Categories
AYU

AYU 1

Shaiɗan Ya Jarraba Ayuba

1 Akwai wani mutum a ƙasar Uz, mai suna Ayuba, amintacce ne, mai tsoron Allah. Shi mutumin kirki ne, natsattse, yana ƙin aikata kowace irin mugunta.

2 Yana da ‘ya’ya bakwai maza, uku mata.

3 Yana da tumaki dubu bakwai (7,000), da raƙuma dubu uku (3,000), da shanu dubu guda (1,000), da jakuna ɗari biyar. Yana kuma da barori masu yawan gaske, don haka ya fi kowa a ƙasar gabas arziki nesa.

4 ‘Ya’yansa maza sukan yi liyafa bi da bi a gidajen junansu, inda su duka sukan taru koyaushe, sukan gayyaci ‘yan’uwan nan nasu mata su halarci liyafar.

5 A kowane lokacin da aka gama da liyafar, Ayuba yakan tashi da sassafe, kashegarin liyafar, yă miƙa hadayu don yă tsarkake ‘ya’yansa. Haka yake yi kullum, don yana zaton mai yiwuwa ne ɗaya daga cikin ‘ya’yan ya yi zunubi, ya saɓi Allah a ɓoye.

6 Sa’ad da ranar da talikan sama masu rai sukan hallara gaban Ubangiji ta yi, Shaiɗan ma ya zo tare da su.

7 Sai Ubangiji ya tambaye shi, ya ce, “Kai fa me kake yi?”

Shaiɗan ya amsa, ya ce, “Ina ta kaiwa da kawowa ne, a ko’ina a duniya.”

8 Ubangiji ya ce masa, “Ko ka lura da bawana Ayuba? Ba wani mutumin kirki, mai aminci, kamarsa a duniya. Yana yi mini sujada, natsattse ne, yana ƙin aikata kowace irin mugunta.”

9 Shaiɗan ya amsa, ya ce, “A banza Ayuba yake yi maka sujada?

10 Ai, don ka kiyaye shi ne, shi da iyalinsa, da dukan abin da yake da shi. Ka kuma sa wa duk abin da yake yi albarka, ka kuwa ba shi shanun da suka isa su cika dukan ƙasan nan.

11 Amma da a ce za ka raba shi da dukan abin hannunsa, to, da zai fito fili yă zage ka ƙiri ƙiri.”

12 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, dukan abin hannunsa yana cikin ikonka, amma shi kansa kada ka cuce shi.” Sai Shaiɗan ya tafi.

An Hallaka ‘Ya’yan Ayuba da Dukiyarsa

13 Wata rana ‘ya’yan Ayuba suna shagali a gidan wansu,

14 sai ga jakada ya zo wurin Ayuba a guje, ya ce, “Muna huɗar gona da shanu, jakuna suna kiwo a makiyayar da suke kusa da wurin,

15 sai Sabiyawa suka auka musu farat ɗaya, suka sace su duka, suka kuma karkashe duk barorinka, sai ni kaɗai na tsira, na zo in faɗa maka.”

16 Kafin yă gama magana, sai wani bara ya zo, ya ce, “Tsawa ta kashe tumaki da makiyayansu duka, ni kaɗai na tsira, na zo in faɗa maka.”

17 Kafin yă gama magana, sai wani bara ya zo, ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa suka auka mana, suka kwashe raƙuma duka, suka kuma karkashe barorinka duka, sai ni kaɗai na tsira, na zo in faɗa maka.”

18 Kafin yă gama magana, sai wani bara ya zo, ya ce, “Sa’ad da ‘ya’yanka suke liyafa a gidan wansu,

19 sai hadiri ya taso daga hamada, ya rushe gidan, ya kashe ‘ya’yanka duka, ni kaɗai na tsira na zo in faɗa maka.”

20 Sai Ayuba ya tashi, ya kyakkece tufafinsa don baƙin ciki. Ya aske kansa, ya fāɗi ƙasa,

21 ya ce, “Ban shigo duniya da kome ba, ba kuma zan fita cikinta da kome ba. Ubangiji ya bayar, shi ne kuma ya karɓe, yabo ya tabbata ga sunansa.”

