Categories
IRM

IRM 11

An Ta da Alkawari

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya cewa,

2 “Ka ji maganar wannan alkawari, sa’an nan ka faɗa wa mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima.

3 Ka faɗa musu cewa, ‘In ji Ubangiji Allah na Isra’ila, la’ananne ne wanda bai kula da maganar alkawarin nan ba.

4 Wato alkawarin da na yi da kakanninku a lokacin da na fito da su daga ƙasar Masar, daga cikin tanderun ƙarfe. Na faɗa musu su yi biyayya da maganata, su aikata dukan abin da na umarce su. Ta haka za su zama mutanena, ni kuma in zama Allahnsu.

5 Sa’an nan zan cika maganar rantsuwa da na rantse wa kakanninku, da na ce zan ba su ƙasa wadda take cike da albarka kamar yadda yake a yau.’ ”

Irmiya ya ce, “Amin, amin, ya Ubangiji.”

6 Ubangiji kuma ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuza da titunan Urushalima duka, cewa su ji maganar alkawarin nan, su aikata.

7 Lokacin da na fito da kakanninsu daga ƙasar Masar na faɗakar da su musamman, na yi ta faɗakar da su har wannan rana, ina cewa, ‘Ku yi biyayya da maganata.’

8 Amma duk da haka ba su yi biyayya ba, ba su kuma kasa kunne ba. Kowa ya bi tattaurar zuciyarsa mai mugunta. Domin haka na kawo musu dukan maganar alkawarin nan wanda na umarce su su yi, amma ba su yi ba.”

9 Ubangiji ya kuma ce mini, “Akwai tawaye a cikin mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima.

10 Sun koma a kan laifofin kakanninsu, waɗanda suka ƙi jin maganata, suka bi gumakansu don su bauta musu, jama’ar Isra’ila da na Yahuza sun ta da alkawarina wanda na yi da kakanninsu.

11 Saboda haka ni Ubangiji na ce, ‘Ga shi, ina kawo musu masifa wadda ba za su iya tsere mata ba, ko da za su yi kuka gare ni ba zan ji su ba.

12 Sa’an nan biranen Yahuza da mazaunan Urushalima za su tafi, su yi kuka ga gumaka waɗanda suka ƙona musu turare, amma ba za su iya cetonsu a lokacin wahalarsu ba.

13 Gama yawan gumakansu sun kai yawan biranensu. Yawan bagadan da suke da su kuma sun kai yawan titunan Urushalima, abin kunya, bagadan ƙona wa Ba’al turare ne.’

14 Don haka kada ka yi wa waɗannan mutane addu’a. Kada ka yi kuka ko addu’a dominsu, gama ba zan kasa kunne gare su ba, ko da sun yi kirana a lokacin wahalarsu.”

15 Ubangiji ya ce, “Wane iko ƙaunatacciyata take da shi cikin Haikalina, da ya ke ta aikata mugayen ayyuka? Ko alkawarai da naman hadayu za su iya kawar miki da ƙaddararki, har da za ki yi taƙama?

16 Dā na kira ki itacen zaitun mai duhuwa, kyakkyawa, mai kyawawan ‘ya’ya, amma da ƙugin babbar iska za a cinna miki wuta, za ta kuwa cinye rassanki.”

17 Ubangiji Mai Runduna, wanda ya dasa ku, ya hurta masifar da za ta same ku saboda muguntar da mutanen Isra’ila da na Yahuza suka yi, suka tsokane ni in yi fushi saboda suna ƙona wa Ba’al turare.

An Shirya Maƙarƙashiya don a Kashe Irmiya

18 Ubangiji ya sanasshe ni,

Na kuwa sani,

Sa’an nan ya nuna mini mugayen

ayyukansu.

19 Amma ina kama da lafiyayyen ɗan

rago,

Wanda aka ja zuwa mayanka,

Ashe, ni suke ƙulla wa munafuncin!

Ni kuwa ban sani ba, da suke cewa,

“Bari mu lalatar da itacen duk da

‘ya’yansa.

Bari mu datse shi daga ƙasar masu

rai,

Har da ba za a ƙara tunawa da

sunansa ba.”

20 Amma ya Ubangiji Mai Runduna,

mai shari’ar adalci,

Kakan gwada zuciya da tunani,

Ka yarda mini in ga sakayyar da za

ka yi mini a kansu,

Gama a gare ka na danƙa

maganata.

21 Saboda haka ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka, da suka ce, “Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji, in ba haka ba, da hannunmu za mu kashe ka.”

22 Domin haka ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ga shi kuwa, zan hukunta su, za a kashe samarinsu da takobi, ‘ya’yansu mata da maza, yunwa za ta kashe su.

23 Ba wanda zai ragu daga cikin mutanen Anatot, gama zan kawo wa mutanen Anatot masifa, a shekarar hukuncinsu.”

Categories
IRM

IRM 12

Fatawar Irmiya da Amsar Ubangiji

1 Ya Ubangiji, kai adali ne sa’ad da na kawo ƙara a gare ka.

Duk da haka zan bayyana ƙarata a

gabanka,

Me ya sa mugaye suke arziki cikin

harkarsu?

Me ya sa dukan maciya amana suke

zaman lafiya,

Suna kuwa ci gaba?

2 Kai ka dasa su, sun kuwa yi saiwa,

Suna girma, suna kuma ba da

‘ya’ya,

Sunanka na a cikin bakinsu, amma

kana nesa da zuciyarsu.

3 Amma kai, ya Ubangiji, kana sane da

ni, kana ganina,

Kai kanka kake gwada tunanina.

Ka jawo su kamar tumaki zuwa

mayanka,

Ka ware su domin ranar yanka.

