Categories
IRM

IRM 1

Kiran Irmiya da Keɓewarsa

1 Maganar Irmiya ɗan Hilkiya ke nan, na cikin firistocin da suke a Anatot, a yankin ƙasar Biliyaminu,

2 wanda Ubangiji ya yi masa magana a zamanin Yosiya ɗan Amon, Sarkin Yahuza, a shekara ta goma sha uku ta mulkinsa,

3 da a zamanin Yehoyakim ɗan Yosiya Sarkin Yahuza kuma, har ƙarshen shekara ta goma sha ɗaya ta Zadakiya ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, har zuwa lokacin da aka kai mazaunan Urushalima zaman talala a wata na biyar.

4 Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,

5 “Na san ka tun kafin a yi cikinka,

Na keɓe ka tun kafin a haife ka,

Na sa ka ka zama annabi ga

al’ummai.”

6 Sai na ce, “Ya Ubangiji Allah!

Ban san abin da zan faɗa ba,

Gama ni yaro ne.”

7 Amma Ubangiji ya ce mini,

“Kada ka ce kai yaro ne,

Kai dai ka tafi wurin mutanen da zan

aike ka,

8 Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da

kai,

Zan kiyaye ka.

Ni Ubangiji na faɗa.”

9 Sa’an nan Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina, ya ce mini,

“Ga shi, na sa maganata a bakinka.

10 Ga shi, a wannan rana na ba ka iko a

kan al’ummai da mulkoki,

Don ka tumɓuke, ka rusar,

Ka hallakar, ka kaɓantar,

Ka gina, ka dasa.”

11 Sai Ubangiji ya tambaye ni, ya ce, “Irmiya, me ka gani?”

Na amsa, na ce, “Sandan itacen almond.”

12 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Ka gani sosai, gama zan lura da maganata don in cika ta.”

13 Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce, “Me kuma ka gani?”

Na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, daga wajen arewa kamar za ta jirkice wajen kudu.”

14 Sai Ubangiji ya ce mini, “Daga wajen arewa masifa za ta fito ta auka wa dukan mazaunan ƙasar.

15 Ga shi kuwa, ina kiran dukan kabilan mulkokin arewa, za su kuwa zo su kafa gadajen sarautarsu a ƙofofin Urushalima, su kewaye dukan garukanta da dukan sauran biranen Yahuza.

16 Zan hurta hukuncin da zan yi musu saboda dukan muguntarsu, da suka bar bina, suka ƙona turare ga gumaka, suka kuma bauta wa gumakan da suka yi.

17 Amma kai, ka tashi ka sha ɗamara, ka faɗa musu dukan abin da na umarce ka. Kada ka ji tsoronsu domin kada in tsoratar da kai a gabansu.

18 Ni kuwa, ga shi, yau na maishe ka birni mai kagara, da ginshiƙin ƙarfe, da bangon tagulla ga dukan ƙasar, da sarakunan Yahuza, da shugabanninta, da firistocinta, da mutanen ƙasar.

19 Za su yi gāba da kai, amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, ni Ubangiji na faɗa.”

Categories
IRM

IRM 2

Ubangiji Ya Ji da Isra’ila da Masu Ridda

1 Ubangiji ya ce mini,

2 in tafi in yi shelar abin da Ubangiji ya ce a kunnen Urushalima, in ce,

“Na tuna da amincinki a lokacin

ƙuruciyarki,

Da ƙaunarki kamar ta amarya da

ango.

Yadda kika bi ni a cikin jeji, da a

ƙasar da ba a shuka ba.

3 Isra’ila tsattsarka ce ta Ubangiji,

Nunar fari ta girbina.

Dukan waɗanda suka ci daga cikinki

sun yi laifi,

Masifa za ta auko miki.

Ni Ubangiji, na faɗa.”

4 Ku ji jawabin Ubangiji, ku zuriyar Yakubu, ku dukan kabilan Isra’ila.

5 Ubangiji ya ce,

“Wane laifi ne na yi wa kakanninku,

Da suka bar bina?

Suka bauta wa gumaka marasa

amfani,

Su kuma suka zama marasa amfani.

6 Ba su kula da ni ba,

Ko da yake na cece su daga ƙasar

Masar.

Na bi da su a cikin hamada,

A ƙasa mai tuddai da kwazazzabai,

Busasshiya mai yawan hatsari,

Ba a bi ta cikinta,

Ba wanda yake zama cikinta kuma.

7 Na kawo su zuwa ƙasa mai dausayi,

Don su more ta su ci amfaninta,

Amma da suka shiga, sun ƙazantar

mini da ita,

Suka sa ƙasar da na gādar musu ta

zama abar ƙyama.

8 Firistoci kuma ba su ce, ‘Ina Ubangiji

Yake?’ ba.

Masanan shari’a ba su san ni ba.

Masu mulki sun yi mini laifi,

Annabawa sun yi annabci da sunan

Ba’al,

Sun bi waɗansu abubuwa marasa

amfani.”

Shari’ar da Ubangiji yake Yi wa Mutanensa

9 “Domin haka, ni Ubangiji zan

gabatar da ku gaban shari’a,

Ku da ‘ya’yanku, da ‘ya’yan

‘ya’yanku, wato jikokinku.

10 Ku haye zuwa tsibirin Kittim wajen

yamma, ku gani,

Ku aika zuwa Kedar wajen gabas, ku

duba da kyau,

A dā an taɓa yin wani abu haka?

11 Akwai wata al’umma da ta taɓa

sāke gumakanta

Ko da yake su ba kome ba ne?

Amma mutanena sun sauya darajarsu

da abin da ba shi da rai.

12 Sammai, ku girgiza saboda wannan,

ku razana,

Ku yi shiru, ni Ubangiji na faɗa.

13 Mutanena sun yi zunubi iri biyu,

Sun rabu da ni, ni da nake

maɓuɓɓugar ruwan rai,

Sun haƙa wa kansu tafkunan ruwa,

hudaddu,

Waɗanda ba za su iya ajiye ruwa ba.

14 “Isra’ila ba bawa ba ne, ba a kuma

haife shi bawa ba,

Amma me ya sa ya zama ganima?

15 Zakuna suna ruri a kansa,

Suna ruri da babbar murya.

Sun lalatar da ƙasarsa,

Garuruwansa sun lalace,

Ba wanda yake zaune cikinsu.

16 Mutanen Memfis kuma da na

Tafanes sun fasa ƙoƙwan kansa.

17 Ya Isra’ila, kai ne ka jawo wa kanka

wannan,

Da ka rabu da Ubangiji Allahnka,

Sa’ad da ya bishe ka a hanya.

18 Wace riba ka samu, har da ka tafi

Masar,

Don ka sha ruwan Kogin Nilu?

Wace riba ka samu, har da ka tafi

Assuriya,

Don ka sha ruwan Kogin

Yufiretis?

19 Muguntarka za ta hore ka,

Riddarka kuma za ta hukunta ka.

Sa’an nan za ka sani, ka kuma

gane,

Ashe, mugun abu ne, mai ɗaci, a gare

ka

Ka rabu da Ubangiji Allahnka,

Ba ka tsorona a zuciyarka.

Ni Ubangiji, Allah Mai Runduna na

faɗa.”

Isra’ila Ya Ƙi Yi wa Ubangiji Biyayya

20 “Ya Isra’ila, tun da daɗewa, ka ƙi

yarda

Ubangiji ya mallake ka,

Ka ƙi yin biyayya da ni,

Ka kuwa ce, ‘Ba zan yi bauta ba.’

