Categories
IRM

IRM 21

An Yi Faɗi a kan Faɗuwar Urushalima

1 Wannan ita ce maganar Ubangiji wadda ya faɗa wa Irmiya sa’ad da sarki Zadakiya ya aiki Fashur ɗan Malkiya, da Zafaniya firist, ɗan Ma’aseya, wurin Irmiya cewa,

2 “Ka tambayar mana Ubangiji, gama Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya kawo mana yaƙi. Ko Ubangiji zai yi mana al’amuran nan nasa masu ban al’ajabi kamar yadda ya saba, ya sa Sarkin Babila ya janye, ya rabu da mu?”

3 Sai Irmiya ya ce musu,

4 “Ku faɗa wa Zadakiya, Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Ga shi, zan juyo kayan yaƙin da suke hannunka waɗanda kake yaƙi da su gāba da Sarkin Babila, da sojojinsa, waɗanda suka kewaye garun birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.

5 Ni kaina zan yi yaƙi da kai da dukan ƙarfina, da hasalata, da dukan zafin fushina.

6 Zan kuwa kashe mazaunan birnin nan, mutum da dabba, da babbar annoba.

7 Bayan wannan zan ceci Zadakiya Sarkin Yahuza, shi da bayinsa, da mutanen birnin nan waɗanda suka tsira daga annoba, da takobi, da yunwa, zan bashe su a hannun Nebukadnezzar Sarkin Babila, da hannun abokan gābansu, da waɗanda suke neman rayukansu. Zai kashe su da takobi, ba zai ji tausayinsu, ko ya rage waɗansunsu, ko ya ji juyayinsu ba.’

8 “Sai ka faɗa wa wannan jama’a, ka ce, ‘Ni Ubangiji na ce, ga shi, na sa tafarkin rai da na mutuwa a gabanku.

9 Shi wanda ya zauna a birnin nan zai mutu da takobi, da yunwa, da annoba, amma shi wanda ya fita ya ba da kansa ga Kaldiyawa waɗanda suke kewaye da ku zai rayu ya tserar da ransa.

10 Gama na ƙudura zan kawo wa wannan birni masifa, ba alheri ba. Zan bashe shi a hannun Sarkin Babila, shi kuwa zai ƙone shi da wuta.’ ”

Annabci a kan Sarakunan Yahuza

11 “Sai ka faɗa wa gidan sarautar Yahuza cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji,

12 Ya gidan Dawuda, ni Ubangiji na ce,

Ku aikata adalci kowace safiya.

Ku ceci wanda aka yi masa ƙwace

daga hannun mai matsa masa,

Don kada hasalata ta tashi kamar

wuta,

Ta yi ƙuna, har ba mai iya kashe

ta,

Saboda mugayen ayyukanku.

13 Ga shi, ina gāba da ku, ya ku

mazaunan kwarin,

Ya dutsen da yake a fili,’ in ji

Ubangiji.

‘Ku da kuke cewa, wa zai iya

gangarowa wurinku,

Ko kuwa wa zai shiga wurin

zamanku?

14 Zan hukunta ku bisa ga ayyukanku,’

in ji Ubangiji,

‘Zan sa wa jejin ƙasar wuta.

Za ta cinye duk abin da yake kewaye da

ita.’ ”

Categories
IRM

IRM 22

1 Haka Ubangiji ya faɗa, “Ka tafi ka gangara zuwa gidan Sarkin Yahuza, ka faɗi wannan magana a can,

2 ka ce, ‘Ka ji maganar Ubangiji, ya Sarkin Yahuza, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda kai da barorinka, da mutanenka waɗanda suke shiga ta ƙofofin nan.

3 Haka Ubangiji ya ce, ka yi gaskiya da adalci, ka ceci wanda ake masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka cuci baƙo, ko maraya, ko gwauruwa, wato matar da mijinta ya rasu, kada kuma ka zubar da jinin marasa laifi a wannan wuri.

4 Hakika idan ka kiyaye wannan magana, sa’an nan sarakunan da za su zauna a kan gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan gida da karusai da dawakai, su da barorinsu da jama’arsu.

5 Amma idan ba ka kula da waɗannan zantuttuka ba, na rantse da zatina,’ in ji Ubangiji, ‘wannan fāda ta zama kufai.’ ”

6 Abin da Ubangiji ya ce ke nan a kan fādar Sarkin Yahuza,

“Kyanta kamar Gileyad take a gare

ni,

Kamar kuma ƙwanƙolin Lebanon.

Duk da haka zan maishe ta hamada,

Birnin da ba kowa ciki.

7 Zan shirya waɗanda za su hallaka

ta.

Kowannensu da makamansa,

Za su sassare zaɓaɓɓun itatuwan

al’ul ɗinta, a jefa su a wuta.

8 “Al’ummai masu yawa za su wuce ta gefen wannan birni, kowane mutum zai ce wa maƙwabcinsa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’

9 Za su amsa, su ce, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada ga gumaka, suka bauta musu.’ ”

10 Ku mutanen Yahuza, kada ku yi

kuka saboda sarki Yosiya,

Kada ku yi makokin rasuwarsa,

Amma ku yi kuka ƙwarai saboda

ɗansa Yehowahaz.

Sun ɗauke shi, sun tafi da shi, ba zai

ƙara komowa ba,

Ba kuma zai ƙara ganin ƙasar da

aka haife shi ba.

11 Gama haka Ubangiji ya ce a kan Yahowahaz, ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, wanda ya gāji sarautar ubansa, Yosiya, wanda ya tafi ya bar wurin nan. Ba zai ƙara komowa nan ba.

12 Amma a wurin da suka kai shi zaman talala, a can zai mutu, ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.

13 Kaiton wanda ya gina gidansa ta

hanyar rashin adalci,

Benayensa kuma ta hanyar rashin

gaskiya.

Wanda ya sa maƙwabcinsa ya yi

masa aiki a banza,

Bai ba shi hakkinsa ba.

14 Kaiton wanda ya ce,

“Zan gina wa kaina babban gida

Da waɗansu irin benaye

musamman.”

Ya yi masa tagogi,

Ya manna masa itacen al’ul,

Sa’an nan ya yi masa jan shafe.

15 Kana tsammani kai sarki ne,

Da yake ƙasarka ta itacen al’ul

ce?

Amma ubanka ya ci, ya sha,

Ya yi gaskiya, ya aikata adalci,

Ya kuwa zauna lafiya.