22 Ko da yake waɗannan al’amura duka sun faru, duk da haka Ayuba bai sa wa Allah laifi ba.

Categories
AYU

AYU 2

Shaiɗan Ya Sāke Jarraba Ayuba

1 Sa’ad da ranar da talikan sama masu rai sukan hallara gaban Ubangiji ta sāke yi, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.

2 Ubangiji ya tambaye shi, ya ce, “Ina ka fito?”

Sai Shaiɗan ya amsa, ya ce, “Ina ta kaiwa da kawowa ne, ko’ina a duniya.”

3 Ubangiji ya tambaye shi, ya ce, “Ko ka lura da bawana Ayuba? Ba wani mutumin kirki, mai aminci, kamarsa a duniya. Yana yi mini sujada, natsattse ne, yana ƙin aikata kowace irin mugunta. Kai ka sa na yardar maka ka far masa, ba tare da wani dalili ba. Amma duk da haka Ayuba yana nan da amincinsa kamar yadda yake.”

4 Shaiɗan ya amsa, ya ce, “Mutum ya iya rabuwa da dukan abin da yake da shi don yă ceci ransa.

5 Amma yanzu da a ce za ka taɓa lafiyar jikinsa, da sai yă fito fili yă zage ka.”

6 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Shi ke nan, yana cikin ikonka, amma fa, kada ka kashe shi.”

7 Sa’an nan Shaiɗan ya rabu da Ubangiji, ya je ya sa ƙuraje su fito ko’ina a jikin Ayuba.

8 Ayuba ya je ya zauna kusa da juji ya ɗauki tsingaro ya yi ta sosa ƙurajen.

9 Sai matarsa ta ce masa, “Har yanzu kana da amincin nan naka? Don me ba za ka zagi Allah ka mutu ba?”

10 Ayuba ya amsa, ya ce mata, “Wace irin maganar gāɓanci ce haka? Lokacin da Allah ya aiko mana da alheri, mukan yi na’am da shi, to, me zai sa sa’ad da ya aiko mana da wahala za mu yi gunaguni?” Cikin dukan wahalar da Ayuba ya sha, bai sa wa Allah laifi ba.

Abokan Ayuba Sun Zo

11 Sa’ad da uku daga cikin abokan Ayuba, wato Elifaz daga birnin Teman, da Bildad daga ƙasar Shuwa, da Zofar daga ƙasar Na’ama, suka ji labarin irin yawan wahalar da Ayuba yake sha, sai suka kama hanya suka tafi su ziyarce shi, su ta’azantar da shi.

12 Suka hango Ayuba tun daga nesa, amma ba su gane shi ba. Da suka gane shi sai suka fara kuka da murya mai ƙarfi. Suka kyakkece tufafinsu saboda baƙin ciki, suka ɗibi ƙura suka watsa a kawunansu.

13 Sa’an nan suka zauna a ƙasa tare da shi, har kwana bakwai, amma ba wanda ya ce uffan, saboda ganin irin yawan wahalar da yake sha.

Categories
AYU

AYU 3

Ayuba Ya Kai Kuka ga Allah

1 Ayuba ya yi magana ya la’anci ranar da aka haife shi.

2 Ya ce,

“Ya Ubangiji, ka la’anci ranan nan da aka haife ni.

3 Ka la’anci daren nan da aka yi cikina.

4 Ka mai da ranan nan ta zama duhu, ya Allah.

Kada a ƙara tunawa da wannan rana,

Kada haske ya ƙara haskakata.

5 Ka sa ta zama ranar duhu baƙi ƙirin.

Ka rufe ta da gizagizai, kada hasken rana ya haskaka ta.

6 Ka shafe wannan dare daga cikin shekara,

Kada kuma a ƙara lasafta shi.

7 Ka sa daren ya zama marar amfani, daren baƙin ciki.

8 Ka faɗa wa masu sihiri su la’anci wannan rana,

Su waɗanda suke umartar dodon ruwa.

9 Ka hana gamzaki haskakawa,

Kada ka bar daren nan ya sa zuciya ga wayewar gari,

10 Ka la’anci daren nan da aka haife ni,

Da ya jefa ni a baƙin ciki da wahala.

11 “Da ma na mutu tun a cikin cikin uwata,

Ko kuwa da haihuwata in mutu.

