Categories
IRM

IRM 31

1 Ubangiji ya ce, “Lokaci yana zuwa da zan zama Allah na dukan iyalan Isra’ila, za su kuwa zama jama’ata.”

2 Haka Ubangiji ya ce, “Jama’ar da

suka tsere wa takobi,

Sun sami alheri a cikin jeji,

A sa’ad da Isra’ila suka nemi

hutawa.”

3-4 Ubangiji ya bayyana gare ni tun

daga nesa cewa,

“Ya Isra’ila, budurwa!

Na kusace ki da madawwamiyar

ƙaunata,

Ba zan fasa amintacciyar ƙaunata a

gare ki ba.

Zan sāke gina ki,

Za ki kuwa ginu,

Za ki ɗauki kayan kaɗe-kaɗe,

Za ki shiga rawar masu murna.

5 Za ki sāke dasa gonar inabi

A kan duwatsun Samariya,

Masu dashe za su dasa,

Za su mori ‘ya’yan.

6 Gama rana tana zuwa sa’ad da mai

tsaro zai yi kira

A ƙasar tudu ta Ifraimu, ya ce,

‘Ku tashi mu haura zuwa Sihiyona

Zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’ ”

7 Ga abin da Ubangiji ya ce,

“Raira wa Yakubu waƙar farin ciki

da ƙarfi,

Ku ta da murya saboda shugaban

al’ummai,

Ku yi shela, ku yi yabo, ku ce,

‘Ya Ubangiji ka ceci jama’arka,

Wato ringin mutanen Isra’ila,’

8 Ga shi, zan fito da su daga ƙasar

arewa,

Zan tattaro su daga manisantan

wurare na duniya,

Tare da su makafi da guragu,

Da mace mai goyo da mai naƙuda,

Za su komo nan a babbar ƙungiya.

9 Da kuka za su komo.

Da ta’aziyya zan bishe su, in komar

da su,

Zan sa su yi tafiya a gefen rafuffukan

ruwa,

A kan miƙaƙƙiyar hanya, inda ba

za su yi tuntuɓe ba.

Gama ni uba ne ga Isra’ila,

Ifraimu kuwa ɗan farina ne.”

10 “Ku ji maganar Ubangiji,

Ya ku al’ummai,

Ku yi shelarsa har a ƙasashen da suke

nesa, na gāɓar teku.

Ku ce, ‘Shi wanda ya warwatsa

Isra’ila zai tattaro ta,

Zai kiyaye ta kamar yadda makiyayi

yakan kiyaye garkensa.’

11 Gama Ubangiji ya fanshi Yakubu.

Ya fanshe shi daga hannuwan

waɗanda suka fi ƙarfinsa.

12 Za su zo su raira waƙa da ƙarfi,

A bisa ƙwanƙolin Sihiyona,

Za su yi annuri saboda alherin

Ubangiji,

Saboda hatsi, da ruwan inabi, da

mai,

Saboda ‘ya’yan tumaki da na shanu.

Rayuwarsu za ta zama kamar

lambu,

Ba za su ƙara yin yaushi ba.

13 Sa’an nan ‘yan mata za su yi rawa

da farin ciki,

Samari da tsofaffi za su yi murna.

Zan mai da makokinsu ya zama

murna,

Zan ta’azantar da su, in ba su farin

ciki maimakon baƙin ciki.

14 Zan yi wa ran firistoci biki da

wadata,

Jama’ata za su ƙoshi da alherina,

Ni Ubangiji na faɗa.”

15 Ga abin da Ubangiji ya ce,

“An ji murya daga Rama,

Muryar baƙin ciki da kuka mai zafi,

Rahila tana kuka saboda ‘ya’yanta,

ba su.

16 Ki yi shiru, ki daina kuka,

Ki shafe hawaye daga idanunki.

Za a sāka miki wahalarki,

Za su komo daga ƙasar abokin gāba,

Ni Ubangiji na faɗa.

17 Akwai sa zuciya dominki a nan

gaba,

Ni Ubangiji na faɗa.

‘Ya’yanki za su komo ƙasarsu.

18 “Na ji Ifraimu yana baƙin ciki, yana

cewa,

‘Ka hore ni, na kuwa horu,

Kamar ɗan maraƙin da ba shi da

horo,

Ka komo da ni don in zama kamar

yadda nake a dā,

Gama kai ne Ubangiji Allahna.

19 Gama na tuba saboda na rabu da

kai,

Bayan da aka ganar da ni, sai na

sunkuyar da kai,

Kunya ta kama ni, na gigice,

Domin ina ɗauke da wulakancin

ƙuruciyata.’

20 Ashe, Ifraimu ba ƙaunataccen

ɗana ba ne?

Ashe, shi ba ɗan gaban goshina ba

ne?

A duk lokacin da na ambace shi a

kan muguntarsa

Nakan tuna da shi da ƙauna.

Saboda na ƙwallafa zuciyata a

kansa,

Hakika zan yi masa jinƙai, ni

Ubangiji na faɗa.”

21 Ki kafa wa kanki alamun hanya,

Ki kafa wa kanki shaidu,

Ki lura da gwadabe da kyau,

Hanyar da kin bi, kin tafi.

Ya budurwa Isra’ila, ki komo,

Komo zuwa biranen nan naki.

22 Har yaushe za ki yi ta shakka,

Ya ke ‘yar marar bangaskiya?

Gama Ubangiji ya halitta sabon abu

a duniya,

Mace ce za ta kāre namiji.”

23 Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya ce, “Nan gaba za su sāke yin magana a ƙasar Yahuza da biranenta a sa’ad da na mayar musu da dukiyarsu.

‘Ubangiji ya sa maka albarka,

Ya wurin zaman adalci,

Ya tsattsarkan tudu!’

24 Yahuza kuwa da dukan biranenta za su zauna tare a can, da manoma, da makiyaya, da garkunansu.

25 Gama zan biya bukatar waɗanda suka gaji, in wartsakar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”

26 Irmiya ya farka, ya ce, “Ina kuwa cikin barcina mai daɗi sai na farka na duba.”

Sabon Alkawari

27 “Ni Ubangiji na ce, ga shi, zan sa mutane da dabbobi su cika ƙasashen Isra’ila da na Yahuza.

28 Zai zama kamar yadda na lura da su don a tumɓuke su, a rushe su, a lalatar da su, a kawo musu masifa, haka kuma zan lura da su, a kuma dasa su, ni Ubangiji na faɗa.

29 A waɗannan kwanaki ba za su ƙara cewa,

‘Ubanni suka ci ‘ya’yan inabi masu

tsami,

Haƙoran ‘ya’ya suka mutu’ ba.

30 Amma kowa zai mutu saboda

zunubin kansa,

Wanda ya ci inabi masu tsami,

Shi ne haƙoransa za su mutu.”

31 Ubangiji ya ce, “Ga shi, kwanaki suna zuwa da zan yi sabon alkawari da mutanen Isra’ila da na Yahuza.

32 Ba irin wanda na yi da kakanninsu ba, sa’ad da na fito da su daga ƙasar Masar, alkawarin da suka karya, ko da yake ni Ubangijinsu ne, ni Ubangiji na faɗa.