16 Ya biya wa matalauta da masu

bukata hakkinsu,

Ya kuwa yi kyau.

Abin da ake nufi da sanina ke nan,

In ji Ubangiji.

17 Amma ka sa idonka da zuciyarka ga

ƙazamar riba,

Da zubar da jinin marar laifi,

Da yin zalunci da danniya.

18 Domin haka ga abin da Ubangiji ya ce a kan Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza,

“Ba za su yi makoki dominsa ba, ko

su ce,

‘Wayyo ɗan’uwanmu!’ ko, ‘Wayyo

‘yar’uwarmu!’

Ba za su yi makoki dominsa ba, su

ce,

‘Wayyo ubangidanmu!’ ko ‘Wayyo mai martaba!’

19 Za a binne shi kamar jaki,

Za a ja shi a yar a bayan ƙofofin

Urushalima.”

20 Ku haura zuwa Lebanon, ku yi

kuka,

Ku ta da muryarku cikin Bashan,

Ku yi kuka daga Abarim,

Gama an hallakar da dukan

ƙaunatattunku.

21 Ubangiji ya yi muku magana a

lokacin wadatarku.

Amma kun ce, “Ba za mu kasa

kunne ba!”

Wannan shi ne halinku tun kuna

samari,

Don ba ku yi biyayya da murya

Ubangiji ba.

22 Iska za ta kwashe shugabanninku,

Za a kai ƙaunatattunku cikin

bauta,

Sa’an nan za ku sha kunya ku ruɗe,

Saboda dukan muguntarku.

23 Ya ku mazaunan Lebanon,

Waɗanda suke zaune cikin itatuwan

al’ul,

Irin nishin da za ku yi sa’ad da azaba

ta same ku,

Azaba ce irin ta mace mai

naƙuda!

24 “Ni Ubangiji na rantse da raina, ko da Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, zoben hatimi ne a yatsan hannun damana, duk da haka zan kwaɓe shi,

25 in bashe shi a hannun waɗanda suke neman ransa, da a hannun wanda yake jin tsoronsa, wato Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da Kaldiyawa.

26 Zan jefar da shi da uwarsa a wata ƙasa inda ba a haife shi ba, a can zai mutu.

27 Amma ƙasan nan da suke marmarin komowa cikinta, ba za su koma cikinta ba.”

28 Ashe, Yekoniya kamar fasasshen

tulu yake,

Wanda ba wanda ya kula da shi?

Me ya sa aka watsar da shi da

‘ya’yansa,

A ƙasar da ba su sani ba?

29 Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa!

Ki ji maganar Ubangiji!

30 Haka Ubangiji ya ce,

“Rubuta wannan mutum, marar

‘ya’ya.

Mutumin da ba zai yi albarka a duk

kwanakinsa ba.

Gama ba wani daga zuriyarsa

Da zai gāji gadon sarautar Dawuda,

Ko ya yi mulki kuma a Yahuza.”

Categories
IRM

IRM 23

Komowar waɗanda suka Ragu

1 “Taku ta ƙare! Makiyayan da suka lalatar, suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.

2 Haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya faɗa a kan makiyayan jama’arsa. “Kun warwatsar da garkena kun kore su, ba ku lura da su ba. Ni ma haka zan yi da ku saboda muguntarku, ni Ubangiji na faɗa.

3 Sa’an nan zan tattaro sauran garkena daga wuraren da aka warwatsa su, zan komo da su cikin garkensu, zan sa su hayayyafa su riɓaɓɓanya.

4 Zan sa makiyayan da za su lura da su. Ba kuwa za su ƙara jin tsoro, ko razana ba, ba kuma wanda zai ɓace, ni Ubangiji na faɗa.

5 “Ga shi, ni Ubangiji na ce, kwanaki

suna zuwa,

Sa’ad da zan tsiro da wani mai adalci

daga zuriyar Dawuda

Wanda zai ci sarauta.

Zai yi sarauta da hikima,

Zai aikata abin da yake daidai a

ƙasar.

6 A zamaninsa za a ceci Yahuza,

Isra’ila kuwa za ta zauna lafiya.

Sunan da za a kira shi da shi ke

nan,

‘Ubangiji Adalcinmu.’

7 “Saboda haka, ga shi, kwanaki suna zuwa, ni Ubangiji na faɗa, sa’ad da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da jama’ar Isra’ila daga cikin ƙasar Masar ba,’

8 amma za su ce, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa, daga kuma dukan ƙasashen da ya warwatsa su!’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu ta kansu.”

Jawabi a kan Annabawan Ƙarya

9 A kan annabawa kuwa, zuciyata ta

karai,

Dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa,

Saboda Ubangiji da kuma maganarsa

mai tsarki.

Na zama kamar mashayi, wanda ya

bugu da ruwan inabi,

10 Gama ƙasar cike take da mazinata,

Saboda la’ana, ƙasar za ta yi

makoki,

Wuraren kiwo na jeji sun bushe,

Manufarsu mugunta ce,

Ba su mori ƙarfinsu a inda ya

kamata ba.

11 “Annabi da firist, dukansu biyu

marasa tsoron Allah ne,

Har a cikin Haikalina na tarar da

muguntarsu.”

Ubangiji ya faɗa.

12 “Saboda haka hanyarsu za ta zama

da santsi da duhu,

Inda za a runtume su, su fāɗi.

Gama zai kawo musu masifa a

shekarar da za su sha

hukuncinsu.”

Ubangiji ya faɗa.

13 “A cikin annabawan Samariya,

Na ga abu marar kyan gani.

Da sunan Ba’al suke yin annabci,

Suna ɓad da jama’ata Isra’ila

14 Amma cikin annabawa na

Urushalima,

Na ga abin banƙyama.

Suna yin zina, suna ƙarya,

Suna ƙarfafa hannuwan masu aikata

mugunta,

Saboda haka ba wanda ya juya ga

barin muguntarsa,

Dukansu suna kama da Saduma,

Mazaunanta kuwa kamar

Gwamrata.”

15 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce a kan annabawa,

“Ga shi, zan ciyar da su da abinci

mai ɗaci,

In shayar da su da ruwan dafi.

Daga wurin annabawan Urushalima

Rashin tsoron Allah ya fito ya

mamaye dukan ƙasar.”