4 Sai yaushe ƙasar za ta daina

makoki,

Ciyawar kowace saura kuma ta daina

yin yaushi?

Saboda muguntar mazaunan ƙasar

ne dabbobi da tsuntsaye suka

ƙare,

Domin mutanen suna cewa, “Ba zai

ga ƙarshenmu ba.”

5 Ubangiji ya ce,

“Idan kai da mutane kun yi tseren

ƙafa sun gajiyar da kai,

Yaya za ka iya gāsa da dawakai?

Idan ka fāɗi a lafiyayyiyar ƙasa,

Ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?

6 Gama har da ‘yan’uwanka da gidan

mahaifinka,

Sun ci amanarka,

Suna binka da kuka,

Kada ka gaskata su,

Ko da yake suna faɗa maka

maganganu masu daɗi.”

7 Ubangiji ya ce,

“Na bar jama’ata.

Na rabu da gādona,

Na ba da wanda raina yake ƙauna a

hannun maƙiyansa.

8 Abin gādona ya zama mini kamar

zaki a cikin kurmi,

Ya ta da murya gāba da ni,

Domin haka na ƙi shi.

9 Ashe, abin gadon nan nawa ya zama

dabbare-dabbaren tsuntsun nan ne

mai cin nama?

Tsuntsaye masu cin nama sun kewaye

shi?

Tafi, ka tattaro namomin jeji,

Ka kawo su su ci.

10 Makiyaya da yawa sun lalatar da

gonar inabina.

Sun tattake nawa rabo,

Sun mai da nawa kyakkyawan rabo

kufai da hamada.

11 Sun maishe shi kufai, ba kowa,

Yana makoki a gare ni,

Ƙasar duka an maishe ta kufai,

Amma ba wanda zuciyarsa ta damu a

kan wannan.

12 A kan dukan tsaunukan nan na

hamada

Masu hallakarwa sun zo,

Gama takobin Ubangiji yana ta kisa

Daga wannan iyakar ƙasa zuwa

waccan,

Ba mahalukin da yake da salama.

13 Sun shuka alkama, sun girbe

ƙayayuwa,

Sun gajiyar da kansu, amma ba su

amfana da kome ba.

Za su sha kunya saboda abin da suke

girbe,

Saboda zafin fushin Ubangiji.”

14 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan mugayen maƙwabtan Isra’ila waɗanda suka taɓa gādon da ya ba jama’arsa Isra’ila su gada. “Saboda haka zan tumɓuke su daga cikin ƙasarsu. Zan kuma tumɓuke mutanen Yahuza daga cikinsu.

15 Bayan na tumɓuke su kuma, zan sāke yi musu jinƙai, in komar da su, kowanne zuwa gādonsa.

16 Zai zama kuwa, idan za su himmantu su koyi al’amuran jama’ata, su yi rantsuwa da sunana, su ce, ‘Da zatin Ubangiji,’ kamar yadda suka koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za a gina su a tsakiyar jama’ata.

17 Amma idan wata al’umma za ta ƙi kasa kunne, to, sai in tumɓuke ta ɗungum, in hallaka ta, in ji Ubangiji.”

Categories
IRM

IRM 13

Misali da Abin Ɗamara

1 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, ya ce, “Tafi ka sayo lilin na yin ɗamara, ka sha ɗamara da shi kada kuwa ka tsoma shi a ruwa.”

2 Sai na sayo abin ɗamara kamar yadda Ubangiji ya ce, na sha ɗamara da shi.

3 Ubangiji kuma ya sāke yin magana da ni sau na biyu,

4 ya ce, “Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi Kogin Yufiretis, ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”

5 Sai na tafi, na ɓoye shi a Yufiretis kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.

6 Bayan an ɗan daɗe, sai Ubangiji ya ce mini, “Tashi, ka tafi Yufiretis, ka ɗauko abin ɗamara wanda na umarce ka ka ɓoye a can.”

7 Sai na tafi Yufiretis, na haƙa na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi. Amma abin ɗamara ya lalace, ba shi da sauran amfani.

8 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,

9 “Haka zan lalatar da alfarmar Yahuza da yawan alfarmar Urushalima.

10 Wannan muguwar jama’a, wadda ta ƙi jin maganata, wadda ta taurare, ta bi son zuciyarta, ta kuma bi gumaka ta bauta musu, ta yi musu sujada, za ta zama kamar abin ɗamaran nan, wanda ba shi da sauran amfani.

11 Gama kamar yadda abin ɗamara yakan kame tam a gindin mutum, haka na sa dukan mutanen Isra’ila da dukan mutanen Yahuza su manne mini domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.”

Misali da Tulun Ruwan Inabi

12 “Sai ka faɗa musu wannan magana cewa, ‘Ni Ubangiji Allah na Isra’ila na ce, a cika kowane tulu da ruwan inabi.’ Su kuwa za su ce maka, sun sani sarai za a cika kowane tulu da ruwan inabi.

13 Sa’an nan za ka faɗa musu, Ubangiji ya ce, ‘Ga shi, zan sa dukan mazaunan ƙasar su bugu da ruwan inabi, wato sarakunan da suka hau gadon sarautar Dawuda, da firistoci, da annabawa, da dukan mazaunan Urushalima.

14 Zan sa su kara da junansu, iyaye maza da ‘ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi, ko juyayi, ko jinƙai ba za su sa in fasa hallaka su duka ba.’ ”

Yahuza bai Tuba ba, za a Kai shi Zaman Talala

15 Ku kasa kunne, ku ji,

Kada ku yi girmankai, gama

Ubangiji ya yi magana.

16 Ku girmama Ubangiji Allahnku,

Kafin ya kawo duhu,

Kafin kuma ƙafafunku su yi tuntuɓe

a kan dutse, da duhu duhu,

Sa’ad da kuke neman haske, sai ya

maishe shi duhu,

Ya maishe shi duhu baƙi ƙirin.

