Categories
IRM

IRM 41

1 A watan bakwai sai Isma’ilu ɗan Netaniya, ɗan Elishama, na cikin zuriyar sarauta, ɗaya daga cikin ma’aikatan sarki, ya zo a wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa tare da mutum goma. Sa’ad da suke cin abinci tare a Mizfa,

2 Isma’ilu ɗan Netaniya, da mutanen nan goma da take tare da shi, suka tashi suka sare Gedaliya ɗan Ahikam ɗan shafan, da takobi, suka kashe shi, wato Gedaliya wanda Sarkin Babila ya naɗa ya zama mai mulkin ƙasar.

3 Isma’ilu kuma ya kashe dukan Yahudawa da suke tare da Gedaliya a Mizfa da waɗansu sojojin Kaldiyawa da suke a wurin.

4 Kashegari bayan da an kashe Gedaliya, tun kafin wani ya sani,

5 sai waɗansu mutane, su tamanin, suka zo daga Shekem, da Shilo, da Samariya, da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage. Suka kawo hadaya ta gari da hadayar turare domin su miƙa a Haikalin Ubangiji.

6 Sai Isma’ilu ɗan Netaniya ya fito daga cikin Mizfa yana kuka, don ya tarye su. Da ya sadu da su, sai ya ce musu, “Ku zo mu tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam!”

7 Sa’ad da suka shiga birnin, sai Isma’ila ɗan Nataniya da mutanen da suke tare da shi suka kashe su, suka jefa su a wata rijiya.

8 Amma waɗansu mutum goma daga cikinsu suka ce wa Isma’ila, “Kada ka kashe mu, gama muna da rumbunan alkama, da na sha’ir, da kuma man zaitun da zuma a ɓoye a cikin gonaki.” Sai ya bar su, bai kashe su tare da abokansu ba.

9 Rijiyar da Isma’ilu ya zuba dukan gawawwakin mutanen da ya kashe mai zurfi ce, sarki Asa ne ya haƙa saboda tsoron Ba’asha Sarkin Isra’ila. Isma’ilu ɗan Netaniya kuwa ya cika ta da gawawwakin mutanen da ya kashe.

10 Sai Isma’ilu ya kwashe dukan sauran mutanen da suke Mizfa, gimbiyoyi da dukan jama’ar da aka bari a Mizfa, waɗanda Nebuzaradan, shugaban matsara, ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Isma’ilu ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya haye da su zuwa yankin Ammonawa.

11 Amma sa’ad da Yohenan ɗan Kareya, tare da dukan shugabannin sojoji da suke tare da shi suka ji irin wannan mugun aiki wanda Isma’ilu ɗan Netaniya ya yi,

12 sai suka kwashe mutanensu duka, suka tafi su yi yaƙi da Isma’ilu ɗan Netaniya. Suka iske shi a babban tafkin da take a Gibeyon.

13 Sa’ad da dukan jama’ar da Isma’ilu ya kwashe suka ga Yohenan ɗan Kareya, da dukan shugabannin sojoji tare da shi, sai suka yi murna.

14 Dukan mutanen nan da Isma’ilu ya kwashe su ganima daga Mizfa, suka juya, suka koma wurin Yohenan ɗan Kareya.

15 Amma Isma’ilu ɗan Netaniya tare da mutum takwas suka tsere suka gudu zuwa wurin Ammonawa.

16 Sai Yohenan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji da suke tare da shi, suka kwashe dukan sauran jama’a, waɗanda Isma’ilu ɗan Netaniya ya kamo daga Mizfa bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato sojoji da mata, da yara, da bābāni, su ne Yohenan ya komo da su daga Gibeyon.

17 Suka fa tafi suka zauna a wurin Kimham kusa da Baitalami. Suna nufin su tafi Masar,

18 don gudun Kaldiyawa, gama suna jin tsoronsu, domin Isma’ilu ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam wanda Sarkin Babila ya naɗa shi mai mulkin ƙasa.

Categories
IRM

IRM 42

Jawabin Irmiya ga Yohenan

1 Shugabannin sojoji, da Yohenan ɗan Kareya, da Yazaniya ɗan Hoshaiya, da jama’a duka, daga ƙarami zuwa babba, suka zo,

2 suka ce wa annabi Irmiya, “Muna roƙonka, ka roƙi Ubangiji Allahnka dominmu, dukanmu da muka ragu, gama mu kima muka ragu daga cikin masu yawa, kamar yadda kake ganinmu da idonka.

3 Ka yi mana addu’a domin Ubangiji Allahnka ya nuna mana hanyar da za mu bi, da kuma abin da za mu yi.”

4 Annabi Irmiya kuwa ya ce musu, “Na ji abin da kuka ce. Ga shi kuwa, zan yi addu’a ga Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka roƙa. Kowace irin amsa da Ubangiji ya bayar, zan faɗa muku, ba zan ɓoye muku kome ba.”

5 Sa’an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji mai gaskiya, mai aminci ya zama shaida a tsakaninmu, idan ba mu yi duk yadda Ubangiji Allahnka ya aiko ka gare mu ba.

6 Ko nagari ne ko mugu ne, za mu yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnmu wanda muka aike ka wurinsa, gama zai zama alheri a gare mu idan mun yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnmu.”

7 Bayan kwana goma sai Ubangiji ya yi magana da Irmiya.

8 Sai Irmiya ya kira Yohenan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda suke tare da shi, da dukan jama’a tun daga ƙarami har zuwa babba.