12 Me ma ya sa uwata ta rungume ni a ƙirjinta,

Ta shayar da ni kuma da mamanta?

13 Da a ce na mutu a lokacin, da yanzu ina huce,

14 Da ina ta barcina kamar sarakuna da masu mulki

Waɗanda suka sāke gina fādodi na dā,

15 Da ina ta sharar barcina kamar shugabanni

Waɗanda suka cika gidajensu da zinariya da azurfa,

16 In yi ta sharar barci kamar jariran da aka haifa matattu.

17 Mugaye za su daina muguntarsu a kabari,

Ma’aikatan da suka gaji da aiki su ma za su huta,

18 Har ‘yan sarƙa ma za su ji daɗin salama,

Su huta daga tsautawa da umarnai masu tsanani.

19 Kowa da kowa yana wurin, babba da ƙarami duk ɗaya ne,

Bayi ma sun sami ‘yanci.

20 “Me ya sa ake barin mutane su yi ta zama cikin damuwa?

Me ya sa ake ba da haske ga waɗanda suke baƙin ciki?

21 Sun jira mutuwa, amma ta ƙi samuwa,

Sun fi son kabari da kowace irin dukiya.

22 Ba su da farin ciki, sai sun mutu an binne su tukuna.

23 Allah ya ɓoye musu sanin abin da zai faru nan gaba,

Ya kalmashe su kowane gefe.

24 A maimakon cin abinci, sai baƙin ciki nake yi,

Ba kuma zan daina yin nishi ba,

25 Dukan abin da nake jin tsoro ko fargaba ya faru.

26 Ba ni da salama, ba ni da hutawa,

Wahala ba za ta taɓa ƙarewa ba.”

Categories
AYU

AYU 4

Elifaz Ya Tsauta wa Ayuba

1 Elifaz ya yi magana.

2 “Ayuba, za ka ji haushi in na yi magana?

Ba zan iya kannewa, in yi shiru ba.

3 Ka koya wa mutane da yawa,

Ka kuma ƙarfafa hannuwan marasa ƙarfi.

4 Idan wani ya yi tuntuɓe,

Ya gaji, ya rasa ƙarfi,

Kalmominka suka ƙarfafa zuciyarsa,

Har ya iya tsayawa kyam.

5 Yanzu naka lokacin wahala ya zo,

Kai kuwa ka rikice, ka kasa ɗaurewa,

6 Kana yi wa Allah sujada,

Ba wani laifi a zamanka,

Ya kamata ka amince ka sa zuciya.

7 “Yanzu fa sai ka yi tunani.

Ka faɗi bala’i ɗaya wanda ya taɓa fāɗa wa adalin mutum.

8 Na taɓa ganin mutane suna huɗe gonar mugunta,

Suna shuka mugunta,

Suka kuwa girbe mugunta.

9 A cikin fushinsa Allah yakan hallaka su kamar hadiri.

10 Mugaye sukan yi ruri suna gurnani kamar zakoki,

Amma Allah yakan sa su yi tsit,

Ya kakkarya haƙoransu.

11 Kamar zakoki da ba su da abin da za su kashe su ci,

Haka nan za su mutu, ‘ya’yansu kuwa su warwatse duka.

12 “Wata rana wani saƙo ya zo a hankali,

Har da ƙyar nake iya ji,

13 Kamar wani irin mafarki mai razanarwa yake,

Wanda ya hana ni jin daɗin barcina.

14 Na yi rawar jiki ina makyarkyata,

Duk jikina yana ta ɓare-ɓare don tsoro.

15 Wata iska marar ƙarfi ta taɓa fuskata,

Sai fatar jikina ta yanƙwane saboda fargaba.

16 Na ga wani abu can yana tsaye,

Na zura ido, amma ban san kowane irin abu ba ne,

Ina cikin wannan hali sai na ji murya,

17 Ta ce, ‘Mutum yana iya zama adali a gaban Allah?

Akwai kuma wanda yake mai tsarki a gaban Mahaliccinsa?

18 Allah ba ya amince wa barorinsa na cikin sammai,

Yakan sami laifi a wurin mala’ikunsa.

