Categories
AMOS

AMOS 1

Horon Allah a kan Maƙwabtan Isra’ila

1 Ga zantuttukan Amos, ɗaya daga cikin makiyayan ƙauyen Tekowa. Allah ya bayyana wa Amos wannan saƙo, tun shekara biyu kafin girgizar duniya, a lokacin da Azariya yake sarautar Yahuza, Yerobowam ɗan Yehowash kuwa yake sarautar Isra’ila.

2 Amos ya ce,

“Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona,

Muryarsa za ta yi tsawa daga

Urushalima.

Da jin wannan, sai wuraren kiwo za

su bushe,

Ƙwanƙolin Dutsen Karmel, da yake

kore zai yi yaushi.”

Suriya

3 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Dimashƙu sun ci gaba da

yin zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun zalunci mutanen Gileyad da

zalunci mai tsanani.

4 Don haka zan aukar da wuta a kan

fādar Sarkin Suriya.

Za ta ƙone kagarar Ben-hadad,

sarki.

5 Zan ragargaje ƙyamaren ƙofofin

birnin Dimashƙu,

In kawar da masu sarautar Bet-eden

da na kwarin Awen.

Za a kwashe mutanen Suriya ganima

zuwa ƙasar Kir.”

Filistiya

6 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Gaza sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun kwashe al’umma duka, sun

sayar wa mutanen Edom.

7 Saboda haka zan aukar da wuta a

kan garun Gaza ta ƙone kagarar

birnin.

8 Zan kawar da masu sarautar biranen

Ashdod da Ashkelon,

Zan karɓe sandan mulkin Ekron.

Sauran Filistiyawa da suka ragu

kuma,

Za su mutu duka.”

Taya

9 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Taya sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun kwashe mutanen sun kai

ƙasar Edom.

Suka karya yarjejeniyar abuta wadda

suka yi.

10 Saboda haka zan aukar da wuta a

kan garun Taya,

Ta ƙone kagarar birnin.”

Edom

11 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Edom sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun farauci ‘yan’uwansu,

Isra’ilawa,

Suka ƙi su nuna musu jinƙai.

Ba su yarda su huce daga fushinsu

ba.

12 Saboda haka zan aukar da wuta a

kan Teman,

Ta ƙone kagarar Bozara.”

Ammon

13 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Ammon sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don haɗamarsu ta ƙasa,

Suka tsaga mata masu ciki a

Gileyad.

14 Saboda haka zan aukar da wuta a

kan garun Rabba,

Ta ƙone kagarar birnin.

Za a yi kururuwa a ranar yaƙi,

Faɗan kuwa zai yi rugugi kamar

hadiri.

15 Sarkinsu da manyan mutanensu za a

kai su wata ƙasa dabam.”

Categories
AMOS

AMOS 2

Mowab

1 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Mowab sun ci gaba da

yin zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun ƙone ƙasusuwan Sarkin

Edom

Don su yi toka da su.

2 Zan aukar da wuta a ƙasar

Mowab,

Ta ƙone kagarar Keriyot.

Jama’ar Mowab za su mutu a

hargitsin yaƙi,

Sa’ad da sojoji suke sowa, ana busa

ƙahoni.

3 Zan kashe Sarkin Mowab da

shugabannin ƙasar.”

Yahuza

4 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Yahuza sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun raina koyarwata sun ƙi

bin umarnaina.

Allolinsu na ƙarya waɗanda

kakanninsu suka bauta wa,

Sun sa su su ratse daga hanya.

5 Saboda haka zan aukar da wuta a

kan Yahuza

Ta ƙone kagarar Urushalima.”

Allah Ya Hukunta Isra’ila

6 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Isra’ila sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun sayar da salihai waɗanda

suka kāsa biyan bashinsu.

Sun kuma sayar da matalauta

Waɗanda bashinsu bai kai ko kuɗin

bi-shanu ba.

7 Sun tattake marasa ƙarfi da

kāsassu,

Suna tunkuɗe matalauta su wuce.