33 Amma wannan shi ne alkawarin da zan yi da mutanen Isra’ila bayan waɗancan kwanaki, ni Ubangiji na faɗa. Zan sa dokokina a cikinsu, zan rubuta su a zukatansu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama jama’ata.

34 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabcinsa, ko ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji’ ba, gama su duka za su san ni, tun daga ƙarami har zuwa babba. Zan gafarta musu laifofinsu, ba kuwa zan ƙara tunawa da zunubansu ba.”

35 Haka Ubangiji ya ce,

Shi wanda ya ba da rana ta haskaka

yini,

Ya sa wata da taurari su ba da haske

da dare,

Shi ne yakan dama teku, ya sa

raƙumanta su yi ruri,

Sunansa Ubangiji Mai Runduna.

36 “Idan dai wannan kafaffiyar ka’ida

ta daina aiki a gabana,

Ni Ubangiji na faɗa,

To, ashe, zuriyar Isra’ila za ta daina

zama al’umma a gabana ke nan

har abada.

37 Idan a iya auna sammai a kuma iya

bincike tushen duniya a ƙarƙas,

To, ashe, zan watsar da dukan

zuriyar Isra’ila ke nan saboda

dukan abin da suka yi,

Ni Ubangiji na faɗa.

38 “Ga shi, kwanaki suna zuwa da za a sāke gina birnin domin Ubangiji, ni Ubangiji na faɗa, tun daga hasumiyar Hananel zuwa yamma, har zuwa Ƙofar Kan Kusurwa.

39 Sa’an nan ma’aunin zai daɗa gaba, har ya kai tudun Gareb, sa’an nan ya nausa zuwa Gowa.

40 Dukan filin kwarin gawawwaki da toka, da dukan filaye har zuwa rafin Kidron zuwa kan kusurwar Ƙofar Doki wajen gabas, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke shi ko a rushe shi ba har abada.”

Categories
IRM

IRM 32

Irmiya Ya Sayi Saura a Anatot

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a shekara ta goma ta mulkin Zadakiya, Sarkin Yahuza. A lokacin kuwa Nebukadnezzar yana da shekara goma sha takwas da sarauta a Babila.

2 A lokacin nan kuwa sojojin Sarkin Babila sun kewaye Urushalima da yaƙi, annabi Irmiya kuwa yana a tsare a gidan waƙafi, a fādar Sarkin Yahuza.

3 Zadakiya Sarkin Yahuza, ya sa shi a kurkuku, gama ya ce, “Don me kake yin annabci? Ka ce, Ubangiji ya ce, ga shi, zai ba da wannan birni a hannun Sarkin Babila, zai kuwa cinye shi da yaƙi.

4 Zadakiya Sarkin Yahuza kuwa, ba zai tsere wa Kaldiyawa ba, amma za a ba da shi a hannun Sarkin Babila. Zai yi magana da shi fuska da fuska, ya kuma gan shi ido da ido.

5 Sarkin Babila kuwa zai tafi da Zadakiya zuwa Babila. Zai zauna can sai lokacin da na ziyarce shi. Ko da ya yi yaƙi da Kaldiyawa ba zai yi nasara ba.”

6 Irmiya ya ce, “Ubangiji ya yi magana da ni, cewa

7 ga shi, Hanamel, ɗan Shallum kawuna, zai zo wurina ya ce mini, ‘Ka sayi gonata wadda take a Anatot, gama kai ne ka cancanci ka fanshe ta, sai ka saye ta.’ ”

8 Sai Hanamel ɗan kawuna ya zo wurina a gidan waƙafi, bisa ga faɗar Ubangiji, ya ce mini, “Ka sayi gonata wadda take a Anatot a ƙasar Biliyaminu, gama kai ne ka cancanta ka mallake ta, kai ne za ka fanshe ta, sai ka saye ta.” Sa’an nan na sani wannan maganar Ubangiji ce.

9 Sai na sayi gonar a Anatot daga hannun Hanamel ɗan kawuna, na biya shi shekel goma sha bakwai na azurfa.

10 Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna kuɗin da ma’auni.

11 Na ɗauki takardun ciniki waɗanda aka rubuta sharuɗan a ciki da wadda aka liƙe da wadda ba a liƙe ba,

12 na ba Baruk, ɗan Neriya, ɗan Ma’aseya, a gaban Hanamel, ɗan kawuna, da gaban shaidun da suka sa hannun a takardar shaidar sayen, da gaban dukan Yahudawa waɗanda suke zaune a gidan waƙafi.

13 Sai na umarci Baruk a gabansu cewa,

14 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya ce, ‘Ka ɗauki waɗannan takardun shaida, wadda aka liƙe da wadda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tukunyar ƙasa domin kada su lalace.’

15 Gama haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya faɗa, ‘Gidaje, da gonaki, da gonakin inabi, za a sāke sayensu a ƙasan nan.’ ”

Addu’ar Irmiya

16 Bayan da na ba Baruk, ɗan Neriya, takardar sharuɗan ciniki, sai na yi addu’a ga Ubangiji, na ce,

17 “Ya Ubangiji Allah, kai ne ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka da ƙarfinka, ba abin da ya fi ƙarfinka.

18 Kakan nuna madawwamiyar ƙauna ga dubbai, amma kakan hukunta wa ‘ya’ya saboda laifin ubanninsu. Ya maigirma Maɗaukaki, Allah, sunanka kuwa Ubangiji Mai Runduna.

19 Kai babban mashawarci ne, mai aikata manyan ayyukanka. Kana ganin dukan ayyukan ‘yan adam. Kakan sāka wa kowa bisa ga halinsa da ayyukansa.

20 Ka aikata alamu da al’ajabai a ƙasar Masar. Har wa yau kuma kana aikata su a Isra’ila da kuma cikin dukan al’ummai, ka yi wa kanka suna kamar yadda yake a yau.

21 Ta wurin alamu da al’ajabai, da iko, da ƙarfi, da banrazana, ka fito da jama’arka Isra’ila daga ƙasar Masar.

22 Ka kuwa ba su wannan ƙasa wadda ka rantse za ka ba kakanninsu. Ƙasar da take cike da yalwar albarka.

23 Amma sa’ad da suka shiga cikinta suka mallake ta, ba su yi biyayya da muryarka ba, ba su kiyaye dokokinka ba, ba su aikata dukan abin da ka umarce su ba, saboda haka ka sa wannan masifa ta auko musu.

24 “Ga shi, Kaldiyawa sun gina mahaurai kewaye da birnin da suka kewaye shi da yaƙi. Saboda takobi, da yunwa, da annoba aka ba da birnin a hannun Kaldiyawa, waɗanda suke yaƙi da birnin. Abin da ka faɗa ya tabbata, ka kuwa gani.