16 Ubangiji Mai Runduna ya ce wa

mazaunan Urushalima,

“Kada ku kasa kunne ga maganar

annabawa,

Gama sukan cika kunnuwanku da

ƙarairayi.

Suna faɗar ganin damarsu,

Ba faɗar Ubangiji ba.

17 Suna ta faɗa wa waɗanda suke raina

maganar Ubangiji cewa,

‘Za ku zauna lafiya!’

Ga kowane mai bin nufin tattaurar

zuciyarsa,

‘Ba masifar da za ta same ka.’ ”

18 Irmiya ya ce, “Gama wane ne a cikin annabawan nan ya taɓa neman shawarar Ubangiji don ya fahimci maganarsa, ko kuwa wane ne ya taɓa kasa kunne don ya ji maganarsa?

19 Ga shi, hadirin hasalar Ubangiji ya

taso,

Kamar iskar guguwa,

Zai tashi a bisa kan mugaye.

20 Ubangiji ba zai huce ba,

Sai ya aikata nufin zuciyarsa.

Amma sai daga baya za ku gane

sarai.”

21 Ubangiji ya ce,

“Ni ban aiki waɗannan annabawa

ba,

Duk da haka sun tafi,

Ban kuwa yi musu magana ba,

Amma sun yi annabci.

22 Amma da a ce sun tsaya cikin

shawarata,

Da sun yi shelar maganata ga

jama’ata,

Da sun juyar da su daga muguwar

hanyarsu,

Da mugayen ayyukansu.

23 “Ni Allah na kusa ne kaɗai,

Banda na nesa?” In ji Ubangiji.

24 “Mutum ya iya ɓoye kansa a wani

lungu

Inda ba zan iya ganinsa ba?” In ji

Ubangiji.

“Ashe, ban cika sammai da duniya

ba?

25 Na ji abin da annabawan nan suka ce, su da suke annabcin ƙarya da sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki!’

26 Har yaushe ƙarya za ta fita daga zuciyar annabawan nan masu annabcin ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗin da yake a zuciyarsu?

27 Suna zaton za su sa mutanena su manta da sunana ta wurin mafarkansu da suke faɗa wa junansu, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana saboda Ba’al.

28 Bari annabin da yake da mafarki ya faɗi mafarkinsa, amma wanda yake da maganata ya faɗe ta da aminci. Me ya haɗa ciyawa da alkama? Ni Ubangiji na faɗa.

29 Maganata kamar wuta ce, kamar guduma mai farfashe dutse. Ni Ubangiji na faɗa.

30 Domin haka, ga shi, ina gāba da annabawan da suke satar maganata daga wurin junansu. Ni Ubangiji na faɗa.

31 Ina kuma gāba da annabawan da suke faɗar ra’ayin kansu, sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya faɗa.’

32 Ina kuma gāba da annabawan da suke annabcin mafarkansu na ƙarya, suna kuwa faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu, saboda rashin hankalinsu. Ni ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan jama’a ba ko kaɗan, ni Ubangiji na faɗa.”

33 “Kai Irmiya, sa’ad da wani mutum daga cikin mutanen nan, ko annabi, ko firist ya tambaye ka cewa, ‘Mece ce nawayar Ubangiji?’ Sai ka ce masa, ‘Ku ne nawayar, zan kuwa rabu da ku,’ ni Ubangiji na faɗa.

34 Idan annabi ko firist, ko wani daga cikin jama’a, ya ce, ‘Nawayar Ubangiji,’ zan hukunta shi duk da iyalin gidansa.

35 Haka kowannenku zai ce wa maƙwabcinsa da ɗan’uwansa, ‘Wace amsa Ubangiji ya bayar? Me Ubangiji ya faɗa?’

36 Amma ba za ku ƙara ambatar nawayar Ubangiji ba, gama maganar kowane mutum za ta zama nawaya, ga shi, kun ɓata maganar Allah mai rai, Ubangiji Mai Runduna, Allahnmu.

37 Haka za ka faɗa wa annabi, ‘Wace amsa Ubangiji ya bayar? Me Ubangiji ya faɗa?’

38 Amma idan kun ce, ‘Nawayar Ubangiji,’ ga abin da ni Ubangiji na ce, tun da yake kun faɗi wannan magana, wato ‘Nawayar Ubangiji,’ alhali kuwa na aika muku cewa, kada ku ce, ‘Nawayar Ubangiji,’

39 saboda haka, hakika zan ɗaga in jefar da ku daga gabana, da ku da birni wanda na ba ku, ku da kakanninku.

40 Zan sa ku zama abin zargi da abin kunya har abada, ba kuwa za a manta da wannan ba.”

Categories
IRM

IRM 24

Kwando Biyu na ‘Ya’yan Ɓaure

1 Bayan da Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya kama Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, daga Urushalima, ya kai shi bautar talala a Babila, tare da sarakunan Yahuza, da gwanayen sana’a, da maƙera, dukansu, ya kawo su Babila. Sai Ubangiji ya nuna mini wannan wahayi. Na ga kwando biyu na ɓaure, an ajiye su a gaban Haikalin Ubangiji.

2 A ɗaya kwandon akwai ɓaure masu kyau, kamar nunan fari. A ɗayan kuwa marasa kyau ne, ba mai iya cinsu.

3 Sai Ubangiji ya ce mini, “Irmiya, me ka gani?”

Sai na ce, “’Ya’yan ɓaure, akwai masu kyau ƙwarai, akwai kuma marasa kyau ƙwarai, har da ba za su ciwu ba.”

4 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini,

5 “Haka ni Ubangiji Allah na Isra’ila na ce, kamar kyawawan ɓauren nan, haka nake ganin mutanen Yahuza waɗanda aka kai su bautar talala a ƙasar Kaldiyawa.

6 Zan lura da su da kyau, in kuma komo da su a wannan ƙasa. Zan gina su, ba zan rushe su ba. Zan kafa su, ba zan tumɓuke su ba.

7 Zan ba su zuciyar da za su sani ni ne Ubangiji. Za su kuwa zama jama’ata, ni kuwa zan zama Allahnsu, gama za su komo wurina da zuciya ɗaya.

8 “Ni Ubangiji na ce, zan mai da Zadakiya Sarkin Yahuza, da sarakunansa, da sauran mutanen Urushalima da suka ragu a ƙasar, da mutanen da suka tafi Masar, kamar ruɓaɓɓen ɓauren nan da suka lalace har ba su ciwuwa.