Tsofaffi da samari sukan tafi wurin

karuwan Haikali.

Ta haka suke ɓata sunana mai

tsarki.

8 A duk wuraren sujadarsu sukan

kwanta

A bisa tufafin da suka karɓe jingina.

A cikin Haikalin Allahnsu, sukan sha

ruwan inabi

Da suka karɓo daga wurin waɗanda

suke bi bashi.

9 “Amma ga shi, saboda ku na

hallakar da Amoriyawa,

Dogayen mutanen nan masu kama

da itatuwan al’ul,

Ƙarfafa kuma kamar itatuwan oak,

Na hallaka su ƙaƙaf.

10 Na fito da ku, wato jama’ata daga

Masar.

Na bi da ku cikin jeji shekara

arba’in,

Na kuwa ba ku ƙasar Amoriyawa ta

zama taku.

11 Na zaɓi waɗansu daga cikin

‘ya’yanku su zama annabawa,

Waɗansu kuma daga cikin samarinku

su zama keɓaɓɓu.

Ko ba haka ba ne, ya ku

Isra’ilawa?

Ni, Ubangiji, na yi magana.

12 Amma kun sa keɓaɓɓu shan ruwan

inabi,

Kuka kuma umarci annabawa kada

su isar da saƙona.

13 Zan danƙare ku a inda kuke

Kamar yadda ake danƙare

amalanke da kayan tsaba.

14 Ko masu saurin gudu ma ba za su

tsere ba,

Ƙarfafa za su zama kumamai,

Sojoji kuma ba za su iya ceton kansu

ba.

15 ‘Yan baka ba za su iya ɗagewa ba.

Masu saurin gudu ba za su tsira ba.

Mahayan dawakai kuma ba za su

tsere da rayukansu ba.

16 Ko sojojin da suka fi jaruntaka duka

ma,

Za su gudu tsirara a ran nan.”

Ubangiji ne ya faɗa.

Categories
AMOS

AMOS 3

Aikin Annabi

1 Jama’ar Isra’ila, ku kasa kunne ga wannan saƙo da Ubangiji ya aiko muku, ya ce, “Na fitar da iyalanku duka daga Masar.

2 Daga cikin dukan al’umman da nake

ƙauna a duniya,

Ku kaɗai ne na sani,

Nake kuma kulawa da ku,

Don haka zan hukunta ku saboda

zunubanku.”

3 Zai yiwu a ce mutum biyu za su yi

tafiya tare,

Amma su rasa shirya magana?

4 Zai yiwu zaki yă yi ruri a jeji

Ba tare da ya kama nama ba?

Zai yiwu sagarin zaki yă yi gurnani a

kogonsa

In bai kama wani abu ba?

5 Zai yiwu tsuntsu ya fāɗi ƙasa

In ba a kafa masa tarko ba?

Zai yiwu tarko ya zargu

In bai kama wani abu ne ba?

6 Zai yiwu mutane su rasa firgita,

Idan aka busa ƙahon yaƙi a

birni?

Zai yiwu wata babbar masifa ta auko

wa birni

Ba da yardar Ubangiji ba?

7 Hakika Ubangiji ba yakan aikata

kome ba,

Sai da sanin bayinsa annabawa.

8 Zaki ya yi ruri!

Wa ba zai ji tsoro ba?

Sa’ad da Ubangiji ya yi magana!

Wa zai ƙi yin shelar maganarsa?

Faɗuwar Samariya

9 Ka yi shela ga mazaunan fādar Ashdod da Masar, ka ce, “Duk ku taru a Samariya ku ga irin babban shashancin da ake yi a can, ku ga irin laifofin da ake aikatawa a birnin.”

10 Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane suka cika gidajensu masu daraja da abubuwan da suka samo ta hanyar zamba, da ta kama-karya. Ta yadda za su yi su yi aminci ma, ba su sani ba.

11 “Saboda haka abokan gaba za su

kewaye ƙasarsu,

Su hallakar da kagaransu,

Su washe gidajen nan nasu masu

daraja.”