9 Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda kuka aike ni da koke-kokenku wurinsa ya ce,

10 ‘Idan za ku zauna a ƙasan nan, to, zan gina ku, ba zan rushe ku ba. Zan dasa ku, ba zan tumɓuke ku ba, gama zan janye masifar da na aukar muku.

11 Kada ku ji tsoron Sarkin Babila, shi wanda kuke jin tsoronsa. Kada ku ji tsoronsa,’ in ji Ubangiji, ‘gama ina tare da ku, zan cece ku, in kuɓutar da ku daga hannunsa.

12 Zan yi muku jinƙai in sa sarkin ya ji ƙanku, ya bar ku ku zauna a ƙasarku.’

13 “Amma idan kuka ce ba za ku zauna a wannan ƙasa ba, kuka ƙi yin biyayya da muryar Ubangiji Allahnku,

14 kuna cewa, ‘Mun ƙi, mu, ƙasar Masar za mu tafi, inda ba za mu ga yaƙi ba, ba za mu ji ƙarar ƙahon yaƙi ba, yunwa kuma ba za ta same mu ba, a can za mu zauna.’

15 To, sai ku ji maganar Ubangiji, ya ku sauran mutanen Yahuza, Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Idan zuwa Masar kuka sa gaba don ku tafi ku zauna a can,

16 to, takobin nan da kuke jin tsoro, zai ci muku can a ƙasar Masar, yunwan nan kuma da kuke jin tsoro za ta bi ku zuwa Masar ta tsananta muku, a can za ku mutu.

17 Duk waɗanda suka sa gaba zuwa Masar domin su zauna can, da takobi, da yunwa, da annoba su ne ajalinsu. Ba wanda zai ragu, ba wanda zai tsira daga masifar da zan aukar musu.’

18 “Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya ce, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa’ad da kuka tafi Masar. Za ku zama najasa, da abin ƙyama, da la’ana, da abin ba’a. Wannan wuri kuwa ba za ku ƙara ganinsa ba.’

19 “Ya ku sauran mutanen Yahuza, Ubangiji ya ce, ‘Kada ku tafi Masar.’ Ku tabbata fa na faɗakar da ku yau,

20 cewa in kun ratse, to, a bakin ranku. Gama kun aike ni wurin Ubangiji Allah cewa, ‘Ka roƙar mana Ubangiji Allahnmu. Dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya ce ka faɗa mana kuma za mu aikata.’

21 A wannan rana kuwa na faɗa muku abin da ya ce, amma ba ku yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku a kan kowane abin da ya aiko ni in faɗa muku ba.

22 Domin haka yanzu fa ku sani takobi, da yunwa, da annoba, su ne ajalinku a wurin can da kuke sha’awar ku zauna.”

Categories
IRM

IRM 43

Tafiya zuwa Masar

1 Sa’ad da Irmiya ya gama faɗa wa dukan jama’a maganar da Ubangiji Allahnsu ya aiko musu da ita,

2 sai Yazaniya ɗan Hoshaiya, da Yohenan ɗan Kareya, da dukan ‘yan tsagera, suka ce wa Irmiya, “Ƙarya kake yi, Ubangiji Allahnmu bai aiko ka da cewa kada mu tafi, mu zauna a Masar ba!

3 Amma Baruk ɗan Neriya shi ne ya sa ka faɗi wannan magana gāba da mu, don ka bashe mu a hannun Kaldiyawa domin su kashe mu, ko kuwa su kai mu bauta a Babila.”

4 Yohenan ɗan Kareya, da dukan shugabannin sojoji, da dukan jama’a, ba su yi biyayya da umarnin Ubangiji, su zauna a ƙasar Yahuza ba.

5 Amma Yohenan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji suka kwashe sauran mutanen Yahuza duka waɗanda suka komo suka zauna a ƙasar Yahuza, daga wurin al’ummai, inda aka kora su,

6 mata, da maza, da yara, da gimbiyoyi, da kowane mutum da Nebuzaradan shugaban matsara ya bar wa Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da annabi Irmiya, da Baruk ɗan Neriya.

7 Suka zo ƙasar Masar, gama ba su yi biyayya da muryar Ubangiji ba. Suka sauka a Tafanes.

8 Ubangiji kuwa ya yi magana da Irmiya a Tafanes ya ce,

9 “Kwashi manyan duwatsu da hannunka, ka ɓoye su a ƙofar shiga fādar Fir’auna a Tafanes a idon mutanen Yahuza,

10 ka kuma ce musu, ‘In ji Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ga shi, zan aika wa bawana Nebukadnezzar ya zo ya kafa kursiyin sarautarsa a kan duwatsun nan waɗanda na ɓoye. Zai buɗe babbar alfarwarsa a wurin.

11 Nebukadnezzar zai zo ya buga ƙasar Masar. Zai ba annoba waɗanda aka ƙaddara su ga annoba, waɗanda aka ƙaddara ga bauta, za a kai su bauta. Waɗanda aka ƙaddara ga takobi, za su mutu ta takobi.

12 Zai cinna wa gidajen gumakan Masar wuta, zai ƙone su, ya tafi da waɗansu, zai tsabtace ƙasar Masar kamar yadda makiyayi yakan kakkaɓe ƙwarƙwata daga cikin tufafinsa, zai kuwa tashi daga wurin lafiya.