17 Amma idan ba za ku ji ba,

Raina zai yi kuka a ɓoye saboda

girmankanku,

Idanuna za su yi kuka ƙwarai, za su

zub da hawaye,

Domin an kai garken Ubangiji zuwa

bauta.

18 Ubangiji ya ce wa Irmiya,

“Ka faɗa wa sarki da sarauniya,

uwarsa, su sauka daga gadon

sarautarsu,

Domin an tuɓe kyakkyawan rawanin

sarautarsu daga kansu.

19 An kulle biranen Negeb,

Ba wanda zai buɗe su,

Yahuza duka an kai ta zaman dole,

Dukanta an kai ta zaman dole.

20 “Ku ta da idanunku, ku ga waɗanda

suke zuwa daga arewa!

Ina kyakkyawan garken nan da aka

ba ku?

21 Me za ku ce sa’ad da aka naɗa muku

shugabanni,

Waɗanda ku da kanku kuka koya

musu, suka zama abokanku?

Ashe, azabai ba za su auko muku ba

Kamar yadda sukan auko wa mace

mai naƙuda?

22 Idan kun ce a zuciyarku,

‘Me ya sa waɗannan abubuwa suka

same mu?’

Saboda yawan zunubanku ne,

Shi ya sa an tone tsiraicinku,

Aka wahalshe ku.

23 Mutumin Habasha zai iya sāke

launin fatar jikinsa?

Ko kuwa damisa za ta iya sāke

dabbare-dabbarenta?

Idan haka ne, ku kuma za ku iya yin

nagarta,

Ku da kuka saba da yin mugunta.

24 Zan warwatsar da ku

Kamar yadda iskar hamada take

watsar da ƙaiƙayi.”

25 Ubangiji ya ce, “Wannan shi ne

rabonku,

Rabon da na auna muku, ni Ubangiji

na faɗa.

Domin kun manta da ni, kun dogara

ga ƙarairayi,

26 Ni kaina kuma zan kware muku

suturarku ta rufe fuskarku

Don a ga tsiraicinku.

27 Na ga abubuwanku masu

banƙyama,

Wato zinace-zinacenku, da haniniya

kamar dawakai,

Da muguwar sha’awarku ta

karuwanci a kan tuddai da filaye,

Ya Urushalima, taki ta ƙare!

Har yaushe za a tsarkake ki?”

Categories
IRM

IRM 14

Babban Fari

1 Maganar da Ubangiji ya yi wa Irmiya a kan fari ke nan,

2 “Yahuza tana makoki,

Ƙofofin biranenta suna lalacewa,

Mutanenta suna kwance a ƙasa,

suna makoki,

Urushalima tana kuka da babbar

murya.

3 Manyan mutanenta sun aiki

barorinsu su ɗebo ruwa.

Da suka je maɓuɓɓuga, sai suka

tarar ba ruwa.

Sai suka koma da tulunansu

haka nan,

An kunyatar da su, an ƙasƙantar

da su,

Suka lulluɓe kansu don kunya.

4 Saboda ƙasar ta bushe,

Tun da ba a yi ruwa a kanta ba,

Manoma sun sha kunya,

Suka lulluɓe kansu don kunya.

5 Barewa ma a saura takan gudu,

Ta bar ɗanta sabon haihuwa,

Domin ba ciyawa.

6 Jakunan jeji suna tsaye a kan tuddan

da ba ciyawa,

Suna haki kamar diloli,

Idanunsu ba su gani

Domin ba abinci.”

7 Irmiya ya ce,

“Ko da yake zunubanmu su ne

shaidunmu,

Ya Ubangiji, ka yi taimako saboda

sunanka!

Gama kāsawarmu ta yi yawa,

Domin mun yi maka zunubi.

8 Ya kai, wanda kake begen Isra’ila,

Mai Cetonta a lokacin wahala,

Ƙaƙa ka zama kamar baƙo a ƙasar?

Kamar matafiyi wanda ya kafa

alfarwarsa a gefen hanya don ya

kwana, ya wuce?

9 Ƙaƙa ka zama kamar wanda bai san

abin da zai yi ba,

Kamar jarumin da ya kasa yin

ceto?

Duk da haka, ya Ubangiji, kana nan

a tsakiyarmu.

Da sunanka ake kiranmu,

Kada ka bar mu!”

10 Haka Ubangiji ya ce a kan waɗannan mutane, “Sun cika son yawaceyawace, ba su iya zama wuri ɗaya, don haka ni Ubangiji, ban yarda da su ba, zan tuna da laifofinsu in hukunta zunubansu.”

11 Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin lafiyar jama’an nan.

12 Ko da sun yi azumi, ba zan ji kukansu ba, ko da sun miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta sha, ba zan karɓe su ba. Amma zan hallaka su da takobi, da yunwa, da annoba.”

13 Sai na ce, “Ya Ubangiji Allah, ga shi, annabawa sun faɗa musu, sun ce, ‘Ba za ku ga takobi ko yunwa ba, amma zan ba ku dawwamammiyar salama a wannan wuri.’ ”

14 Ubangiji kuwa ya ce mini, “Annabawa, annabcin ƙarya suka yi da sunana. Ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba, ban kuma yi magana da su ba. Annabcin da suke yi muku na wahayin ƙarya ne, dubar da suke yi marar amfani ce, tunaninsu ne kawai.

15 Domin haka ga abin da ni Ubangiji na ce a kan annabawan da suke yin annabci da sunana, ko da yake ban aike su ba, waɗanda suke cewa, ‘Takobi da yunwa ba za su shigo ƙasan nan ba.’ Za a hallaka su da takobi da yunwa.