12 Ubangiji ya ce,

“Kamar yadda makiyayi yakan ceci

ƙafafu biyu

Ko kunne ɗaya na tunkiya daga

bakin zaki,

Haka nan kuma kima daga cikin

mutanen Samariya

Waɗanda suke zaman jin daɗi za su

tsira.

13 Ku saurara yanzu,

Ku yi wa zuriyar Yakubu kashedi,”

In ji Ubangiji, Maɗaukaki.

14 “Ran da na hukunta mutanen

Isra’ila saboda zunubansu,

Zan hallakar da bagadan Betel.

Za a kakkarya zankayen bagaden,

Su fāɗi ƙasa.

15 Zan murmushe gidajensu na rani da

na damuna.

Zan hallakar da gidajen da aka

ƙawata da hauren giwa,

Kowane babban gida kuwa za a

rushe shi.”

Categories
AMOS

AMOS 4

1 Ku kasa kunne ga wannan, ya ku

matan Samariya,

Ku da kuka yi ƙiba kamar

turkakkun shanu,

Ku da kuke wulakanta kasassu,

Kuna yi wa matalauta danniya,

Kukan umarci mazajenku,

Ku ce, “Kawo mini abin sha!”

2 Da yake Ubangiji Mai Tsarki ne

Ya riga ya yi alkawari,

Ya ce, “Hakika kwanaki za su zo

Da za a jawo ku da ƙugiyoyi,

Kowannenku zai zama kamar kifi a

ƙugiya.

3 Za a kwashe ku, a fitar da ku

Ta inda garu ya tsage na mafi kusa

duka, a jefar.”

Isra’ila Sun Kāsa Koyo

4 Ubangiji ya ce,

“Jama’ar Isra’ila,

Ku tafi Betel, tsattsarkan wuri,

Ku yi ta zunubi!

Ku tafi Gilgal ku ƙara zunubi!

Ku yi ta kawo dabbobi sadaka

kowace safiya.

A kowace rana ta uku

Ku yi ta ba da zaka.

5 Ku miƙa abincinku hadaya ta

godiya.

Ku yi ta yin fariya da hadayarku ta

yardar rai!

Gama irin abin da kuke jin daɗin yi

ke nan.”

6 Ubangiji ya ce,

“Ai, ni ne, na sa a yi yunwa a

biranenku.

Shi ya sa ba ku da abinci.

Duk da haka ba ku juyo gare ni ba.

7 Na hana wa shuke-shukenku ruwa

A lokacin da suka fi bukata.

Na sa a yi ruwa a wani birni,

A wani birni kuwa na hana,

Wata gonar ta sami ruwan sama,

Amma wadda ba ta samu ba ta

bushe.

8 Ƙishirwa ta sa jama’a su tafke har

birane biyu ko uku

Suka tafi neman ruwa a birnin da

suke maƙwabtaka da shi,

A nan ma ba su sami isasshen ruwan

sha ba,

Duk da haka ba ku komo wurina

ba.

9 “Na sa darɓa, da domana

Su lalatar da amfanin gonakinku.

Fāra kuma ta cinye lambunanku

Da gonakin inabinku, da itatuwan

ɓaurenku,

Da na zaitun ɗinku.

Duk da haka ba ku komo wurina ba.

10 “Na aukar muku da annoba irin

wadda na aukar wa Masar.

Na karkashe samarinku a wurin

yaƙi,

Na kwashe dawakanku.

Na cika hancinku da ɗoyin

sansaninku.

Duk da haka ba ku komo wurina ba.

11 “Na hallakar da waɗansunku

Kamar yadda na hallakar da Saduma

da Gwamrata.

Kamar sanda kuke, wanda aka fizge

daga wuta.

Duk da haka ba ku komo wurina

ba.

12 Saboda haka, jama’ar Isra’ila,

Ga abin da zan yi muku,

Zan kuwa yi shi duk,

Sai ku yi shirin zuwa gaban

Ubangiji.”