Amma ka yi karuwanci a kan

kowane tudu,

Da kowane ɗanyen itace.

21 Na dasa ka kamar zaɓaɓɓiyar

kurangar inabi, zaɓaɓɓen iri mafi

kyau.

Ta yaya ka lalace haka ka zama

rassan kurangar inabi ta jeji,

Waɗanda ba zan yarda da su ba?

22 Ko da za ka yi wanka da sabulun

salo,

Ka yi amfani da sabulu mai yawa,

Duk da haka zan ga tabban

zunubanka.

Ni Ubangiji Allah na faɗa.

23 Ƙaƙa za ka ce ba ka ƙazantar da

kanka ba,

Ba ka taɓa bin gunkin nan Ba’al ba?

Ka duba hanyarka ta zuwa cikin

kwari, ka san abin da ka yi.

Kana kama da taguwa, mai yawon

neman barbara.

24 Kamar jakar jeji kake, wadda take

son barbara,

Wadda take busar iska,

Sa’ad da take son barbara, wa zai iya

hana ta?

Jakin da take sonta, ba ya bukatar

wahalar da kansa

Gama a watan barbararta za a same

ta.

25 Kai Isra’ila, kada ka bar ƙafafunka

ba takalma,

Kada kuma ka bar maƙogwaronka

ya bushe.

Amma ka ce, ‘Wannan ba amfani,

Gama na ƙaunaci baƙi, su kuwa

zan bi.’

26 “Kamar yadda ɓarawo yakan sha

kunya sa’ad da aka kama shi,

Haka nan mutanen Isra’ila za su sha

kunya,

Da su, da sarakunansu, da

shugabanninsu,

Da firistocinsu, da annabawansu.

27 Waɗanda suka ce wa itace, ‘Kai ne

mahaifinmu.’

Suna kuma ce wa dutse, ‘Kai, ka

haife mu.’

Gama sun ba ni baya, ba su fuskance

ni ba.

Amma sa’ad da suke shan wahala,

sukan ce,

‘Ka zo ka taimake mu.’

28 Ina gumakan da kuka yi wa

kanku?

Bari su tashi in sun iya cetonku

lokacin wahalarku.

Yahuza, yawan gumakanku sun kai

Yawan garuruwanku.

29 Ni Ubangiji, ina tambayarku, ‘Wace

ƙara kuke da ita game da ni?’

Kun yi mini tawaye dukanku.

30 Na hori ‘ya’yanku, amma a banza, ba

su horu ba,

Kun kashe annabawanku da takobi

kamar mayunwacin zaki.

31 Ya ku mutanen zamanin nan, ku

saurari maganata.

Na zamar wa Isra’ila jeji? Ko ƙasar

da take da kurama?

Don me fa mutanena suke cewa,

‘Mu ‘yantattu ne,

Ba za mu ƙara zuwa wurinka ba’?

32 Budurwa ta manta da kayan

kwalliyarta?

Ko kuwa amarya ta manta da kayan

adonta?

Amma mutanena sun manta da ni

kwanaki ba iyaka.

33 Kun sani sarai yadda za ku yi ku

farauci masoya,

Har mugayen mata ma, kun koya

musu hanyoyinku.

34 Tufafinku sun ƙasantu da jinin

marasa laifi,

Waɗanda ba ku same su suna fasa

gidajenku ba.

Amma duk da haka kuna cewa,

35 ‘Ba mu da laifi, hakika kuwa,

Ubangiji bai yi fushi da mu ba.’

Amma ni Ubangiji zan hukunta ku,

Domin kun ce ba ku yi zunubi ba.

36 Me ya sa ba ku da tsayayyiyar zuciya,

Sai ku yi nan ku yi can?

Masar za ta kunyata ku kamar yadda

Assuriya ta yi.

37 Da hannuwanku a kā za ku komo

daga Masar don kunya.

Gama waɗanda kuke dogara gare su,

ni Ubangiji, na ƙi su,

Ba za ku yi arziki tare da su ba.”

Categories
IRM

IRM 3

1 Ubangiji ya ce,

“Idan mutum ya saki matarsa,

Ta kuwa rabu da shi, har ta auri

wani,

Ya iya ya komo da ita?

Ashe, yin haka ba zai ƙazantar da

ƙasar ba?

Ya Isra’ila, kin yi karuwanci,

Abokan sha’anin karuwancinki, suna

da yawa.

Za ki sāke komowa wurina?

Ni, Ubangiji, na faɗa.

2 Ki ta da idonki, ki duba filayen

tuddai ki gani,

Akwai wurin da ba ki laɓe kin yi

karuwanci ba?

Kin yi ta jiran abokan sha’anin

karuwancinki a kan hanya,

Kamar Balaraben da yake fako a

hamada.

Kin ƙazantar da ƙasar da mugun

karuwancinki.

3 Saboda haka aka ƙi yin ruwa,

Ruwan bazara bai samu ba.

Goshinki irin na karuwa ne, ba ki jin

kunya.

4 “Yanzu kin ce, ‘Kai ne mahaifina,

Ka ƙaunace ni tun ina cikin

ƙuruciyata.

5 Za ka dinga yin fushi da ni?

Za ka husata da ni har abada?’

Ga shi, ke kika faɗa, amma ga shi,

kin aikata dukan muguntar da

kika iya yi.”

Dole Isra’ila da Yahuza su Tuba

6 A zamanin sarki Yosiya, Ubangiji ya ce mini, “Ka ga abin da take yi, ita marar amincin nan, wato Isra’ila? Yadda a kowane tudu mai tsayi, da a gindin kowane itace mai duhuwa, a wurare ne ta yi karuwancinta.

7 Na yi zaton bayan da ta aikata wannan duka, za ta komo wurina. Amma ba ta komo ba, maƙaryaciyar ‘yar’uwarta, wato Yahuza, ta gani.

8 Yahuza kuwa ta ga dukan karuwancin da marar amincin nan, Isra’ila ta yi, na sake ta, na ba ta takardar sarki. Amma duk da haka maƙaryaciyar ‘yar’uwan nan tata, Yahuza, ba ta ji tsoro ba, amma ita ma ta tafi ta yi karuwanci.

9 Domin karuwanci a wurinta abu ne mai sauƙi, ta ƙazantar da ƙasar. Ta yi karuwanci da duwatsu, da itatuwa.

10 Duk da haka maƙaryaciyar ‘yar’uwan nan tata, Yahuza ba ta juyo wurina da zuciya ɗaya ba, sai a munafunce, ni Ubangiji na faɗa.”

11 Ubangiji kuma ya faɗa mini, ko da yake Isra’ila ta bar binsa, duk da haka ta nuna laifinta bai kai na Yahuza marar aminci ba.

12 Ya ce mini in tafi wajen arewa in yi shela in ce,

“Ki komo ya Isra’ila, marar aminci,

Ni Ubangiji, na faɗa.

Domin ni mai jinƙai ne,

Ba zan yi fushi da ke ba.

Ba zan yi fushi da ke har abada ba,

Ni, Ubangiji na faɗa.

13 Ke dai ki yarda da laifinki,

Da kika yi wa Ubangiji Allahnki,

Kin kuma watsar da mutuncinki a

wurin baƙi

A gindin kowane itace mai duhuwa.

