Categories
AYU

AYU 31

Ayuba Ya Tabbatar da Mutuncinsa

1 “Na yi alkawari da idanuna,

Me zai sa in ƙyafaci budurwa?

2 Wane rabo zan samu daga wurin Allah a Sama?

Wane gādo kuma zan samu daga wurin Mai Iko Dukka a can samaniya?

3 Yakan aika da masifa da lalacewa

Ga waɗanda suke aikata abin da ba daidai ba.

4 Allah ya san dukan abin da nake yi,

Yana ƙididdige dukan takawata.

5 “Idan ina tafiya da rashin gaskiya,

Ina hanzari don in aikata yaudara,

6 Bari Allah ya auna ni da ma’aunin da yake daidai,

Zai kuwa san mutuncina.

7 Idan dai na kauce daga hanya,

Ko kuwa zuciyata ta bi sha’awar idanuna,

Idan akwai ko ɗan sofane a hannuna,

8 To, bari in shuka, wani ya ci amfanin,

Bari a tumɓuke amfanin gonata.

9 “Idan na yi sha’awar wata mace,

Har na je na laɓe a ƙofar maƙwabcina,

10 To, bari matata ta yi wa wani abinci,

Bari waɗansu su kwana da ita.

11 Gama wannan mugun laifi ne ƙwarai,

Wanda alƙalai ne za su hukunta.

12 Za ta zama wuta mai ci har ta hallaka,

Za ta cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.

13 “Idan a ce ban kasa kunne ga kukan barorina mata da maza ba,

Sa’ad da suka kawo koke-kokensu a kaina,

14 To, wace amsa zan ba Allah sa’ad da ya tashi don ya hukuntar?

Me zan iya faɗa sa’ad da Allah ya zo yi mini shari’a?

15 Ashe, shi wanda ya halicce ni a cikin mahaifa,

Ba shi ne ya halicce su ba?

Shi wanda ya siffata mu a cikin mahaifa?

16 “Ban taɓa ƙin taimakon matalauta ba,

Ban kuma taɓa sa gwauruwar da mijinta ya mutu ta yi kuka ba,

17 Ko kuwa in bar marayu da yunwa sa’ad da nake cin abincina,

18 Tun suna yara nake goyonsu,

Ina lura da su kamar ‘ya’yan cikina.

19 “Amma idan na ga wani yana lalacewa saboda rashin sutura,

Ko wani matalauci marar abin rufa,

20 Idan a zuciyarsa bai sa mini albarka ba,

Ko bai ji ɗumi da ulun tumakina ba,

21 Ko na ɗaga hannuna don in cuci maraya,

Don na ga ina da kafar kuɓuta,

22 To, ka sa kafaɗuna su ɓaɓɓalle daga inda suke.

Ka kakkarya gwiwoyin hannuna.

23 Gama bala’i daga wurin Allah ya razanar da ni,

Saboda ɗaukakarsa ba zan iya yin kome ba.

24 “Idan na ce ga zinariya na dogara, ko zinariya tsantsa ita ce jigona,

25 Idan kuma saboda yawan dukiyata nake fariya,

Ko saboda abin da na mallaka ne,

26 Idan ga hasken rana nake zuba ido,

Ko ga hasken farin wata ne,

27 Zuciyata ta jarabtu ke nan a asirce,

Ni da kaina ina sumbatar hannuna,

28 Wannan ma zai zama laifi ne wanda alƙalai za su hukunta,

Gama na zama munafukin Allah Mai Iko Dukka ke nan.

29 “Idan na yi murna saboda wahala ta sami maƙiyana,

Ko na yi fariya saboda mugun abu ya same shi,

30 Ban yi zunubi da bakina ba,

Ban nemi ran wani ta wurin la’anta shi ba.

31 Ko mutanen da suke cikin alfarwata ba wanda zai ce,

Ga wani can da bai ƙoshi da nama ba.

32 Ban bar baƙi su kwana a titi ba,

Ƙofar gidana a buɗe take ga matafiya.

33 Idan na ɓoye laifofina a zuciyata,

34 Ko na tsaya shiru saboda tsoron taron jama’a,

Saboda kuma baƙar maganar mutane ta razanar da ni,

35 Da a ce ina da wanda zai kasa kunne gare ni,

Da sai in sa hannu a kan abin da na faɗa,

Allah kuwa Mai Iko Dukka ya amsa mini.

“Da ƙarar da maƙiyana suke kai ni, a rubuce ne,

36 Hakika da sai in ɗauke ta a kafaɗata,

In kuwa naɗa ta a kaina kamar rawani.

37 Da na ba Allah dukan lissafin abin da na taɓa yi,

In tinƙare shi kamar ni basarauce ne.