25 Duk da haka ya Ubangiji Allah, ka ce mini, ‘Sayi gonar da kuɗi, a gaban shaidu, ko da yake an ba da birnin a hannun Kaldiyawa.’ ”

26 Ubangiji kuwa ya ce wa Irmiya,

27 “Ni ne Ubangiji Allah na dukan ‘yan adam, ba abin da ya fi ƙarfina.

28 Saboda haka, ni Ubangiji, na ce zan ba da wannan birni a hannun Kaldiyawa da hannun Nebukadnezzar Sarkin Babila, za su ci birnin.

29 Kaldiyawa da suke yaƙi da wannan birni za su zo, za su ƙone wannan birni da wuta ƙurmus, da gidaje waɗanda aka ƙona turare ga Ba’al a kan rufinsu. Aka kuma miƙa hadayu na sha ga gumaka, don su tsokane ni in yi fushi.

30 Gama jama’ar Isra’ila da ta Yahuza, tun daga ƙuruciyarsu, ba su aikata kome a gabana ba sai mugunta, ba abin da jama’ar Isra’ila suka yi, sai tsokanata da gumaka don in yi fushi da ayyukan hannuwansu, ni Ubangiji na faɗa.

31 Wannan birni ya tsokane ni ƙwarai tun lokacin da aka gina shi har zuwa yau, domin haka zan kawar da shi daga gabana.

32 Wannan kuwa saboda muguntar jama’ar Isra’ila ce da ta Yahuza, wadda suka yi don su tsokane ni in yi fushi, su da sarakunansu, da shugabanninsu, da firistocinsu, da annabawansu, da mutanen Yahuza, da mazaunan Urushalima.

33 Sun juya mini baya, ba su fuskance ni ba, ko da yake na yi ta koya musu, amma ba su saurara ga koyarwata ba.

34 Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin Haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.

35 Sun gina wa Ba’al masujadai a kwarin ɗan Hinnom don su miƙa ‘ya’yansu mata da maza hadaya ga Molek, ni kuwa ban umarce su ba, ba shi kuwa a tunanina. Ga shi, sun aikata wannan abin banƙyama, don su sa Yahuza ta yi zunubi.”

Alkawari na Sa Zuciya

36 “Domin haka ga abin da ni Ubangiji Allah na Isra’ila na ce a kan wannan birni wanda ka ce, ‘An ba da shi ga Sarkin Babila, da takobi, da yunwa, da annoba.’

37 Ga shi, zan tattaro su daga dukan ƙasashe inda na kora su, da fushina, da hasalata, da haushina. Zan komo da su a wannan wuri, zan sa su su zauna lafiya.

38 Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.

39 Zan ba su zuciya ɗaya, da tafarki ɗaya domin su yi tsorona har abada, domin amfanin kansu da na ‘ya’yansu a bayansu.

40 Zan yi madawwamin alkawari da su, ba zan fasa nuna musu alheri ba, zan kuwa sa tsorona a zukatansu domin kada su bar bina.

41 Zan ji daɗin yi musu alheri. Zan dasa su a wannan ƙasa da aminci da zuciya ɗaya.”

42 Gama haka Ubangiji ya faɗa, “Daidai kamar yadda na kawo wannan babbar masifa a kan jama’an nan, haka kuma zan kawo musu dukan waɗannan alherai da na alkawarta musu.

43 Za a sayi gonaki a wannan ƙasa wadda kake cewa ta zama kufai, ba mutum, ba dabba a ciki, wadda aka ba da ita ga Kaldiyawa.

44 Za a sayi gonaki da kuɗi, a sa hannu a kan sharuɗa, a hatimce su a gaban shaidu, a ƙasar Biliyaminu da wuraren da suke kewaye da Urushalima, da cikin garuruwan Yahuza, da na garuruwan ƙasar tudu, da a garuruwan kwaruruka, da a garuruwan Negeb, gama zan komar wa mutane da wadatarsu a ƙasarsu, ni Ubangiji na faɗa.”

Categories
IRM

IRM 33

Komo da Harka a Urushalima

1 Ubangiji ya sāke yin magana da Irmiya sa’ad da yake a kulle a gidan waƙafi.

2 Ubangiji wanda ya halitta duniya, ya siffata ta, ya kafa ta, sunansa Ubangiji, ya ce,

3 “Ka kira ni, ni kuwa zan amsa maka, zan kuwa nuna maka manyan al’amura masu girma da banmamaki, waɗanda ba ka sani ba.”

4 Gama haka Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya ce, a kan gidajen da suke a wannan birni, da gidajen sarakunan Yahuza, waɗanda aka rurrushe domin a yi wa garukan jigo saboda mahaurai da suka kewaye birni, da kuma saboda yaƙi.

5 “Sa’ad da ake zuwa yaƙi da Kaldiyawa gidaje za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata, gama na ɓoye wa wannan birni zatina saboda dukan muguntarsu.

6 Ga shi, zan kawo wa birnin lafiya, gama zan warkar da su, in wadata su da salama da gaskiya.

7 Zan kuma mayar wa mutanen Yahuza da mutanen Isra’ila da arzikinsu, in sāke kafa su kamar yadda suke a dā.

8 Zan shafe dukan laifin da suka yi mini, in kuma gafarta musu dukan zunubansu da tayarwar da suka yi mini.

9 Sunan wannan birni zai zama mini abin murna, da abin yabo, da darajantawa ga dukan al’umman duniya waɗanda za su ji dukan alherin da na yi dominsu, za su ji tsoro su yi rawar jiki saboda dukan alheri da dukan wadata da na tanada musu.”

10 Haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan wuri da ka ce ya zama kufai, ba mutum ko dabba, wato a biranen Yahuza da titunan Urushalima, inda ba kowa, ba mutum ko dabba a ciki,

11 za a sāke jin muryar murna da ta farin ciki, da muryar ango da ta amarya, da muryoyin mawaƙa, sa’ad da suke kawo hadayun godiya a cikin Haikalin Ubangiji, suna cewa,

‘Ku yi godiya ga Ubangiji Mai

Runduna,

Gama Ubangiji nagari ne,

Gama madawwamiyar ƙaunarsa

tabbatacciya ce.’

Gama zan mayar da arzikin ƙasar kamar yadda yake a dā, ni Ubangiji na faɗa.”

12 Haka Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Wannan wuri wanda yake kufai, inda ba mutum ko dabba, da cikin dukan biranensa, zai sāke zama makiyaya, inda masu kiwo za su zauna da garkunansu.

13 A garuruwan ƙasar tuddai, da na kwaruruka, da na Negeb, da na ƙasar Biliyaminu, da na wuraren da suke kewaye da Urushalima, da na Yahuza, garkuna za su sāke bi ta ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,” in ji Ubangiji.

14 “Ga shi, kwanaki suna zuwa sa’ad da zan cika alkawarin da na yi wa mutanen Isra’ila da na Yahuza.

15 A waɗannan kwanaki da a lokacin nan, zan sa wani reshe mai adalci ya fito daga zuriyar Dawuda, zai aikata gaskiya da adalci a ƙasar.