Kika ƙi yin biyayya da maganata,

Ni, Ubangiji, na faɗa.

14 “Ku komo, ya ku mutane marasa

aminci,

Gama ni ne Ubangijinku.

Zan ɗauki mutum guda daga kowane

gari,

In ɗauki mutum biyu daga kowane

iyali,

Zan komo da su zuwa Dutsen

Sihiyona.

15 Zan ba ku sarakuna waɗanda suke yi mini biyayya da hikima da fahimi.

16 Sa’ad da kuka yawaita a ƙasar, mutane ba za su ƙara yin magana a kan akwatin alkawari na Ubangiji ba. Ba za su ƙara yin tunaninsa ko su tuna da shi, ko su bukace shi, ko kuwa su yi wani irinsa ba.

17 In lokacin nan ya yi, za a kira Urushalima gadon sarautar Ubangiji, dukan sauran a’umma za su taru a Urushalima da sunana. Ba za su ƙara bin tattaurar zuciyarsu mai mugunta ba.

18 A waɗannan kwanaki mutanen Yahuza za su haɗu da mutanen Isra’ila. Tare za su zo daga ƙasar arewa zuwa cikin ƙasar da na ba kakanninku gādo.”

19 “Isra’ila, na yi niyya in karɓe ku

kamar ɗana,

In gādar muku da kyakkyawar

ƙasa

Mafi kyau a dukan duniya.

Na zaci za ku ce ni ne mahaifinku,

Ba za ku ƙara rabuwa da bina ba.

20 Hakika kamar yadda mace marar

aminci takan bar mijinta,

Haka kun zama marar aminci a gare

ni, ya jama’ar Isra’ila.

Ni Ubangiji, na faɗa.”

21 An ji murya a kan filayen tuddai,

Kūka da roƙo ne na ‘ya’yan

Isra’ila maza,

Domin sun rabu da hanyarsu,

Sun manta da Ubangiji Allahnsu.

22 “Ku juyo ku marasa aminci,

Zan warkar da rashin amincinku.”

“To, ga shi, mun zo gare ka,

Gama kai ne Ubangiji Allahnmu,

23 Daga kan tuddai ba mu da wani

taimako,

Ko daga hayaniyar da ake yi a kan

duwatsu,

Daga wurin Ubangiji Allahnmu ne

kaɗai taimakon Isra’ila yake

fitowa.

24 Amma yin sujada ga gunkin nan Ba’al ya cinye mana amfanin wahalar da kakanninmu suka sha tun muna yara, wato na garkunan tumakinsu, da na awakinsu, da na shanunsu, da ‘ya’yansu mata da maza.

25 Bari mu kwanta mu sha kunyarmu, bari kuma rashin kirkinmu ya rufe mu. Gama mun yi wa Ubangiji Allahnmu zunubi mu da kakanninmu, tun daga ƙuruciyarmu har zuwa yau, ba mu yi biyayya ga maganar Ubangiji Allahnmu ba.”

Categories
IRM

IRM 4

1 Ubangiji ya ce,

“Ya mutanen Isra’ila, idan za ku

juyo ku komo wurina,

Idan kuka kawar da abubuwan

banƙyama daga gabana,

Kuka kuma bar yin shakka,

2 Idan kun yi rantsuwa kuka ce,

‘Har da ran Ubangiji kuwa,‘

Da gaskiya, da aminci, da adalci,

Sa’an nan sauran al’umma za su so

in sa musu albarka,

Za su kuma yabe ni.”

3 Ubangiji ya ce wa mutanen Yahuza da na Urushalima,

“Ku kafce saurukanku,

Kada ku yi shuka cikin ƙayayuwa.

4 Ya ku mutanen Yahuza da na

Urushalima,

Ku yi wa kanku kaciya domin

Ubangiji,

Ku kawar da loɓar zukatanku

Don kada fushina ya fito kamar

wuta,

Ya cinye, ba mai iya kashewa,

Saboda mugayen ayyukan da kuka

aikata.”

Yahuza tana cikin Barazanar Yaƙi

5 “Ku yi shela a cikin Yahuza,

Ku ta da murya a Urushalima, ku

ce,

‘Ku busa ƙaho a dukan ƙasar!’

Ku ta da murya da ƙarfi, ku ce,

‘Ku tattaru, mu shiga birane masu

garu.’

6 Ku ta da tuta wajen Sihiyona!

Ku sheƙa a guje neman mafaka,

kada ku tsaya!

Gama zan kawo masifa da babbar

halaka daga arewa.

7 Zaki ya hauro daga cikin

ruƙuƙinsa,

Mai hallaka al’ummai ya kama

hanya,

Ya fito daga wurin zamansa don ya

mai da ƙasarku kufai,

Ya lalatar da biranenku, su zama

kango, ba kowa.

8 Domin haka sai ku sa tufafin

makoki,

Ku yi makoki ku yi kuka,

Gama fushin Ubangiji bai rabu da

mu ba.”

9 Ubangiji ya ce, “A ranan nan, sarki da sarakuna, za su rasa ƙarfin hali, firistoci za su firgita, annabawa kuwa za su yi mamaki.”

10 Sai na ce, “Kaito, kaito, ya Ubangiji Allah, ka ruɗi jama’an nan da Urushalima, da ka ce musu, ‘Za ku zauna lafiya,’ amma ga shi, takobi zai sassare su.”

11 Lokaci yana zuwa da za a faɗa wa mutanen Urushalima cewa, “Iska mai zafi za ta huro daga tuddan hamada zuwa wajen jama’ata, ba domin a sheƙe ta ko a rairaye ta ba!

12 Wannan iska da za ta zo daga wurin Ubangiji, tana da mafificin ƙarfi. Yanzu fa zan yanke hukunci a kansu.”

Abokan Gāba sun Kewaye Yahuza da Yaƙi

13 Duba, ga abokin gāba yana zuwa

kamar gizagizai,

Karusan yaƙinsa suna kama da

guguwa,

Dawakansa sun fi gaggafa sauri.

Kaitonmu, mun shiga uku!

14 Ya Urushalima, ki wanke mugunta

daga zuciyarki,

Domin a cece ki,

Har yaushe mugayen tunaninki za su

yi ta zama a cikinki?

15 Gama wata murya daga Dan ta

faɗa,

Ta kuma yi shelar masifar da za ta

fito daga duwatsun Ifraimu.

16 “A faɗakar da al’ummai, yana zuwa,

A faɗa wa Urushalima cewa,

‘Masu kawo mata yaƙi suna zuwa

daga ƙasa mai nisa,

Suna yi wa biranen Yahuza ihu.

17 Za su kewaye Yahuza kamar masu

tsaron saura,

Saboda ta tayar wa Ubangiji.’ Ni

Ubangiji na faɗa.

18 “Al’amuranki da ayyukanki suka

jawo miki wannan halaka,

Tana da ɗaci kuwa,

Ta soki har can cikin zuciyarki.”

Irmiya ya yi Baƙin Ciki don Mutanensa

19 Azaba! Ba zan iya daurewa da azaba

ba!

Zuciyata! Gabana yana faɗuwa da

ƙarfi,

Ba zan iya yin shiru ba,

Gama na ji amon ƙaho da hargowar

yaƙi.

20 Bala’i a kan bala’i,

Ƙasa duka ta zama kufai,

An lalatar da alfarwaina, ba zato ba

tsammani,

Labulena kuwa farat ɗaya.