9 Zan maishe su abin ƙyama da masifa ga mulkokin duniya duka. Za su zama abin zargi, da karin magana, da ba’a, da la’ana a dukan wuraren da zan warwatsa su.

10 Zan aika musu da takobi, da yunwa, da annoba har an hallaka su sarai daga cikin ƙasar da na ba su, su da kakanninsu.”

Categories
IRM

IRM 25

Za a Zama Kufai har Shekara Saba’in

1 A shekara ta huɗu ta mulkin Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, Ubangiji ya yi wa Irmiya magana a kan dukan mutanen Yahuza. A shekarar da Nebukadnezzar ya ci sarautar Babila,

2 a shekarar ce, annabi Irmiya ya yi wa dukan mutanen Yahuza da dukan mazaunan Urushalima magana cewa,

3 “Shekaru ashirin da uku ke nan tun daga shekara ta goma sha uku ta mulkin Yosiya, ɗan Amon, Sarkin Yahuza, har zuwa yau, Ubangiji ya yi mini magana, ni kuwa na yi ta faɗa muku, amma ba ku ji ba.

4 Ba ku saurara ba, ba ku kasa kunne don ku ji ba, ko da yake Ubangiji ya yi ta aiko muku da dukan bayinsa annabawa,

5 yana cewa, ‘Sai kowane ɗayanku ya juyo daga mugun halinsa da mugayen ayyukansa don ya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku, ku da kakanninku tun daga zamanin dā har abada.

6 Kada ku bi gumaka, ku bauta musu, ku yi musu sujada, ko ku tsokane ni da ayyukan hannuwanku, sa’an nan ba zan hore ku ba.’

7 Duk da haka ba ku kasa kunne gare shi ba, shi Ubangiji ya faɗa, sai kuka tsokane shi da ayyukan hannuwanku. Wannan kuwa zai cuce ku.

8 “Domin haka Ubangiji Mai Runduna ya ce, ‘Tun da yake kun ƙi yin biyayya da maganata,

9 zan aiko kabilai daga arewa da bawana Nebukadnezzar, Sarkin Babila. Zan kawo su, su yi yaƙi da ƙasan nan da mazaunanta, da dukan al’umman da take kewaya da ita. Zan hallaka su sarai, in sa su zama abin ƙyama, da abin raini, da abin zargi har abada.

10 Banda haka zan kawar da muryar sowa da ta farin ciki, da ta ango da ta amarya, da amon dutsen niƙa daga gare su. Zan kashe hasken fitilunsu.

11 Ƙasar duka za ta zama kufai marar amfani, waɗannan al’ummai za su bauta wa Sarkin Babila har shekara saba’in.

12 Sa’an nan bayan cikar shekara saba’in ɗin, zan hukunta Sarkin Babila da ƙasarsa, wato ƙasar Kaldiyawa. Zan maishe ta kango har abada, saboda zunubinsa.

13 Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abin da na faɗa gāba da ita. Dukan abin da aka rubuta a wannan littafi, wato dukan abin da Irmiya ya yi annabcinsa gāba da dukan al’umman nan.

14 Al’ummai da yawa da manyan sarakuna za su bautar da su, ni kuwa zan yi musu sakayya bisa ga ayyukan hannuwansu.’ ”

Hukuncin da Allah zai Yi wa Al’ummai

15 Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce mini, “Ka karɓi ƙoƙon ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.

16 Za su sha, su yi tangaɗi su yi hauka saboda takobin da zan aiko a cikinsu.”

17 Sai na karɓi ƙoƙon daga wurin Ubangiji, na sa dukan al’umman da Ubangiji ya aike ni gare su, su sha daga cikinsa.

18 Urushalima, da biranen Yahuza, da sarakunanta, da shugabanninta, za su zama kango da abin ƙyama da abin raini, da abin la’ana. Haka yake a yau.

19-26 Ga lissafin sauran da za su sha

ƙoƙon.

Fir’auna Sarkin Masar da kuma

barorinsa, da sarakunansa,

Dukan jama’arsa, da dukan

baƙin da suke tare da su,

dukan sarakunan ƙasar Uz,

dukan sarakunan ƙasar

Filistiyawa, wato Ashkelon, da

Gaza, da Ekron, da saura na

Ashdod,

Edom da Mowab, da ‘ya’yan

Ammon maza,

dukan sarakunan Taya, da dukan

sarakunan Sidon,

dukan sarakunan da suke gaɓar

Bahar Rum da waɗanda suke a

tsibiran tekun,

Dedan, da Tema, da Buz, da

dukan waɗanda suke yi wa

kansu sanƙo,

dukan sarakunan Arabiya,

dukan sarakunan tattarmukan

mutane da suke zaune a

hamada,

dukan sarakunan Zimri, da dukan

sarakunan Elam, da dukan

sarakunan Mediya,

dukan sarakunan arewa, na nesa

da na kusa bi da bi.

Dukan mulkokin da suke fuskar duniya za su sha daga ciki. Daga nan sai Sarkin Babila a bayansu duka, zai sha nasa.

27 “Za ka kuma faɗa musu cewa, ‘In ji Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ku sha, ku bugu, ku yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku tashi saboda takobin da zan aiko muku.’

28 Idan kuwa sun ƙi su karɓi ƙoƙon daga hannunka su sha sai ka faɗa musu cewa, ‘Ubangiji Mai Runduna ya ce, dole ne ku sha!

29 Gama ga shi, na fara sa masifa ta yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana. To, kuna tsammani ba za a hukunta ku ba? Sai an hukunta ku, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.’

30 “Kai Irmiya kuma sai ka yi annabcin dukan waɗannan magana gāba da su, ka faɗa musu cewa,

‘Ubangiji zai yi ruri daga Sama,

Zai yi magana daga wurin zamansa

mai tsarki,

Zai yi wa garkensa ruri da ƙarfi

ƙwarai,

Zai yi ihu kamar masu matse

‘ya’yan inabi,

Zai yi gāba da dukan mazaunan

duniya.

31 Za a ji hayaniya har iyakar duniya,

Gama Ubangiji yana da ƙara game

da al’ummai,

Zai shiga hukunta wa dukan ‘yan

adam,

Zai kashe mugaye da takobi,

Ubangiji ya faɗa.’ ”

32 Haka Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Ga masifa tana tahowa daga

al’umma zuwa al’umma,

Hadiri kuma yana tasowa daga

dukan manisantan wurare na

duniya.