38 “Idan ƙasata tana kuka da ni,

Ita da kunyoyinta,

39 Ko na ci amfaninta ban biya ba,

Ko na yi sanadin mutuwar mai ita,

40 Ka sa ƙayayuwa su tsiro maimakon alkama,

Tsire-tsire marasa amfani kuma maimakon sha’ir.”

Maganar Ayuba ta ƙare.

Categories
AYU

AYU 32

Jawaban Elihu

1 Mutanen nan uku sun daina ba Ayuba amsa, saboda yana ganin kansa adali ne.

2 Sai Elihu, ɗan Barakel, mutumin Buz, daga cikin iyalin Arama, ya husata, yana fushi da Ayuba saboda ya baratar da kansa, bai bari Allah ya baratar da shi ba.

3 Yana kuma fushi da abokan nan uku na Ayuba, domin sun rasa amsar da za su ba Ayuba, ko da yake sun hurta Ayuba ne yake da laifi.

4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.

5 Sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da wata amsa da za su ba Ayuba, sai ya yi fushi.

6 Elihu ɗan Barakel, mutumin Buz, ya fara magana, ya ce,

“A shekaru dai ni yaro ne ku kuwa manya ne,

Don haka ina jin nauyi,

Ina kuma jin tsoro in faɗa muku ra’ayina.

7 Na ce wa kaina, ‘Ya kamata kwanaki su yi magana,

Yawan shekaru kuma su koyar da hikima.’

8 Amma Ruhun Allah Mai Iko Dukka ne wanda yake cikin mutum,

Yakan ba mutane basira.

9 Ba tsofaffi ne masu wayo ba,

Ba kuma masu yawan shekaru kaɗai yake gane abin da yake daidai ba.

10 Don haka na ce ku kasa kunne gare ni,

Bari in faɗa muku nawa ra’ayi.

11 “Ga shi, na dakata na ji maganarku,

Na kasa kunne ga maganarku ta hikima,

Tun kuna tunani a kan abin da za ku faɗa.

12 Na kasa kunne gare ku sosai,

Amma ko ɗaya ba wanda ya kā da Ayuba.

Ba kuma wanda ya ba shi amsar tambayarsa.

13 Ku lura kada ku ce kuna da hikima,

Allah ne kaɗai yake da iko ya kā da shi, ba mutum ba.

14 Ba da ni Ayuba yake magana ba,

Saboda haka ba zan amsa masa da irin amsarku ba.

15 “Abin ya cika musu ciki, ba su ƙara amsawa ba,

Wato ba su da ta cewa.

16 Ni kuma sai in tsaya don ba su ce kome ba?

Sun tsaya kurum, don ba su da ta cewa?

17 A’a, ni kuma zan ba da tawa amsa,

In kuma faɗi ra’ayina.

18 Cike nake da magana,

Ruhun da ka cikina ya iza ni.

19 Ga zuciya tana kama da ruwan inabin da ba shi da mafitar iska,

Kamar sabuwar salkar ruwan inabi wadda take shirin fashewa.

20 Tilas in yi magana don in huce,

Dole in ba da amsa.

21 Ba zan yi wa kowa son zuciya ba,

Ko kuma in yi wa wani fādanci.

22 Gama ni ban iya fādanci ba,

Idan na yi haka kuwa

Mahaliccina zai kashe ni nan da nan.”

Categories
AYU

AYU 33

Elihu Ya Tsauta wa Ayuba

1 “Amma yanzu, kai Ayuba, ka yarda ka ji maganata,

Ka kasa kunne ga dukan abin da zan faɗa.

2 Ga shi, na buɗe baki in yi magana.

3 Maganar da zan hurta ainihin gaskiyar da take a zuciyata ce,

Abin da zan faɗa kuma dahir ne.

4 Ruhun Allah ne ya yi ni, Mai Iko Dukka ya hura mini rai.

5 “Ka amsa mini, in ka iya,

Ka shirya abubuwan da za ka faɗa mini, ka yi tsaye a kansu.

6 Duba, ni da kai ɗaya muke a wajen Allah,

Dukanmu biyu kuma daga yumɓu aka siffata mu.

7 Don haka kada ka razana saboda ni,

Abin da zan faɗa maka, ba abin da zai fi ƙarfinka.

8 “Hakika na ji maganar da ka yi,

Na kuwa ji amon maganganunka,

9 Ka ce kai tsattsarka ne, ba ka da laifi,

Kai tsabtatacce ne, ba ka da wata ƙazanta.

10 Ka ce Allah ya zarge ka ya ɗauke ka tankar maƙiyansa,

11 Ya saka ka a turu,

Yana duban dukan al’amuranka.

12 “Amma a kan wannan, Ayuba, ka yi kuskure, zan ba ka amsa,

Gama Allah ya fi kowane mutum girma.