21 Har yaushe zan yi ta ganin tuta,

In yi ta jin amon ƙaho?

22 Ubangiji ya ce,

“Mutanena wawaye ne,

Ba su san ni ba,

Yara ne dakikai,

Ba su da ganewa.

Suna gwanance da aikin mugunta,

Amma ba su san yadda za su yi

nagarta ba.”

23 Da na duba duniya sai na ga kufai ce

kawai ba kome,

Na kuma dubi sammai sai na ga ba

haske.

24 Da na duba duwatsu, sai na ga suna

makyarkyata,

Dukan tuddai kuma suna rawar jiki,

su yi gaba su yi baya.

25 Na duba sai na ga ba ko mutum

ɗaya,

Dukan tsuntsaye kuma sun tsere.

26 Na duba, sai na ga ƙasa mai dausayi

ta zama hamada,

An mai da dukan biranenta

kangwaye

A gaban Ubangiji saboda zafin

fushinsa.

27 Gama Ubangiji ya ce, “Ƙasar duka za ta zama kufai, amma duk da haka, ba wannan ne zai zama ƙarshenta na har abada ba.

28 Duniya za ta yi makoki saboda

wannan,

Sammai za su duhunta,

Gama ni na faɗa, haka kuwa na nufa

in yi,

Ba zan ji tausayi ba,

Ba zan kuwa fāsa ba.”

29 Da jin motsin mahayan dawakai da

na maharba

Kowane gari zai fashe.

Waɗansu za su shiga kurama,

Waɗansu kuma su hau kan duwatsu.

Dukan birane za su fashe tas,

Ba wanda zai zauna a cikinsu.

30 Ya ke da kike kufai marar kowa,

Me kike nufi da kika ci ado da mulufi,

Kike caɓa ado da kayan zinariya,

Kika sa wa idanunki tozali ram?

Kin yi kwalliyarki a banza,

Abokan sha’anin karuwancinki sun

raina ki,

Ranki suke nema.

31 Na ji kuka kamar na mace wadda take

naƙuda,

Na ji nishi kamar na mace a lokacin

haihuwarta ta fari,

Na ji kukan ‘yar Sihiyona tana

kyakyari,

Tana miƙa hannuwanta tana cewa,

“Wayyo ni kaina, gama ina suma a

gaban masu kisankai!”

Categories
IRM

IRM 5

Zunubin Urushalima da Yahuza

1 “Ku bi titunan Urushalima ko’ina!

Ku dudduba ku lura!

Ku bincika kowane dandali, ku gani,

Ko za ku iya samun ko mutum ɗaya

Mai aikata adalci, mai son gaskiya,

Sai in gafarta mata.

2 Ko da yake suna cewa, ‘Na rantse da

ran Ubangiji,’

Duk da haka rantsuwar ƙarya suke

yi.”

3 Ya Ubangiji, ashe, ba masu gaskiya

kake so ba?

Ka buge su, amma ba su yi nishi ba,

Ka hore su, amma sun ƙi horuwa,

Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse,

Sun ƙi tuba.

4 Sai na ce,

“Waɗannan mutane ba su da kirki,

Ba su da hankali,

Ba su san hanyar Ubangiji,

Ko shari’ar Allahnsu ba.

5 Zan tafi wurin manyan mutane, in yi

musu magana,

Gama sun san nufin Ubangiji, da

shari’ar Allahnsu.”

Amma dukansu sun ƙi yarda

Ubangiji ya mallake su,

Suka ƙi yi masa biyayya.

6 Domin haka zaki daga kurmi zai

kashe su,

Kyarkeci kuma daga hamada zai

hallaka su.

Damisa tana yi wa biranensu

kwanto,

Duk wanda ya fita daga cikinsu sai a

yayyage shi,

Domin laifofinsu sun yi yawa,

Karkacewarsu babba ce.

7 “Don me zan gafarce ki?

‘Ya’yanki sun rabu da ni,

Sun yi rantsuwa da gumaka,

Na ciyar da su har sun ƙoshi sosai,

Suka yi karuwanci, suka ɗunguma

zuwa gidajen karuwai,

8 Kamar ƙosassun ingarmu suke,

masu jaraba,

Kowa yana haniniya, yana neman

matar maƙwabcinsa.

9 Ba zan hore su saboda waɗannan

abubuwa ba?

Ni Ubangiji na ce, ba zan ɗauka wa

kaina fansa a kan wannan

al’umma ba?

10 Ku haura, ku lalatar da gonar

kurangar inabinta,

Amma kada ku yi mata ƙarƙaf,

Ku sassare rassanta,

Gama su ba na Ubangiji ba ne.

11 Gama mutanen Isra’ila da mutanen

Yahuza

Sun zama marasa aminci a gare ni.

Ni Ubangiji na faɗa.”

12 Sun yi ƙarya a kan Ubangiji,

Suka ce, “Ba abin da zai yi,

Ba wata masifa da za ta same mu.

Ba kuwa za mu ga takobi ko yunwa

ba.

13 Annabawa holoƙo ne kawai,

Maganar ba ta cikinsu.

Haka za a yi da su!”

Urushalima tana gab da Faɗuwa

14 Saboda haka Ubangiji Allah Mai

Runduna ya ce,

“Domin sun hurta wannan magana,

Ga shi, zan sa maganata a bakinka ta

zama wuta,

Waɗannan mutane kuwa su zama

itace,

Wutar za ta cinye su.

15 “Ya ku mutanen Isra’ila, ga shi, ina

kawo muku

Wata al’umma daga nesa,” in ji

Ubangiji,

“Al’umma ce mai ƙarfin hali ta tun

zamanin dā.

Al’umma wadda ba ku san harshenta

ba,

Ba za ku fahimci abin da suke faɗa

ba.

16 Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari

ne,

Dukansu jarumawa ne.

17 Za su cinye amfanin gonakinku da

abincinku.

Za su ƙare ‘ya’yanku mata da maza.

Za su cinye garkunanku na tumaki,

da na awaki, da na shanu,

Za su kuma cinye ‘ya’yan inabinku

da na ɓaurenku.

Za su hallaka biranenku masu kagara

da takobi, waɗanda kuke fariya da

su.

18 “Amma ko a cikin waɗancan kwanaki ba zan yi muku ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.

19 “Sa’ad da mutanenki suka ce, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi mana waɗannan abubuwa duka?’ sai ki ce musu, ‘Kamar yadda kuka rabu da ni kuka bauta wa gumaka a ƙasarku, haka kuma za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’ ”

20 “Ka sanar wa zuriyar Yakubu da

wannan,

Ka kuma yi shelarsa a Yahuza, ka

ce,

21 ‘Ku ji wannan, ya ku wawaye,

marasa hankali,

Kuna da idanu, amma ba ku gani,

Kuna da kunnuwa, amma ba ku

ji.’ ”

22 Ubangiji ya ce, “Ba za ku ji tsorona

ba?

Ba za ku yi rawar jiki a gabana ba?

Ni ne na sa yashi ya zama iyakar

teku,

Tabbatacciyar iyaka, wadda ba ta

hayuwa,

Ko da yake raƙuman ruwa za su yi

hauka, ba za su iya haye ta ba,

Ko da suna ruri, ba za su iya wuce ta

ba.

23 Amma mutanen nan suna da taurin

zuciya, masu halin tayarwa ne,

Sun rabu da ni, sun yi tafiyarsu.