13 Zai kuma farfashe al’amudan duwatsu na On a ƙasar Masar. Zai ƙone gidajen gumakan Masar da wuta.’ ”

Categories
IRM

IRM 44

Jawabin Ubangiji zuwa ga Yahudawan da suke Masar

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan dukan Yahudawan da suke zaune a ƙasar Masar, a garin Migdol, da Tafanes, da Memfis, da dukan ƙasar Fatros, ya ce,

2 “Ni Ubangiji Mai Runduna Allah na Isra’ila, na ce, ku da kanku kun ga masifar da na aukar wa Urushalima, da dukan garuruwan Yahuza. Yanzu sun zama kufai, ba wanda yake zaune a cikinsu,

3 domin mutanen da suke cikinsu sun aikata mugayen abubuwa da suka tsokane ni. Sun miƙa wa gumaka hadayu, suka kuma bauta musu, ko da yake su, ko ku, ko kakanninku, ba ku san su ba.

4 Na yi ta aika muku da dukan bayina annabawa waɗanda suka faɗa muku kada ku aikata wannan mugun abin banƙyama.

5 Amma ba su kasa kunne ba, ba su kuwa ji ba, da za su juyo daga mugayen ayyukansu na miƙa wa gumaka hadayu.

6 Saboda haka fushina ya yi zafi a kan garuruwan Yahuza da titunan Urushalima, don haka a yanzu sun lalace, suka zama kufai.

7 “Yanzu, ni Ubangiji Allah Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ina tambaya, me ya sa kuke jawo wa kanku wannan babbar masifa, kuna so ku hallakar da mata da maza, yara da jarirai daga cikin Yahuza, har a rasa wanda zai wanzu?

8 Me ya sa kuke tsokanata da ayyukan hannuwanku, kuna miƙa wa gumaka hadayu a ƙasar Masar inda kuka zo don ku zauna? Yin haka zai sa a hallaka ku, ku zama abin la’ana da zargi a cikin dukan ƙasashen duniya.

9 Ko kun manta da mugayen ayyukan kakanninku, da na sarakunan Yahuza da na matansu, da naku, da na matanku, waɗanda suka aikata a ƙasar Yahuza da kan titunan Urushalima?

10 Amma har wa yau ba ku ƙasƙantar da kanku ba, ba ku ji tsorona ba, ba ku kuwa kiyaye dokokina da umarnaina ba, waɗanda na ba ku ku da kakanninku.

11 “Domin haka, ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, zan aukar muku da masifa, in hallaka mutanen Yahuza duka.

12 Sauran mutanen Yahuza kuwa waɗanda suka ragu, waɗanda suke niyyar zuwa ƙasar Masar da zama, zan sa dukansu su halaka a can. Takobi da yunwa za su kashe dukansu a Masar, da yaro da babba. Za su zama abin la’antawa, da abin tausayi, da abin zargi, da abin kunya.

13 Zan hukunta dukan waɗanda suke zaune a Masar kamar yadda na hukunta wa Urushalima da takobi, da yunwa, da annoba.

14 Ba waɗansu daga cikin mutanen Yahuza da suka ragu, waɗanda suka zo Masar da zama, da za su tsere ko su rayu. Ba wani daga cikinsu da zai koma Yahuza inda suke marmarin komawa da zama, ba wanda zai koma, sai dai ‘yan gudun hijira.”

15 Sai dukan mazan da suka sani matansu sun miƙa wa gumaka hadayu, da dukan matan da suke tsaye a wurin, da dukan Yahudawan da suke zaune a Fatros, babban taron jama’a, suka ce wa Irmiya,

16 “Ba za mu kasa kunne ga jawabin da kake yi mana da sunan Ubangiji ba!

17 Za mu aikata dukan abin da muka faɗa. Za mu miƙa wa gunkiyan nan, wato sarauniyar sama, hadayu, da hadayu na sha kamar yadda kakanninmu, da shugabanninmu suka yi a garuruwan Yahuza, da kan titunan Urushalima. A lokacin kuwa muna da abinci a wadace, muka arzuta, ba wata wahala.

18 Amma tun da muka daina miƙa wa sarauniyar sama hadayu, da hadayu na sha, ba mu da kome, sai dai takobi da yunwa suke kashe mu.”

19 Mata kuma suka ce, “Sa’ad da muka toya waina ga siffar sarauniyar sama, muka miƙa mata hadayu, da hadayu na sha, ai, mazanmu sun goyi bayan abin da muka yi.”

20 Sa’an nan Irmiya ya ce wa dukan mutane, mata da maza, waɗanda suka ba shi irin amsan nan, ya ce,

21 “A kan turaren da ku da kakanninku, da sarakunanku, da shugabanninku, da mutanen ƙasar, kuka ƙona a garuruwan Yahuza da a titunan Urushalima, kuna tsammani Ubangiji bai san su ba, ko kuna tsammani ya manta?

22 Ubangiji ba zai yarda da mugayen ayyukanku ba, da ƙazantarku da kuka aikata, don haka ƙasarku a yau ta zama kufai ba mai zama a cikinta. Ta zama abin ƙyama da la’ana.

23 Saboda kun ƙona turare, kun yi wa Ubangiji zunubi, ba ku yi biyayya da muryarsa ba, ba ku kiyaye dokokinsa, da umarnansa, da sharuɗansa ba, shi ya sa wannan masifa ta auko muku a yau.”

24 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutane duk da mata, “Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuza da suke a Masar.

25 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya ce, ‘Ku da matanku kun faɗa da bakinku, kun kuma aikata da hannuwanku, cewa za ku aikata wa’adodin da kuka yi na ƙona turare, da miƙa hadayu na sha ga sarauniyar sama.’ To, sai ku tabbatar da wa’adodinku, ku cika su!

26 Domin haka ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuza da yake zaune a ƙasar Masar. ‘Ni Ubangiji na rantse da sunana Maɗaukaki, cewa ba zan yarda kuma wani mutumin Yahuza da yake ƙasar Masar ya ambaci sunana da yin rantsuwa, cewa ya rantse da zatin Ubangiji ba.’