13 Me ya sa kake yi wa Allah gunaguni,

Cewa ba ya karɓar maganarka ko ɗaya?

14 Gama Allah yakan yi magana sau ɗaya ne,

I, har sau biyu, duk da haka mutum ba ya lura.

15 Yakan sanar a mafarkai ko a wahayi

Sa’ad da barci mai nauyi ya ɗauke su,

A sa’ad da suke barci a gadajensu.

16 Yakan buɗe kunnuwan mutane,

Ya tsorata su da faɗakarwarsa,

17 Domin ya kawar da su daga aikin da suke yi,

Ya kuma kawar musu da girmankai.

18 Yakan hana su zuwa kabari,

Ya hana ransu halaka da takobi.

19 “Akan hori mutum da cuta mai zafi a gadonsa,

Ya yi ta fama da azaba a cikin ƙasusuwansa,

20 Ransa yana ƙyamar abinci,

Yana ƙyamarsa kome daɗinsa kuwa.

21 Yakan rame ƙangayau, ƙasusuwansa duk a waje.

22 Yana gab da shiga kabari,

Ransa yana hannun mala’ikun mutuwa.

23 “Da a ce akwai wani mala’ika mai sulhuntawa a tsakani,

Ko da ɗaya daga cikin dubu ne wanda zai faɗa wa mutum,

24 Mala’ikan da zai yi masa alheri ya ce,

‘Ka cece shi daga gangarawa zuwa cikin kabari,

Na sami abin da zai fanshe shi!’

25 Naman jikinsa zai koma kamar na saurayi,

Zai komo kamar lokacin da yake gaɓar ƙarfinsa.

26 Sa’an nan ne mutum zai yi addu’a ga Allah, ya karɓe shi,

Ya zo gabansa da murna,

Allah zai komar wa mutum da adalcinsa.

27 Zai raira waƙa a gaban jama’a, ya ce, ‘Na yi zunubi. Ban yi daidai ba,

Amma ba a sa ni in biya ba.

28 Allah ya fanshe ni daga gangarawa zuwa kabari,

Raina kuwa zai ga haske.’

29 “Ga shi kuwa, Allah ya yi dukan waɗannan abubuwa sau biyu, har ma sau uku ga mutum,

30 Don ya komo da ran mutum daga kabari,

Domin a haskaka shi da hasken rai.

31 “Haba Ayuba, ka kula fa, ka kasa kunne,

Ga abin da nake faɗa,

Ka yi shiru, zan yi magana.

32 Amma idan kana da ta cewa, to, amsa,

Yi magana, gama ina so in kuɓutar da kai.

33 In kuwa ba haka ba, sai ka yi shiru,

Ka kasa kunne gare ni,

Zan kuwa koya maka hikima.”

Categories
AYU

AYU 34

Elihu ya ga Allah ya yi Daidai

1 Elihu ya ci gaba.

2 “Ku mutane masu hikima, ku ji maganata,

Ku kasa kunne ga abin da zan faɗa, ku masana.

3 Kunne yake rarrabewa da magana,

Kamar yadda harshe yake rarrabewa da ɗanɗanar abinci.

4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai,

Bari kuma mu daidaita abin da yake mai kyau tsakanin junanmu.

5 Gama Ayuba ya ce, ‘Ni marar laifi ne,

Amma Allah ya ƙwace mini halaliyata.

6 Duk da rashin laifina an ɗauke ni a maƙaryaci,

Raunina ba ya warkuwa ko da yake ba ni da laifin kome.’

7 “Wane irin mutum ne kai, Ayuba,

Da kake shan raini kamar yadda kake shan ruwa,

8 Wanda yake cuɗanya da ƙungiyar masu aikata laifi,

Kana yawo tare da mugaye?

9 Gama ka ce, ‘Bai amfana wa mutum kome ba

Ya yi murna da Allah.’

10 “Saboda haka ku kasa kunne gare ni, ku da kuke haziƙai,

Sam, Allah ba mai aikata mugunta ba ne,

A wurin Mai Iko Dukka ba kuskure,

11 Gama bisa ga aikin mutum yake sāka masa,

Yana sa aniyarsa ta bi shi.

12 Gaskiya ce, Allah ba zai aikata mugunta ba,

Mai Iko Dukka ba zai kauce wa adalci ba.

13 Wa ya shugabantar da shi a kan duniya?

Wa ya mallakar masa da duniya duka?

14 Da zai amshe ruhu da numfashin da ya hura wa mutum,

15 Da duk mai rai ya halaka,

Mutum kuma ya koma ƙura.

16 “Idan kai haziƙi ne, to, ji wannan,

Kasa kunne ga abin da zan faɗa.