19 Ta ƙaƙa zai amince da talikinsa wanda aka yi da ƙasa,

Abin da yake na ƙura, ana kuwa iya murƙushe shi kamar asu.

20 Mai yiwuwa ne mutum yana raye da safe

Amma ya mutu ba a sani ba kafin maraice.

21 Duk abin da ya mallaka an ɗauke,

Duk da haka ya mutu cikin rashin hikima.’ ”

Categories
AYU

AYU 5

1 “Ka yi kira, ya Ayuba, ka gani, ko wani zai amsa!

Akwai wani mala’ika da za ka juya zuwa gare shi?

2 Ba shi da amfani ka dami kanka

Har ka mutu, saboda tsarguwa, gama wannan wawanci ne,

Da aikin rashin hankali.

3 Na ga waɗansu wawaye waɗanda ake gani kamar suna zaune lafiya,

Amma nan da nan sai na la’anci gidajensu.

4 Ko kaɗan, ‘ya’yansu maza ba za su taɓa zama lafiya ba.

Ba wanda zai tsaya musu a ɗakin shari’a.

5 Mayunwata za su ci amfanin gonar wawa,

Har da hatsin da yake girma cikin ƙayayuwa,

Waɗanda suke jin ƙishirwa za su ji ƙyashin dukiyarsa.

6 Zunubi ba ya tsirowa daga ƙasa,

Haka ma wahala ba ta tsirowa daga ƙasa.

7 Ai, an haifi mutum domin wahala ne,

Tabbatacce ne kamar yadda tartsatsin wuta suke tashi.

8 “In da ni ne kai, da sai in juya wurin Allah,

In kai ƙarata a wurinsa.

9 Ba za mu iya fahimtar manyan abubuwa da yake yi ba,

Al’ajabansa kuwa ba su da iyaka.

10 Yakan aiko da ruwan sama,

Ya shayar da gonaki.

11 I, Allah ne yake ɗaukaka masu tawali’u,

Shi yake kuɓutar da dukan waɗanda suke makoki.

12 Yakan birkitar da shirye-shiryen masu wayo.

13 Yakan sa wa masu wayo tarko cikin dabarunsu,

Har ba za su yi nasara a dukan abin da suke yi ba.

14 Da rana sukan yi karo da duhu,

Ko da tsakar rana ma lalube suke kamar ana duhu.

15 Amma Allah yakan ceci matalauta daga mutuwa,

Yakan kuma ceci masu bukata daga zalunci.

16 Yakan sa matalauta su sa zuciya,

Ya sa mugaye su yi shiru.

17 “Mai farin ciki ne mutumin da Allah ya hora,

Kada ka tsargu sa’ad da ya tsauta maka.

18 Allah yakan yi maganin raunin da ya yi maka,

Ciwon da ya ji maka da hannunsa,

Da hannunsa yakan warkar.

19 Yakan tsare ka daga cuta sau shida har sau bakwai,

Ba muguntar da za ta taɓa ka.

20 Yakan kiyaye ka da rai a lokacin yunwa,

A yaƙi kuma yakan tsare ka daga mutuwa.

21 Allah yakan kuɓutar da kai daga ƙarairayi da ɓata suna,

Yakan cece ka daga hallaka.

22 Aikin kama-karya da yunwa za su zama abin dariya a gare ka,

Ba kuwa za ka ji tsoron namomin jeji ba.

23 Ba za a sami duwatsu a gonakin da kake nomawa ba,

Mugayen namomin jeji ba za su far maka ba.

24 Sa’an nan za ka zauna lafiya a alfarwanka,

A sa’ad da ka dubi tumakinka, za ka tarar suna nan lafiya.

25 ‘Ya’yanka za su yi yawa kamar ciyawa,

Kamar yadda alkama take a lokacin kakarta.

26 Haka kai ma za ka rayu, har ka tsufa da kyakkyawan tsufa.

27 Kai, Ayuba, mun koyi wannan don mun daɗe muna nazari,

Gaskiya ce, don haka ka yarda da wannan.”

Categories
AYU

AYU 6

Ayuba Ya Zargi Abokansa

1 Ayuba ya amsa.

2 “In da za a auna wahalata da ɓacin raina da ma’auni,

3 Da sun fi yashin teku nauyi.

Kada ka yi mamaki da maganganun da nake yi.