13 Allah ne ya yi duwatsu

Ya kuma halicci iska.

Ya sanar da nufinsa ga mutum,

Ya juya rana ta zama dare.

Yana sarautar duniya duka.

Sunansa kuwa Ubangiji Maɗaukaki!

Categories
AMOS

AMOS 5

Kira Zuwa Tuba

1 Ku kasa kunne, ku jama’ar

Isra’ila, ga waƙar makoki da zan yi

a kanku.

2 Isra’ila ta fāɗi,

Ba kuwa za ta ƙara tashi ba.

Tana fa kwance a ƙasa,

Ba wanda zai tashe ta.

3 Ubangiji ya ce,

“Wani birnin Isra’ila ya aika da soja

dubu,

Ɗari ne kaɗai suka komo,

Wani birni kuma ya aika da soja ɗari

ne,

Amma goma kaɗai suka komo.”

4 Ubangiji ya ce wa jama’ar Isra’ila,

“Ku zo gare ni, za ku tsira.

5 Kada ku tafi ku yi sujada a Biyer-

sheba.

Kada ku yi ƙoƙarin nemana a

Betel,

Gama Betel lalacewa za ta yi.

Kada ku tafi Gilgal,

Gama an ƙaddara wa jama’arta su

yi ƙaura.”

6 Ku tafi wurin Ubangiji ku tsira.

Idan kuwa kun ƙi,

Shi zai babbaka jama’ar Yusufu

Kamar yadda a kan babbaka da

wuta.

Wuta za ta ƙone jama’ar Betel,

Ba kuwa mai kashe wutar.

7 Abin tausayi ne ku da kuke ɓata

shari’a,

Kuna hana wa mutane hakkinsu.

8 Ubangiji ne ya yi taurarin

Kaza da ‘ya’yanta

Da mai farauta da kare.

Ya mai da duhu haske,

Rana kuwa dare.

Shi ya kirawo ruwan teku ya

bayyana,

Ya shimfiɗa shi a bisa ƙasa.

Sunansa Ubangiji ne.

9 Ya kawo halaka a kan ƙarfafa,

Da a kan birane masu garu.

10 Kun ƙi wanda ya tsaya a kan

adalci,

Da mai faɗar ainihin gaskiya a gaban

shari’a.

11 Kun matsa wa talakawa lamba,

Kun ƙwace musu abincinsu.

Saboda haka kyawawan gidajen nan

da kun gina da dutse,

Ba za ku zauna a cikinsu ba,

Ba kuwa za ku sha ruwan inabin

nan

Daga kyawawan gonakin inabinku

ba.

12 Na san irin zunuban da kuke yi,

Da mugayen laifofin da kuka aikata.

Kuna wulakanta mutanen kirki,

Kuna cin hanci,

Kuna hana a yi wa talakawa shari’ar

adalci a majalisa.

13 Ashe, ba abin mamaki ba ne,

Da masu hankali suka kame bakinsu

A waɗannan kwanaki na mugunta.

14 Ku yi ƙoƙari, ku yi nagarta, ba

mugunta ba,

Domin ku tsira.

Sa’an nan ne Ubangiji Allah

Maɗaukaki

Zai kasance tare da ku sosai,

Kamar yadda kuka ɗauka!

15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci

nagarta,

Ku yi adalci cikin majalisar

alƙalanku!

Watakila Ubangiji Allah Mai

Runduna

Zai yi wa sauran da suka ragu na

wannan al’umma alheri.

16 Haka Ubangiji Allah Mai Runduna

ya ce,

“Za a yi kuka, a yi kururuwa a

titunan birninku saboda azaba.

Daga ƙauyuka za a kirawo

mutane

Su zo su yi makokin.

Waɗanda suka mutu, tare da masu

makoki da aka ijarar da su.

17 Za a yi kuka ko’ina cikin dukan

gonakin inabinku

Gama zan zo in yi muku horo.”