17 Da Allah maƙiyin adalci ne, da ya yi mallaka?

Ka iya sa wa Adali, Mai Iko Dukka laifi?

18 Ka iya sa wa Allah laifi,

Shi da ya ce, ‘Sarki marar amfani ne,

Hakimai kuma mugaye’?

19 Ba ya nuna sonkai ga sarakuna,

Ko kuma ya fi kulawa da attajira fiye da matalauta,

Gama shi ya halicce su duka.

20 Sukan mutu nan da nan,

Da tsakar dare manya da ƙanana sukan shuɗe farat ɗaya,

An kawar da su ba da hannun mutum ba.

21 “Gama yana ganin al’amuran mutum,

Yana kuma ganin dukan manufarsa.

22 Ba wani duhu, ko duhu baƙi ƙirin

Inda masu aikata mugunta za su ɓuya.

23 Ba ajiyayyen lokacin da ya ajiye wa kowane mutum

Da zai je shari’a a gaban Allah.

24 Yakan ragargaza ƙarfafa ba tare da wani bincike ba,

Ya sa waɗansu a madadinsu.

25 Saboda sanin ayyukansu,

Yakan kaɓantar da su da dare ya ragargaza su,

26 Yakan buge su a gaban mutane saboda muguntarsu,

27 Don sun daina binsa, ba su kula da ko ɗaya

Daga cikin umarnansa ba.

28 Suka sa matalauta su yi kuka ga Allah,

Ya kuwa ji kukan waɗanda ake tsananta wa.

29 Idan Allah zai yi shiru, da wa zai sa wa wani laifi?

Idan ya ɓoye fuskarsa, wa zai iya ganinsa,

Ko aka yi wa al’umma ko ga mutum?

30 Bai kamata marar tsoron Allah ya yi mulki ba,

Don kada ya tura jama’a cikin tarko.

31 “Akwai wanda zai ce wa Allah, ‘Ni horarre ne,

Ba zan ƙara yin laifi ba?

32 Ka koya mini abin da ban sani ba,

Idan na yi laifi, ba zan ƙara yi ba.’

33 Zai kuɓutar domin ya gamshe ka saboda ka ƙi yarda?

Tilas kai za ka zaɓa, ba ni ba,

Saboda haka sai ka hurta abin da ka sani.

34 “Haziƙan mutane da mutum mai hikima da suka ji ni za su ce,

35 ‘Ayuba yakan yi magana ne ba tare da sanin abin da yake yi ba,

Maganarsa ba ta mai hangen nesa ba ce.

36 Da ma a gwada Ayuba har ƙarshe,

Saboda amsar da yake bayarwa ta mugaye.

37 Gama ya ƙara zunubinsa da tayarwa,

Yana tafa hannunsa a tsakaninmu,

Yana yawaita maganganunsa gāba da Allah.’ ”

Categories
AYU

AYU 35

1 Elihu kuwa ya yi magana.

2 “Ayuba, ba daidai ba ne, ka ce,

Ba ka yi laifi a gaban Allah ba,

3 Ka kuwa ce, ‘Wace riba na ci?

Wane fifiko nake da shi fiye da idan na yi zunubi?’

4 Zan ba ka amsa, kai da abokanka.

5 Ka duba sama,

Ka dubi gizagizai waɗanda suke can sama da kai.

6 Idan ka yi zunubi, da me ka cuci Allah?

Idan ka aikata laifofi da yawa, wace cuta ka yi masa?

7 Idan kai adali ne da me ka ƙara masa,

Ko kuwa me ya samu daga gare ka?

8 Muguntarka ta shafi mutum ne kamarka,

Haka kuma adalcinka ya shafi ɗan adam ne kawai.

9 “Saboda yawan zalunci, jama’a sukan yi kuka,

Suka nemi taimako, saboda matsin masu ƙarfi.

10 Amma ba su juyo wurin Allah Mahaliccinsu ba,

Wanda yakan sa a raira waƙa da dare,

11 Wanda yake koya mana fiye da namomin jeji da suke a duniya,

Wanda ya sa muka fi tsuntsayen sama hikima.

12 Suka yi kira don taimako, amma Allah bai amsa ba,

Saboda suna da girmankan mugaye.

13 Hakika Allah bai ji holoƙon kukansu ba,

Allah Mai Iko Dukka kuwa bai kula da shi ba.

14 “Ayuba, kai wane ne da za ka ce ba ka gan shi ba?

Da kake cewa ƙararka tana gabansa,

Jiransa kake yi?

15 Yanzu fa saboda bai yi hukunci da fushinsa ba,

Kamar kuma bai kula da laifi ba,

16 Ayuba, maganarka marar ma’ana ce,

Ka yi ta maganganu marasa hikima.”

