kafa wa Hazayel ido, yana kallonsa, har Hazayel ya ji kunya. Elisha kuwa ya fashe da kuka.

12 Hazayel ya ce, “Me ya sa shugabana yake kuka?”

Elisha ya amsa ya ce, “Domin na san irin muguntar da za ka yi wa jama’ar Isra’ila. Za ka ƙone kagaransu da wuta, ka karkashe samarinsu da takobi, za ka kuma fyaffyaɗe ƙananansu a ƙasa, ka tsattsage matansu masu ciki.”

13 Hazayel kuwa ya ce, “Ni wane ne? Ina na sami wannan iko? Ni ba kome ba ne.”

Elisha ya amsa ya ce, “Ubangiji ya nuna mini za ka zama Sarkin Suriya.”

14 Sa’an nan Hazayel ya tashi daga wurin Elisha ya koma wurin Ben-hadad. Ben-hadad ya tambaye shi, “Me Elisha ya faɗa maka?”

Sai ya ce, “Ya faɗa mini, cewa lalle za ka warke.”

15 Amma kashegari sai Hazayel ya ɗauki bargo, ya tsoma a ruwa, sa’an nan ya rufe fuskar sarki da shi har ya mutu.

Sai ya hau gadon sarautarsa.

Sarki Yehoram na Yahuza

16 A shekara ta biyar ta sarautar Yehoram ɗan Ahab Sarkin Isra’ila, Yoram ɗan Yehoshafat Sarkin Yahuza, ya ci sarauta.

17 Yana da shekara talatin da biyu da haihuwa sa’ad da ya ci sarautar. Ya yi shekara takwas yana sarauta a Urushalima.

18 Ya bi halin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ya yi, gama ya auri ‘yar Ahab. Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji.

19 Duk da haka Ubangiji bai hallaka Yahuza ba, saboda bawansa Dawuda, tun da yake ya alkawarta zai ba shi haske, shi da ‘ya’yansa har abada.

20 A zamanin Yoram, Edomawa suka tayar wa Yahuza, suka naɗa wa kansu sarki.

21 Sa’an nan Yoram ya haye zuwa Zayar tare da dukan karusansa. Sai ya tashi da dare da shugabannin karusansa, ya bugi Edomawan da suka kewaye shi, amma sojojinsa suka gudu zuwa alfarwansu.

22 Haka kuwa Edom ta tayar wa Yahuza har wa yau. A lokacin kuma Libna ta tayar wa Yahuza.

23 Sauran ayyukan Yoram da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

24 Yoram kuwa ya mutu, aka binne shi a makabartar kakanninsa a birnin Dawuda. Ahaziya ɗansa ya gāji sarautarsa.

Sarki Ahaziya na Yahuza

25 A shekara ta goma sha biyu ta sarautar Yehoram ɗan Ahab Sarkin Isra’ila, Ahaziya ɗan Yoram Sarkin Yahuza, ya ci sarauta.

26 Ya ci sarauta yana da shekara ashirin da biyu da haihuwa, ya kuwa yi mulki shekara guda a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Ataliya jikanyar Omri, Sarkin Isra’ila.

27 Ya ɗauki halin gidan Ahab. Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji kamar yadda gidan Ahab ya yi, gama shi surukin gidan Ahab ne.

28 Sarki Ahaziya kuwa ya tafi tare da Yehoram ɗan Ahab don su yi yaƙi da Hazayel, Sarkin Suriya, a Ramot cikin Gileyad. Suriyawa suka yi wa Yehoram rauni.

29 Sai sarki Yehoram ya koma zuwa Yezreyel don ya yi jiyyar raunukan da Suriyawa suka yi masa sa’ad da yake yaƙi da Hazayel Sarkin Suriya. Sai Ahaziya, ɗan Yoram, Sarkin Yahuza ya tafi ya ziyarci Yehoram ɗan Ahab cikin Yezreyel saboda yana ciwo.