24 A zuciya ba su cewa,

‘Bari mu ji tsoron Ubangiji

Allahnmu

Wanda yake ba mu ruwan sama a

kan kari,

Na kaka da na bazara,

Wanda yake ba mu lokacin girbi.’

25 Laifofinku sun raba ku da waɗannan

abubuwa.

Zunubanku kuma sun hana ku

samun alheri.

26 “Gama an sami mugaye, a cikin

jama’ata,

Suna kwanto kamar masu kafa

ashibta.

Sun ɗana tarko su kama mutane.

27 Kamar kwando cike da tsuntsaye,

Haka nan gidajensu suke cike da cin

amana,

Don haka suka zama manya, suka

sami dukiya.

28 Sun yi ƙiba, sun yi bul-bul,

Ba su da haram a kan aikata

mugunta,

Ba su yi wa marayu shari’ar adalci,

don kada su taimake su.

A wajen shari’a ba su bin hakkin

matalauta.

29 “Ba zan hukunta su saboda

waɗannan abubuwa ba?

Ba zan ɗaukar wa kaina fansa a kan

al’umma irin wannan ba?

30 “Abin banmamaki da bantsoro

Ya faru a ƙasar.

31 Annabawa sun yi annabcin ƙarya,

Firistoci kuma sun yi mulki da ikon

kansu,

Mutanena kuwa suna so haka!

Amma sa’ad da ƙarshe ya zo, me za

ku yi?”

Categories
IRM

IRM 6

Ajalin Urushalima da Yahuza

1 “Ya ku mutanen Biliyaminu, ku

gudu neman mafaka,

Daga cikin Urushalima!

Ku busa ƙaho a Tekowa,

Ku ba da alama a Bet-akkerem,

Gama masifa da babbar halaka sun

fito daga arewa.

2 Ya Sihiyona, ke kyakkyawar

makiyaya ce, zan hallaka abin da

kika hahhaifa.

3 Makiyaya da garkunansu za su zo

wurinki,

Za su kafa alfarwansu kewaye da ke,

Kowa zai yi kiwo a makiyayarki.

4 Za su ce, ‘Mu yi shiri mu fāɗa mata

da yaƙi!

Ku tashi, mu fāɗa musu da tsakar

rana!’

Sai kuma suka ce, ‘Kaitonmu, ga

rana tana faɗuwa, ta yi ruɗa-

kuyangi.

5 Mu tashi mu fāɗa mata da dare,

Mu lalatar da fādodinta.’ ”

6 Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Ku sassare itatuwanta,

Ku tula ƙasa kewaye da

Urushalima,

Dole in hukunta wannan birni

saboda ba kome cikinsa sai

zalunci,

7 Kamar yadda rijiya take da ruwa

garau,

Haka Urushalima take da

muguntarta,

Ana jin labarin kama-karya da na

hallakarwa a cikinta,

Kullum akwai cuce-cuce, da raunuka

a gabana,

8 Ku ji faɗaka, ya ku mutanen

Urushalima,

Don kada a raba ni da ku,

Don kada in maishe ku kufai,

Ƙasar da ba mazauna ciki.”

9 Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Za a kalace ringin Isra’ila sarai,

kamar yadda ake wa inabi,

Ka miƙa hannunka a kan rassanta

kamar mai tsinkar ‘ya’yan

inabi.”

10 Da wa zan yi magana don in faɗakar

da shi, don su ji?

Ga shi, kunnuwansu a toshe suke, su

ji,

Ga shi, maganar Ubangiji kuwa ta

zama abin ba’a a gare su,

Ba su marmarinta.

11-12 Don haka ina cike da fushin

Ubangiji

Na gaji da kannewa.

Ubangiji ya ce,

“Zan kwararo fushi kan yara da suke a

titi.

Da kuma kan tattaruwar samari.

Za a ɗauke mata da miji duka biyu,

Da tsofaffi, da waɗanda suka tsufa

tukub-tukub.

Za a ba waɗansu gidajensu, da

gonakinsu, da matansu,

Gama zan nuna ikona in hukunta

mazaunan ƙasar.

13 Gama daga ƙaraminsu zuwa babba,

Kowannensu yana haɗama ya ci

ƙazamar riba,

Har annabawa da firistoci,

Kowannensu ya shiga aikata rashin

gaskiya.

14 Sun warkar da raunin mutanena

sama sama,

Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali

kuwa ba lafiya.

15 Sun ji kunya sa’ad da suka aikata

abubuwan banƙyama?

Ba su ji kunya ba ko kaɗan.

Ko gezau ba su yi ba,

Don haka za su fāɗi tare da

fāɗaɗɗu,

Sa’ad da na hukunta su, za a

hamɓarar da su.

Ni Ubangiji na faɗa.”

16 Haka Ubangiji ya ce,

“Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba,

Ku nemi hanyoyin dā, inda hanya

mai kyau take,

Ku bi ta, don ku hutar da

rayukanku.

Amma suka ce, ‘Ai, ba za mu bi ta ba.’

17 Na sa muku matsara cewa, in kun ji

an busa ƙaho ku kula!

Amma suka ce, ‘Ba za mu kula ba.’

18 “Don haka, ku ji, ya ku al’ummai,

Ku sani, ku taron jama’a,

Don ku san abin da zai same ku.

19 Ki ji, ya ke duniya,

Ga shi, ina kawo masifa a kan

wannan jama’a,

Sakayyar ƙulle-ƙullensu,

Don ba su kula da maganata ba,

Sun ƙi dokokina.

20 Da wane nufi kuke kawo mini turare

daga Sheba,

Ko raken da kuke kawowa daga

ƙasa mai nisa?

Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa

ba,

Ba kuwa zan ji daɗin sadakokinku

ba.

21 Don haka, ni Ubangiji na ce,

Zan sa abin tuntuɓe a gaban wannan

jama’a,

Za su kuwa yi tuntuɓe, su fāɗi.

Iyaye tare da ‘ya’yansu, da

maƙwabci,

Do abokansu za su lalace.”

22 Haka Ubangiji ya ce,

“Ga shi, jama’a tana fitowa daga

ƙasar arewa.

Babbar al’umma ce,

Ta yunƙuro tun daga manisantan

wurare na duniya.

23 Suna riƙe da baka da māshi,

Mugaye ne marasa tausayi,

Motsinsu kamar ƙugin teku ne.

Suna haye a kan dawakai,

A jere kamar wanda ya yi shirin

yaƙi

Gāba da ke, ya ‘yar Sihiyona.”

24 Mutanen Urushalima sun ce,

“Mun ji labarin yaƙin,

Hannuwanmu suka yi rauni.

Azaba ta kama mu,

Ciwo irin na mai naƙuda.

25 Kada ku fita zuwa gona,

Kada kuma ku yi yawo a kan

hanya,

Gama abokin gāba yana da takobi,

Razana a kowane sashi.”

26 “Ya mutanena, ku sa tufafin makoki,

Ku yi birgima cikin toka,

Ku yi makoki mai zafi irin wanda

akan yi wa ɗa tilo,

Gama mai hallakarwa zai auko mana

nan da nan.”

27 Ubangiji ya ce wa Irmiya,

“Na maishe ka mai aunawa da mai

jarraba mutanena

Domin ka sani, ka auna

al’amuransu,

28 Su duka masu taurinkai ne, ‘yan

tawaye,

Suna yawo suna baza jita-jita.