16 A waɗannan kwanaki za a ceci mutanen Yahuza, mutanen Urushalima kuwa za su zauna lafiya. Sunan da za su sa wa Urushalima birninsu, shi ne, ‘Adalcinmu Ubangiji ne.’

17 Gama ni Ubangiji na ce Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba.

18 Lawiyawa kuma ba za su rasa firistocin da za su tsaya a gabana, suna miƙa hadayun ƙonawa ba, da hadayu na gari na ƙonawa, su kuma miƙa sadaka har abada.”

19 Ubangiji kuma ya yi magana da Irmiya ya ce, “Haka Ubangiji ya faɗa,

20 idan ka iya hana dare da yini su bayyana a ƙayyadaddun lokatansu,

21 to, ashe, alkawarin da na yi wa bawana Dawuda zai tashi ke nan, har ya rasa ɗan da zai yi mulki a gadon sarautarsa, alkawarin kuma da na yi wa firistoci masu yi mini hidima, da ma’aikatana, zai tashi.

22 Kamar yadda ba a iya ƙidaya rundunan sammai ba, ba a iya kuma auna yashin teku ba, haka nan zan yawaita zuriyar bawana Dawuda da Lawiyawa, firistoci, masu yi mini hidima.”

23 Ubangiji kuma ya ce wa Irmiya,

24 “Ba ka ji abin da mutanen nan suke cewa ba? Wai, ‘Ubangiji ya ƙi iyalin nan biyu da ya zaɓa!’ Suka raina jama’ata, ba su kuma maishe ta al’umma ba.

25 Amma ni Ubangiji na ce, idan ban kafa alkawarina game da yini, da kuma game da dare, da ka’idodin da take mulkin sammai da duniya ba,

26 sa’an nan zan ƙi zuriyar Yakubu da bawana Dawuda. Ba kuma zan zaɓi wani daga cikin zuriyarsa ya yi mulkin zuriyar Ibrahim, da ta Ishaku, da ta Yakubu ba. Amma zan mayar musu da arzikinsu, in nuna jinƙai a kansu.”

Categories
IRM

IRM 34

Faɗaka ga Zadakiya

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya sa’ad da Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da dukan sojojinsa, da dukan sojojin mulkokin al’umman da suke a ƙarƙashinsa, da dukan mutane suke yaƙi da Urushalima da dukan biranenta.

2 Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce wa Irmiya ya tafi, ya faɗa wa Zadakiya Sarkin Yahuza cewa, “Ni Ubangiji, zan ba da wannan birni a hannun Sarkin Babila, zai kuwa ƙone shi da wuta.

3 Ba za ka tsere masa ba, amma lalle za a kama ka, a ba da kai a hannunsa. Za ka ga Sarkin Babila ido da ido, ka kuma yi magana da shi fuska da fuska. Za ka tafi Babila.

4 Ya Zadakiya, Sarkin Yahuza, ka ji maganar da ni Ubangiji na faɗa a kanka, ba za ka mutu ta wurin takobi ba.

5 Za ka mutu da salama. Kamar yadda aka ƙona wa sarakuna marigayanka turare, haka kai ma mutane za su ƙona maka turare, za su yi makoki dominka suna cewa, ‘Kaito, sarki ya rasu.’ Ni Ubangiji na faɗa.”

6 Sai annabi Irmiya ya faɗa wa Zadakiya, Sarkin Yahuza, dukan maganan nan a Urushalima,

7 sa’ad da sojojin Sarkin Babila suke yaƙi da Urushalima da kuma dukan biranen da suka ragu na Yahuza, wato Lakish da Azeka. Waɗannan su kaɗai ne biranen Yahuza masu garu da suka ragu.

Ta da Alkawari game da Bayin Ibraniyawa

8 Ubangiji kuma ya yi magana da Irmiya bayan da Zadakiya ya yi alkawari da dukan mutanen Urushalima don a yi musu shelar ba da ‘yanci,

9 cewa kowa ya saki bayinsa, mata da maza, waɗanda suke Yahudawa. Kada kowa ya riƙe bawa wanda yake Bayahude, ɗan’uwansa.

10 Sai suka yi biyayya. Dukan sarakuna da dukan jama’a waɗanda suka yi alkawarin, cewa kowa zai ‘yantar da bawansa ko baiwarsa, ba za su ƙara bautar da su ba, suka yi biyayya, suka ‘yantar da su.

11 Daga baya kuwa suka sāke komo da waɗannan bayi, mata da maza waɗanda suka ‘yantar, suka kuma mai da su bayi.

12 Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce,

13 “Ni Ubangiji Allah na Isra’ila, na yi alkawari da kakanninku lokacin da na fito da su daga ƙasar Masar daga bauta, na ce,

14 ‘A shekara ta bakwai, dole ne ku ‘yantar da ‘yan’uwanku, Ibraniyawa, waɗanda aka sayar muku, suka kuwa bauta muku shekara shida. Dole ne ku ‘yantar da su daga bautarku.’ Amma kakanninku ba su kasa kunne gare ni ba.

15 A ‘yan kwanakin da suka wuce kuka yi abu mai kyau a gabana da kuka tuba, har kuka yi wa juna shelar ‘yanci. Kuka yi alkawari a gabana a Haikalin da ake kira da sunana.

16 Amma sai kuka sāke tunaninku, kuka ɓata sunana sa’ad da kowannenku ya komo da bayinsa, mata da maza, waɗanda kuka ‘yantar, don su zauna yadda suke so. Ga shi kuma, kun komo da su su zama bayinku.

17 Domin haka ni Ubangiji na ce, ba biyayya kuka yi mini ba, da irin shelar ‘yancin da kowannenku ya yi wa ɗan’uwansa da maƙwabcinsa, saboda haka ni zan yi muku shelar ‘yanci zuwa mutuwa ta takobi, da annoba, da yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya.

18 Mutanen da suka keta alkawarina, ba su kuma kiyaye maganar alkawarin da suka yi a gabana ba, sa’ad da suka raba ɗan maraƙi kashi biyu, suka bi ta tsakiyarsa,

19 wato manyan fādawan Yahuza, da na Urushalima, da ‘yan majalisa, da firistoci da dukan jama’ar ƙasa, waɗanda suka bi ta tsakanin rababben ɗan maraƙin,

20 zan bashe su a hannun abokan gabansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsaye da namomin jeji.

21 Zadakiya, Sarkin Yahuza kuwa, da sarakunansa, zan bashe su a hannun abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, wato sojojin Sarkin Babila, waɗanda suka tashi suka bar ku.

22 Ni Ubangiji zan umarce su su komo zuwa wannan birni don su yi yaƙi da shi, su ci shi, su ƙone shi da wuta. Zan sa biranen Yahuza su zama kufai, ba masu zama a ciki.”

Categories
IRM

IRM 35

Biyayyar Rekabawa

1 A lokacin da Yehoyakim, ɗan Yosiya yake mulkin Yahuza, sai Ubangiji ya ce wa Irmiya,

2 “Ka tafi gidan Rekabawa, ka yi magana da su, ka kawo su a Haikalin Ubangiji, cikin ɗayan ɗakunan, sa’an nan ka ba su ruwan inabi su sha.”