33 Waɗanda Ubangiji ya kashe a

wannan rana,

Za su zama daga wannan bangon

duniya zuwa wancan.

Ba za a yi makoki dominsu ba,

Ba kuwa za a tattara gawawwakinsu

a binne ba.

Za su zama taki ga ƙasa.

34 “Ku yi makoki, ku yi kuka, ku

makiyaya,

Ku yi ta birgima a cikin toka ku

iyayengijin garke,

Gama ranar da za a yanka ku da

ranar da za a warwatsa ku ta zo,

Za ku fāɗi kamar zaɓaɓɓen kasko.

35 Ba mafakar da ta ragu domin

makiyaya,

Iyayengijin garken ba za su tsira ba.

36 Ji kukan makiyayan,

Da kukan iyayengijin garken,

Gama Ubangiji yana lalatar da wurin

kiwonsu.

37 Garkunan da suke zaune lafiya kuwa,

an yi kaca-kaca da su

Saboda zafin fushin Ubangiji.

38 Ya rabu da wurin ɓuyarsa kamar

zaki,

Gama ƙasarsu ta zama marar

amfani,

Saboda takobin Ubangiji, da kuma

zafin fushinsa.”

Categories
IRM

IRM 26

Maƙarƙashiya a Kashe Irmiya

1 A farkon sarautar Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce,

2 “Ka tsaya a filin Haikalin Ubangiji, ka yi wa dukan biranen Yahuza magana, su waɗanda suka zo Haikalin Ubangiji domin su yi sujada. Ka faɗa musu dukan maganar da na umarce ka, kada ka rage ko ɗaya.

3 Mai yiwuwa ne su ji, har kowa ya juyo ya bar muguwar hanyarsa. Ni ma sai in janye masifar da na yi niyyar aukar musu da ita, saboda mugayen ayyukansu.”

4 Ubangiji ya faɗa wa Irmiya ya ce wa jama’a, “Haka Ubangiji ya ce, idan ba za ku kasa kunne gare ni ba, ku yi tafiya a dokata wadda na sa a gabanku ba,

5 ku kuma kula da zantuttukan bayina, annabawa, waɗanda na yi ta aiko muku, to, amma ba ku kula ba.

6 Saboda haka zan mai da wannan Haikali kamar Shilo, in mai da wannan birni ya zama abin la’ana ga dukan al’umman duniya.”

7 Firistoci, da annabawa, da dukan jama’a sun ji dukan maganan nan da Irmiya ya faɗa a cikin Haikalin Ubangiji.

8 Sa’ad da Irmiya ya gama faɗar dukan abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa wa dukan jama’a, sai firistoci, da annabawa, da dukan jama’a suka kama shi, suna cewa, “Mutuwa za ka yi!

9 Don me ka yi annabci da sunan Ubangiji, ka ce wannan Haikali zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kufai, ba mazauna a ciki?” Sai jama’a duk suka taru, suka kewaye Irmiya cikin Haikalin Ubangiji.

10 Sa’ad da sarakunan Yahuza suka ji waɗannan al’amura, sai suka fito daga gidan sarki zuwa Haikalin Ubangiji, suka zauna a bakin Sabuwar Ƙofa ta Haikalin Ubangiji.

11 Sai firistoci da annabawa suka faɗa wa sarakunan nan da jama’a duka, suka ce, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa, gama ya yi annabci gāba da wannan birni kamar yadda kuka ji da kunnuwanku.”

12 Sa’an nan sai Irmiya ya yi magana da dukan sarakuna da dukan jama’a, ya ce, “Ubangiji ne ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan Haikali da wannan birni, da irin maganar da kuka ji.

13 Saboda haka yanzu sai ku gyara al’amuranku da ayyukanku, ku yi biyayya kuma da muryar Ubangiji Allahnku. Ubangiji kuwa zai janye masifar da ya hurta gāba da ku.

14 Amma ni kaina kuwa a hannunku nake, sai ku yi mini yadda kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku.

15 Ku tabbata dai, idan kuka kashe ni, za ku jawo hakkin jinin marar laifi a kanku da a kan wannan birni da mazauna a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”

16 Sarakuna kuwa da dukan jama’a suka ce wa firistoci da annabawa, “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.”

17 Sai waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka miƙe tsaye, suka ce wa dukan taron jama’a,

18 “Mika kuwa, mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya, Sarkin Yahuza, ya faɗa wa dukan mutanen Yahuza cewa,

‘Ga abin da Ubangiji Mai Runduna

ya ce,

Za a nome Sihiyona kamar gona,

Urushalima kuwa za ta zama tsibin

juji,

Ƙwanƙolin dutsen Haikalin zai zama

kurmi.’

19 Ashe, Hezekiya Sarkin Yahuza da dukan Yahuza sun kashe shi ne? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji, ya roƙi alherinsa ba? Ashe, Ubangiji bai janye masifar da ya hurta a kansu ba? Yanzu fa gab muke da mu jawo wa kanmu babbar masifa.”

20 Akwai wani mutum kuma wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji. Sunansa Uriya ɗan Shemaiya mutumin Kiriyat-yeyarim. Ya yi annabci gāba da birnin nan da ƙasan nan da magana irin ta Irmiya.

21 Sa’ad da sarki Yehoyakim, da dukan jarumawansa, da dukan sarakunansa suka ji maganarsa, sai sarki yana so ya kashe shi, amma sa’ad da Uriya ya ji, sai ya ji tsoro, ya gudu ya tsere zuwa Masar.

22 Sa’an nan sai sarki Yehoyakim ya aiki waɗansu mutane zuwa Masar, wato Elnatan ɗan Akbor da waɗansu tare da shi.

23 Suka kamo Uriya daga Masar suka kawo shi wurin sarki Yehoyakim, sai ya sa aka kashe shi da takobi, aka binne gawarsa a makabartar talakawa.

24 Amma Ahikam ɗan Shafan yana tare da Irmiya, saboda haka ba a bashe shi ga mutane don su kashe shi ba.

Categories
IRM

IRM 27

Irmiya Ya Ɗaura Karkiyar Shanu a Wuyansa

1 A farkon sarautar Zadakiya ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, Ubangiji ya yi wa Irmiya magana.

2 Ya ce ya yi wa kansa karkiyar itace da maɗaurai na fata ya ɗaura su a wuyansa,

3 ya aika da magana zuwa ga Sarkin Edom, da Sarkin Mowab, da Sarkin Ammon, da Sarkin Taya, da Sarkin Sidon ta hannun manzannin da suka zo Urushalima wurin Zadakiya Sarkin Yahuza.