16 Mutanen da suka yi wa annabci, za a jefar da su waje a kan titunan Urushalima, a karkashe su da yunwa da takobi, ba wanda zai binne su, da su, da matansu, da ‘ya’yansu mata da maza. Zan sa muguntarsu ta koma kansu.

17 “Irmiya, ka faɗa wa mutanen baƙin

ciki da ya same ka,

Ka ce, ‘Bari idanuna su yi ta zub da

hawaye dare da rana,

Kada su daina, saboda an buge

budurwa, ‘yar jama’ata,

An yi mata babban rauni da dūka

mai tsanani.

18 Idan na tafi cikin saura,

Sai in ga waɗanda aka kashe da

takobi!

Idan kuma na shiga birni,

Sai in ga waɗanda suke ta fama da

yunwa!

Gama annabi da firist, sai harkarsu

suke ta yi a ƙasar,

Amma ba su san abin da suke yi

ba.’ ”

Mutane Sun Roƙi Ubangiji

19 “Ka ƙi Yahuza ke nan ɗungum?

Ranka kuma yana jin ƙyamar

Sihiyona ne?

Me ya sa ka buge mu, har da ba za

mu iya warkewa ba?

Mun zuba ido ga samun salama,

amma ba wani abin alheri da ya

zo.

Mun kuma sa zuciya ga warkewa,

amma sai ga razana.

20 Mun san muguntar da muka yi, ya

Ubangiji,

Da wadda kakanninmu suka yi,

Gama mun yi maka zunubi.

21 Saboda darajar sunanka, kada ka

wulakanta mu,

Kada kuma ka ƙasƙantar da

darajar kursiyinka,

Ka tuna da alkawarin da ka yi

mana,

Kada ka ta da shi.

22 A cikin gumakan al’ummai akwai

mai iya sa a yi ruwa?

Sammai kuma su yi yayyafi?

Ashe, ba kai ne ba, ya Ubangiji

Allahnmu?

Domin haka a gare ka muke sa

zuciya,

Gama kai ne mai yin waɗannan

abubuwa duka.”

Categories
IRM

IRM 15

Fushin Ubangiji da Yahuza bai Huce Ba

1 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da a ce Musa da Sama’ila za su tsaya a gabana, duk da haka zuciyata ba za ta komo wurin mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana su yi tafiyarsu!

2 Sa’ad da suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu cewa, Ubangiji ya ce,

‘Waɗanda suke na annoba, su tafi ga

annoba!

Waɗanda suke na takobi, su tafi ga

takobi!

Waɗanda suke na yunwa, su tafi ga

yunwa!

Waɗanda suke na bauta, su tafi ga

bauta!’

3 Zan sa musu masu hallakarwa huɗu,” in ji Ubangiji, “da takobi don kisa, da karnuka don yayyagawa, da tsuntsayen sararin sama, da dabbobin duniya don su cinye, su hallakar.

4 Zan kuma sa su zama abin banƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manassa ɗan Hezekiya, Sarkin Yahuza ya aikata a Urushalima.

5 “Wa zai ji tausayinki, ya

Urushalima?

Wa zai yi baƙin ciki dominki?

Wa kuma zai ratso wurinki don ya

tambayi lafiyarki?

6 Ni Ubangiji na ce, kun ƙi ni, kuna ta

komawa da baya,

Don haka na nuna ikona gāba da ku,

na hallaka ku,

Na gaji da jin tausayinku!

7 Na sheƙe su da abin sheƙewa a

ƙofofin garuruwan ƙasar.

Na sa ‘ya’yansu su mutu, na hallaka

mutanena,

Ba su daina yin mugayen ayyukansu

ba.

8 Na yawaita gwauraye, wato mata da

mazansu suka mutu,

Fiye da yashin teku.

Na kawo wa uwayen samari mai

hallakarwa da tsakar rana.

Na sa azaba da razana su auka musu

farat ɗaya.

9 Ita wadda ta haifi ‘ya’ya bakwai ta

yi yaushi ta suma,

Ranarta ta faɗi tun lokaci bai yi ba,

An kunyatar da ita, an wulakantar

da ita.

Waɗanda suka ragu daga cikinsu

Zan bashe su ga takobi gaban abokan

gābansu.

Ni Ubangiji na faɗa.”

10 Kaitona, ya mahaifiyata, da kika haife ni, mai jayayya mai gardama da kowa cikin dukan ƙasar! Ban ba da rance ba, ba kuma wanda ya ba ni rance, duk da haka dukansu suna zagina.

11 Ubangiji ya ce mini, “Zan keɓe ka domin alheri, hakika zan sa abokan gaba su yi roƙo gare ka a lokacin bala’i da kuma lokacin damuwa.

12 Wa zai iya karya ƙarfe ko tagulla daga arewa?”

13 Ubangiji ya ce mini, “Zan ba da wadatarku da dukiyarku ganima kyauta, saboda dukan zunubanku a dukan ƙasar.

14 Zan sa ku bauta wa abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina ya kama kamar wuta, zai yi ta ci har abada.”

15 Sa’an nan Irmiya ya ce, “Ya

Ubangiji, ka sani.

Kai ne, ka ziyarce ni,

Ka kuma sāka wa waɗanda suke

tsananta mini.

Ka sani saboda kai nake shan zargi.

16 Maganarka da na samu na ci.

Maganarka kuwa ta zama abar

murna a gare ni,

Ta faranta mini zuciya.

Gama ana kirana da sunanka,

Ya Ubangiji Allah Mai Runduna.

17 Ban zauna cikin ƙungiyar masu

annashuwa ba.

Ban kuwa yi murna ba,

Na zauna ni kaɗai saboda kana tare

da ni,

Gama ka sa na cika da haushi.