3 Sai na ɗauki Yazaniya ɗan Irmiya, ɗan Habazziniya, da ‘yan’uwansa, da dukan ‘ya’yansa maza da dukan iyalin gidan Rekabawa.

4 Na kawo su cikin Haikalin Ubangiji, a ɗakin ‘ya’yan Hanan da Igdaliya, mutumin Allah. Ɗakin yana kusa da na shugabanni, a kan ɗakin Ma’aseya ɗan Shallum mai tsaron bakin ƙofa.

5 Sa’an nan na sa tuluna cike da ruwan inabi, da ƙoƙuna a gaban Rekabawa, sai na ce musu, “Ku sha ruwan inabi!”

6 Sai suka amsa, suka ce, “Ba za mu sha ruwan inabi ba, gama Yonadab ɗan Rekab, kakanmu, ya umarce mu cewa, ‘Ko ku, ko ‘ya’yanku, ba za ku sha ruwan inabi ba har abada,

7 ba kuma za ku gina ɗaki ba, ba kuwa za ku yi shuka ba, ba za ku yi dashe ba, ba za ku yi gonar inabi ba. Za ku zaune cikin alfarwai dukan kwanakin ranku, domin ku yi tsawon rai a ƙasar baƙuncinku.’

8 Mu kuma muka yi biyayya da umarnin da Yonadab ɗan Rekab, kakanmu, ya yi mana, cewa kada mu sha ruwan inabi, mu da matanmu, da ‘ya’yanmu mata da maza,

9 kada kuma mu gina wa kanmu gidajen zama. Ba mu da gonar inabi, ko gona ko iri.

10 Amma a alfarwai muke zamanmu. Mun yi biyayya da dukan abin da Yonadab kakanmu ya umarce mu.

11 Amma sa’ad da Nebukadnezzar Sarkin Babila ya kawo yaƙi a ƙasar, sai muka ce, ‘Bari mu tafi Urushalima domin muna jin tsoron sojojin Kaldiyawa da Suriyawa.’ Shi ya sa muke zaune a Urushalima.”

12 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce,

13 “Haka ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, na faɗa, ka tafi ka faɗa wa mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima cewa, ‘Ba za ku karɓi umarnina, ku kasa kunne ga maganata ba?’

14 Umarnin da Yonadab ɗan Rekab ya yi wa ‘ya’yansa, kada su sha ruwan inabi, sun kuwa kiyaye shi. Ba su taɓa shan ruwan inabi ba har wa yau, domin suna biyayya da umarnin kakansu. Ni kuwa na yi ta yi muku magana, amma ba ku kasa kunne gare ni ba.

15 Na yi ta aiko muku da bayina annabawa, ina cewa, kowa ya bar muguwar hanyarsa, ya gyara ayyukansa, kada ya bauta wa gumaka. Ta haka za ku zauna a ƙasa wadda na ba ku, ku da kakanninku, amma ba ku kasa kunne, ku ji ni ba.

16 ‘Ya’yan Yonadab ɗan Rekab sun kiyaye umarnin da kakansu ya yi musu. Amma jama’an nan ba su yi mini biyayya ba.

17 Domin haka, ni Ubangiji Allah Mai Runduna, Allah na Isra’ila, na ce zan kawo wa mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima masifar da na ce zan kawo musu, domin na yi musu magana, ba su ji ba, na kira su, ba su amsa ba.”

18 Sai Irmiya ya ce wa Rekabawa, “Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Tun da yake kun kiyaye dukan abin da Yonadab kakanku ya umarce ku,

19 saboda haka Yonadab ɗan Rekab ba zai taɓa rasa magaji wanda zai tsaya a gabana ba.’ ”

Categories
IRM

IRM 36

An Ƙone Littafi

1 A sa’ad da Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, yana shekara huɗu da sarauta, sai Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce,

2 “Ka ɗauki takarda, ka rubuta dukan maganar da na yi maka a kan Isra’ila, da Yahuza, da dukan al’ummai, tun daga ran da na fara yi maka magana a zamanin Yosiya har ya zuwa yau.

3 Mai yiwuwa ne idan mutanen Yahuza suka ji dukan masifar da na yi niyya in aukar musu da ita, za su bar mugayen ayyukansu don in gafarta musu muguntarsu da zunubinsu.”

4 Sai Irmiya ya kirawo Baruk ɗan Neriya. Baruk kuwa ya rubuta maganar da Irmiya ya faɗa masa a takarda, wato dukan maganar da Ubangiji ya faɗa wa Irmiya.

5 Sai Irmiya ya umarci Baruk, ya ce, “An hana ni zuwa Haikali,

6 saboda haka kai za ka tafi. A ranar azumi za ka karanta wa mutane maganar Ubangiji, wadda take a takardar da ka rubuta ta wurin shibtar da na yi maka. Ka karanta ta a cikin Haikali, a gaban mutanen Yahuza waɗanda suka fito daga biranensu.

7 Mai yiwuwa ne za su roƙi Ubangiji, su tuba, su bar mugayen ayyukansu, gama Ubangiji yana fushi ƙwarai, Ubangiji ya hurta hasala a kan wannan jama’a.”

8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya umarce shi. Ya karanta takardan nan ta maganar Ubangiji a Haikalin Ubangiji.

9 A watan tara a shekara ta biyar ta sarautar Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, sai dukan jama’ar Urushalima da dukan jama’ar da suka zo Urushalima daga biranen Yahuza suka yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji.

10 Sai Baruk ya karanta maganar Irmiya wadda take a takardar, kowa yana ji, a cikin Haikali a ɗakin Gemariya ɗan Shafan, magatakarda. Ɗakinsa yana a shirayi na bisa a hanyar shiga Sabuwar Ƙofa ta Haikalin Ubangiji.

11 Sa’ad da Mikaiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji da take a littafin,

12 sai ya gangara gidan sarki, ya shiga ɗakin magatakarda, inda dukan shugabanni suke zaune, wato Elishama magatakarda, da Delaiya ɗan Shemaiya, da Elnatan ɗan Akbor, da Gemariya ɗan Shafan, da Zadakiya ɗan Hananiya, da dukan sarakuna.

13 Sai Mikaiya ya faɗa musu dukan maganar da ya ji sa’ad da Baruk ya karanta littafin a kunnuwan jama’a.

14 Sai dukan sarakunan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya faɗa wa Baruk ya kawo littafin nan da ya karanta wa jama’a. Sai Baruk ɗan Neriya ya ɗauki littafin ya je wurinsu.