27 Ga shi, ina lura da su, ba domin alheri ba, amma domin in aukar musu da masifa. Takobi da yunwa za su hallaka dukan mutanen Yahuza waɗanda suke a ƙasar Masar.

28 ‘Yan kaɗan ne za su tsere wa takobi, za su kuwa koma daga ƙasar Masar zuwa ƙasar Yahuza. Sauran mutanen Yahuza da suka ragu, waɗanda suka zo Masar da zama, za su sani ko maganar wa za ta cika, tasu ko kuwa tawa.

29 Ni Ubangiji na ce, wannan zai zama muku alama, cewa zan hukunta ku a wannan wuri domin ku sani lalle maganata ta aukar muku da masifa za ta cika.

30 Zan kuma ba da Fir’auna Hofra, Sarkin Masar, a hannun abokan gabansa, da waɗanda suke neman ransa, kamar yadda na ba da Zadakiya, Sarkin Yahuza, a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila wanda ya zama abokin gābansa, ya kuwa nemi ransa.’ ”

Categories
IRM

IRM 45

Jawabin Irmiya ga Baruk

1 A shekara ta huɗu ta sarautar Yehoyakim, ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, Baruk ɗan Neriya ya rubuta abin da Irmiya ya faɗa masa.

2 “Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce maka, kai Baruk,

3 kai ka ce, ‘Kaitona, gama Ubangiji ya ƙara baƙin ciki a kan wahalaina, na gaji da nishina, ba ni da hutu!’

4 “Sai ka faɗa wa Baruk cewa, ‘Ni Ubangiji na ce, ga shi, abin da na gina zan rushe shi, abin da kuma na dasa zan tumɓuke shi, wato ƙasar ɗungum.

5 Kana nemar wa kanka manyan abubuwa? Kada ka neme su, gama zan kawo masifa a kan dukan ‘yan adam, amma zan kuɓutar da ranka kamar ganima, a dukan wuraren da za ka tafi.’ ”

Categories
IRM

IRM 46

Annabci a kan Masar

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan sauran al’umma.

2 Ya yi magana game da sojojin Fir’auna, Sarkin Masar, waɗanda suke a bakin Kogin Yufiretis a Karkemish, waɗanda Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya ci su da yaƙi a shekara ta huɗu ta sarautar Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza.

3 Masarawa suka yi ihu, suka ce,

“Ku shirya kutufani da garkuwa,

Ku matso zuwa wurin yaƙi!

4 Ku ɗaura wa dawakanku sirdi, ku

hau!

Ku tsaya a wurarenku da kwalkwali

a ka!

Ku wasa māsunku!

Ku sa kayan yaƙi!”

5 Ubangiji ya yi tambaya ya ce,

“Me nake gani?

Sun tsorata, suna ja da baya,

An ci sojojinsu, suna gudu,

Ba su waiwayen baya, akwai tsoro a

kowane sashi.”

6 Masu saurin gudu ba za su tsere ba,

Haka nan kuma jarumi,

A arewa a gefen Kogin Yufiretis,

Sun yi tuntuɓe, sun fādi.

7 Wane ne wannan mai tashi kamar

Kogin Nilu,

Kamar kogunan da ruwansu yake

ambaliya?

8 Masar tana tashi kamar Nilu,

Kamar kogunan da ruwansu yake

ambaliya.

Masar ta ce, “Zan tashi, in rufe

duniya,

Zan hallaka birane da mazauna

cikinsu.”

9 Ku haura, ku dawakai,

Ku yi sukuwar hauka, ku karusai!

Bari sojoji su fito,

Mutanen Habasha da Fut masu

riƙon garkuwoyi,

Da mutanen Lud, waɗanda suka iya

riƙon baka.

10 Wannan rana ta Ubangiji, Allah Mai

Runduna ce,

Ranar ɗaukar fansa ce don ya rama

wa maƙiyansa.

Takobi zai ci, ya ƙoshi,

Ya kuma sha jininsu, ya ƙoshi,

Gama Ubangiji Allah Mai Runduna

zai hallaka maƙiyansa,

A arewa, a bakin Kogin Yufiretis.

11 Ku mutanen Masar, ku haura zuwa

Gileyad

Don ku samo ganye!

A banza kuke morar magunguna,

Ba za ku warke ba.

12 Kunyarku ta kai cikin sauran

al’umma,

Kukanku kuma ya cika duniya.

Soja na faɗuwa bisa kan soja.

Dukansu biyu sun faɗi tare.

13 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan zuwan Nebukadnezzar, Sarkin Babila, don ya yi yaƙi da ƙasar Masar.

14 “Ku yi shelarsa cikin garuruwan

Masar,

Cikin Migdol, da Memfis, da

Tafanes,

Ku ce, ‘Ku tsaya, ku yi shiri,

Gama takobi yana cin waɗanda suke

kewaye da ku!’

15 Me ya sa gunkinka, Afis, ya fāɗi,

Wato bijimi, gunkinka bai tsaya ba?

Domin Ubangiji ya tunkuɗe shi

ƙasa!

16 Sun yi ta fāɗuwa,

Suna faɗuwa a kan juna,

Sai suka ce, ‘Mu tashi mu koma

wurin mutanenmu,

Zuwa ƙasar haihuwarmu, mu gudu

daga takobin azzalumi!’

17 “Ku ba Fir’auna Sarkin Masar

sabon suna,

‘Mai yawan surutu, wanda bai rifci

zarafi ba!’