4 Ubangiji ya ce wa Irmiya ya umarce su, su tafi, su faɗa wa iyayengijinsu cewa, “In ji Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ga abin da za ku faɗa wa iyayengijinku,

5 ‘Ni ne da ikona da ƙarfina na yi duniya, da mutane, da dabbobi waɗanda suke cikinta. Nakan ba da ita ga wanda na ga dama.

6 Yanzu fa na ba bawana Nebukadnezzar, Sarkin Babila, dukan ƙasashen nan, na kuma ba shi namomin jeji su bauta masa.

7 Dukan ƙasashe za su bauta masa, da shi da ɗansa, da jikansa, har lokacin da na sa ƙasar ta fāɗi, sa’an nan al’ummai masu yawa da manyan sarakuna za su bautar da shi.

8 “ ‘Amma idan wata al’umma ko wani mulki bai yarda ya bauta wa Nebukadnezzar, Sarkin Babila ba, bai kuma ɗaura karkiyar Sarkin Babila a wuyansa ba, zan hukunta wa wannan al’umma da takobi, da yunwa, da annoba, har in hallaka ta, ta hannun Nebukadnezzar, ni Ubangiji na faɗa.

9 Saboda haka kada ku saurari annabawanku, da masu duba, da masu mafarkai, da matsubbata, ko masu sihiri waɗanda suka ce muku ba za ku bauta wa Sarkin Babila ba.

10 Suna yi muku annabcin ƙarya ne, za su kuwa sa a kai ku wata ƙasa nesa da ƙasarku. Zan kore ku, za ku kuwa lalace.

11 Amma duk al’ummar da za ta ɗaura karkiyar Sarkin Babila a wuyanta, ta kuma bauta masa, zan bar ta a ƙasarta, ta yi noman ƙasarta, ta zauna a ciki, ni Ubangiji na faɗa.’ ”

12 Sai na faɗa wa Zadakiya Sarkin Yahuza wannan magana cewa, “Ka ɗaura karkiyar Sarkin Babila a wuyanka, ka bauta masa, shi da mutanensa, don ka rayu!

13 Don me kai da mutanenka za ku mutu ta takobi, da yunwa, da annoba, kamar yadda Ubangiji ya yi magana a kan kowace al’umma da ta ƙi ta bauta wa Sarkin Babila?

14 Kada ka kasa kunne ga maganar annabawan da suke ce maka, ‘Ba za ku bauta wa Sarkin Babila ba.’ Annabcin ƙarya suke yi muku.

15 Gama Ubangiji ya ce shi bai aike su ba, annabcin ƙarya suke yi muku da sunansa, don ya kore ku, ku halaka, ku da annabawan da suke yi muku annabci.”

16 Sa’an nan na faɗa wa firistoci da jama’a cewa, “In ji Ubangiji, kada ku kasa kunne ga abin da annabawanku suke muku annabci cewa, ‘Ba da daɗewa ba za a komo da kayan Haikalin Ubangiji daga Babila.’ Ƙarya ce suke yi muku.

17 Kada ku ji su, amma ku bauta wa Sarkin Babila don ku rayu! Don me birnin nan zai zama kufai?

18 Idan su annabawa ne, idan kuwa Ubangiji yana magana da su, to, bari su roƙi Ubangiji Mai Runduna kada a tafi Babila da kayayyakin da suka ragu a Haikalin Ubangiji, da a fādar Sarkin Yahuza, da a Urushalima.

19 Gama Ubangiji Mai Runduna ya faɗi zancen ginshiƙai, da babbar kwatarniya, da dakalai, da sauran kayayyaki da aka bar su a birnin nan,

20 wato waɗanda Nebukadnezzar, Sarkin Babila bai kwashe ba a lokacin da ya tafi da Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, da dukan dattawan Yahuza da na Urushalima zuwa bauta a Babila.

21 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya faɗa a kan kayayyakin da suka ragu a Haikalin Ubangiji, da a fādar Sarkin Yahuza, da a Urushalima,

22 ‘Za a kwashe su a kai Babila, a can za su kasance har lokacin da zan sāke kulawa da su. Sa’an nan ne zan komo da su, in maishe su a wannan wuri.’ ”

Categories
IRM

IRM 28

Annabcin Ƙarya na Hananiya

1 Ya zama fa a wannan shekara, a watan biyar, a shekara ta huɗu ta sarautar Zadakiya Sarkin Yahuza, sai annabi Hananiya ɗan Azzur mutumin Gibeyon, ya yi magana da ni a Haikalin Ubangiji, a gaban firistoci da dukan jama’a, ya ce,

2 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya faɗa, ‘Na karya karkiyar Sarkin Babila.

3 Bayan shekara biyu zan komo da kayayyakin Haikalin Ubangiji zuwa wurin nan. Kayayyakin da Nebukadnezzar, Sarkin Babila ya kwashe daga wannan wuri, ya kai Babila.

4 Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, da dukan waɗanda aka kai su zaman talala daga Yahuza, gama zan karya karkiyar Sarkin Babila.’ ”

5 Sa’an nan annabi Irmiya ya yi magana da annabi Hananiya a gaban firistoci da dukan jama’ar da suke tsaye a Haikalin Ubangiji, ya ce,

6 “Amin, amin, Ubangiji ya sa ya zama haka, Ubangiji ya sa annabcin da ka yi ya zama gaskiya, Ubangiji ya komo da kayayyakin Haikalinsa da dukan waɗanda aka kai su zaman talala a Babila.

7 Amma yanzu sai ka ji maganan nan da zan faɗa maka, kai da dukan jama’an nan.

8 Annabawan da suka riga mu, ni da kai a zamanin dā, sun yi wa ƙasashe masu yawa da manyan mulkoki annabcin yaƙi da yunwa, da annoba.

9 Idan maganar wannan annabi kuwa da ya yi annabcin salama ta cika, sa’an nan ne za a sani gaskiya Ubangiji ne ya aiko shi.”

10 Sai annabi Hananiya ya cire karkiyar daga wuyan annabi Irmiya ya karya ta.

11 Sa’an nan Hananiya ya yi magana a gaban dukan jama’a, ya ce, “In ji Ubangiji, haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar, Sarkin Babila, daga wuyan dukan al’ummai kafin shekara biyu.” Sai annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.