Su tagulla ne da baƙin ƙarfe,

Dukansu lalatattu ne.

29 Ana zuga da ƙarfi,

Dalma ta ƙone,

Tacewar aikin banza ne,

Gama ba a fitar da mugaye ba.

30 Ana ce da su ƙwan maƙerar azurfa

ne,

Gama ni na ƙi su.”

Categories
IRM

IRM 7

Ku Gyara Hanyoyinku da Ayyukanku

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce,

2 “Ka tafi ka tsaya a ƙofar Haikalin Ubangiji, ka yi shelar wannan magana, ka ce, su kasa kunne ga maganar Ubangiji, dukansu mutanen Yahuza, su da suke shiga ta ƙofofin nan don su yi wa Ubangiji sujada!

3 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, ni kuwa zan ƙyale ku, ku zauna a wannan wuri.

4 Kada ku amince da maganganun nan na ruɗarwa, cewa wannan shi ne Haikalin Ubangiji. Wannan shi ne Haikalin Ubangiji, wannan shi ne Haikalin Ubangiji!

5 “ ‘Idan dai kun gyara hanyoyinku, da ayyukanku bisa kan gaskiya, idan da gaskiya kuke aikata adalci ga junanku,

6 idan ba ku tsananta wa baƙo, ko maraya, ko gwauruwa, wato matar da mijinta ya rasu, idan ba ku zubar da jinin marar laifi a wannan wuri ba, idan kuma ba ku bi abin da zai cuce ku ba, wato gumaka,

7 sa’an nan zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasa wadda tuni na ba kakanninku har abada.

8 “ ‘Ga shi, kun amince da maganganu na ruɗami, marasa amfani.

9 Za ku yi ta yin sata, da kisankai, da zina, da rantsuwar ƙarya, da ƙona wa Ba’al turare, da bin waɗansu gumakan da ba ku sani ba?

10 Sa’an nan za ku zo ku tsaya a gabana a wannan Haikali, wanda ake kira da sunana, ku ce, “An cece mu,” don kawai ku ci gaba da yin dukan waɗannan abubuwan banƙyama?

11 Wannan Haikali wanda ake kira da sunana ya zama kogon mafasa a idanunku. Ga shi, ni da kaina na gani.’ ” in ji Ubangiji.

12 “ ‘Ku tafi Shilo wurin da na fara zaunar da sunana, ku ga abin da na yi mata saboda muguntar mutanena Isra’ila.

13 Yanzu kuwa saboda kun aikata waɗannan al’amura, sa’ad da na yi ta yi muku magana, amma ba ku kasa kunne ba, sa’ad da na kira ku, ba ku amsa ba,

14 domin haka zan yi wa Haikali wanda ake kira da sunana, wanda kuma kuka amince da shi, da kuma wurin da na ba ku, ku da kakanninku, kamar yadda na yi wa Shilo.

15 Zan kore ku daga gabana kamar yadda na yi wa dukan ‘yan’uwanku, dukan zuriyar Ifraimu.’ ”

Fushin Allah a kan Bin Gumaka

16 “Kai kuwa, Irmiya kada ka yi wa mutanen nan addu’a. Kada ka yi kuka ko addu’a dominsu, kada ka roƙe ni, gama ba zan ji ka ba.

17 Ba ka ga abin da suke yi a biranen Yahuza da titunan Urushalima ba?

18 Yara sukan tara itace, iyaye maza sukan haɗa wuta, iyaye mata sukan kwaɓa ƙullu don su yi wa gunkin nan wadda ake kira sarauniyar sama, waina. Sukan kuma miƙa wa gumaka hadayu na sha domin su tsokane ni.”

19 In ji Ubangiji, “Ni suke tsokana? Ashe, ba kansu ba ne don su ruɗar da kansu?”

20 Saboda haka ga abin da Ubangiji Allah ya ce, “Duba, zan kwarara fushina da hasalata a kan wannan wuri, a kan mutum duk da dabba, da akan itatuwan saura da amfanin gona. Zai yi ta cin wuta, ba kuwa za a kashe ba.”

Horon Yahuza saboda Tayarwa

21 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya ce, “Ku ba da hadayunku na ƙonawa da na sadakarku, ku ci naman.

22 A ranar da na fito da kakanninku daga ƙasar Masar, ban yi magana da su, ko na umarce su, a kan hadayun ƙonawa da na sadaka ba.

23 Amma na umarce su su yi biyayya da maganata, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena, su bi dukan al’amuran da na umarce su, domin lafiyarsu, don su zama lafiya.

24 Amma ba su yi biyayya ba, ba su kuma kula ba. Sai suka bi shawarar kansu da ta tattaurar muguwar zuciyarsu. Suka koma baya maimakon su yi gaba.

25 Tun daga ran da kakanninku suka fito ƙasar Masar, har zuwa yau na yi ta aika musu da dukan bayina annabawa kowace rana.

26 Duk da haka ba su saurare ni ba, ba su kula su ji ba, sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.

27 “Saboda haka za ka faɗa musu waɗannan abubuwa duka, amma ba za su ji ka ba. Za ka kira su, amma ba za su amsa ba.

28 Za ka faɗa musu ka ce, wannan ita ce al’ummar da ba ta yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnta ba, ba ta karɓi horo ba. Gaskiya kuma ta ƙare sam, ba ta a bakinsu.

29 “Ku aske gashin kanku, ku zubar da shi. Ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi ‘yan zamanin nan, ya rabu da su saboda fushinsa.

30 Ni Ubangiji, na faɗa, cewa mutanen Yahuza sun yi mugun abu a gabana. Suna ajiye gumakansu a Haikalina, sun ƙazantar da shi.

31 A cikin kwarin ɗan Hinnon sun gina bagade, mai suna Tofet, don su miƙa ‘ya’yansu mata da maza hadayar ƙonawa. Ni ban umarce su su yi haka ba, irin wannan abu ba shi a zuciyata.

32 Domin haka, ni Ubangiji na ce, kwanaki suna zuwa lokacin da ba za a ƙara faɗar Tofet, ko kwarin ɗan Hinnom ba, amma za a kira shi Kwarin Kisa, gama za a binne mutane a Tofet domin ba sauran wuri a ko’ina.

33 Gawawwakin mutanen nan za su zama abincin tsuntsaye da na namomin jeji, ba wanda zai kore su.

34 Zan sa muryar murna da ta farin ciki, da muryar ango da ta amarya su ƙare a biranen Yahuza da titunan Urushalima, gama ƙasar za ta zama kufai.”

Categories
IRM

IRM 8

1 “Ni Ubangiji na faɗa, cewa a wancan lokaci, za a fitar da ƙasusuwa daga kaburburan sarakunan Yahuza, da na sarakansu, da na firistoci, da na annabawa, da na mazaunan Urushalima.

2 Za a shimfiɗa su a rana, da a farin wata, da a gaban dukan rundunan sama, waɗanda suka ƙaunata, suka bauta wa, waɗanda suka nemi shawararsu, suka yi musu sujada. Ba za a tattara su a binne ba, amma za su zama juji a bisa ƙasa.

3 Sauran mutanen muguwar tsaran nan waɗanda suke a wuraren da na warwatsa su, za su fi son mutuwa fiye da rayuwa. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”

Zunubi da Hukunci

4 “Ka faɗa musu, ka ce, ni Ubangiji na

ce,

‘Wanda ya fāɗi ba zai sāke tashi ba?