Categories
AYU

AYU 36

Elihu Ya Ɗaukaka Girman Allah

1 Elihu ya ci gaba da magana.

2 “Ka yi mini haƙuri kaɗan, ni kuwa zan nuna maka,

Gama har yanzu ina da abin da zan faɗa in kāre Allah.

3 Zan tattaro ilimina daga nesa,

In bayyana adalcin Mahaliccina.

4 Gaskiya nake faɗa ba ƙarya ba,

Wanda yake da cikakken sani yana tare da kai.

5 “Ga shi kuwa, Allah Mai Girma, ba ya raina kowa,

Shi mai girma ne, mai cikakkiyar basira.

6 Ba ya rayar da masu laifi,

Amma yakan ba waɗanda ake tsananta wa halaliyarsu.

7 Yakan kiyaye waɗanda suke aikata gaskiya,

Yakan kafa su har abada tare da sarakuna,

A gadon sarauta, ya ɗaukaka su.

8 Amma idan aka ɗaure su da sarƙoƙi,

Da kuma igiyar wahala,

9 Sa’an nan yakan sanar da su aikinsu

Da laifofin da suke yi na ganganci.

10 Yakan sa su saurari koyarwa,

Da umarnai, cewa su juya, su bar mugunta.

11 Idan suka kasa kunne suka bauta masa,

Za su cika kwanakinsu da wadata,

Shekarunsu kuma da jin daɗi.

12 Amma idan ba su kasa kunne ba,

Za a hallaka su da takobi,

Su mutu jahilai.

13 “Waɗanda ba su da tsoron Allah a zuciyarsu,

Suna tanada wa kansu fushi,

Ba su neman taimako sa’ad da ya ɗaure su.

14 Sukan yi mutuwar ƙuruciya,

Sukan ƙare kwanakinsu da kunya.

15 Zai kuɓutar da waɗanda suke shan tsanani,

Ta wurin tsananin da suke sha,

Yakan buɗe kunnuwansu ta wurin shan wahala.

16 Allah ya tsamo ka daga cikin wahala,

Ya kawo ka yalwataccen wuri inda ba matsi,

Abincin da aka yi na addaras aka jera maka a kan tebur.

17 “Ka damu ƙwarai don ka ga an hukunta mugaye,

Amma hukunci da adalci sun kama ka.

18 Ka lura kada ka bar hasalarka ta sa ka raina Allah,

Kada kuma ka bar wahalar da kake sha ta sa ka ɓata da mai fansarka.

19 Kukanka ya iya raba ka da wahala,

Ko kuwa dukan ƙarfin da kake da shi?

20 Kada ka ƙosa dare ya yi,

Domin a lokacin nan ne mutane sukan watse,

Kowa ya kama gabansa.

21 Ka lura kada ka rinjayu a kan aikata mugunta,

Gama saboda haka kake shan wannan tsanani,

Don a tsare ka daga aikata mugunta.

22 “Duba, Allah Maɗaukaki ne cikin ikonsa,

Wa ya iya koyarwa kamarsa?

23 Ba wanda zai iya tsara wa Allah abin da zai yi,

Wa ya isa ya ce masa ya yi kuskure?

24 “Ka tuna ka girmama aikinsa,

Wanda mutane suke yabo.

25 Dukan mutane sun ga ayyukansa,

Sun hango shi daga nesa.

26 Ga shi kuwa, Allah Maɗaukaki ne,

Ba mu kuwa san iyakar ɗaukakarsa ba,

Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.

27 “Allah yakan sa ruwa ya zama tururi,

Ya maishe shi ruwan sama,

28 Wanda yakan kwararo daga sama,

Ya zubo wa ɗan adam a yalwace.

29 Wa zai iya gane yadda gizagizai suke shimfiɗe a sararin sama,

Da tsawar da ake yi a cikinsu?

30 Ga shi, yakan baza waƙiya kewaye da shi,

Yakan rufe ƙwanƙolin duwatsu.

Zurfin teku yana nan da duhunsa.

31 Gama ta haka yakan shara’anta mutane,

Yakan ba da abinci a yalwace.

32 Ya cika hannunsa da walƙiya,

Yakan sa ta faɗa a kan abin da ya bārata.

33 Tsawarta tana nuna kasancewar Allah,

Ko shanu sun san da zuwan hadiri.”

Categories
AYU

AYU 37

1 “Saboda wannan zuciyata takan kaɗu,

Kamar ta yi tsalle daga inda take.

2 Ku kasa kunne ga tsawar muryarsa,

Ku saurara ga maganarsa mai ƙarfi.

3 Yakan sako ta a ƙarƙashin samaniya duka,

Walƙiyarsa takan zagaya dukan kusurwoyin duniya.

4 Bayan walƙiyar akan ji rugugin muryarsa,

Ya yi tsawa da muryarsa ta ɗaukaka,

Ko da yake an ji muryarsa bai dakatar da tsawar ba.