18 Ni wanda sunana Ubangiji Mai

Runduna Sarki ne,

Na rantse da raina, wani zai ɓullo,

Kamar Tabor a cikin tsaunuka,

Ko kuwa kamar Karmel a bakin

teku.

19 Ya ku mazaunan Masar,

Ku shirya kayanku don zuwa bauta,

Gama Memfis za ta lalace, ta zama

kufai,

Ba mai zama a ciki.

20 “Masar kyakkyawar karsana ce,

Amma bobuwa daga arewa ta aukar

mata!

21 Sojojin ijararta kamar ‘yan maruƙa

ne, masu yawan kitse,

Sun ba da baya, sun gudu, ba su

tsaya ba,

Domin ranar masifarsu ta zo,

Lokacin halakarsu ya yi.

22 Masar tana gudu, tana huci kamar

maciji,

Gama abokan gābanta suna zuwa da

ƙarfi,

Za su faɗo mata da gatura kamar

masu saran itatuwa.

23 Ni Ubangiji na ce, za su sari

kurminta,

Ko da yake ba su ƙirguwa,

Gama suna da yawa kamar fara,

Ba su lasaftuwa.

24 Za a kunyatar da mutanen Masar,

An bashe su a hannun mutanen

arewa.”

25 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya ce, “Ga shi, zan hukunta Amon na No, da Fir’auna, da Masar, tare da allolinta, da sarakunanta, wato Fir’auna, tare da waɗanda suke dogara gare shi.

26 Zan bashe su a hannun waɗanda suke neman ransu, wato a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da shugabanninsa. Daga baya kuma mutane za su zauna a Masar kamar dā. Ni Ubangiji na faɗa.

27 “Ya bawana Yakubu, kada ka ji

tsoro,

Kada ka firgita, ya Isra’ila.

Gama zan cece ka daga ƙasa mai

nisa,

Zan ceci zuriyarka daga ƙasar

bautarsu.

Yakubu zai komo, ya yi zamansa da

rai kwance,

Ba wanda zai razanar da shi.

28 Ni Ubangiji na ce,

Kada ka ji tsoro, ya bawana

Yakubu,

Gama ina tare da kai.

Zan hallaka dukan sauran al’umma

sarai inda na kora ka.

Amma ba zan hallaka ka sarai ba.

Zan hukunta ka yadda ya kamata,

Ba zan bar ka ba hukunci ba.”

Categories
IRM

IRM 47

Jawabin Ubangiji a kan Filistiyawa

1 Kafin Fir’auna ya ci Gaza da yaƙi Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan Filistiyawa.

2 Ubangiji ya ce,

“Ga shi, ruwa yana tasowa daga

arewa,

Zai zama kogi da yake ambaliya.

Zai malala bisa ƙasa da dukan abin

da yake cikinta,

Da birni da mazauna cikinsa,

Maza za su yi kuka,

Dukan mazaunan ƙasar za su yi kuka.

3 Da jin takawar kofatan dawakai,

Da amon karusai da ƙafafun karusai,

Ubanni ba su juya, su dubi

‘ya’yansu ba,

Domin hannuwansu sun yi laƙwas,

4 Domin lokacin hallaka dukan

Filistiyawa ya yi.

Za a datse wa Taya da Sidon kowane

taimakon da ya ragu,

Gama Ubangiji zai hallaka

Filistiyawa

Waɗanda suke baƙin teku na Kaftor.

5 Baƙin ciki zalla ya sami Gaza,

Ashkelon ta lalace.

Ya ƙattin mutane, yaushe za ku

daina tsattsage kanku?

6 Ya takobin Ubangiji, yaushe za ka

huta?

Sai ka koma ƙubenka,

Ka huta, ka yi shiru!

7 Ƙaƙa zai huta, tun da ni Ubangiji ne

na umarce shi?

Ni Ubangiji na umarce shi ya yi yaƙi

da Ashkelon

Da mazauna a bakin teku.”

Categories
IRM

IRM 48

Jawabin Ubangiji a kan Mowab

1 Ga abin da Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya faɗa a kan Mowab,

“Kaiton Nebo, gama ta lalace!

An kunyatar da Kiriyatayim, an ci ta

da yaƙi,

An kunyatar da kagararta, an rushe

ta.

2 Darajar Mowab ta ƙare.

Ana shirya mata maƙarƙashiya a

Heshbon,

‘Bari mu je mu ɓata ta daga zaman

al’umma!’

Ke kuma Madmen za ki yi shiru,

Takobi zai runtume ki.

3 Muryar kuka daga Horonayim tana

cewa,

‘Risɓewa da babbar halaka!’

4 “An hallakar da Mowab,

Ƙanananta suna kuka.

5 Gama a hawan Luhit, za su hau da

kuka,

Gama a gangaren Horonayim,

Suna jin kukan wahalar halaka.

6 Ku gudu don ku tserar da

rayukanku,

Ku gudu kamar jakin jeji.

7 “Kun dogara ga ƙarfinku da

wadatarku,

Amma yanzu za a ci ku da yaƙi,

Kemosh zai tafi bauta

Tare da firistocinsa da

shugabanninsa.

8 Mai hallakarwa zai shiga kowane

gari,

Don haka ba garin da zai tsira.

Kwari da tudu za su lalace,

Ni Ubangiji na faɗa.

9 Ku ba Mowab fikafikai,

Gama za ta tashi ta gudu,

Garuruwanta za su zama kango,

Ba mazauna cikinsu.

10 “La’ananne ne shi wanda yake yin

aikin Ubangiji da ha’inci,

La’ananne ne shi kuma wanda ya

hana wa takobinsa jini.