18 Me ya sa azabata ta ƙi ƙarewa,

Raunukana kuma ba su warkuwa,

Sun kuwa ƙi warkewa?

Za ka yaudare ni kamar rafi,

Ko kamar ruwa mai ƙafewa?”

19 “Domin haka ga abin da ni, Ubangiji

na ce,

Idan ka komo sa’an nan zan kawo

ka.

Za ka tsaya a gabana.

Idan ka hurta abin da yake gaskiya

ba na ƙarya ba,

Za ka zama kakakina.

Za su komo gare ka,

Amma kai ba za ka koma wurinsu

ba.

20 Zan maishe ka garun tagulla saboda

waɗannan mutane,

Za su yi yaƙi da kai, amma ba za

su yi nasara a kanka ba,

Gama ina tare da kai don in cece ka,

in kuɓutar da kai.

21 Zan kuɓutar da kai daga hannun

mugaye,

Zan ɓamɓare ka daga hannun

marasa tausayi.”

Categories
IRM

IRM 16

Umarnin Ubangiji zuwa ga Irmiya

1 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,

2 “Ba za ka yi aure ka haifi ‘ya’ya mata da maza a wannan wuri ba.

3 Ga abin da ni Ubangiji na faɗa a kan ‘ya’ya mata da maza da aka haifa a wannan wuri, da kuma a kan iyayensu mata da maza da suka haife su a wannan ƙasa,

4 za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi makoki dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba. Za su zama juji. Takobi da yunwa za su kashe su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namomin jeji.”

5 Ubangiji kuma ya ce, “Kada ka shiga gidan da ake makoki, ko ka tafi inda ake baƙin ciki, kada ka yi baƙin ciki saboda su, gama na ɗauke salamata, da ƙaunata, da jinƙaina daga wurin jama’an nan.

6 Yaro da babba za su mutu a wannan ƙasa, ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi baƙin ciki dominsu ba. Ba kuwa wanda zai tsaga jikinsa ko ya aske kansa ƙwal dominsu.

7 Ba wanda zai ba mai makoki abinci don ya ta’azantar da shi saboda mamacin, ba kuma wanda zai ba shi abin sha don ya ta’azantar da shi saboda mahaifinsa ko mahaifiyarsa.

8 “Kada kuma ka shiga gidan da ake biki, ka zauna ka ci ka sha tare da su.

9 Gama ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, zan sa muryar murna, da ta farin ciki, da ta ango, da ta amarya, su ƙare a wurin nan a idonka da zamaninka.

10 “Sa’ad da ka faɗa wa mutanen nan wannan magana duka, za su kuwa ce maka, ‘Me ya sa Ubangiji ya hurta wannan babbar masifa a kanmu? Mene ne laifinmu? Wane irin zunubi muka yi wa Ubangiji Allahnmu?’

11 Sai ka faɗa musu cewa, Ubangiji ya ce, ‘Domin kakanninku sun rabu da ni, sun bi gumaka, sun bauta musu, sun yi musu sujada. Sun rabu da ni, sun ƙi kiyaye dokokina.

12 Ku kuma kun yi laifi fiye da na kakanninku. Kowannenku kuwa ya bi tattauran mugun nufin zuciyarsa, yana ƙin kasa kunne gare ni.

13 Don haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasa wadda ku ko kakanninku ba ku sani ba. A can za ku bauta wa gumaka dare da rana, gama ba zan nuna muku ƙauna ba.’

14 “Saboda haka, ga shi, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da ba za a ƙara cewa, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da jama’ar Isra’ila daga ƙasar Masar ba.’

15 Amma za a ce, ‘Na rantse da Ubangiji wanda ya fito da jama’ar Isra’ila daga ƙasar arewa, da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su,’ gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba kakanninsu.

16 “Ga shi, ina aiko da masunta da yawa,” in ji Ubangiji, “za su kuwa kama su, daga baya kuma zan aika da mafarauta da yawa, za su farauce su daga kowane tsauni, da tudu, da kogwannin duwatsu.

17 Gama ina ganin dukan ayyukansu, ba a ɓoye suke a gare ni ba, muguntarsu kuma ba a ɓoye take a gare ni ba.

18 Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, abin gādona kuma sun cika shi da abubuwansu na banƙyama.”

Addu’ar Irmiya ta Dogara ga Allah

19 “Ya Ubangiji, ƙarfina da kagarata,

Mafakata a ranar wahala,

A gare ka al’ummai za su zo,

Daga ƙurewar duniya, su ce,

‘Kakanninmu ba su gāji kome ba, sai

ƙarya,

Da abubuwan banza marasa

amfani.’

20 Mutum zai iya yi wa kansa alloli?

Ai, waɗannan ba alloli ba ne!”

21 Ubangiji ya ce,

“Saboda haka, ga shi, zan sa su sani,

Sau ɗayan nan kaɗai zan sa su su san

ikona da ƙarfina,

Za su kuma sani sunana Ubangiji

ne.”

Categories
IRM

IRM 17

Zunubin Yahuza Ya Yi Kanta

1 Ubangiji ya ce, “An rubuta zunubin mutanen Yahuza da alƙalamin ƙarfe, mai bakin yakutu. An zana shi a allon zuciyarsu da a zankayen bagadansu.

2 Idan sun tuna da ‘ya’yansu haka sun tuna da bagadansu da Ashtarot ɗinsu a gindin itatuwa masu duhuwa da kan tuddai masu tsayi.

3 Ku mazauna a tsaunuka da cikin saura, zan ba da dukiyarku da wadatarku ganima saboda dukan zunuban da kuka yi a dukan ƙasar.