18 Taku ta ƙare, ku da kuke marmarin

zuwan ranan nan ta Ubangiji!

Wane amfani wannan rana za ta yi

muku?

Rana ta baƙin ciki ce,

Ba ta murna ba.

19 Zai zama kamar wanda ya tsere wa

zaki

Ya fāɗa a bakin beyar!

Ko kuwa kamar wanda ya komo

gida,

Ya dāfa bango, maciji ya sare shi.

20 Ranar Ubangiji za ta kawo baƙin

ciki,

Ba murna ba.

Rana ce ta damuwa ba ta fara’a ba.

21 Ubangiji ya ce,

“Na ƙi bukukuwanku na addini.

Ina ƙyamarsu!

22 Sa’ad da kuka kawo mini hadayun

ƙonawa

Da hadayunku na tsaba, ba zan

karɓa ba.

Ba kuma zan karɓi turkakkun

dabbobinku

Waɗanda kuka miƙa mini hadayun

godiya ba.

23 Ku yi shiru da yawan hargowar

waƙoƙinku.

Ba na so in saurari kaɗe-kaɗenku da

bushe-bushenku.

24 Sai ku sa adalci da nagarta su gudano

a yalwace

Kamar kogin da ba ya ƙafewa.

25 “Ya ku, jama’ar Isra’ila, ai, a waɗannan shekaru arba’in da kuka yi cikin jeji kuka kawo mini sadaka da hadayu,

26 duk da haka, kuka ɗauki siffofin gumakanku na taurari, wato Sakkut da Kaiwan, waɗanda kuka yi wa kanku.

27 Ni kuwa zan sa ku yi ƙaura zuwa wata ƙasa gaba da Dimashƙu.” Ubangiji, Allah Mai Runduna, shi ne ya faɗa.

Categories
AMOS

AMOS 6

Halakar Isra’ila

1 Taku ta ƙare, ku da kuke zaman

sakewa a Sihiyona,

Da ku da kuke tsammani kuna

zaman lafiya a Samariya,

Ku da kuke manyan mutane

Na wannan babbar al’umma ta

Isra’ila,

Waɗanda jama’a suke zuwa a gare su

neman taimako!

2 Ku je ku duba a birnin Kalne.

Sa’an nan ku zarce zuwa babban

birnin Hamat,

Har zuwa birnin Gat ta Filistiyawa.

Sun fi mulkin Yahuza da Isra’ila ne?

Ko kuwa, yankin ƙasarsu ya fi

naku?

3 Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan

rana ta masifa,

Amma ga shi, goyon bayan hargitsi

kuke ta yi,

Ta wurin ayyukanku.

4 Taku ta ƙare, ku da kuke kwance

kan gadajen hauren giwa,

Kuna jin daɗin miƙe jiki a dogayen

kujerunku,

Ku ci naman maraƙi da na rago.

5 Kukan so ku tsara waƙoƙi kamar

yadda Dawuda ya yi,

Ku raira su da garayu.

6 Da manyan kwanoni kuke shan

ruwan inabi,

Ku shafe jiki da mai mafi kyau,

Amma ba ku yin makoki saboda

lalacewar Isra’ila.

7 Don haka, ku ne na fari da za a sa su

yi ƙaura

Bukukuwanku da shagulgulanku za

su ƙare.

8 Ubangiji kansa ne ya rantse.

Ubangiji Allah Mai Runduna ya ce,

“Ba na son girmankai na jama’ar

Isra’ila.

Ba na son fādodinsu.

Zan ba da birnin da dukan abin da

yake cikinsa ga abokan gābansu.”

9 Ko da a ce mutum goma ne suka ragu a gida guda, duk za su mutu.

10 Sa’ad da dangin mamacin ya shiga don ya fitar da gawar, ya ƙone, sai ya yi kira ga ko wane ne da yake ɓoye a gidan, ya ce, “Ko akwai wani kuma a nan?”

Sai a amsa, “A’a.”

Zai ce, “Kul! Kada a ambaci sunan Ubangiji.”