4 Allah Maɗaukaki ya harbe ni da kibau,

Dafinsu kuwa ya ratsa jikina.

Allah ya jera mini abubuwa masu banrazana.

5 “Idan jaki ya sami ciyawar ci, muradinsa ya biya,

In ka ji saniya ta yi shiru, tana cin ingirici ne.

6 Amma wane ne zai iya cin abinci ba gishiri?

Akwai daɗin ɗanɗano ga farin ruwan ƙwai?

7 Ba na jin marmarin cin abinci irin haka,

Kowane irin abu da na ci yakan sa mini cuta.

8 “Me ya sa Allah ya ƙi ba ni abin da nake roƙo?

Me ya sa ya ƙi yin abin da nake so?

9 Da ma ya ci gaba kawai ya kashe ni,

Ko ya sake ikonsa ya datse ni!

10 Da na san zai yi haka, da sai in yi tsalle don murna,

Da ba zan kula da tsananin azabar da nake ciki ba.

Ban taɓa yin gāba da umarnan Allah ba.

11 Wane ƙarfi ne nake da shi na rayuwa?

Wane sa zuciya kuma nake da ita,

tun da na tabbata mutuwa zan yi?

12 Da dutse aka yi ni?

Ko da tagulla aka yi jikina?

13 Ba ni da sauran ƙarfi da zan ceci kaina,

Ba inda zan juya in nemi taimako.

14 “A cikin irin wannan wahala

Ina bukatar amintattun abokai,

Ko da na rabu da Allah, ko ina tare da shi.

15 Amma ku abokaina,kun ruɗe ni,

Kamar rafi wanda yakan ƙafe da rani.

16-17 Rafin yana cike da iska mai laima da ƙanƙara,

Amma lokacin zafi sai su ɓace,

Kwacciyar rafin, sai ta bushe ba kome.

18 Ayari sukan ɓata garin neman ruwa,

Su yi ta gilo, har su marmace a hamada.

19 Ayari daga Sheba da Tema suka yi ta nema,

20 Amma sa zuciyarsu ta ƙare a gefen busassun rafuffuka,

21 Kamar rafuffukan nan kuke a gare ni,

Kun ga abin da ya same ni, kun gigita.

22 Na roƙe ku ku ba ni kyauta ne?

Ko kuwa na roƙe ku ku ba wani rashawa domina?

23 Ko kuma na roƙe ku ku cece ni daga maƙiyi ko azzalumi ne?

24 “To, sai ku koya mini, ku bayyana mini laifofina,

Zan yi shiru in kasa kunne gare ku.

25 Kila muhawara mai ma’ana ta rinjaye ni,

Amma yanzu duk maganar shirme kuke yi.

26 Kuna so ku amsa maganganuna?

Don me?

Mutumin da yake cikin halin ƙaƙa naka yi,

Ba wata maganar da zai yi in ba shirme ba.

27 Kukan jefa wa bayi da marayu kuri’a,

Kukan arzuta kanku daga abokanku na kurkusa.

28 Ku dubi fuskata,

Lalle ba zan faɗi ƙarya ba.

29 Kai, kun zaƙe, ku daina aikata rashin adalci,

Kada ku sa mini laifi, nake da gaskiya.

30 Amma duk da haka kuna tsammani ƙarya nake yi.

Kuna tsammani ba zan iya rarrabe tsakanin gaskiya da ƙarya ba.”

Categories
AYU

AYU 7

Ayuba Ya Damu da Abin da Allah Ya Yi

1 “Kamar kamen soja na tilas,

Haka zaman ‘yan adam take,

Kamar zaman mai aikin bauta.

2 Kamar bawa ne wanda yake sa zuciya ga inuwa mai sanyi,

Kamar ma’aikaci wanda yake sa zuciya ga lokacin biya.

3 Wata da watanni ina ta aikin banza,

Kowane dare ɓacin rai yake kawo mini.

4 Sa’ad da na kwanta barci, sai daren ya daɗa tsawo

In yi ta jujjuyawa duk dare, in ƙosa gari ya waye.

5 Jikina cike yake da tsutsotsi,

Ƙuraje duka sun rufe shi,

Daga miyakuna mugunya tana ta zuba.