4 Za ku rasa abin da yake hannunku daga cikin gādon da na ba ku. Zan sa ku bauta wa abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama da fushina wuta ta kama wadda za ta yi ta ci har abada.”

5 Ubangiji ya ce,

“La’ananne ne mutumin da yake

dogara ga mutum,

Wanda jiki ne makaminsa,

Wanda ya juya wa Ubangiji baya,

6 Gama yana kama da sagagi a

hamada,

Ba zai ga wani abu mai kyau yana

zuwa ba.

Zai zauna a busassun wuraren

hamada,

A ƙasar gishiri, inda ba kowa.

7 “Mai albarka ne mutumin da yake

dogara ga Ubangiji,

Wanda Ubangiji ne madogararsa.

8 Shi kamar itace ne wanda ake dasa a

bakin rafi

Wanda yake miƙa saiwoyinsa zuwa

cikin rafin,

Ba zai ji tsoron rani ba,

Kullum ganyensa kore ne,

Ba zai damu a lokacin fari ba,

Ba zai ko fasa yin ‘ya’ya ba.

9 “Zuciya ta fi kome rikici,

Cuta gare ta matuƙa,

Wa zai san kanta?

10 Ni Ubangiji nakan bincike tunani,

In gwada zuciya,

Domin in sāka wa kowane mutum

gwargwadon al’amuransa,

Da kuma gwargwadon ayyukansa.

11 “Kamar makwarwar da ta kwanta

kan ƙwan da ba ita ta nasa ba,

Haka yake ga wanda ya sami dukiyar

haram,

Yana gaɓar ƙarfinsa, za ta rabu da

shi,

A ƙarshe zai zama wawa.”

12 Kursiyi mai daraja,

Da aka sa a bisa tun daga farko,

Wurin ke nan inda Haikalinmu

yake.

13 Ya Ubangiji, begen Isra’ila,

Duk waɗanda suka rabu da kai, za su

sha kunya.

Waɗanda suka ba ka baya a duniya

za a rubuta su

Domin sun rabu da Ubangiji,

maɓuɓɓugar ruwan rai.

Irmiya Ya Roƙi Ubangiji ya Kiyaye Shi

14 Ubangiji, ka warkar da ni, zan kuwa

warke,

Ka cece ni, zan kuwa cetu,

Gama kai ne abin yabona.

15 Ga shi, suna ce mini,

“Ina maganar Ubangiji take?

Ta zo mana!”

16 Amma ni ban yi gudun zaman

makiyayi a gabanka ba,

Ban kuma so zuwan ranar bala’i ba,

Ka kuwa sani.

Abin da ya fito daga bakina kuwa,

A bayyane yake gare ka.

17 Kada ka zamar mini abin razana,

Kai ne mafakata cikin ranar masifa,

18 Bari waɗanda suka tsananta mini su

sha kunya,

Amma kada ka bar ni in kunyata.

Bari su tsorata,

Amma kada ka bar ni in tsorata.

Ka aukar musu da ranar masifa,

Ka hallaka su riɓi biyu!

A kan Kiyaye Ranar Asabar

19 Haka Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi ka tsaya a ƙofar Biliyaminu, wadda sarakunan Yahuza suke shiga da fita ta cikinta, ka kuma tafi dukan ƙofofin Urushalima.

20 Ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuza, da dukan Yahuza, da dukan mazaunan Urushalima, waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.

21 Haka Ubangiji ya ce, ku yi hankali saboda rayukanku, kada ku ɗauki kaya a ranar Asabar, ko ku shigar da kowane abu ta ƙofofin Urushalima.

22 Kada ku ɗauki kaya, ku fita da shi daga gidajenku a ranar, ko ku yi kowane irin aiki, amma ku kiyaye ranar Asabar da tsarki, kamar yadda na umarci kakanninku.’

23 Amma duk da haka ba su kasa kunne, ko su mai da hankali ba. Amma suka taurare don kada su ji, su karɓi koyarwa.

24 “ ‘Amma idan kun kasa kunne gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofin wannan birni a ranar Asabar ba, amma kuka kiyaye ranar Asabar da tsarki, ba ku yi aiki a cikinta ba,

25 sa’an nan ne sarakuna waɗanda za su zauna a kan gadon sarautar Dawuda, za su shiga ta ƙofofin wannan birni, suna hawan karusai, da dawakai, su da sarakunansu, da jama’ar Yahuza da mazaunan Urushalima. Za a zauna a wannan birni har abada.

26 Mutane za su zo daga biranen Yahuza da wuraren da yake kewaye da Urushalima, daga ƙasar Biliyaminu, da ta Shefela, da ta ƙasar tuddai, da kuma ta Negeb, suna kawo hadayu na ƙonawa da sadakoki, da hadayu na sha, da na turare, za su kuma kawo hadayu na godiya a Haikalin Ubangiji.

27 Amma idan ba ku kasa kunne gare ni ba, ba ku kuwa kiyaye ranar Asabar da tsarki ba, kun kuma ɗauki kaya kun shiga ta ƙofofin Urushalima a ranar Asabar, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wuta. Za ta kuwa cinye fādodin Urushalima, ba kuwa za ta kasu ba.’ ”

Categories
IRM

IRM 18

Irmiya a Gidan Maginin Tukwane

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce,

2 “Ka tashi, ka gangara zuwa gidan maginin tukwane, a can zan yi maka magana.”

3 Sai na gangara zuwa gidan maginin tukwanen, na iske shi yana ginin tukwane a kan na’urar ginin tukwanen.

4 Abin da yake ginawa ya lalace a hannunsa, sai ya sāke gina wani abu dabam da yumɓu ɗin, yadda ya ga dama.

5 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini,

6 “Ya jama’ar Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku kamar yadda maginin tukwanen nan ya yi ba? Duba, kamar yadda yumɓu yake a hannun maginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya ku jama’ar Isra’ila.