11 “Tun daga ƙuruciya Mowab tana

zama lami lafiya,

Hankali kwance,

Ba a jujjuya ta daga tulu zuwa tulu

ba,

Ba a taɓa kai ta bauta ba,

Domin haka daɗin ɗanɗanonta bai

rabu da ita ba,

Ƙanshinta kuma bai sāke ba.”

12 Ubangiji ya ce, “Domin haka kwanaki suna zuwa, sa’ad da zai aika da mutane su tuntsurar da tuluna, su zubar da ruwan inabi, su farfasa tulunanta.

13 Sa’an nan Kemosh zai kunyatar da Mowab, kamar yadda Betel wadda Isra’ilawa suka dogara gare ta ta kunyatar da su.

14 “Don me kake cewa,

‘Mu jarumawa ne, mayaƙan gaske?’

15 Mai hallaka Mowab da garuruwanta

ya taho,

Zaɓaɓɓun majiya ƙarfinta sun

gangara mayanka,

Ni sarki, mai suna Ubangiji Mai

Runduna, na faɗa.

16 Masifar Mowab ta kusato,

Halakarta kuma tana gaggabtowa.

17 “Ku yi makoki dominta, ku da kuke

kewaye da ita,

Dukanku da kuka san sunanta, ku

ce,

‘Ƙaƙa sandan sarauta mai iko

Da sanda mai daraja ya karye?’

18 Ku da kuke zaune a Dibon,

Ku sauka daga wurin zamanku mai

daraja,

Ku zauna a busasshiyar ƙasa,

Gama mai hallaka Mowab ya zo ya

yi gab da ku.

Ya riga ya rushe kagararku.

19 Ku mazaunan Arower,

Ku tsaya a kan hanya, ku jira,

Ku tambayi wanda yake gudu

Da wanda yake tserewa,

Abin da ya faru.

20 An kunyatar da Mowab, ta rushe.

Ku yi kuka dominta,

Ku faɗa a Arnon, cewa Mowab ta

halaka.

21 “Hukunci ya auka kan garuruwan da suke a ƙasar fili, wato Holon, da Yahaza, da Mefayat,

22 da Dibon, da Nebo, da Bet-diblatayim,

23 da Kiriyatayim, da Bet-gamal, da Ba’almeyon,

24 da Kiriyot, da Bozara. Hukunci ya zo a kan dukan garuruwan Mowab na nesa da na kusa.

25 An karye ikon Mowab da ƙarfinta, ni Ubangiji na faɗa.

26 “Ku sa Mowab ta yi maye domin ta tayar wa Ubangiji. Za ta yi birgima cikin amanta, mutane kuwa za su yi dariya.

27 Kin yi wa mutanen Isra’ila dariya. A kowane lokacin da kika ambaci sunansu, sai ki taɗa kanki da raini kamar an kama su tare da ɓarayi.

28 “Ku mazaunan Mowab, ku bar

garuruwanku,

Ku tafi, ku zauna a kogwanni,

Ku zama kamar kurciya wadda take

yin sheƙarta a bakin kwazazzabo.

29 Mun ji labarin girmankan Mowab,

da ɗaukaka kanta,

Da alfarmarta, da izgilinta,

Tana da girmankai ƙwarai.

30 Ni Ubangiji na san Mowab tana da

girmankai,

Alfarmarta ta banza ce,

Ayyukanta kuma na banza ne.

31 Don haka zan yi kuka saboda

Mowab duka,

Zan kuma yi baƙin ciki saboda

mutanen Kir-heres.

32 Zan yi kuka saboda kurangar inabin

Sibma

Fiye da yadda zan yi kuka saboda

mutanen Yazar.

Rassanku sun haye teku har sun kai

Yazar,

Amma mai hallakarwa ya faɗo a kan

‘ya’yan itatuwanku da damuna

Da kan amfanin inabinku.

33 An ɗauke farin ciki da murna daga

ƙasa mai albarka ta Mowab,

Na hana ruwan inabi malala daga

wurin matsewarsa,

Ba wanda yake matse shi, yana ihu na

murna,

Ihun da ake yi ba na murna ba ne.

34 “Mutanen Heshbon da na Eleyale suna kururuwa ana iya jin kururuwansu a Yahaza. Ana iya jinta kuma a Zowar, da Horonayim, da Eglat-shelishiya. Har ma ruwan Nimra ya ƙafe.

35 Zan hana mutanen Mowab miƙa hadayu na ƙonawa a tuddai, da miƙa wa gumakansu sadaka, ni Ubangiji na faɗa.

36 “Zuciyata tana makoki domin Mowab da Kir-heres kamar wanda yake kukan makoki da sarewa saboda wadatarsu ta ƙare.

37 Gama kowa ya aske kansa da gemunsa, sun tsattsage hannuwansu. Kowa kuma ya sa rigar makoki.

38 Ba abin da ake yi a bisa kan soraye da dandali na Mowab sai baƙin ciki, gama na farfashe Mowab kamar tulun da ba a so, ni Ubangiji na faɗa.

39 An farfashe Mowab, ta yi kuka, ta kunyata! Ta zama abin dariya da abin tsoro ga waɗanda suke kewaye da ita.

40 “Ni Ubangiji na ce,

Wani zai yi firiya da sauri kamar

gaggafa,

Zai shimfiɗa fikafikansa a kan

Mowab.

41 Za a ci garuruwa da kagarai da

yaƙi,

A wannan rana zukatan sojojin

Mowab

Za su zama kamar zuciyar macen da

take naƙuda.

42 Za a hallaka Mowab daga zaman

al’umma,

Domin ta tayar wa Ubangiji.