5 Muryar tsawar Allah mai banmamaki ce,

Yana aikata manyan abubuwa da suka fi ƙarfin ganewarmu.

6 Yakan umarci dusar ƙanƙara ta fāɗo bisa duniya,

Yayyafi da ruwan sama kuwa su yi ƙarfi.

7 Yakan tsai da kowane mutum daga aikinsa,

Domin dukan mutane su san aikinsa.

8 Namomin jeji sukan shiga wurin kwanciyarsu,

Su yi zamansu a ciki.

9 Guguwa takan taso daga inda take,

Sanyi kuma daga cikin iska mai hurawa.

10 Numfashin Allah yakan sa ƙanƙara,

Yakan sa manyan ruwaye su daskare farat ɗaya.

11 Yakan cika girgije mai duhu da ruwa,

Gizagizai sukan baza walƙiyarsa.

12 Sukan yi ta kewayawa ta yadda ya bishe su,

Don su cika dukan abin da ya umarce su a duniya da ake zaune a ciki.

13 Allah yakan aiko da ruwan sama ya shayar da duniya,

Saboda tsautawa, ko saboda ƙasa, ko saboda ƙauna.

14 “Ka ji wannan, ya Ayuba,

Tsaya ka tuna da ayyukan Allah masu banmamaki.

15 Koka san yadda Allah yakan ba su umarni,

Ya sa walƙiyar girgijensa ta haskaka?

16 Ko kuma ka san yadda gizagizai suke tsaye daram a sararin sama?

Ayyukan banmamaki na Allah, cikakken masani!

17 Ko ka san abin da yake sa ka jin gumi

Sa’ad da iskar kudu take hurowa?

18 Ka iya yin yadda ya yi,

Kamar yadda ya shimfiɗa sararin sama daram,

Kamar narkakken madubi?

19 Ka koya mana abin da za mu faɗa masa,

Ba za mu iya gabatar da ƙararrakinmu ba, gama mu dolaye ne.

20 A iya faɗa masa, cewa zan yi magana?

Mutum ya taɓa so a haɗiye shi da rai?

21 “A yanzu dai mutane ba su iya duban haske,

Sa’ad da yake haskakawa a sararin sama,

Bayan da iska ta hura ta share gizagizai sarai.

22 Daga arewa wani haske kamar na zinariya ya fito mai banmamaki,

Allah yana saye da ɗaukaka mai bantsoro.

23 Mai Iko Dukka, ya fi ƙarfin ganewarmu,

Shi mai girma ne, da iko, da gaskiya,

Da yalwataccen adalci,

Ba ya garari.

24 Saboda haka mutane suke tsoronsa,

Bai kula da waɗanda suke ɗaukar kansu su masu hikima ba ne.”

Categories
AYU

AYU 38

Ubangiji Ya Tabbatar da Jahilcin Ayuba

1 Ubangiji ya yi magana da Ayuba ta cikin guguwa.

2 “Wane ne wannan da yake ɓāta shawara

Da maganganu marasa ma’ana?

3 Ka tashi tsaye ka sha ɗamara kamar namiji,

Zan yi maka tambaya, kai kuwa ka ba ni amsa.

4 A ina kake sa’ad da na aza harsashin gina duniya?

Faɗa mini idan ka sani.

5 Wane ne ya zayyana kusurwoyinta?

Hakika ka sani.

Wane ne kuma ya auna ta?

6 A kan me aka kafa tushenta?

Wa ya aza dutsen kan kusurwarta?

7 Sa’ad da taurarin asuba suka raira waƙa tare,

Sai mala’iku duka suka yi sowa saboda murna.

8 “Wa ya yi wa teku iyaka

Sa’ad da ta tumbatso daga zurfafa?

9 Sa’ad da na suturta ta da gizagizai,

Na yi mata maɗauri da duhu ƙirin.

10 Na sa mata iyakoki,

Na sa mata ƙyamare da ƙofofi,

11 Na ce mata, ‘Iyakar inda za ki tsaya ke nan,

Ba za ki wuce ba.

Nan raƙuman ruwanki masu tumbatsa za su tsaya.’

12 “Ayuba, a dukan kwanakinka

Ka taɓa umartar wayewar gari,

Ko ka sa alfijir ya keto?

13 Da gari ya waye,

Ka kawar da muguntar da ake yi da dare?

14 Yakan sāke kamar lakar da take ƙarƙashin hatimi,

Yakan rine kamar riga.

15 Akan hana wa mugaye haske,

Sa’ad da sukan ɗaga hannuwansu sama akan kakkarya su.

16 “Ko ka taɓa shiga cikin maɓuɓɓugan teku?