7 A duk lokacin da na ce zan tumɓuke, in kakkarya in hallaka wata al’umma, ko wani mulki,

8 idan wannan al’umma da na yi magana a kanta, ta juyo, ta tuba daga mugayen ayyukanta, zan janye masifar da na yi niyyar aukar mata.

9 A duk kuma lokacin da na ce zan gina, in kafa wata al’umma, ko wani mulki,

10 amma idan al’ummar ta aikata mugunta a gabana, ta ƙi saurarawa ga maganar, zan janye alherin da na yi niyyar yi mata.

11 Saboda haka yanzu, sai ka faɗa wa jama’ar Yahuza da mazaunan Urushalima, ka ce, haka Ubangiji ya faɗa, ‘Ga shi, na shirya muku masifa, ina tsara wahalar da za ta same ku. Bari kowannenku ya koma ya bar muguwar hanyarsa, ya gyara al’amuransa da ayyukansa.’

12 Amma za su ce, ‘Wannan ba abin da za mu kula da shi ba ne, mu ra’ayinmu za mu bi, kowannenmu kuwa zai yi bisa ga nufin tattaurar muguwar zuciyarsa.’

13 “Domin haka ni Ubangiji na ce,

‘Ka tambayi sauran al’umma.

Wa ya taɓa jin irin wannan?

Budurwa Isra’ila, ta yi mugun abu

ƙwarai!

14 Dusar ƙanƙara mai danshi ta taɓa

rabuwa da tsaunukan Lebanon?

Ko ruwan rafuffuka mai sanyi na kan

dutse ya taɓa ƙonawa?

15 Amma mutanena sun manta da ni,

Sun ƙona wa gumaka turare.

Sun yi tuntuɓe a cikin al’amuransu,

a hanyoyin dā,

Sun bi ɓarayin hanyoyi, ba su bi

karauka ba.

16 Sun mai da ƙasarsu abar

banƙyama,

Abin raini har abada.

Duk wanda ya wuce ta wurin zai

razana ya kaɗa kansa.

17 Haka zan warwatsa su

Kamar yadda iskar gabas take yi, a

gaban abokan gābansu,

Zan juya musu baya, ba za su ga

fuskata ba,

A ranar masifarsu.’ ”

Maƙarƙashiyar Mutane da Addu’ar Irmiya

18 Sa’an nan suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya, gama firist ba zai bar bin shari’a ba. Haka nan ma masu hikima ba za su bar yin shawara ba, haka nan kuma annabi ba zai bar yin magana ba! Ku zo mu kai ƙararsa, kada mu kula da abin da zai faɗa.”

19 Irmiya kuwa ya yi addu’a ya ce,

“Ya Ubangiji, ka kasa kunne gare ni,

ka ji ƙarar maƙiyana!

20 Daidai ne a rama alheri da

mugunta?

Duk da haka sun kafa wa raina tarko.

Ka tuna yadda na tsaya a gabanka,

Na yi maganar alheri a kansu,

Domin ka janye fushinka daga gare

su.

21 Saboda haka ka kawo wa ‘ya’yansu

yunwa,

Ka bashe su ga takobi,

Bari matansu su rasa ‘ya’ya,

mazansu su mutu,

Ka sa annoba ta kashe mazansu,

A kashe samarinsu da takobi a

yaƙi.

22 Bari a ji kururuwa daga gidajensu,

Saboda maharan da ka aika musu

farat ɗaya,

Gama sun haƙa rami don in fāɗa,

Sun kafa wa ƙafafuna tarkuna.

23 Amma ya Ubangiji,

Ka san dukan maƙarƙashiyarsu,

su kashe ni,

Kada ka gafarta musu muguntarsu,

kada kuma ka shafe zunubinsu

daga gabanka.

Ka sa a jefar da su daga gabanka,

Ka yi da su sa’ad da kake fushi!”

Categories
IRM

IRM 19

Fasasshen Tulu

1 Ubangiji ya ce mini, “Tafi ka sayo tulu a wurin maginin tukwane. Sa’an nan kuma ka ɗauki waɗansu daga cikin dattawan jama’a, da waɗansu manyan firistoci,

2 ku tafi kwarin ɗan Hinnom na mashigin Ƙofar Kasko, ka yi shelar maganar da zan faɗa maka a can.

3 Za ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya ku sarakunan Yahuza da mazaunan Urushalima, Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce, zan kawo wata irin masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.

4 Ga shi, mutanen nan sun rabu da ni, sun ƙazantar da wannan wuri sun ƙona wa gumaka turare, waɗanda su, ko kakanninsu, ko sarakunan Yahuza, ba su san su ba. Sun cika wannan wuri da jinin marasa laifi.

5 Sun gina wa Ba’al masujadai don su miƙa masa ‘ya’yansu maza hadayar ƙonawa, abin da ban umarta ba, ban kuma ba da izni ba, ban ma yi tunanin haka ba.

6 Saboda haka rana tana zuwa da ba za a ƙara ce da wannan wuri Tofet, ko kwarin ɗan Hinnom ba, amma za a ce da shi Kwarin Kisa.

7 A wannan wuri zan wofinta dabarun Yahuza da na Urushalima, zan sa a kashe jama’arsu da takobi, a gaban abokan gābansu, ta hannun waɗanda suke neman ransu. Zan ba da gawawwakinsu su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namomin jeji.

8 Zan mai da wannan birni abin ƙyama, abin raini, dukan wanda ya wuce wurin zai yi mamaki, ya yi tsaki saboda dukan masifun da suka auka wa birnin.