15 Suka ce masa ya zauna, ya karanta musu littafin. Baruk kuwa ya karanta musu.

16 Da suka ji dukan maganar, suka dubi juna a firgice, suka ce wa Baruk, “Ai, sai mu faɗa wa sarki wannan magana.”

17 Suka kuma tambayi Baruk, suka ce, “Ka faɗa mana yadda ka yi ka rubuta wannan magana. Ya yi maka shibta ne?”

18 Sai Baruk ya ce musu, “Ya yi mini shibtar dukan wannan magana ne, na kuwa rubuta su da tawada a takarda.”

19 Sarakunan kuwa suka ce wa Baruk, “Ka tafi, da kai da Irmiya ku ɓuya kada ku bari kowa ya san wurin da kuke.”

20 Suka tafi zauren sarki bayan sun ajiye littafin a ɗakin Elishama, magatakarda, suka sanar da sarki dukan abin da yake cikin littafin.

21 Sarki ya aiki Yehudi ya je ya kawo littafin. Sai ya je ya ɗauko littafin daga ɗakin Elishama magatakarda. Yehudi kuwa ya karanta wa sarki tare da dukan sarakunan da suke tsaye kewaye da sarkin.

22 A watan tara ne, sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, ga wuta tana ci cikin kasko a gabansa.

23 Da Yehudi ya karanta sakin layi uku ko huɗu sai sarki ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone littafin duka.

24 Duk da haka da sarkin da barorinsa suka ji maganar, ba wanda ya ji tsoro, balle su keta rigunansu don baƙin ciki.

25 Ko da yake Elnatan, da Delaiya, da Gemariya, sun faɗa wa sarki kada ya ƙone littafin, amma ya yi biris da su.

26 Sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, da Seraiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel, su kamo Baruk magatakarda da annabi Irmiya, amma Ubangiji ya ɓoye su!

27 Bayan da sarki ya ƙone littafin da Baruk ya rubuta ta wurin shibtar da Irmiya ya yi masa, sai Ubangiji ya yi wa Irmiya magana, ya ce,

28 ya ɗauki wata takarda ya rubuta dukan maganar da take cikin littafin da Yehoyakim Sarkin Yahuza, ya ƙone.

29 Zai kuma ce wa Yehoyakim Sarkin Yahuza, “Haka Ubangiji ya ce maka, ka ƙone littafin, kana cewa, ‘Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle Sarkin Babila zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?’

30 Saboda haka Ubangiji ya ce Yehoyakim, Sarkin Yahuza, ba zai sami magāji wanda zai zauna a gadon sarautar Dawuda ba. Za a jefar da gawarsa a waje ta sha zafin rana, da dare kuma za ta sha matsanancin sanyi.

31 Zan hukunta shi, shi da zuriyarsa, da barorinsa saboda muguntarsu. Zan kawo dukan masifar da na hurta a kansu, da a kan mazaunan Urushalima, da a kan mutanen Yahuza, amma sun ƙi ji.”

32 Sai Irmiya ya ɗauko wata takarda ya ba Baruk, magatakarda, ɗan Neriya. Shi kuwa ta wurin shibtar Irmiya, ya rubuta dukan maganar da take a wancan littafi, wanda Yehoyakim Sarkin Yahuza ya ƙone a wuta. An ƙara magana da yawa kamar ta dā.

Categories
IRM

IRM 37

An Sa Irmiya a Kurkuku

1 Zadakiya ɗan Yosiya, wanda Nebukadnezzar, Sarkin Babila ya naɗa Sarkin Yahuza, ya yi mulki a maimakon Yekoniya ɗan Yehoyakim.

2 Amma shi da barorinsa, da mutanen ƙasar, ba wanda ya kasa kunne ga maganar Ubangiji wadda ya yi musu ta bakin annabi Irmiya.

3 Sai sarki Zadakiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya, da Zafaniya firist, ɗan Ma’aseya, a wurin annabi Irmiya cewa, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allah dominmu.”

4 A lokacin nan Irmiya yana kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a tsare shi a kurkuku ba tukuna.

5 Rundunar sojojin Fir’auna kuwa ta taho daga Masar, amma da Kaldiyawa waɗanda suka kewaye Urushalima da yaƙi suka ji labari, sai suka janye daga Urushalima.

6 Sai Ubangiji ya yi magana da annabi Irmiya, ya ce,

7 “Ni Ubangiji Allah na Isra’ila, na ce ka faɗa wa Sarkin Yahuza wanda ya aiko ka ka tambaye ni, ka faɗa masa cewa, ‘Rundunar sojojin Fir’auna, wadda ta kawo maka gudunmawa tana gab da juyawa zuwa ƙasarta a Masar.

8 Kaldiyawa kuwa za su komo su yi yaƙi da wannan birni. Za su ci birnin, su ƙone shi da wuta.

9 Ni Ubangiji, na ce kada ku ruɗi kanku da cewa Kaldiyawa ba za su dawo ba, gama ba shakka za su zo.

10 Ko da a ce za ku ci dukan rundunar sojojin Kaldiyawa wadda take yaƙi da ku, sauran waɗanda kuka yi wa rauni da suke kwance a alfarwai za su tashi su ƙone birnin da wuta.’ ”

11 Da rundunar sojojin Kaldiyawa ta janye daga Urushalima saboda zuwan rundunar sojojin Fir’auna,

12 sai Irmiya ya tashi daga Urushalima zai tafi can ƙasar Biliyaminu, don ya karɓi nasa rabo tare da dangi.

13 A sa’ad da ya isa Ƙofar Biliyaminu, shugaban matsara, Irija ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama annabi Irmiya ya ce, “Kai kana gudu zuwa wurin Kaldiyawa ne.”

14 Sai Irmiya ya ce, “Ƙarya ce, ni ba gudu zuwa wurin Kaldiyawa nake yi ba.” Amma Irija bai yarda ba, sai ya kai shi wurin shugabanni.

15 Shugabanni suka yi fushi da Irmiya, suka yi masa dūka, suka tsare shi a gidan Jonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.

16 Irmiya ya yi kwanaki da yawa can cikin kurkukun.

Zadakiya Ya Nemi Shawara ga Irmiya

17 Sarki Zadakiya ya aika a kawo masa Irmiya. Sarki kuwa ya shigar da shi gidansa, ya tambaye shi a asirce, ya ce, “Ko akwai wata magana daga wurin Ubangiji?”

Sai Irmiya ya ce, “Akwai kuwa!” Ya ci gaba ya ce, “Za a ba da kai a hannun Sarkin Babila.”

18 Sai kuma ya tambayi sarki Zadakiya ya ce, “Wane laifi na yi maka, ko barorinka, ko wannan jama’a da ka sa ni a kurkuku?

19 Ina annabawanku waɗanda suka yi maka annabci cewa, ‘Sarkin Babila ba zai kawo wa ƙasarku yaƙi ba?’

20 Yanzu ya maigirma sarki, ina roƙonka ka ji wannan roƙo da nake yi maka, kada ka mai da ni a gidan Jonatan magatakarda, domin kada in mutu a can.”

21 Sai sarki Zadakiya ya ba da umarni, suka sa Irmiya a gidan waƙafi. Aka riƙa ba shi malmalar abinci daga unguwar masu tuya kowace rana, har lokacin da abinci ya ƙare duka a birnin. Haka kuwa Irmiya ya zauna a gidan waƙafi.