Idan wani ya kauce ba zai komo kan

hanya ba?

5 Me ya sa, mutanen nan na

Urushalima suke ratsewa, suke

komawa baya kullayaumin?

Sun riƙe ƙarya kan-kan

Sun ƙi komowa.

6 Na kula sosai, na saurara,

Amma ba wanda ya faɗi wata

maganar kirki,

Ba wanda ya taɓa barin muguntarsa,

Kowa cewa yake, “Me na yi?”

Kamar dokin da ya kutsa kai cikin

fagen fama.

7 Ko shamuwa ta sararin sama ma, ta

san lokatanta,

Tattabara da tsattsewa, da gauraka

suna kiyaye lokacin komowarsu.

Amma mutanena ba su san dokokina

ba.

8 Ƙaƙa za ku ce, “Muna da hikima,

Dokar Ubangiji tana tare da mu”?

Ga shi kuwa, alkalamin ƙarya na

magatakarda, ya yi ƙarya.

9 Za a kunyatar da masu hikima.

Za su tsorata, za a kuma tafi da su.

Ga shi, sun ƙi maganar Ubangiji.

Wace hikima suke da ita?

10 Saboda haka zan ba da matansu ga

waɗansu,

Gonakinsu kuma ga waɗanda suke

cinsu da yaƙi,

Saboda tun daga ƙarami har zuwa

babba

Kowannensu yana haɗamar cin

muguwar riba,

Tun daga annabawa zuwa firistoci

Kowannensu aikata ha’inci yake yi.

11 Sun warkar da raunin mutanena

sama sama,

Suna cewa, “Lafiya, lafiya,” alhali

kuwa ba lafiya.

12 Ko sun ji kunya

Sa’ad da suka aikata ayyuka masu

banƙyama?

A’a, ba su ji kunya ba ko kaɗan,

Fuskarsu ko gezau ba ta yi ba.

Domin haka za su faɗi tare da

fāɗaɗɗu,

Sa’ad da na hukunta su, za a ci su da

yaƙi.

Ni Ubangiji na faɗa.’

13 “Ni Ubangiji na ce,

‘Sa’ad da zan tattara su kamar

amfanin gona,

Sai na tarar ba ‘ya’ya a kurangar

inabi,

Ba ‘ya’ya kuma a itacen ɓaure,

Har ganyayen ma sun bushe.

Abin da na ba su kuma ya kuɓuce

musu.

Ni Ubangiji na faɗa.’ ”

14 Mutanen Urushalima sun ce,

“Don me muke zaune kawai?

Bari mu tattaru, mu tafi cikin

garuruwa masu garu,

Mu mutu a can,

Gama Ubangiji Allahnmu ya

ƙaddara mana mutuwa,

Ya ba mu ruwan dafi,

Domin mun yi masa laifi.

15 Mun sa zuciya ga salama, amma ba

lafiya,

Mun sa zuciya ga lokacin samun

warkewa,

Amma sai ga razana!

16 Daga Dan, an ji firjin dawakai.

Dakan ƙasar ta girgiza saboda

haniniyar ingarmunsu.

Sun zo su cinye ƙasar duk da abin

da suke cikinta,

Wato da birnin da mazauna

cikinsa.”

17 “Ni Ubangiji na ce, ‘Zan aiko muku

da macizai, da kāsā,

Waɗanda ba su da makari,

Za su sassare ku.’ ”

18 Baƙin cikina ya fi ƙarfin warkewa,

Zuciyata ta ɓaci ƙwarai!

19 Ku ji kukan jama’ata ko’ina a

ƙasar,

“Ubangiji, ba shi a Sihiyona

ne?

Sarkinta ba ya a cikinta ne?”

Ubangiji ya ce,

“Me ya sa suka tsokane ni da

sassaƙaƙƙun gumakansu,

Da baƙin gumakansu?”

20 Mutane suna ta cewa,

“Damuna ta ƙare, kaka kuma ta

wuce,

Amma ba a cece mu ba.”

21 Raunin da aka yi wa jama’ata,

Ya yi wa zuciyata rauni.

Ina makoki, tsoro kuma ya kama ni

ƙwarai.

22 Ba abin sanyayawa a Gileyad ne?

Ba mai magani a can ne?

Me ya sa ba a warkar da jama’ata

ba?

Categories
IRM

IRM 9

1 Da ma kaina ruwa ne kundum,

Idanuna kuma maɓuɓɓuga ne,

Da sai in yi ta kuka dare da rana,

Saboda an kashe jama’ata!

2 Da ma ina da wurin da zan fake a

hamada,

Da sai in rabu da mutanena, in tafi

can!

Gama dukansu mazinata ne,

Ƙungiyar mutane maciya amana.

3 Ubangiji ya ce,

“Sun tanƙwasa harshensu kamar

baka,

Ƙarya ce take rinjayar gaskiya a

ƙasar.

Suna ta cin gaba da aikata mugunta,

Ba su kuwa san ni ba.

4 “Bari kowane mutum ya yi hankali

da maƙwabcinsa,

Kada kuma ya amince da kowane

irin ɗan’uwa,

Gama kowane ɗan’uwa munafuki

ne,

Kowane maƙwabci kuma mai kushe

ne.

5 Kowane mutum yana ruɗin

maƙwabcinsa da abokinsa,

Ba mai faɗar gaskiya,

Sun koya wa harshensu faɗar

ƙarya.

Suna aikata laifi,

Sun rafke, sun kasa tuba.

6 Suna ƙara zalunci a kan zalunci,

Yaudara a kan yaudara,

Sun ƙi sanina,” in ji Ubangiji.

7 Saboda haka, Ubangiji Mai

Runduna, ya faɗa cewa,

“Zan tsabtace su, in gwada su,

Gama me zan yi kuma saboda

jama’ata?

8 Harshensu kibiya ce mai dafi, yana

faɗar ƙarya,

Kowa yana maganar alheri da

maƙwabcinsa

Amma a zuciyarsa yana shirya masa

maƙarƙashiya.

9 Ba zan hukunta su saboda waɗannan

al’amura ba?

Ba zan sāka wa al’umma irin

wannan ba?”

10 Zan yi kuka in yi kururuwa saboda

tsaunuka,

Zan yi kuka saboda wuraren kiwo,

Domin sun bushe sun zama marasa

amfani.

Ba wanda yake bi ta cikinsu.

Ba a kuma jin kukan shanu,

Tsuntsaye da namomin jeji, sun gudu

sun tafi.

11 “Ni Ubangiji na ce, zan mai da

Urushalima tsibin kufai,

Wurin zaman diloli,

Zan kuma mai da biranen Yahuza

kufai, inda ba kowa.”

Za a Rushe Birni a Kai su Zaman Talala

12 Wa yake da isasshiyar hikimar da zai fahimci wannan? Wa Ubangiji ya faɗa masa don ya sanar? Me ya sa ƙasar ta lalace ta zama kufai, har ba wanda yake iya ratsa ta, kamar hamada?

13 Sai Ubangiji ya ce, “Saboda sun bar dokata wadda na sa a gabansu, ba su yi biyayya da maganata ko su yi aiki da ita ba.

14 Amma suka taurare, suka biye wa zuciyarsu, suka bi Ba’al, kamar yadda kakanninsu suka koya musu.

15 Domin haka, ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, zan ciyar da mutanen nan da abinci mai ɗaci, in shayar da su da ruwan dafi.