9 Zan sa su ci naman ‘ya’yansu mata da maza. Kowa zai ci naman maƙwabcinsa cikin damuwa a lokacin da za a kewaye su da yaƙi, zai sha wahala daga wurin abokan gābansa da waɗanda suke neman ransa.’

10 “Sa’an nan sai ka fasa tulun a gaban mutanen da suka tafi tare da kai,

11 ka kuwa ce musu, ‘Ubangiji Mai Runduna ya ce, haka zai farfasa jama’a, da wannan birni kamar yadda aka fashe tulun maginin tukwanen, ba kuwa zai gyaru ba. Za a binne mutane a Tofet domin za a rasa makabartar da za a binne su.

12 Haka zai yi wa wurin nan da mazauna cikinsa, ya mai da birnin nan kamar Tofet.

13 Gidajen Urushalima da gidajen sarakunan Yahuza da dukan gidaje waɗanda a kan rufinsu aka ƙona wa rundunar sararin sama turare, aka zuba wa gumaka hadayu na sha, za su ƙazantu kamar Tofet.’ ”

14 Sa’an nan Irmiya ya komo daga Tofet, inda Ubangiji ya aike shi don ya yi annabci, sai ya tsaya a fili na Haikalin Ubangiji, ya ce wa dukan jama’a,

15 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Ga shi, ina aukar wa wannan birni da dukan garuruwansa dukan masifu da na ambata a kansa, domin sun taurare zukatansu, sun ƙi jin maganata.’ ”

Categories
IRM

IRM 20

Saɓani Tsakanin Irmiya da Fashur Firist

1 Sa’ad da Fashur, firist, ɗan Immer, shugaban Haikalin Ubangiji ya ji Irmiya yana annabci a kan waɗannan abubuwa,

2 sai ya sa aka yi wa Irmiya dūka, aka kuma sa shi cikin turu a ƙofar Biliyaminu, a Haikalin Ubangiji.

3 Kashegari sa’ad da Fashur ya fitar da Irmiya daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashur ba, amma ya ba ka suna Magormissabib, wato razana ta kowace fuska.

4 Haka Ubangiji ya ce, ‘Ga shi, zan maishe ka abin tsoro ga kai kanka, da dukan abokanka. Abokan gābansu za su kashe su da takobi a kan idonka. Zan ba da dukan Yahuza a hannun Sarkin Babila, shi kuwa zai kwashe waɗansu ya kai bautar talala a Babila, ya kuma kashe waɗansu da takobi.

5 Banda haka kuma zan ba da dukan dukiyar wannan birni, da dukan ribarsa, da dukan abubuwa masu tamani, da dukan dukiyar sarakunan Yahuza, ga abokan gābansu, waɗanda za su washe su, su kama su, su kai Babila.

6 Kai kuma, Fashur, da dukan waɗanda suke a gidanka, za ku tafi bauta a Babila, za ku shiga Babila, a can za ku mutu, a can za a binne ku, kai da abokanka waɗanda ka yi wa annabcin ƙarya.’ ”

Kukan Irmiya

7 “Ya Ubangiji ka ruɗe ni, na kuwa

ruɗu,

Ka fi ni ƙarfi, ka kuwa rinjaye ni.

Na zama abin dariya dukan yini,

Kowa yana ta yi mini ba’a.

8 Duk lokacin da zan yi magana,

Nakan ta da murya in yi magana da

ƙarfi cewa,

‘Hargitsi da hallakarwa!’

Gama saboda maganar Ubangiji na

zama abin zargi,

Da abin ba’a dukan yini.

9 Idan na ce, ‘Ba zan ambaci Ubangiji

ba,

Ban zan ƙara yin magana da sunansa

ba,’

Sai in ji damuwa a zuciyata,

An kulle ta a ƙasusuwana,

Na gaji da danne ta a cikina,

Ba zan iya jurewa ba.

10 Na ji mutane da yawa suna sa mini

laƙabi cewa,

‘Razana ta kowace fuska,’

Suna cewa, ‘Mu la’anta shi!

Mu la’anta shi!’

Har ma da abokaina shaƙiƙai

Suna jira su ga fāɗuwata.

Suka ce, ‘Watakila a ruɗe shi,

Sa’an nan ma iya rinjayarsa

Mu ɗauki fansa a kansa.’

11 Amma Ubangiji kana tare da ni

Kamar jarumi mai bantsoro,

Don haka masu tsananta mini za su

yi tuntuɓe,

Ba za su rinjaye ni ba.

Za su sha kunya ƙwarai,

Gama ba za su yi nasara ba.

Ba za a manta da su ba.

12 Ya Ubangiji Mai Runduna, mai

gwada adali,

Mai ganin zuciya duk da tunani,

Ka sa in ga sakayyar da za ka yi

musu,

Gama a gare ka nake kawo

ƙarata.”

13 Ku raira waƙa ga Ubangiji!

Ku yabi Ubangiji!

Gama ya kuɓutar da ran mabukaci

daga hannun mugaye.

14 La’ananniya ce ranar da aka haife

ni,

Kada ranar da uwata ta haife ni ta yi

albarka!

15 La’ananne ne mutum da ya kai wa

mahaifina labari

Cewa, “An haifa maka ɗa,” don ya

sa shi farin ciki.

16 Bari wannan mutum ya zama kamar

biranen da Ubangiji ya kaɓantar

ba tausayi.

Bari ya ji kuka da safe,

Da rana kuma ya ji gangamin yaƙi,

17 Domin bai kashe ni tun ina ciki ba.

Da ma cikin uwata ya zama mini

kabari,

In yi ta kwanciya a ciki har abada.

18 Me ya sa na fito daga cikin mahaifa,

Don in ga wahala da baƙin ciki,

Don kwanakin raina su ƙare da

kunya?