6 Kwanakina sun wuce ba sa zuciya,

Sun wuce da sauri kamar ƙoshiyar saƙa.

7 “Ka tuna, ya Ubangiji, raina iska ne kawai,

Farin cikina ya riga ya ƙare.

8 Kuna ganina yanzu, amma ba za ku sāke ganina ba.

Idan kuka neme ni, za ku tarar ba na nan.

9 Kamar girgijen da yake bajewa ya tafi,

Haka nan mutum yake mutuwa.

10 Ba kuwa zai ƙara komowa ba,

Mutanen da suka san shi, duka za su manta da shi.

11 A’a, ko kaɗan ba zan yi shiru ba!

Haushi nake ji, zuciyata ta ɓaci,

Dole ne in yi magana.

12 “Ya Ubangiji, don me ka sa ni a waƙafi?

Kana tsammani ni dodon ruwa ne?

13 Na kwanta ina ƙoƙari in huta,

Ina neman taimako don azabar da nake sha.

14 Amma kai kana firgita ni da mafarkai,

Kana aiko mini da wahayi da ganegane,

15 Har nakan fi so a rataye ni,

Gara in mutu da in rayu a wannan hali.

16 Na fid da zuciya. Na gaji da rayuwa.

Ku rabu da ni. Rayuwa ba ta da wata ma’ana.

17 “Ya Ubangiji, me ya sa mutum yake da daraja haka a gare ka?

Me ya sa kake lura da abin da yake yi?

18 Kakan dube shi kowace safiya.

Kana jarraba shi a kowane daƙiƙa.

19 Ba za ka ko ɗan kawar da kai ba,

Don in samu in haɗiye yau?

20 Ko na yi zunubi ina ruwanka,

Kai mai ɗaure mutane?

Me ya sa ka maishe ni abin bārata?

Ni wani babban kaya mai nauyi ne a gare ka?

21 Ba za ka iya gafarta mini zunubina ba?

Ba za ka kawar da kai ga muguntar da na aikata ba?

Ba da daɗewa ba zan rasu in koma a ƙura,

Lokacin da ka neme ni ba za ka same ni ba.”

Categories
AYU

AYU 8

Bildad Ya Ƙarfafa Hukuncin Allah Daidai Ne

1 Sai Bildad ya yi magana.

2 “Ka gama maganganunka marasa kan gado duka?

3 Allah bai taɓa yin danniya ba,

Bai kuma taɓa fāsa aikata abin da yake daidai ba.

4 Lalle ‘ya’yanka sun yi wa Allah zunubi,

Don haka ya hukunta su yadda ya cancanta.

5 Amma sai ka juyo ka yi roƙo ga Allah Maɗaukaki.

6 Idan kana da tsarki da aminci, Allah zai taimake ka,

Ya maido da iyalin gidanka, ya yi maka sakayya.

7 Duk hasarar dukiyan nan da ka yi, ba kome ba ne

In aka gwada da abin da Allah zai ba ka nan gaba.

8 “Ka tsai da zuciyarka a kan hikima irin ta zamanin dā.

Ka kuma yi ta yin tunani a kan gaskiyar da kakanninmu suka koya.

9 Kwanakinmu ‘yan kaɗan ne kawai,

Ba mu san kome ba,

Mu inuwa ne kawai a fuskar duniya.

10 Amma ka yarda masu hikima na zamanin dā su koya maka,

Ka kasa kunne ga abin da za su faɗa.

11 “Iwa ba ta tsirowa inda ba ruwa,

Ba a taɓa samunta a ko’ina ba sai a fadama.

12 In ruwan ta ƙafe, ita ce za ta fara bushewa,

Tun tana ƙanƙana ba ta isa a yanke a yi amfani da ita ba.

13 Marasa tsoron Allah kamar iwan nan suke,

Ba su da sa zuciya muddin sun rabu da Allah.

14 Suna dogara ga silin zare, murjin gizo-gizo.

15 Idan suka jingina ga saƙar gizo-gizo, za ta iya tokare su?

Idan sun kama ta, za ta taimake su tsayawa?

16 “Mugaye sukan tsiro kamar ciyayi a hasken rana,

Ciyayin da sukan yaɗu su cinye gona duka.