11 Sa’ad da Ubangiji ya ba da umarni, babban gida da ƙarami rushewa za su yi.

12 Dawakai sukan yi sukuwa a

duwatsu?

Ana huɗan teku da garmar

shanu?

Duk da haka kuka mai da adalci

dafi,

Kuka mai da nagarta, mugunta.

13 Kuna fariyar cin garin Lodebar, wato

wofi, da yaƙi.

Kun ce, “Ƙarfinmu ya isa har mu ci

Karnayim, wato ƙaho biyu, da

yaƙi.”

14 Ubangiji Allah Mai Runduna

kansa, ya amsa ya ce,

“Zan aiko da wata al’umma ta yi

gāba da ku, ya Isra’ilawa.

Za ta matse muku

Tun daga mashigin Hamat wajen

arewa,

Har zuwa Kwarin Urdun a kudu.”

Categories
AMOS

AMOS 7

Wahayin Fāra

1 A wahayin da Ubangiji ya nuna mini, sai na ga ya yi cincirindon fara nan da nan bayan da aka ƙarasa yankan rabon ingiricin da yake na sarki, ciyawar kuma ta soma tohuwa.

2 A wahayin, na ga fara ta cinye kowane ɗanyen ganye a ƙasar. Sai na ce,

“Ka gafarta wa jama’arka, ya

Ubangiji!

Ƙaƙa za su tsira?

Ga su ‘yan kima ne, marasa

ƙarfi.”

3 Ubangiji kuwa ya dakatar da

nufinsa,

Ya ce, “Abin da ka gani, ba zai faru

ba.”

Wahayin Wuta

4 A wahayin da Ubangiji ya nuna mini, na gan shi yana shirin hukunta jama’arsa da wuta. Wutar ta ƙone babbar teku, har ma ta fara ƙone ƙasar.

5 Sa’an nan na ce,

“Ya Ubangiji, in nufinka ne ka bari!

Ƙaƙa jama’arka za su tsira?

Ga su ‘yan kima ne, marasa

ƙarfi.”

6 Ubangiji kuwa ya dakatar da nufinsa, ya ce,

“Wannan ma ba zai faru ba.”

Wahayin Ma’auni

7 Ubangiji kuma ya nuna mini wani wahayi. A wahayin sai na gan shi, yana tsaye kusa da bangon da ake ginawa. Yana riƙe da igiyar awon gini.

8 Ya tambaye ni, ya ce, “Amos, me ka gani?”

Sai na ce, “Igiyar awon gini na gani.”

Ya kuma ce,

“Duba, da wannan zan nuna yadda

jama’ata sun zama kamar bangon

da ya karkace.

Ba zan sāke nufina a kan yi musu

hukunci ba.

9 Zan hallakar da wuraren sujada na

zuriyar Ishaku.

Za a hallakar da tsarkakan wurare na

Isra’ila.

Zan fāɗa wa zuriyar sarki

Yerobowam da yaƙi.”

Amos da Amaziya

10 Amaziya, firist, na Betel kuwa, ya tafi ya faɗa wa Yerobowam Sarkin Isra’ila, ya ce, “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a cikin jama’ar Isra’ila. Maganganunsa za su hallakar da ƙasar.

11 Abin da ya faɗa ke nan, ‘Za a kashe Yerobowam a bakin dāga, a sa jama’ar Isra’ila su yi ƙaura zuwa wata ƙasa.’ ”

12 Amaziya kuwa ya ce wa Amos, “Kai maƙaryaci ne na ainihi! Koma ƙasar Yahuza ka nemi abin zaman gari, ka yi ta annabcinka a can.