Categories
IRM

IRM 38

An Fitar da Irmiya daga Rijiya Marar Ruwa

1 Shefatiya ɗan Mattan, da Gedaliya ɗan Fashur, da Yehukal ɗan Shelemiya, da Fashur ɗan Malkiya, suka ji maganar da Irmiya yake faɗa wa dukan mutane cewa,

2 “Ubangiji ya ce wanda ya zauna a wannan birni zai mutu da takobi, da yunwa, da annoba, amma wanda ya fita ya je wurin Kaldiyawa zai rayu, zai sami ransa kamar ganimar yaƙi.

3 Gama Ubangiji ya ce, hakika za a ba da wannan birni a hannun rundunar sojojin Sarkin Babila su ci shi.”

4 Sarakunan suka ce wa sarki, “A kashe mutumin nan, gama yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran jama’a duka ta wurin irin maganganun da yake faɗa musu. Gama wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan jama’a sai dai wahala yake nemar musu.”

5 Sarki Zadakiya ya ce, “Ai, ga shi nan a hannunku, gama sarki ba zai yi abin da ba ku so ba.”

6 Sai suka ɗauki Irmiya suka saka shi a rijiyar Malkiya ɗan sarki, wadda take gidan waƙafi. Suka zurara Irmiya a ciki da igiya. Ba ruwa a rijiyar, sai dai lāka, Irmiya ya nutse cikin lākar.

7 Ebed-melek, bābā, mutumin Habasha, wanda yake a gidan sarki, ya ji labari sun saka Irmiya a rijiya. A lokacin nan, sarki yana zaune a Ƙofar Biliyaminu.

8 Sai Ebed-melek ya fita, ya tafi gaban sarki, ya ce masa,

9 “Ya maigirma sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu da suka saka annabi Irmiya cikin fijiya, Zai mutu can da yunwa, gama ba sauran abinci a birnin.”

10 Sa’an nan sarki ya umarci Ebedmelek, mutumin Habasha, ya tafi da mutum talatin su tsamo annabi Irmiya daga cikin rijiyar kafin ya mutu.

11 Sai Ebed-melek ya tafi da mutanen, ya kuma tafi gidan sarki, a ɗakin ajiya, ya kwaso tsummoki da tsofaffin tufafi, ya zurara wa Irmiya a rijiyar.

12 Ebedmelek, mutumin Habasha, ya ce wa Irmiya ya sa tsummokin da tsofaffin tufafin a hammatarsa, ya zarga igiya, Irmiya kuwa ya yi yadda aka ce masa.

13 Suka jawo Irmiya da igiyoyi, suka fito da shi daga rijiya. Irmiya kuwa ya zauna a gidan waƙafi.

Zadakiya Ya Nemi Shawarar Irmiya

14 Sarki Zadakiya ya aika a kirawo annabi Irmiya. Ya tafi ya sadu da Irmiya a ƙofa ta uku ta Haikalin Ubangiji. Sarki kuwa ya ce wa Irmiya, “Zan yi maka tambaya, kada kuwa ka ɓoye mini kome.”

15 Irmiya kuwa ya ce wa Zadakiya, “Idan na faɗa maka gaskiya za ka kashe ni, idan kuma na ba ka shawara, ba za ka karɓi shawarata ba.”

16 Sarki Zadakiya ya rantse wa Irmiya a ɓoye, ya ce, “Na rantse da Ubangiji, wanda yake ba mu rai, ba zan kashe ka ko in bashe ka a hannun waɗannan mutane da suke neman ranka ba.”

17 Irmiya ya ce wa Zadakiya, “Haka Ubangiji Allah Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce, idan ka miƙa wuya ga sarakunan Sarkin Babila, za ka tsira, ba kuwa za a ƙone birnin da wuta ba, kai da gidanka za ku tsira.

18 Amma idan ba ka miƙa wuya ga sarakunan Sarkin Babila ba, to, za a ba da wannan birni a hannun Kaldiyawa, za su ƙone shi da wuta. Kai kuma ba za ka tsira daga hannunsu ba.”

19 Sarki Zadakiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawa waɗanda suka gudu zuwa wurin Kaldiyawa. Kila a bashe ni a hannunsu, su ci mutuncina.”

20 Irmiya kuwa ya ce masa, “Ba za a bashe ka gare su ba. Kai dai ka yi biyayya da maganar Ubangiji wadda nake faɗa maka yanzu. Yin haka zai fi maka amfani, za ka tsira.

21 Amma idan ka ƙi miƙa wuya, to, ga abin da Ubangiji ya nuna mini a wahayi.

22 Ga shi, dukan matan da suka ragu a gidan Sarkin Yahuza, za a kai su wurin sarakunan Sarkin Babila, suna cewa,

‘Aminanka sun ruɗe ka,

Sun rinjaye ka.

Yanzu sun ga ƙafafunka sun nutse

cikin laka,

Sai suka rabu da kai.’

23 “Dukan matanka da ‘ya’yanka za a kai su wurin Kaldiyawa, kai kanka kuma ba za ka tsere musu ba, amma Sarkin Babila zai kama ka, birnin kuma za a ƙone shi da wuta.”

24 Sai Zadakiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan magana, kai kuwa ba za a kashe ka ba.

25 Idan sarakuna suka ji, wai na yi magana da kai, in suka zo wurinka, suka ce, ‘Ka faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da abin da sarki ya faɗa maka, kada ka ɓoye mana kome mu kuwa ba za mu kashe ka ba.’

26 Sai ka ce musu, ‘Na roƙi sarki da ladabi don kada ya mai da ni a gidan Jonatan, don kada in mutu a can.’ ”

27 Dukan sarakuna suka tafi wurin Irmiya suka tambaye shi. Shi kuwa ya amsa musu yadda sarki ya umarce shi. Sai suka daina magana da shi, tun da yake ba wanda ya ji maganar da ya yi da sarki.

28 Irmiya kuwa ya yi zamansa a gidan waƙafi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi.

Categories
IRM

IRM 39

Faɗuwar Urushalima

1 A watan goma a na shekara ta tara ta sarautar sarki Zadikiya, Sarkin Yahuza, sai Nebukadnezzar Sarkin Babila, da dukan sojojinsa suka zo, suka kewaye Urushalima da yaƙi.

2 A rana ta tara ga watan huɗu, a shekara ta goma sha ɗaya ta sarautar Zadakiya, sai aka huda garun birnin.

3 Sa’an nan da aka ci Urushalima, sai dukan sarakunan Sarkin Babila suka shiga, suka zauna a Ƙofar Tsakiya. Sarakuna, su ne Nergal-sharezer, da Samgar-nebo, da Sarsekim, wato Rabsaris, da Nergal-sharezer, wato Rabmag, da dukan sauran shugabannin Sarkin Babila.

4 Sa’ad da Zadakiya, Sarkin Yahuza, da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu, suka fita daga birnin da dare, ta hanyar gonar sarki a ƙofar da take a tsakanin garu biyu. Suka nufi zuwa wajen Araba.