17 Saiwoyinsu sukan nannaɗe duwatsu,

Su riƙe kowane dutse da ƙarfi.

18 Amma idan aka tumɓuke su,

Ba wanda zai taɓa cewa sun kasance a wurin.

19 Hakika matuƙar murnar da mugaye suke da ita ke nan,

Yanzu waɗansu ne za su zo su gāje wurarensu.

20 “Amma daɗai Allah ba zai rabu da amintattu ba,

Ba kuwa zai taɓa taimakon mugun mutum ba.

21 Zai sāke barinka ka yi dariya ka ƙyalƙyata kamar dā,

Ka kuma yi sowa da murna matuƙa.

22 Amma zai sa maƙiyanka su sha kunya,

Za a shafe gidajen mugaye.”

Categories
AYU

AYU 9

Ayuba Ya Kasa Amsa wa Allah

1 Ayuba ya amsa.

2 “Ai, na taɓa jin waɗannan duka,

Amma ta ƙaƙa mutum zai yi jayayya da Allah har ya yi nasara?

3 Ta ƙaƙa za ka iya jayayya da shi?

Yana yiwuwa ya yi maka tambayoyi guda dubu

Waɗanda ba wanda zai iya ba da amsarsu.

4 Allah mai hikima ne, mai iko,

Ba wanda zai iya ja in ja da shi.

5 Yakan kawar da manyan duwatsu farat ɗaya,

Ya hallaka su da fushinsa,

6 Allah yakan aiko da girgizar ƙasa, ya girgiza duniya,

Yakan jijjiga ginshiƙan da duniya take zaune a kansu.

7 Allah yana da iko ya hana rana fitowa,

Ko kuma ya hana taurari haskakawa da dare.

8 Ba wanda ya taimaki Allah shimfiɗa sammai,

Wanda yake taka raƙuman ruwan teku, ya kuma kwantar da su.

9 Allah ya rataye taurari a sararin sama,

Wato su mafarauci da kare da zomo,

Da kaza da ‘ya’yanta da taurarin kudu.

10 Ba shi yiwuwa mu gane manyan abubuwa da yake yi.

Ayyukan al’ajabansa ba su da iyaka.

11 “Allah yana wucewa kusa da ni,

Amma ba na ganinsa.

12 Yakan ɗauki abin da yake so, ba wanda yake hana shi,

Ba wanda yake tambayarsa cewa,

‘Me kake yi?’

13 “Allah ba zai huce fushinsa ba.

Ya murƙushe maƙiyansa waɗanda suka taimaki dodon ruwan nan da ake kira Rahab, wanda ya tayar masa.

14 To, ƙaƙa zan yi in samo kalmomin da zan amsa wa Allah?

15 Ko da yake ba ni da laifi,

Duk da haka iyakar abin da zan iya yi ke nan,

In roƙi Allah ya yi mini jinƙai,

Shi da yake alƙalina.

16 Amma duk da haka ko ya yardar mini in yi magana ma,

Ban yi tsammani zai saurare ni ba.

17 Shi ya aiko da hadura, suka yi kacakaca da ni,

Suka ƙuƙƙuje ni, ga shi kuwa, ba wani dalilin da ya sa ya yi mini rauni.

18 Ya hana ni in ko shaƙata,

Ina jin haushin dukan abin da yake yi mini.

19 In gwada ƙarfi ne?

To, a iya gwada wa Allah ƙarfi?

In kai shi ƙara ne?

Wa zai sa shi ya je?

20 Ni ba ni da laifin kome, amintacce ne ni,

A kunne sai a ji kalmomina kamar na marar gaskiya ne.

Kowane abu da na fāɗa, kā da ni yake yi.

21 Ba ni da laifin kome, amma ba na ƙara damuwa.

Na gaji da rayuwa.

22 Don haka ban damu da kome ba.

Da marar laifin da mai laifin duk, Allah zai hallaka mu.

23 Sa’ad da marar laifi ya mutu farat ɗaya,

Allah yakan yi dariya.

24 Allah ya ba da duniya ga mugaye,

Ya makantar da dukan alƙalai,

Idan ba Allah ne ya yi haka nan ba, to, wa ya yi?