Categories
2 SAR

2 SAR 9

An Naɗa Yehu Sarkin Isra’ila

1 Elisha kuwa ya kirawo ɗaya daga cikin annabawa matasa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kurtun mai, ka tafi Ramot-gileyad.

2 Sa’ad da ka isa can, sai ka nemi Yehu, ɗan Yehoshafat, wato jikan Nimshi, ka shiga, ka sa ya tashi daga wurin abokansa, ka kai shi cikin ɗaki.

3 Sa’an nan ka ɗauki kurtun man, ka zuba masa a ka, ka ce, ‘Ubangiji ya ce ya keɓe ka Sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa, ka gudu, kada ka tsaya.”

4 Sai saurayin nan, annabin, ya tafi Ramot-gileyad.

5 Sa’ad da ya isa, sai ga shugabannin sojoji suna taro. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka, ya shugaba.”

Yehu kuwa ya ce, “Wane ne a cikinmu?”

Sai ya ce, “Kai ne, ya shugaba.”

6 Sai Yehu ya tashi ya shiga ɗaki, saurayin kuwa ya zuba masa mai a ka, ya ce, “Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya keɓe ka sarkin jama’arsa, wato Isra’ila.

7 Za ka hallaka gidan Ahab, maigidanka, domin in ɗau fansar jinin annabawa bayinsa, da fansar jinin sauran bayin Ubangiji a kan Yezebel.

8 Gama dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan datse wa Ahab kowane ɗa namiji, bawa ko ‘yantacce, cikin Isra’ila.

9 Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yeroboam ɗan Nebat, da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahija.

10 Karnuka za su cinye Yezebel a cikin Yezreyel, ba wanda zai binne ta.” Sa’an nan ya buɗe ƙofar, ya gudu.

11 Da Yehu ya fita zuwa wurin sauran shugabannin, sai suka tambaye shi, “Lafiya kuwa, me ya sa mahaukacin nan ya zo wurinka?”

Sai ya ce musu, “Ai, kun san mutumin da irin maganarsa.”

12 Suka ce, “Ba mu sani ba, sai ka faɗa mana.”

Shi kuwa ya ce, “Ya faɗa mini, wai Ubangiji ya ce ya keɓe ni Sarkin Isra’ila.”

13 Sai kowane mutum a cikinsu ya yi maza ya tuɓe rigarsa, ya shimfiɗa a kan matakan, sa’an nan suka busa ƙaho, suna cewa, “Yehu ne sarki.”

Yehu Ya Kashe Yehoram Sarkin Isra’ila

14 Ta haka Yehu, ɗan Yehoshafat, wato jikan Nimshi, ya tayar wa Yehoram. A lokacin, Yehoram tare da dukan Isra’ila suna tsaron Ramot-gileyad, don kada Hazayel, Sarkin Suriya, ya fāɗa mata.

15 Amma sarki Yehoram ya komo Yezreyel, don ya yi jiyyar raunukan da Suriyawa suka yi masa sa’ad da ya yi yaƙi da Hazayel Sarkin Suriya. Sai Yehu ya ce, “Idan wannan shi ne nufinku, to, kada kowa ya zurare, ya tafi, ya ba da labari a Yezreyel.”

16 Sa’an nan Yehu ya hau karusarsa ya tafi Yezreyel, gama a can ne Yehoram yake kwance. Ahaziya Sarkin Yahuza ya gangara don ya gai da Yehoram.

17 Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezreyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.”

Sai Yehoram ya ce, “Ka aiki wani, ya hau doki, ya tafi ya tarye su, ya tambaye su, ko lafiya.”

18 Sai wani mutum ya hau doki ya tafi ya tarye su, ya ce, “Sarki ya ce, lafiya kuwa?”

Sai Yehu ya ce, “Ina ruwanka da lafiya? Kewaya ka bi bayana.”

Mai tsaro kuma ya ce, “Manzo ya kai wurinsu, amma bai komo ba.”