12 Da ɗan daɗewa bayan da annabi Hananiya ya karya karkiyar da take a wuyan annabi Irmiya, sai Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce

13 ya tafi ya faɗa wa Hananiya, ya ce, “Haka Ubangiji ya ce, ‘Ka karya karkiya ta itace, amma zan yi karkiya ta ƙarfe a maimakonta.

14 Gama haka, ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, na faɗa. Na sa wa wuyan dukan waɗannan al’ummai karkiya ta ƙarfe, don su bauta wa Nebukadnezzar, Sarkin Babila, za su kuwa bauta masa, gama na ba shi su, har da namomin jeji.’ ”

15 Sai annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka ji, ya Hananiya, Ubangiji bai aike ka ba, kana sa mutanen nan su dogara ga ƙarya.

16 Saboda haka, in ji Ubangiji, ‘Zan kawar da kai daga duniya. Za ka mutu a wannan shekara domin ka kuta tayarwa ga Ubangiji.’ ”

17 A wannan shekara kuwa, a watan bakwai, sai annabi Hananiya ya mutu.

Categories
IRM

IRM 29

Wasiƙar Irmiya Zuwa ga Yahudawan da suke Babila

1 Ga maganar wasiƙar da annabi Irmiya ya aika daga Urushalima zuwa ga dattawa, da firistoci, da annabawa, da dukan mutanen da Nebukadnezzar ya kwaso daga Urushalima zuwa Babila. (

2 Ya rubuta wannan bayan tashin sarki Yekoniya, da uwa tasa, da bābāni, da sarakunan Yahuza, da na Urushalima, da gwanayen aikin hannu, da maƙera daga Urushalima.)

3 Ya aika da wasiƙar ta hannun Elasa ɗan Shafan, da Gemariya ɗan Hilkiya waɗanda Zadakiya Sarkin Yahuza ya aika zuwa Babila, wurin Nebukadnezzar, Sarkin Babila. Ga abin da wasiƙar ta ce.

4 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce wa dukan waɗanda aka kai bauta, wato waɗanda ya aika da su bauta daga Urushalima zuwa Babila.

5 ‘Ku gina gidaje, ku zauna a ciki, ku dasa gonaki, ku ci amfaninsu.

6 Ku auri mata, ku haifi ‘ya’ya mata da maza. Ku auro wa ‘ya’yanku mata, ku aurar da ‘ya’yanku mata, domin su haifi ‘ya’ya mata da maza, ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.

7 Amma ku nemi zaman lafiyar birni inda na sa aka kai ku zaman talala, ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, gama zaman lafiyar birnin shi ne naku zaman lafiyar.’

8 Gama haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya faɗa. ‘Kada ku yarda annabawanku da malamanku na duba waɗanda suke tare da ku su ruɗe ku, kada ku kasa kunne ga mafarkansu.

9 Gama annabcin da suke yi muku da sunana, ƙarya ne, ni ban aike su ba.’

10 “Ubangiji ya ce, ‘Sa’ad da kuka cika shekara saba’in a Babila, zan ziyarce ku, zan kuwa cika muku alkawarina. Zan komo da ku zuwa wannan wuri.

11 Gama na san irin shirin da na yi muku, ni Ubangiji na faɗa. Shirin alheri, ba na mugunta ba. Zan ba ku gabata da sa zuciya.

12 Sa’an nan za ku yi kira a gare ni, ku yi addu’a a wurina, zan kuwa ji ku.

13 Za ku neme ni ku same ni, idan kun neme ni da zuciya ɗaya.

14 Za ku same ni, ni Ubangiji na faɗa, zan mayar muku da arzikinku, in tattaro ku daga cikin dukan al’ummai da dukan wurare inda na kora ku, ni Ubangiji na faɗa, zan komo da ku a wurin da na sa a kwashe ku a kai ku zaman talala.’

15 “Domin kun ce, Ubangiji ya ba ku annabawa a Babila,

16 ku ji abin da Ubangiji ya faɗa a kan sarkin da ya hau gadon sarautar Dawuda, da a kan dukan jama’ar da suke zaune a wannan birni, wato a kan danginku waɗanda ba a kwashe su zuwa zaman talala ba.

17 Haka Ubangiji Mai Runduna ya ce, ‘Ga shi, zan aiko musu da takobi, da yunwa, da masifa, zan maishe su kamar ruɓaɓɓen ɓaure waɗanda suka lalace ƙwarai, har ba su ciwuwa.

18 Zan fafare su da takobi, da yunwa, da masifa. Zan maishe su abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya. Za su zama abin la’ana, da abin razana, da abin raini, da abin zargi, ga dukan al’ummai, inda na kora su.

19 Domin ba su ji maganata wadda ni Ubangiji na faɗa ba, na yi ta aika muku da ita ta wurin bayina annabawa, amma kuka ƙi, ni Ubangiji na faɗa.

20 Ku ji maganar Ubangiji, dukanku da aka kai ku zaman talala waɗanda na kora daga cikin Urushalima zuwa Babila.’

21 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce a kan Ahab ɗan Kolaya, da Zadakiya ɗan Ma’aseya, waɗanda suke yi muku annabcin ƙarya da sunana. ‘Ga shi, zan bashe su a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila, zai kashe su a kan idonku.

22 Saboda su duka waɗanda aka kai bautar talala daga Yahuza zuwa Babila, za su mori kalman nan suna yin la’ana cewa, “Ubangiji ya maishe ka kamar Zadakiya da Ahab, waɗanda Sarkin Babila ya gasa da wuta!”

23 Gama sun yi wauta a Isra’ila, sun yi zina da matan maƙwabtansu, sun yi ƙarya da sunana, ni kuwa ban umarce su ba. Ni na sani, ni ne kuma shaida, ni Ubangiji na faɗa.

Saƙo ga Shemaiya

24 “Zancen Shemaiya mutumin Nehelam,

25 haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya faɗa. Ga shi, ka aika da wasiƙu da sunanka zuwa ga dukan jama’ar da suke a Urushalima, da zuwa ga Zafaniya ɗan Ma’aseya, firist, da kuma ga dukan firistoci, cewa

26 Ubangiji ya naɗa ka firist a madadin Yehoyada firist, ka lura da Haikalin Ubangiji, ka sa kowane mahaukacin da zai yi annabci a turu, ka sa masa ƙangi.