25 “Kwanakina suna shuɗewa da sauri, ba mai kyau ko ɗaya.

26 Raina na wucewa kamar jirgin ruwa mafi sauri,

Da sauri ƙwarai kamar juhurma ya kai wa zomo sura.

27 Idan an yi murmushi,

Ina ƙoƙari in manta da azabata,

28 Sai dukan wahalar da nake sha ta yi ta firgita ni,

Na sani Allah ya ɗauke ni mai laifi.

29 Tun da yake Allah ya ɗauka, ni mai laifi ne,

To, me zai sa in damu?

30 Ba sabulun da zai iya wanke zunubaina.

31 Allah ya jefa ni a kwatami,

Har tufafina ma suna jin kunyata.

32 Da a ce Allah mutum ne,

Da sai in mayar masa da magana,

Da sai mun je ɗakin shari’a a yanka mana shari’a.

33 Amma ga shi, ba wanda zai shiga tsakaninmu,

Ba wanda zai shara’anta tsakanina da Allah.

34 Ka daina hukunta ni, ya Allah!

Ka daina razanar da ni.

35 Ba na jin tsoro,

Zan yi magana, domin na san zuciyata.”

Categories
AYU

AYU 10

Ayuba Ya Yi Kukan Matsayin da Yake Ciki

1 “Na gaji da rayuwa,

Ku ji ina fama da baƙin ciki.

2 Kada ka hukunta ni, ya Allah.

Ka faɗa mini laifin da kake tuhumata da shi.

3 Daidai ne a gare ka ka yi mugunta?

Ka wulakanta abin da kai da kanka ka yi?

Sa’an nan ka yi murmushi saboda dabarun mugaye?

4 Yadda mutane suke duban abu, haka kake duba?

5 Kai ma ranka gajere ne kamar namu?

6 In haka ne, me ya sa kake bin diddigin dukan laifofina,

Kana farautar dukan abin da na yi?

7 Ka sani, ba ni da laifi,

Ka kuma sani, ba wanda zai cece ni daga gare ka.

8 “Da ikonka ne ka yi ni, ka siffata ni,

Yanzu kuma da ikon nan naka ne za ka hallaka ni.

9 Ka tuna, ya Allah, kai ka halicce ni, da yumɓu kuwa ka yi ni.

Za ka murtsuke ni ne, in kuma koma ƙura?

10 Kai ne ka ba mahaifina ƙarfin da zai haife ni,

Kai ne ka sa na yi girma a cikin cikin mahaifiyata.

11 Kai ne ka siffata jikina da ƙasusuwa da jijiyoyi,

Ka rufe ƙasusuwan da nama, naman kuma ka rufe da fata.

12 Kai ne ka ba ni rai da madawwamiyar ƙauna,

Kulawarka ce ta sa ni rayuwa.

13 Amma yanzu na sani,

Dukan lokacin nan kana da wani nufi a ɓoye game da ni.

14 Jira kake ka ga ko zan yi zunubi,

Don ka ƙi gafarta mini.

15 Da cewa na yi zunubi, na shiga uku ke nan a wurinka.

Amma sa’ad da na yi abin kirki ba na samun yabo.

Ina baƙin ciki ƙwarai, kunya ta rufe ni.

16 Da zan ci nasara a kan kowane abu,

Da sai ka yi ta farautata kamar zaki,

Kana aikata al’ajabai don ka cuce ni.

17 A koyaushe kakan karɓi shaida gāba da ni,

Fushinka sai gaba gaba yake yi a kaina,

Kakan yi mini farmaki a koyaushe.

18 “Ya Allah, me ya sa ka bari aka haife ni?

Da ma na mutu tun kafin wani ya gan ni!

19 Da a ce daga cikin cikin mahaifiyata an wuce da ni zuwa kabari

Da ya fi mini kyau bisa ga kasancewata.

20 Raina bai kusa ƙarewa ba? A bar ni kawai!

Bari in ci moriyar lokacin da ya rage mini.

21 An jima kaɗan zan tafi, ba kuwa zan komo ba faufau,

Zan tafi ƙasa mai duhu, inda ba haske,

22 Ƙasa mai duhu, da inuwoyi da ɗimuwa

Inda ko haske ma kansa duhu ne.”