Ka taɓa yin tafiya a cikin zurfin lallokin teku?

17 An taɓa nuna maka ƙofofin mutuwa?

Ko kuwa ka taɓa ganin ƙofofin duhu ƙirin?

18 Ko ka san iyakar fāɗin duniya?

Ka amsa mini in ka san dukan waɗannan.

19 “Ina hanya zuwa wurin da haske yake?

A ina kuma duhu yake?

20 Ka san iyakarsa ko mafarinsa?

21 Ka sani, gama a lokacin nan an haife ka,

Shekarunka kuwa suna da yawa.

22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara?

Ko kuwa ka taɓa shiga rumbunan ajiyar ƙanƙara?

23 Na adana su ne don lokacin wahala,

Domin ranar faɗa da ta yaƙi.

24 Ina hanya zuwa inda rana take fitowa,

Ko kuma ta inda iskar gabas take hurowa ta māmaye ko’ina?

25 “Wa ya haƙa hanyar da ruwan sama mai kwararowa zai bi?

Da kuma hanyar da gatarin aradu zai bi?

26 Wa ya kuma kawo ruwan sama a ƙasar da ba mutane,

Da a cikin hamada inda ba kowa,

27 Don a shayar da zozayar ƙasa inda ba kowa,

Har ta tsiro da ciyayi?

28 “Ruwan sama yana da mahaifi?

Wa ya haifi ɗiɗɗigar raɓa?

29 Wace ce mahaifiyar ƙanƙara?

Wace ce kuma ta haifi jaura?

30 Ruwa ya daskare ya yi ƙarfi kamar dutse,

Teku ta daskare.

31 “Za ka iya ɗaure sarƙoƙin kaza-da-‘ya’yanta?

Ko ka iya kwance igiyoyin mafarauci-da-kare-da-zomo?

32 Za ka iya bi da yaneyanen sararin sama bisa ga fasalinsu?

33 Ka san ka’idodin sammai?

Ko ka iya faɗar yadda suka danganta da duniya?

34 “Kana iya yi wa gizagizai tsawa,

Don su kwararo ruwan sama, ya rufe ka?

35 Ka iya aikar walƙiyoyi su tafi,

Sa’an nan su ce maka, ‘Ga mu mun zo?’

36 Wa ya sa hikima a gizagizai,

Ko kuma wa ya ba da ganewa ga kāsashi?

37 Akwai mai hikimar da zai iya ƙidaya gizagizai?

Ko kuwa wa zai iya karkato da salkunan ruwan sammai,

38 Sa’ad da ƙura ta murtuke ta taru jingim, ta game kam?

39 “Ka iya farauto wa zakoki abinci?

Ko ka ƙosar da yunwar sagarun zakoki,

40 Sa’ad da suke fako a kogwanninsu,

Ko suna kwance suna jira a maɓoyarsu?

41 Wa yake tanada wa hankaka abincinsa,

Sa’ad da ‘ya’yansa suke kuka ga Allah,

Suna kai da kawowa saboda rashin abinci?”

Categories
AYU

AYU 39

1 “Ka san lokacin da awakan dutse suke haihuwa?

Ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?

2 Ka san ko watanni nawa suke yi kafin su haihu?

Ka san lokacin haihuwarsu?

3 Ka san lokacin naƙudarsu, sa’ad da suke haihuwar ‘ya’yansu,

Lokacin da ‘ya’yansu suke fita cikinsu?

4 ‘Ya’yansu sukan yi ƙarfi su girma a fili cikin saura,

Sukan yi tafiyarsu ba su komawa wurin iyayensu.

5 “Wa ya bar jakin jeji ya yi yadda yake so?

Wa ya ɓalle dabaibayin jaki mai sauri,

6 Wanda na ba fili fetal ya zama gidansa,

Da ƙasa mai gishiri a wurin zamansa?

7 Yakan yi wa hayaniyar birane ba’a,

Ba ruwansa da tsawar masu kora.

8 Tsaunukan duwatsu ne wurin kiwonsa,

A can yake neman kowane ɗanyen abu.

9 “Kutunkun ɓauna zai yarda ya yi maka aiki?

Zai yarda ya kwana ɗaya a dangwalinka?

10 Ka iya ɗaure shi da igiya a kwarin kunya?

Ko kuwa zai yi maka kaftu a fadamarka?

11 Za ka dogara gare shi saboda tsananin ƙarfinsa?

Za ka kuma bar masa aikinka?

12 Ka gaskata zai komo,

Ya kawo maka hatsi a masussukarka?

13 “Jimina takan karkaɗa fikafikanta da alfarma!

Amma ba su ne gashin fikafikan ƙauna ba.

14 Jimina takan bar wa ƙasa ƙwayayenta,

Ta bar ƙasa ta ɗumama su.