5 Amma sojojin Kaldiyawa suka bi su, suka ci wa Zadakiya a filayen Yariko. Suka kama shi, suka kawo shi gaban Sarkin Babila a Ribla a ƙasar Hamat, a can Nebukadnezzar ya yanka masa hukunci.

6 Sarkin Babila ya kashe ‘ya’yan Zadakiya, maza, a Ribla a kan idon Zadakiya. Ya kashe dukan shugabannin Yahuza.

7 Ya kuma ƙwaƙule idanun Zadakiya, ya buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babila.

8 Sai Kaldiyawa suka ƙone gidan sarki, da gidajen jama’a. Suka kuma rushe garun Urushalima.

9 Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashi sauran mutane da suka ragu a birnin zuwa babila, wato mutanen da suka gudu zuwa wurinsa.

10 Amma ya bar matalauta waɗanda ba su da kome a ƙasar. Ya ba su gonakin inabi da waɗansu gonaki a ran nan.

Nebukadnezzar Ya Lura da Irmiya

11 Sai Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya yi wa Nebuzaradan shugaban matsara umarni a kan Irmiya ya ce,

12 “Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”

13 Sai Nebuzaradan shugaban matsara, da Nebushazban, wato Rabsaris, da Nergal-sharezer, wato Rabmag, da dukan shugabannin Sarkin Babila,

14 suka aika aka kawo Irmiya daga gidan waƙafi, suka ba da Irmiya amana ga Gedaliya, ɗan Ahikam ɗan Shafan, don ya kai shi gida. Da haka Irmiya ya zauna tare da mutane.

Ebed-melek yana Sa Zuciya ga Kuɓuta

15 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a lokacin da aka kulle shi a gidan waƙafi, ya ce,

16 “Ka tafi ka faɗa wa Ebedmelek mutumin Habasha, cewa Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan sa masifa, ba alheri ba, ta auko wa wannan birni. Wannan kuwa zai faru a kan idanunka a wannan rana.

17 Amma a ranan nan, ni Ubangiji zan cece ka, ba za a ba da kai a hannun mutanen da kake jin tsoronsu ba.

18 Gama hakika zan cece ka, ba za ka mutu ta takobi ba. Za ka sami ranka kamar ganimar yaƙi, domin ka dogara gare ni, ni Ubangiji na faɗa.’ ”

Categories
IRM

IRM 40

Irmiya da waɗanda Suka Ragu Sun Zauna tare da Gedaliya

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya bayan da Nebuzaradan shugaban matsara ya sake shi daga Rama, sa’ad da ya yi masa ƙuƙumi tare da waɗanda aka kwaso daga Urushalima da Yahuza, za su Babila.

2 Shugaban matsara ya ware Irmiya, sa’an nan ya ce masa, “Ubangiji Allahnka ne ya hurta wannan masifa a kan wurin nan.

3 Ga shi kuwa, ya yi kamar yadda ya faɗa, domin kun yi wa Ubangiji zunubi, ba ku yi biyayya da muryarsa ba, don haka wannan masifa ta auko muku.

4 Yau na kwance ƙuƙumin da yake a wuyanka, idan ka ga ya fi maka kyau, ka zo mu tafi tare zuwa Babila, to, sai ka zo, zan lura da kai da kyau, amma idan ba ka ga haka ya yi maka daidai ba, to, kada ka bi ni. Ga dukan ƙasa shimfiɗe a gabanka, ka tafi duk inda ka ga ya fi maka kyau.”

5 Amma Irmiya bai tafi ba, sai Nebuzaradan ya ce masa, “Ka koma wurin Gedaliya ɗan Ahikam, jikan Shafan, wanda Sarkin Babila ya sa ya zama mai mulkin garuruwan Yahuza, ka zauna tare da shi da mutanen, ko kuwa ka tafi duk inda ka ga ya fi maka kyau.” Sai ya ba Irmiya abinci da kyauta, sa’an nan ya sallame shi.

6 Irmiya kuwa ya tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, a Mizfa, ya zauna tare da shi da mutanen da suka ragu a ƙasar.

7 Sa’ad da shugabannin sojoji waɗanda suke a karkarar Yahudiya tare da mutanensu, suka ji labari Sarkin Babila ya sa Gedaliya ɗan Ahikam ya zama mai mulkin ƙasar, a kan matalauta, wato mata da maza, da yara na ƙasar, waɗanda ba a kwashe su zuwa bautar talala a Babila ba,

8 sai shugabannin, wato Isma’ilu ɗan Netaniya, da Yohenan da Jonatan, ‘ya’yan Kareya, da Seraiya ɗan Tanhumet, da ‘ya’yan Efai, mutumin Netofa, da Yazaniya ɗan mutumin Ma’aka suka tafi tare da mutanensu zuwa wurin Gedaliya a Mizfa.

9 Gedaliya ɗan Ahikam, jikan shafan ya rantse musu da mutanensu, ya ce, “Kada ku ji tsoron bauta wa Kaldiyawa, ku yi zamanku a ƙasar, ku bauta wa Sarkin Babila, za ku kuwa zauna lafiya.

10 Amma ni zan zauna a Mizfa, in zama wakilinku a wurin Kaldiyawa waɗanda za su zo wurinmu. Ku tattara inabi, da ‘ya’yan itatuwa na kaka, da man zaitun, ku tanada su a gidajenku, ku zauna a garuruwan da kuka ci.”

11 Haka kuma Yahudawan da suke a Mowab, da Ammon, da Edom, da kuma sauran ƙasashe suka ji, cewa Sarkin Babila ya bar waɗansu mutane a Yahuza, ya kuma shugabantar da Gedaliya ɗan Ahikam, jikan Shafan a kansu,

12 sai dukan Yahudawa suka koma daga inda aka kora su zuwa ƙasar Yahuza. Suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Suka tattara ruwan inabi da ‘ya’yan itatuwa na kaka da yawa.

Maƙarƙashiyar Isma’ilu gāba da Gedaliya

13 Yohenan ɗan Kareya kuwa, tare da dukan shugabannin sojojin da suke cikin sansani a karkara, suka zo wurin Gedaliya a Mizfa.

14 Suka ce masa, “Ko ka sani Ba’alis Sarkin Ammonawa ya aiko Isma’ilu ɗan Netaniya ya kashe ka?” Amma Gedaliya ɗan Ahikam, bai gaskata su ba.

15 Sai Yohenan ɗan Kareya ya yi magana da Gedaliya a Mizfa a asirce ya ce, “Ka bar ni in tafi in kashe Isma’ilu ɗan Netaniya, ba wanda zai sani. Don me shi zai kashe ka, ya watsa dukan Yahudawan da suke tare da kai, har sauran Yahudawan da suka ragu su halaka.”

16 Amma Gedaliya ɗan Ahikam ya ce wa Yohenan ɗan Kareya, “Kada ka kuskura ka yi wannan abu, gama ƙarya ce kake yi wa Isma’ilu.”