19 Ya kuma aiki wani, na biyu, a kan doki, ya je wurinsu ya ce musu, “Sarki ya ce, lafiya kuwa?”

Yehu ya amsa, ya ce, “Ina ruwanka da lafiya? Kewaya ka bi bayana.”

20 Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma bai komo ba. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa da hauka.”

21 Yehoram kuwa ya ce, “Ku shirya karusa.” Suka shirya masa karusa. Sa’an nan Yehoram Sarkin Isra’ila, da Ahaziya Sarkin Yahuza suka fita, kowa a cikin karusarsa, suka tafi su taryi Yehu. Suka sadu da shi a daidai gonar Nabot mutumin Yezreyel.”

22 Da Yehoram ya ga Yehu, sai ya ce, “Lafiya dai?”

Yehu ya ce, “Ina fa lafiya, tun da karuwanci da sihirin uwarka, Yezebel, sun yi yawa haka?

23 Yehoram kuwa ya juyar da karusarsa baya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Maƙarƙashiya ce, ya Ahaziya!”

24 Sai Yehu ya ja bakansa da iyakar ƙarfinsa ya ɗirka wa Yehoram kibiya, ta sha zarar zuciyarsa, sai ya ɓingire cikin karusarsa.

25 Yehu ya ce wa Bidkar, “Ka ɗauke shi ka jefar a gonar Nabot mutumin Yezreyel, gama ka tuna sa’ad da ni da kai muke kan dawakai muna biye da Ahab, tsohonsa, yadda Ubangiji ya faɗi wannan magana a kansa cewa,

26 ‘Hakika, kamar yadda jiya na ga jinin Nabot da na ‘ya’yansa, ni Ubangiji, zan sāka maka saboda wannan gona.’ Yanzu sai ka ɗauke shi, ka jefar da shi a wannan gona kamar yadda Ubangiji ya faɗa.”

Yehu Ya Kashe Ahaziya

27 Da Ahaziya Sarkin Yahuza, ya ga haka, sai ya gudu ta hanyar Bet-haggan.Yehu kuwa ya bi shi, ya ce, “Shi ma a harbe shi.” Sai suka harbe shi a cikin karusarsa a hawan Gur, wanda yake kusa da Ibleyam. Sai ya gudu zuwa Magiddo, ya mutu a can.

28 Fādawansa suka ɗauke shi a cikin karusar zuwa Urushalima, suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.

29 Ahaziya ya ci sarautar Yahuza a shekara ta goma sha ɗaya ta sarautar Yehoram ɗan Ahab.

Mutuwar Yezebel

30 Da Yezebel ta ji Yehu ya zo Yezreyel, sai ta shafa wa idanunta launi, ta gyara gashin kanta, sa’an nan ta leƙa ta taga.

31 Da Yehu ya shiga ƙofar garin, sai ta ce, “Kai Zimri, mai kashe maigidansa, me kake yi a nan?”

32 Sai ya ɗaga idanunsa wajen tagar, ya ce, “Wa yake wajena?” Sai babani biyu ko uku suka dube shi,

33 shi kuwa ya ce, “Ku wurgo ta ƙasa.” Sai suka wurgo ta ƙasa. Jininta ya fantsama a jikin bangon da jikin dawakan da suka tattake ta.

34 Sa’an nan Yehu ya shiga gida, ya ci ya sha, ya ce, “Ku san yadda za ku yi da wannan la’ananniyar mace, ku binne ta, gama ita ‘yar sarki ce.”

35 Amma da suka tafi don su binne ta, ba su tarar da kome ba sai ƙwaƙwalwa, da ƙafafu, da tafin hannuwanta.

36 Sai suka komo, suka faɗa masa. Sai ya ce musu, “Wannan, ai, faɗar Ubangiji, wadda ya faɗa ta bakin bawansa Iliya Batishbe, ya ce, ‘Karnuka za su cinye naman Yezebel a cikin Yezreyel.