15 Takan manta wani ya iya taka su su fashe,

Ya yiwu kuma wani naman jeji ya tattake su.

16 Takan yi wa ‘ya’yanta mugunta,

Sai ka ce ba nata ba ne,

Ko da yake ta sha wahala a banza,

Duk da haka ba ta damu ba.

17 Gama Allah bai ba ta hikima ba,

Bai kuwa ba ta fahimi ba.

18 Amma sa’ad da ta sheƙa a guje,

Takan yi wa doki maguji da mahayinsa dariya.

19 “Kai ka yi wa doki ƙarfinsa?

Kai ne kuma ka daje wuyansa da geza?

20 Kai ne ka sa shi tsalle kamar ɗango?

Kwarjinin firjinsa yana da bantsoro.

21 Yakan yi nishi a fadama,

Yana murna saboda ƙarfinsa,

A wurin yaƙi ba ya ja da baya, ba ya jin tsoron kibau.

22 Tsoro abin dariya ne a gare shi, bai damu ba.

Ba ya ba da baya ga takobi,

23 Kibau na ta shillo a kansa,

Māsu suna ta gilmawa a gabansa.

24 Da tsananin fushi da hasala yana kartar ƙasa,

Da jin ƙarar ƙaho, sai ya yi ta zabura.

25 Sa’ad da aka busa ƙaho yana ce, ‘Madalla.’

Yakan ji warin yaƙi daga nesa, da hargowar sarakunan yaƙi da ihunsu.

26 “Ta wurin hikimarka ne shirwa take tashi,

Ta buɗe fikafikanta ta nufi kudu?

27 Ta wurin umarninka ne gaggafa take tashi sama

Ta yi sheƙarta can ƙwanƙoli?

28 A kan dutse take zaune, a can take gidanta,

Cikin ruƙuƙin duwatsu.

29 Daga can takan tsinkayi abincinta

Idanunta sukan hango shi tun daga nesa.

30 ‘Yayanta sukan tsotsi jini,

A inda kisassu suke, can take.”

Categories
AYU

AYU 40

1 Ubangiji ya yi wa Ayuba magana.

2 “Mai neman sa wa wani laifi ya jā da Mai Iko Dukka?

Wanda yake gardama da Allah, bari ya ba da amsa.”

3 Ayuba ya amsa wa Ubangiji ya ce,

4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba,

Wace amsa zan ba ka?

Na rufe bakina na yi gam.

5 Ai, na riga na yi magana sau ɗaya, har ma sau biyu,

Ba zan amsa ba, ba zan ƙara cewa kome ba.”

Bayyanuwar Ikon Allah

6 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba daga cikin guguwa, ya ce,

7 “Tashi tsaye ka sha ɗamara kamar namiji,

Zan yi maka tambaya, kai kuwa ka ba ni amsa.

8 Kai kanka za ka sa mini laifi?

Za ka kā da ni don kai ka barata?

9 Kana da ƙarfi kamar na Allah?

Kana iya tsawa da murya kamar tasa?

10 “Ka caɓa ado da kwarjini da ɗaukaka,

Ka yafa daraja da maƙami.

11 Ka kwararar da rigyawar fushinka,

Ka dubi dukan wanda yake alfarma, a wulakance.

12 Ka dubi dukan wanda yake alfarma ka ƙasƙantar da shi,

Ka tattake mugaye a inda suke.

13 Dukansu ka binne su a ƙasa,

Ka ɗaure fuskokinsu, ka jefa su a lahira.

14 Sa’an nan ni kaina kuma zan sanar da kai,

Cewa da hannun damanka za ka yi nasara.

15 “Ga dorina wanda ni na halicce ta,

Kamar yadda na halicce ka,

Tana cin ciyawa kamar sa.

16 Ga shi, ƙarfinta yana cikin ƙugunta,

Ikonta yana cikin tsakar cikinta.

17 Na yi mata wutsiya miƙaƙƙiya, mai ƙarfi kamar itacen al’ul,

Jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe wuri ɗaya

18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne,

Gaɓoɓinta kamar sandunan ƙarfe ne.

19 “Ita ce ta farko cikin ayyukan Allah,

Sai Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkararta da takobi!

20 Gama duwatsu suke ba ta abinci,

A inda dukan namomin jeji suke wasa.

21 Takan kwanta a inuwar ƙaddaji,

Ta ɓuya a cikin iwa, da a fadama.

22 Gama inuwar da take rufe ta ta ƙaddaji ce,

Itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.

23 Ga shi, ba ta jin tsoron tumbatsar kogi,

A natse take, ko da ta bakinta rigyawar Urdun take wucewa.

24 Akwai wanda zai iya kama ta da ƙugiya,

Ko ya sa mata asirka?”