16 Zan watsa su cikin sauran al’umma waɗanda su da kakanninsu ba su san su ba, zan sa takobi ya bi su don in hallaka su.

17 “Haka ni Ubangiji Mai Runduna na

ce,

Ku yi tunani, ku kirawo mata masu

makoki su zo,

Ku aika wa gwanaye fa.”

18 Jama’a suka ce,

“Su gaggauta, su ta da murya,

Su yi mana kuka da ƙarfi,

Har idanunmu su cika da hawaye,

Giranmu kuma su jiƙe sharaf.

19 “Gama ana jin muryar kuka daga

Sihiyona cewa,

‘Ga yadda muka lalace! Aka kunyatar

da mu ɗungum!

Don mun bar ƙasar, domin sun

rurrushe wuraren zamanmu.’ ”

20 Irmiya ya ce,

“Ya ku mata, ku ji maganar

Ubangiji,

Ku kasa kunne ga maganar da ya

faɗa,

Ku koya wa ‘ya’yanku mata kukan

makoki,

Kowacce ta koya wa maƙwabciyarta

waƙar makoki,

21 Gama mutuwa ta shiga tagoginmu,

Ta shiga cikin fādodinmu,

Ta karkashe yara a tituna,

Ta kuma karkashe samari a dandali.

22 Ubangiji ya ce mini,

‘Ka yi magana, cewa gawawwakin

mutane za su fāɗi tuli

Kamar juji a saura,

Kamar dammunan da masu girbi

suka ɗaura,

Ba wanda zai tattara su.’ ”

23 Ubangiji ya ce, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa, kada mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa, kada kuma mawadaci ya yi fariya da wadatarsa.

24 Amma bari wanda zai yi fariya, ya yi fariya a kan cewa ya fahimce ni, ya kuma san ni. Ni ne Ubangiji mai yin alheri, da gaskiya, da adalci a duniya, gama ina murna da waɗannan abubuwa, ni Ubangiji na faɗa.”

25 Ubangiji ya ce, “Kwanaki suna zuwa sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya,

26 da Masar, da Yahuza, da Edom, da ‘ya’yan Ammon, maza, da na Mowab, da dukan waɗanda suke zaune a hamada, da waɗanda suke yi wa kansu sanƙo, gama dukan al’umman nan marasa kaciya ne, dukan jama’ar Isra’ila kuma marasa kaciya ne a zuci.”

Categories
IRM

IRM 10

Gumaka da Allah na Gaskiya

1 Ya jama’ar Isra’ila, ku ji jawabin da Ubangiji yake yi muku.

2 Ubangiji ya ce,

“Kada ku koyi abubuwan da

al’ummai suke yi,

Kada ku ji tsoron alamun da suke a

sama,

Ko da yake al’ummai suna jin

tsoronsu.

3 Gama al’adun mutane na ƙarya ne,

Daga cikin jeji aka sare wani itace,

Gwanin sassaƙa ya sassaƙa shi da

gizago.

4 Mutane sukan yi masa ado na azurfa

da zinariya,

Sukan ɗauki guduma su kafa shi da

ƙusoshi,

Don kada ya motsa.

5 Gumakansu dodon gona suke, a

cikin gonar kabewa,

Ba su iya yin magana,

Ɗaukarsu ake yi domin ba su iya

tafiya!

Kada ku ji tsoronsu.

Gama ba su da ikon aikata mugunta

ko alheri.”

6 Ya Ubangiji, ba wani kamarka,

Kai mai girma ne,

Sunanka kuma yana da girma da

iko.

7 Wane ne ba zai ji tsoronka ba, ya

Sarkin dukan al’ummai?

Ka isa a ji tsoronka,

Gama babu kamarka a cikin dukan

masu hikima na al’ummai,

Da kuma cikin dukan mulkokinsu,

Ba wani kamarka.

8 Dukansu dakikai ne wawaye,

Koyarwar gumaka ba wani abu ba

ne, itace ne kawai!

9 An kawo fallayen azurfa daga

Tarshish,

Da zinariya kuma daga Ufaz,

Aikin gwanaye da maƙeran

zinariya.

Tufafinsu na mulufi ne da shunayya,

duka aikin gwanaye.

10 Amma Ubangiji shi ne Allah na

gaskiya,

Shi Allah mai rai ne,

Shi Sarki ne madawwami.

Saboda hasalarsa duniya ta girgiza,

Al’ummai ba za su iya jurewa da

fushinsa ba.

11 Haka za ku faɗa musu, “Gumakan da ba su yi sammai da duniya ba, za su lalace a duniya da a ƙarƙashin sammai.”

12 Shi ne, ta wurin ikonsa ya yi duniya,

Ta wurin hikimarsa ya kafa ta,

Ta wurin basirarsa kumaya ya shimfiɗa

sammai.

13 Sa’ad da ya yi murya akan ji ƙugin

ruwa a cikin sammai

Yakan kawo ƙasashi daga ƙurewar

duniya,

Yakan yi walƙiyoyi saboda ruwan

sama,

Daga cikin taskokinsa yakan kawo

iska.

14 Kowane mutum dakiki ne, marar

ilimi,

Kowane maƙerin zinariya zai sha

kunya saboda gumakansa,

Gama siffofinsa ƙarya ne,

Ba numfashi a cikinsu.

15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne,

A lokacin da za a hukunta su za su

lalace.

16 Gama shi ba kamar waɗannan yake

ba,

Shi na Yakubu ne.

Shi ne ya yi dukan kome,

Kabilan Isra’ilawa gādonsa,

Sunansa Ubangiji Mai Runduna.

Risɓewar Yahuza

17 Ku tattara kayayyakinku,

Ku mazaunan wurin da aka kewaye

da yaƙi.

18 Gama haka Ubangiji ya ce,

“Ga shi, ina jefar da mazaunan

ƙasar daga ƙasarsu a wannan

lokaci,

Zan kawo musu wahala, za su kuwa

ji jiki.”

19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka

yi mini.

Raunina mai tsanani ne,

Amma na ce, lalle wannan azaba ce,

Tilas in daure da ita.

20 An lalatar da alfarwata,

Dukan igiyoyi sun tsintsinke,

‘Ya’yana maza sun bar ni, ba su

nan.

Ba wanda zai kafa mini alfarwata

Ya kuma rataya labulena.

21 Makiyayan dakikai ne,

Ba su roƙi Ubangiji ba,

Don haka ba su sami wadata ba,

An watsa dukan garkensu.

22 Ku ji fa, an ji ƙishin-ƙishin! Ga shi

kuma, yana tafe.

Akwai babban hargitsin da ya fito

daga arewa,

Don a mai da biranen Yahuza kufai,

wurin zaman diloli.

23 “Ya Ubangiji, na sani al’amuran

mutum ba a hannunsa suke ba,

Ba mutum ne yake kiyaye takawarsa

ba

24 Ka tsauta mini, ya Ubangiji, amma

da adalcinka,

Ba da fushinka ba, don kada ka

wofinta ni.

25 Ka kwarara hasalarka a kan sauran

al’umma da ba su san ka ba,

Da a kan jama’ar da ba su kiran

sunanka,

Gama sun cinye Yakubu,

Sun cinye shi, sun haɗiye shi,

Sun kuma mai da wurin zamansa

kufai.”