13 Amma a nan Betel kada ka ƙara yin annabci. Nan wurin yin sujada na sarki ne, haikali ne na al’umma.”

14 Sai Amos ya amsa ya ce, “Ni ba annabi ba ne. Wannan ba aikina ba ne. Ni makiyayi ne, mai kuma lura da itatuwan ɓaure.

15 Amma Ubangiji ya raba ni da aikina na kiwo, ya umarce ni in tafi in yi magana da jama’arsa, wato Isra’ila.

16 Domin haka, sai ka kasa kunne ga abin da Ubangiji ya ce. Saboda ka ce mini in daina yin annabci gāba da jama’ar Isra’ila, kada kuwa in yi wa zuriyar Ishaku ɓaɓatu,

17 to, ga abin da Ubangiji ya ce maka, ya kai Amaziya, ‘Matarka za ta zama karuwa a birni, za a karkashe ‘ya’yanka a cikin yaƙi. Za a rarraba wa waɗansu ƙasarka, kai kanka kuwa za ka mutu a ƙasar arna. Za a sa jama’ar Isra’ila su yi ƙaura zuwa wata ƙasa.’ ”

Categories
AMOS

AMOS 8

Wahayi na Huɗu, Kwandon Ɓaure na Ci

1 Ubangiji ya nuna mini wahayi, sai na ga kwandon ɓaure na ci.

2 Sai Ubangiji ya ce, “Amos, me ka gani?”

Na ce, “Kwandon ɓaure na ci.”

Ubangiji kuma ya ce mini, “Ƙarshen jama’ata Isra’ila ya zo. Ba zan sāke nufina a kan yi musu hukunci ba.

3 Waƙoƙin da akan raira a fāda, za su zama na makoki a wannan rana. Za a iske gawawwaki ko’ina. Ba za a ji motsin kome ba.”

An kai Ƙarshen Isra’ila

4 Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata, kuna ƙoƙari ku hallakar da matalautan ƙasar.

5 Kuna ce wa kanku, “Mun ƙosa

keɓaɓɓun kwanakin nan su wuce,

Mu sami damar yin kasuwancinmu.

Yaushe Asabar ɗin za ta ƙare ne?

Ko mā sami damar kai hatsinmu

kasuwa,

Mu sayar musu da tsada,

Mu yi awo da ma’aunin zalunci,

Mu daidaita ma’auni yadda za mu

cuci mai saya?

6 Za mu sayi matalauci da azurfa ya

zama bawa,

Mai fatara kuma da takalma

bi-shanu.

Za mu sayar da ruɓaɓɓen hatsi,

Mu ci riba mai yawa.”

7 Ubangiji Allahn Isra’ila ya riga ya

rantse,

Ya ce, “Ba zan manta da mugayen

ayyukanku ba.

8 Shi ya sa ƙasar za ta girgiza,

Duk wanda yake cikinta zai yi baƙin

ciki.

Ƙasa duka za ta girgiza.

Za ta hau ta sauka kamar Kogin Nilu.

9 A wannan lokaci rana za ta fāɗi da

tsakar rana,

Duniya ta duhunta da rana kata.

Ni, Ubangiji ne na faɗa.

10 Zan mai da bukukuwanku makoki,

In sa waƙoƙinku na murna su zama

na makoki.

Zan sa muku tufafin makoki,

In sa ku aske kanku.

Za ku yi makoki kamar iyayen da

suka rasa tilon ɗansu.

Ranan nan mai ɗaci ce har ƙarshe.

11 “Lokaci yana zuwa da zan aiko da

yunwa a ƙasar.

Mutane za su ji yunwa,

Ba ta abinci ba,

Za su ji ƙishi,

Ba na ruwa ba.

Za su ji yunwar rashin samun saƙo

daga wurin Ubangiji.

Ni Ubangiji ne, na faɗa.

12 Mutane za su raunana, su riƙa kai

da kawowa,

Daga gabas zuwa yamma, daga

kuma kudu zuwa arewa.

Za su dudduba ko’ina suna neman

saƙo daga Ubangiji,

Ba kuwa za su samu ba.

13 A ranan nan kyawawan ‘yan mata

da samari

Za su faɗi saboda ƙishirwa.