27 To, me ya sa ba ka tsauta wa Irmiya, mutumin Anatot, wanda yake yin maka annabci ba?

28 Gama ya aiko mana a Babila, cewa za mu daɗe a zaman talala, mu gina wa kanmu gidaje, mu zauna a ciki, mu dasa gonaki mu ci amfaninsu.”

29 Sai Zafaniya firist, ya karanta wasiƙan nan a gaban annabi Irmiya.

30 Ubangiji kuwa ya yi magana da Irmiya, ya ce,

31 ya aika wa dukan waɗanda suke zaman talala ya ce, “Haka Ubangiji ya ce a kan Shemaiya mutumin Nehelam, ‘Saboda Shemaiya ya yi muku annabci, alhali ni ban aike shi ba, ya sa ku dogara ga ƙarya,’

32 saboda haka Ubangiji ya ce, ‘ga shi, zan hukunta Shemaiya, mutumin Nehelam, shi da zuriyarsa ba za a bar masa mai rai ko ɗaya a wannan jama’a ba, wanda zai ga irin alherin da zan yi wa jama’ata, gama ya kuta tayarwa ga Ubangiji,’ ” in ji Ubangiji.

Categories
IRM

IRM 30

Tabbatarwar Komowa daga Zaman Talala

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce,

2 “Ni Ubangiji Allah na Isra’ila na ce, ‘Ka rubuta dukan maganar da na faɗa maka a littafi.

3 Gama kwanaki suna zuwa sa’ad da zan komo da mutanena, wato Isra’ila da Yahuza. Zan komo da su zuwa ƙasar da na ba kakanninsu, za su kuwa mallake ta,’ ni Ubangiji na faɗa.”

4 Waɗannan ne maganar da Ubangiji ya faɗa a kan Isra’ila da Yahuza.

5 “Ni Ubangiji na ce,

Mun ji kukan gigitacce,

Kukan firgita ba kuma salama.

6 Yanzu ku tambaya, ku ji,

Namiji ya taɓa haihuwa?

To, me ya sa nake ganin kowane

namiji yana riƙe da kwankwaso,

Kamar mace mai naƙuda,

Fuskar kowa kuma ta yi yaushi?

7 Kaito, gama wannan babbar rana ce,

Ba kuma kamarta,

Lokaci ne na wahala ga Yakubu,

Duk da haka za a cece shi daga

cikinta.”

8 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “A wannan rana zan karya karkiya da take a wuyansu, in cire musu ƙangi, ba kuma za su ƙara zama bayin baƙi ba.

9 Amma za su bauta mini, ni Ubangiji Allahnsu, da Dawuda sarkinsu, wanda zan tayar musu da shi.”

10 Ubangiji ya ce,

“Kada ka ji tsoro, ya barana

Yakubu,

Kada kuma ka yi fargaba, ya

Isra’ila,

Gama zan cece ka daga ƙasa mai

nisa,

Zan kuma ceci zuriyarka daga ƙasar

bautarsu.

Yakubu zai komo, ya yi zamansa rai

a kwance,

Ba kuwa za a tsoratar da shi ba.

11 Gama ina tare da kai don in cece ka,

Zan hallaka dukan al’ummai sarai,

Inda na warwatsa ku.

Amma ku ba zan hallaka ku ba,

Zan hore ku da adalci,

Ba yadda za a yi in ƙyale ku ba

hukunci,

Ni Ubangiji na faɗa.”

12 Ubangiji ya ce,

“Rauninku ba ya warkuwa,

Mikinku kuwa mai tsanani ne

ƙwarai.

13 Ba wanda zai kula da maganarku,

Ba magani domin mikinku,

Ba za ku warke ba.

14 Dukan masu ƙaunarku sun manta

da ku,

Ba su ƙara kulawa da ku,

Domin na yi muku bugu irin na

maƙiyi.

Na yi muku horo irin na maƙiyi

marar tausayi,

Domin laifofinku masu girma ne,

Domin zunubanku da yawa suke.

15 Don me kuke kuka a kan

rauninku?

Ciwonku ba zai warke ba.

Saboda laifofinku masu girma ne,

Domin zunubanku da yawa suke,

Shi ya sa na yi muku waɗannan

abubuwa.

16 Domin haka dukan waɗanda suka

cinye ku, za a cinye su,

Dukan maƙiyanku, kowane ɗayansu

zai tafi bauta,

Waɗanda suka washe ku, za a washe

su.

Dukan waɗanda suka kwashe ku

ganima, su ma za a kwashe su

ganima.

17 Zan mayar muku da lafiyarku,

Zan kuma warkar da raunukanku,

Ko da yake maƙiyanku suna

kiranku yasassu,

Suna cewa, ‘Ai, Sihiyona ce, ba

wanda ya kula da ita.’

Ni Ubangiji na faɗa.”

18 Ubangiji ya ce,

“Ga shi, zan komar wa alfarwar

Yakubu arzikinta,

Zan kuma nuna wa wuraren zamansa

jinƙai,

Za a sāke gina birnin a kufansa,

Fādar kuma za ta kasance a inda

take a dā.

19 Daga cikinsu za a ji waƙoƙin godiya.

Da muryoyin masu murna.

Zai riɓaɓɓanya su, ba za su zama

kaɗan ba,

Zan kuwa ɗaukaka su, ba za a

ƙasƙantar da su ba.

20 ‘Ya’yansu za su zama kamar dā,

Jama’arsu kuma za su kahu a

gabana,

Zan hukunta dukan waɗanda suka

zalunce su.

21 Sarkinsu zai zama ɗaya daga

cikinsu,

Mai mulkinsu kuma zai fito daga

cikinsu.

Zan kawo shi kusa, zai kuwa kusace

ni,

Gama wane ne zai yi ƙarfin hali ya

kusace ni? Ni Ubangiji na faɗa.

22 Za ku zama mutanena,

Ni kuwa zan zama Allahnku.”

23 Ga hadirin hasalar Ubangiji ya taso,

wato iskar guguwa,

Zai huce a kan mugaye.

24 Zafin fushin Ubangiji ba zai huce ba,

Sai ya aikata, ya kammala abubuwan

da ya yi niyya a tunaninsa.

A nan gaba mutanensa za su fahimci

wannan.