43 Tsoro, da rami, da tarko suna

jiranku,

Ya mazaunan Mowab,

Ni Ubangiji na faɗa.

44 Wanda ya guje wa tsoro,

Zai fāɗa a rami,

Wanda kuma ya fito daga cikin

rami,

Tarko zai kama shi.

Gama na sa wa Mowab lokacin da

zan hukunta ta,

Ni Ubangiji na faɗa.

45 “A ƙarƙashin inuwar Heshbon ‘yan

gudun hijira suna tsaye ba ƙarfi.

Gama wuta ta ɓullo daga Heshbon,

Harshen wuta kuma ya fito daga

Sihon,

Ta ƙone goshin Mowab da

ƙoƙwan kai na ‘yan tayarwa.

46 Kaitonku, ya Mowabawa!

Mutanen Kemosh sun lalace,

An kai ‘ya’yanku mata da maza

cikin bauta.

47 “Amma zan komar da mutanen

Mowab nan gaba,

Ni Ubangiji na faɗa.”

Wannan shi ne hukuncin Mowab.

Categories
IRM

IRM 49

Jawabin Ubangiji a kan Ammonawa

1 Wannan shi ne abin da Ubangiji ya faɗa akan Ammonawa,

“Isra’ila ba shi da ‘ya’ya ne?

Ko kuwa ba shi da māgada ne?

Me ya sa waɗanda suke bautar Milkom

suka mallaki inda Gad take zama,

Suka zauna a garuruwanta?

2 Domin haka lokaci yana zuwa,

Sa’ad da zan sa mutanen garin

Rabba ta Ammon su ji busar

yaƙi.

Rabba za ta zama kufai,

Za a ƙone ƙauyukanta da wuta,

Sa’an nan Isra’ila zai mallaki

waɗanda suka mallake shi.

Ni Ubangiji na faɗa.

3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama Ai ta

zama kufai!

Ku yi kuka, ku mutanen Rabba, ku

sa tufafin makoki.

Ku yi gudu, kuna kai da kawowa a

cikin garuka,

Gama za a kai Milkom bauta tare da

firistocinsa da wakilansa.

4 Me ya sa kuke taƙama da

ƙarfinku,

Ƙarfinku da yake ƙarewa, ku mutane

marasa aminci?

Kun dogara ga dukiyarku,

Kuna cewa, ‘Wane ne zai iya gāba da

mu?’

5 Ga shi, zan kawo muku razana daga

waɗanda suke kewaye da ku,

Za a kore ku, kowane mutum zai

kama gabansa,

Ba wanda zai tattara ‘yan gudun

hijira.

Ni Ubangiji Allah Mai Runduna

na faɗa.

6 “Amma daga baya zan sa

Ammonawa su wadata kuma,

Ni Ubangiji na faɗa.”

Jawabin Ubangiji a kan Edom

7 Ga abin da Ubangiji Mai Runduna

ya faɗa a kan Edom,

“Ba hikima kuma a cikin Teman?

Shawara ta lalace a wurin masu

basira?

Hikima ta lalace ne?

8 Ku mazaunan Dedan, ku juya, ku

gudu,

Ku ɓuya cikin zurfafa,

Gama zan kawo masifa a kan Isuwa

A lokacin da zan hukunta shi,

9 Idan masu tsinkar ‘ya’yan inabi sun

zo wurinka

Ba za su rage abin kala ba?

Idan kuma ɓarayi sun zo da dare,

Za su ɗauki iyakacin abin da suke so

kurum.

10 Amma na tsiraita Isuwa sarai,

Na buɗe wuraren ɓuyarsa,

Har bai iya ɓoye kansa ba,

An hallakar da mutanen Isuwa

Tare da ‘yan’uwansa da

maƙwabtansa,

Ba wanda ya ragu.

11 Ka bar marayunka, ni zan rayar da

su.

Matanka da mazansu sun mutu,

Sai su dogara gare ni.”

12 Ubangiji ya ce, “Ga shi, waɗanda ba a shara’anta su ga shan ƙoƙon hukunci ba, za su sha shi, to, kai za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, amma lalle za ka sha shi!

13 Gama ni Ubangiji na rantse da zatina, cewa Bozara za ta zama abar tsoro, da abar dariya, da kufai, da abar la’ana. Dukan garuruwanta za su zama kufai har abada.”

14 Irmiya ya ce,

“Na karɓi saƙo daga wurin

Ubangiji.

An aiki jakada a cikin al’ummai

cewa,

‘Ku tattara kanku, ku zo ku yi gāba

da ita,

Ku tasar mata da yaƙi!’

15 Gama ga shi, zan maishe ki

ƙanƙanuwa cikin al’ummai,

Abar raini a wurin mutane.

16 Tsoronki da ake ji da girmankanki

sun ruɗe ki,

Ke da kike zaune a kogon dutse, a

kan tsauni,

Ko da yake kin yi gidanki can sama

kamar gaggafa,

Duk da haka zan komar da ke ƙasa,

Ni Ubangiji na faɗa.”

17 Ubangiji ya ce, “Edom za ta lalace, duk wanda ya bi ta wurin zai gigice, ya yi tsaki saboda dukan masifunta.

18 Abin da zai faru ga Edom zai zama daidai da abin da ya faru ga Saduma, da Gwamrata, da biranen da suke kusa da su, a lokacin da aka kaɓantar da su. Ba wanda zai zauna cikinta, ba wanda kuma zai yi zaman baƙunci a cikinta, ni Ubangiji na faɗa.