14 Waɗanda suka yi rantsuwa da

gumakan Samariya,

Waɗanda suka ce, ‘Na rantse da

gunkin Dan,

Da ran gunkin Biyer-sheba,’

Irin waɗannan mutane za su fāɗi,

Ba za su ƙara tashi ba.”

Categories
AMOS

AMOS 9

Ba a Kauce wa Hukuncin Allah

1 Na ga Ubangiji na tsaye a wajen bagade. Ya yi umarni, ya ce,

“Bugi ginshiƙan Haikali don shirayi

duka yă girgiza.

Farfasa su, su fāɗi a kan mutane!

Sauran mutane kuwa,

Zan kashe su a wurin yaƙi.

Ba wanda zai tsere, ko ɗaya.

2 Ko da za su nutsa zuwa lahira,

Zan kama su.

Ko sun hau Sama,

Zan turo su.

3 Ko da za su hau su ɓuya a bisa

ƙwanƙolin Dutsen Karmel,

Zan neme su in cafko su.

Ko da za su ɓuya mini a ƙarƙashin

teku,

Sai in sa dodon ruwa yă yayyage su.

4 Idan kuwa abokan gābansu ne suka

kama su,

In umarce su su hallaka su da

takobi,

Tun da na yi ƙudurin ƙare su.”

5 Ubangiji Allah Mai Runduna

Ya taɓi duniya, ta girgiza.

Duk waɗanda suke zaune cikinta

Suna baƙin ciki.

Duniya duka takan hau

Ta kuma gangara kamar ruwan

Kogin Nilu.

6 Ubangiji ya gina al’arshinsa a sama,

Ya shimfiɗa samaniya a bisa duniya.

Ya sa ruwan teku ya zo,

Ya kwarara shi a bisa duniya.

Sunansa Ubangiji ne!

7 Ubangiji ya ce, “Jama’ar Isra’ila,

Ina yi da ku daidai yadda nake yi da

Habashawa.

Na fito da Filistiyawa daga Kaftor,

Suriyawa kuwa daga Kir,

Daidai yadda na fito da ku daga

Masar.

8 Ina dai kallon mulkin nan mai zunubi.

Zan hallaka su daga duniya,

Amma ba zan hallaka dukan jama’ar

Yakubu ba.

9 “Zan umarta a rairayi jama’ar Isra’ila

Da matankaɗi kamar hatsi.

Zan rairaye su daga cikin sauran

al’umma,

Duk da haka ko ƙwaya ɗaya ba za

ta salwanta ba.

10 Masu zunubi daga cikin jama’ata za

su mutu a yaƙi,

Wato dukansu da suke cewa,

‘Allah ba zai bar wata masifa ta

kusace mu ba!’ ”

Ceton da Za a Yi wa Isra’ila Nan Gaba

11 “Wata rana zan sāke tayar da birnin

Dawuda

Tankar yadda akan ta da gidan da ya

rushe.

Zan gyara garunsa, in sāke mai da

shi.

Zan sāke gina shi in mai da shi

kamar yadda yake tun dā.

12 Ta haka jama’ar Isra’ila za ta ci

nasara bisa sauran ƙasar Edom

wadda ta ragu,

Da bisa dukan al’umman da a dā su

nawa ne,”

In ji Ubangiji, wanda zai sa

al’amarin ya auku.

13 Ubangiji ya ce, “Kwanaki suna

zuwa,

Sa’ad da girbi zai bi bayan huda nan

da nan,

Matsewar ruwan inabi kuma

Za ta bi bayan shuka nan da

nan.

Duwatsu za su zubo da ruwan inabi

mai zaƙi,

Tuddai kuma su gudano da shi.

14 Zan komo da mutanena ƙasarsu,

Za su giggina biranensu da suka

rurrushe,

Su zauna a cikinsu.

Za su shuka gonakin inabi, su sha

ruwan inabin.

Za su yi lambuna, su ci amfaninsu.

15 Zan dasa su a ƙasar da na ba su,

Ba kuwa za a ƙara tumɓuke su

ba.”

Ubangiji Allahnku ne ya faɗa.