37 Gawar Yezebel za ta zama wa ƙasa taki a Yezreyel don kada wani ya iya cewa wannan ita ce Yezebel.’ ”

Categories
2 SAR

2 SAR 10

An Kashe Zuriyar Ahab

1 Ahab yana da ‘ya’ya maza saba’in a Samariya, sai Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika zuwa Samariya wurin shugabanni da dattawan birni, da masu lura da ‘ya’yan Ahab.

2 Ya ce, “Yanzu dai, da zarar wasiƙun nan sun iso wurinku, da yake kuke lura da ‘ya’yan Ahab, kuna kuma da karusai, da dawakai, da kagara, da makamai,

3 sai ku zaɓi wanda ya fi dacewa duka daga cikin ‘ya’yan Ahab, ku naɗa shi sarki, ku yi yaƙi, domin ku tsare gidan Ahab.”

4 Amma suka ji tsoro ƙwarai, suka ce, “Ga shi, sarakuna biyu ba su iya karawa da shi ba, balle mu.”

5 Sai wakilin gidan, da wakilin birnin, da dattawa, da masu lura da ‘ya’yan sarki, suka aika wurin Yehu suka ce, “Mu barorinka ne, duk abin da ka umarce mu, za mu yi. Ba za mu naɗa wani sarki ba, sai ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”

6 Sa’an nan Yehu ya rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “Idan kuna goyon bayana, idan kuma kun shirya za ku yi mini biyayya, to, sai ku fille kawunan ‘ya’yan Ahab, sa’an nan ku zo wurina a Yezreyel gobe war haka.”

‘Ya’yan sarki, maza, su saba’in ne, suna a hannun manyan mutanen birni ne waɗanda suke lura da su.

7 Da wasiƙar ta iso wurinsu, sai suka kwashi ‘ya’yan sarki guda saba’in, suka karkashe su. Suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezreyel.

8 Da aka faɗa masa cewa an kawo kawunan ‘ya’yan sarki, sai ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar garin har safiya.”

9 Da safe, sa’ad da ya fita, ya tsaya, sai ya ce wa mutane duka, “Ba ku da laifi, ni ne na tayar wa maigidana har na kashe shi, amma wane ne ya kashe dukan waɗannan?

10 Ku sani fa ba maganar da Ubangiji ya faɗa a kan gidan Ahab da ba za ta cika ba, gama Ubangiji ya aikata abin da ya faɗa ta bakin bawansa Iliya.”

11 Haka kuwa Yehu ya karkashe waɗanda suka ragu na gidan Ahab a Yezreyel, wato dukan manyan mutanensa, da abokansa, da firistocinsa. Bai rage masa ko guda ba.

An Kashe Dangin Ahaziya

12 Yehu kuma ya fita zai tafi Samariya. A hanya, sa’ad da yake a Bet-eked ta makiyaya,

13 sai ya sadu da ‘yan’uwan Ahaziya Sarkin Yahuza, sai ya ce, “Ku su wane ne?”

Sai suka amsa, “Mu ‘yan’uwan Ahaziya ne, mun zo mu gai da ‘ya’yan sarki ne da ‘ya’yan sarauniya.”

14 Yehu kuwa ya ce, “Ku kama su da rai.” Sai suka kama su da rai, suka karkashe su a ramin Bet-eked, su arba’in da biyu ne, ba a rage ko ɗaya a cikinsu ba.

An Kashe Dukan Sauran Dangin Ahab

15 Da ya tashi daga can, sai ya sadu da Yehonadab ɗan Rekab yana zuwa ya tarye shi. Yehu ya gaishe shi, ya tambaye shi, “Zuciyarka ta amince da ni kamar yadda tawa ta amince da kai?”

Yehonadab ya amsa, “I.”

Sai Yehu ya ce, “Idan haka ne, to, miƙo mini hannunka.” Sai ya miƙa masa hannunsa. Yehu kuwa ya ɗauke shi zuwa cikin karusa.

