Categories
AYU

AYU 41

1 “Ka iya kama dodon ruwa da ƙugiyar kama kifi?

Ko kuma ka iya zarge harshensa da igiya?

2 Ka iya sa wa hancinsa asirka?

Ko ka iya huda muƙamuƙinsa da ƙugiya?

3 Zai ta yi maka godo?

Zai yi maka magana da tattausar murya?

4 Zai ƙulla alkawari da kai,

Cewa zai zama baranka har abada?

5 Za ka yi wasa da shi kamar yadda za ka yi da tsuntsu?

Ko za ka ɗaure shi da tsarkiya domin barorinka mata?

6 ‘Yan kasuwa za su saye shi?

Za su karkasa shi ga fatake?

7 Za ka iya huhhuda fatarsa da zaguna?

Ko kuwa kansa da māsu?

8 In ka kama shi, ka daɗe kana tunawa da yaƙin da ba za ka ƙara marmarin yi ba!

9 Ba ma amfani a yi ƙoƙarin kama shi,

Tunanin yin haka ma abin tsoro ne.

10 Ba wani mai zafin hali da zai kuskura ya tsokane shi.

Wane ne wannan da zai iya tsayawa a gabana?

11 Wa ya ba ni har da zan biya shi?

Dukan abin da yake cikin duniyan nan nawa ne.

12 “Ba zan yi shiru a kan zancen gaɓoɓinsa ba,

Ko babban ƙarfinsa, ko kyan ƙirarsa.

13 Wa zai iya yaga babbar rigarsa?

Ko kuwa ya kware sulkensa da aka ninka biyu?

14 Wa zai iya buɗe leɓunansa?

Gama haƙoransa masu bantsoro ne.

15 An yi gadon bayansa da jerin garkuwoyi ne,

An haɗa su daɓa-daɓa kamar an liƙe.

16 Suna haɗe da juna gam,

Ko iska ba ta iya ratsa tsakaninsu.

17 Sun manne da juna har ba su rabuwa.

18 Atishawarsa takan walƙata walƙiya,

Idanunsa kuma kamar ketowar alfijir.

19 Harsunan wuta kamar jiniya suna fitowa daga bakinsa,

Tartsatsin wuta suna ta fitowa.

20 Hayaƙi na fita daga hancinsa

Kamar tururi daga tukunya mai tafasa,

Ko bāgar da ta kama wuta.

21 Numfashinsa yakan kunna gawayi,

Harshen wuta yana fita daga bakinsa.

22 A wuyansa ƙarfi yake zaune,

Razana tana rausaya a gabansa.

23 Namansa yana ninke, manne da juna,

Gama ba ya motsi.

24 Zuciyarsa tana da ƙarfi kamar dutse,

Ƙaƙƙarfa kamar dutsen niƙa.

25 Sa’ad da ya miƙe tsaye, ƙarfafa sukan tsorata,

Su yi ta tutturmushe juna.

26 Ko an sare shi da takobi,

Ko an nashe shi da māshi ko hargi, ko an jefe shi,

Ba sa yi masa kome.

27 Kamar ciyawa baƙin ƙarfe yake a gare shi,

Tagulla ma kamar ruɓaɓɓen itace take.

28 Kibiya ba za ta sa ya gudu ba,

Jifar majajjawa a gare shi kamar jifa da tushiyoyi ce.

29 A gare shi kulake kamar tushiyoyi ne,

Kwaranniyar karugga takan ba shi dariya.

30 Kaifin ƙamborin cikinsa kamar tsingaro ne.

Yana jan ciki a cikin laka kamar lular ƙarfe.

31 Yakansa zurfafa su tafasa kamar tukunya,

Teku kuwa kamar kwalabar man shafawarsa.

32 Idan yana wucewa sai a ga hasken dārewar ruwa,

Yakansa zurfafa su yi kumfa.

33 A duniya ba kamarsa,

Taliki ne wanda ba shi da tsoro.

34 Yakan dubi kowane abu da yake mai alfarma,

Shi sarki ne a bisa dukan masu girmankai.”

Categories
AYU

AYU 42

Ayuba Ya Tuba aka kuma Karɓe Shi

1 Ayuba ya amsa wa Ubangiji.

2 “Na sani kai kake da ikon yin dukan abu,

Ba wanda ya isa ya hana ka yin abin da ka nufa.

3 Wane ne wannan marar ilimi da zai ɓoye shawara?

Saboda haka na hurta abin da ban gane ba,

Abubuwa waɗanda ban gane ba suna banmamaki ƙwarai.

4 Ka ce, ‘Kasa kunne, zan yi magana da kai,

Zan yi maka tambaya, ka ba ni amsa.’

5 Dā jin labarinka nake,

Amma yanzu na gan ka ido da ido.

6 Saboda haka na ga ni ba kome ba ne,

Na tuba, ina hurwa da ƙura da toka.”

Ƙarshen Magana

7 Bayan da Ubangiji ya gama faɗa wa Ayuba waɗannan magana, sai ya ce wa Elifaz, mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokan nan naka biyu, gama ba ku faɗi gaskiya game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.

8 Yanzu fa, sai ku kama bijimai bakwai da raguna bakwai, ku kai wa Ayuba, ku miƙa su hadaya ta ƙonawa domin kanku. Ayuba zai yi addu’a dominku, ni kuwa zan amsa addu’arsa don kada in sāka muku bisa ga wautarku. Gama ba ku faɗi gaskiya game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.”

9 Sai Elifaz mutumin Teman, da Bildad mutumin Shuwa, da Zofar mutumin Na’ama suka tafi suka yi kamar yadda Ubangiji ya faɗa musu, Ubangiji kuwa ya karɓi addu’ar Ayuba.

Allah Ya Mayar wa Ayuba da Wadatarsa

10 Ubangiji kuwa ya mayar wa Ayuba da dukiyarsa, sa’ad da ya yi addu’a domin abokansa, sai Ubangiji ya mayar masa da riɓin abin da yake da shi dā.

11 Sa’an nan dukan ‘yan’uwan Ayuba mata da maza da dukan waɗanda suka san shi a dā, suka zo gidansa suka ci abinci tare da shi, suka yi juyayin abin da ya same shi, suka ta’azantar da shi,saboda dukan wahalar da Ubangiji ya aukar masa. Kowannensu ya ba shi ‘yan kuɗi da zoben zinariya.

12 Ubangiji ya sa wa wannan zamani na Ayuba albarka, har fiye da na farko. An ba shi tumaki dubu goma sha huɗu (14,000), da raƙuma dubu shida (6,000), da takarkari dubu biyu (2,000), da jakai mata dubu ɗaya (1,000).

13 Ya kuma haifi ‘ya’ya maza bakwai, mata uku.

14 Ya raɗa wa ta farin suna Yemima, da ta biyun Keziya,da ta ukun Keren-Haffuk.

15 Duk ƙasar ba ‘yan mata kyawawa kamar ‘ya’yan Ayuba. Mahaifinsu kuwa ya ba su gādo tare da ‘yan’uwansu maza.

16 Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba’in bayan wannan, ya ga ‘ya’yansa, ya ga jikokin jikokinsa har tsara ta huɗu.

17 Sa’an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.