16 Ya ce, “Ka zo tare da ni, ka ga kishin da nake da shi domin Ubangiji.” Sai suka tafi cikin karusarsa.

17 Da suka isa Samariya, sai ya kashe duk wanda ya ragu na gidan Ahab a Samariya. Ya share mutanen gidan Ahab kaf kamar yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin annabi Iliya.

An Kashe Masu Sujada ga Ba’al

18 Yehu kuwa ya tara mutane duka, ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan, amma Yehu zai bauta masa da yawa.

19 Saboda haka, yanzu sai ku kirawo mini dukan annabawan Ba’al, da dukan masu yi masa sujada, da dukan firistocinsa. Kada a manta da wani, gama ina da babbar hadayar da zan miƙa wa Ba’al. Duk wanda bai zo ba, za a kashe shi.” Amma dabara ce Yehu yake yi don ya hallaka waɗanda suke yi wa Ba’al sujada.

20 Yehu kuma ya sa a yi muhimmin taro saboda Ba’al. Aka kuwa kira taron,

21 sai ya aika cikin Isra’ila duka, dukan masu yi wa Ba’al sujada kuwa suka zo, ba wanda bai zo ba. Suka shiga, suka cika haikalin Ba’al makil daga wannan gefe zuwa wancan.

22 Sa’an nan Yehu ya ce wa wanda yake lura da ɗakin tufafi, “Ku fito da tufafi na dukan waɗanda suke yi wa Ba’al sujada.” Shi kuwa ya fito musu da tufafin.

23 Bayan wannan Yehu ya shiga haikalin Ba’al tare da Yehonadab ɗan Rekab, ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku bincike, ku tabbata, ba wani bawan Ubangiji tare da ku, sai dai masu yi wa Ba’al sujada kaɗai.”

24 Sa’an nan Yehu da Yehonadab suka shiga don su miƙa sadaka da hadayu na ƙonawa. Yehu ya riga ya sa mutum tamanin a waje, ya ce musu, “Mutumin da ya bar wani daga cikin waɗanda na bashe su a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”

25 Nan da nan da Yehu ya gama miƙa hadaya ta ƙonawa, sai ya ce wa mai tsaro da shugabannin, “Ku shiga, ku karkashe su, kada ku bar wani ya tsere.” Da suka karkashe su, sai suka fitar da su waje, sa’an nan suka shiga can cikin haikalin Ba’al.

26 Suka fitar da gumakan da suke cikin haikalin Ba’al, suka ƙone su.

27 Suka yi kaca kaca da gunkin Ba’al da haikalinsa, suka mai da haikalin ya zama salga har wa yau.

28 Yehu ya kawar da Ba’al daga cikin Isra’ila.

29 Amma bai rabu da zunubin Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila su yi zunubi. Siffofin maruƙa biyu suna nan a Betel da Dan.

30 Ubangiji kuwa ya ce wa Yehu, “Da yake ka yi abin da yake daidai a gare ni, ka yi wa gidan ahab bisa ga dukan abin da yake a zuciyata, ‘ya’yanka, har tsara ta huɗu, za su ci sarautar Isra’ila.”

31 Amma Yehu bai mai da hankali ya yi tafiya a tafarkin Ubangiji Allah na Isra’ila da zuciya ɗaya ba. Bai rabu da zunuban Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila su yi zunubi.

Mutuwar Yehu

32 A kwanakin an Ubangiji ya soma rage ƙasar Isra’ila. Hazayel kuwa ya yaƙe su a karkarar Isra’ila,

33 tun daga Urdun har zuwa wajen gabas, da dukan ƙasar Gileyad, da ta Gad, da ta Ra’ubainu, da ta Manassa, tun daga Arower wadda dake kusa da kwarin Arnon haɗe da Gileyad da Bashan.

34 Sauran ayyukan Yehu da dukan abin da ya yi, da dukan ƙarfinsa an rubuta su a littafin tarihin sarakuna Isra’ila.

35 Yehu kuwa ya rasu, aka binne shi a Samariya. Yehowahaz ɗansa ya gaji sarautarsa.

36 Yehu ya yi mulkin Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.