19 Kamar yadda zaki yakan fito daga cikin kurmin Urdun, garin ya fāda wa babban garken tumaki, haka zan sa nan da nan su gudu daga gare ta. Zan naɗa wani wanda na zaɓa, gama wa yake kama da ni? Wa zai yi ƙarata? Ina makiyayin da ya isa ya yi gāba da ni?

20 Domin haka, ku ji shirin da ni Ubangiji na yi wa Edom, da abin da nake nufin yi wa mazaunan Teman. Hakika za a tafi da su, har da ƙanana na garken tumaki, zan kuma sa wurin kiwonsu ya zama ƙeƙuwa saboda su.

21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza, za a kuma ji muryar kukansu har a Bahar Maliya.

22 Wani zai tashi da sauri, ya yi sama kamar gaggafa. Zai buɗe fikafikansa a kan Bozara. Zukatan sojojin Edom za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.”

Jawabin Ubangiji a kan Dimashƙu

23 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Dimashƙu,

“Hamat da Arfad sun gigice,

Domin sun ji mugun labari,

sun narke saboda yawan damuwa,

Ba za su iya natsuwa ba.

24 Dimashƙu ta yi halin ƙaƙa naka yi,

Ta juya, ta gudu,

Tsoro ya kama ta,

Azaba da baƙin ciki sun kama ta

kamar na naƙuda.

25 Ƙaƙa aka manta da sanannen birni,

Birnin da take cike da murna?

26 A waccan rana samarinta za su fāɗi a

dandalinta.

Za a hallaka sojojinta duka,

Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.

27 Zan kuma sa wuta a garun Dimashƙu,

Za ta kuwa cinye fādodin

Ben-hadad.”

Jawabin Ubangiji a kan Kedar da Hazor

28 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Kedar da sarakunan Hazor, waɗanda sarki Nebukadnezzar ya ci da yaƙi,

“Ku tashi zuwa Kedar,

Ku hallaka mutanen gabas.

29 Za a kwashe alfarwansu da

garkunansu,

Da labulan alfarwansu, da dukan

kayansu.

Za a kuma tafi da raƙumansu,

Za a gaya musu cewa, ‘Razana ta

kewaye ku!’

30 “Ku mazaunan Hazor, ku gudu zuwa

nesa,

Ku ɓuya cikin zurfafa, ni Ubangiji na

faɗa,

Gama Nebukadnezzar, Sarkin

Babila, ya shirya muku

maƙarƙashiya,

Ya ƙulla mugun nufi game da ku.

31 Ku tashi ku fāɗa wa al’ummar da take

zama lami lafiya,

Waɗanda ba su da ƙofofi ko ƙyamare,

Suna zama su kaɗai.

32 “Za a washe raƙumansu da

garkunan shanunsu ganima,

Zan watsar da masu yin kwaskwas

ko’ina,

Zan kuma kawo musu masifu daga

kowace fuska,

Ni Ubangiji na faɗa.

33 Hazor za ta zama kufai har abada,

wurin zaman diloli,

Ba wanda zai zauna a ciki, ba wanda

kuma zai yi zaman baƙunci a wurin.”

Jawabin Ubangiji a kan Elam

34 Maganar da Ubangiji ya yi wa annabi Irmiya a kan Elam a farkon sarautar Zadakiya Sarkin Yahuza.

35 Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Zan karya bakan Elam, inda

ƙarfinta yake.

36 Zan sa iska ta hura a kan Elam daga

kusurwoyi huɗu na samaniya.

Za ta watsar da mutane ko’ina,

Har ba ƙasar da za a rasa mutumin

Elam a ciki.

37 Zan sa mutanen Elam su ji tsoron

maƙiyansu waɗanda suke neman

ransu.

Da zafin fushina zan kawo musu

masifa,

In sa a runtume su da takobi,

Har in ƙare su duka,

Ni Ubangiji na faɗa.

38 Zan kafa gadon sarautata a Elam,

Zan hallaka sarkinta da

shugabanninta.

39 Amma daga baya zan sa Elam kuma

ta wadata.

Ni Ubangiji na faɗa.”

Categories
IRM

IRM 50

Jawabin Ubangiji a kan Babila

1 Jawabin da Ubangiji ya yi wa annabi Irmiya a kan

Babila da ƙasar Kaldiyawa ke nan,

2 “Ku ba da labari ga sauran

al’umma, ku yi shela,

Ku ta da tuta, ku yi shela,

Kada ku ɓuya, amma ku ce,

‘An ci Babila da yaƙi,

An kunyatar da Bel,

An kunyatar da siffofinta,

Merodak ya rushe,

Gumakanta kuma sun ragargaje!’

3 “Wata al’umma za ta taso daga arewa gāba da ita, za ta mai da ƙasar abar ƙyama, ba wanda zai zauna ciki. Mutum da dabba duk sun watse, kowa ya bar ta.”

4 Ubangiji ya ce, “Sa’ad da lokacin nan ya yi, mutanen Isra’ila da na Yahuza za su zo tare, suna kuka, suna nemana, ni Ubangiji Allahnsu.

5 Za su tambayi hanyar Sihiyona, sa’an nan su bi ta, suna cewa, ‘Bari mu haɗa kanmu don mu yi madawwamin alkawari da Ubangiji, alkawari wanda ba za a manta da shi ba.’

6 “Mutanena sun zama kamar ɓatattun

tumaki,

Waɗanda makiyayansu suka bauɗar

da su,

Suka ɓata a cikin tsaunuka,

Suna kai da kawowa daga wannan

dutse zuwa wancan.

Sun manta da shingensu.

7 Duk waɗanda suka same su, sun

cinye su.

Maƙiyansu suka ce, ‘Ba mu yi laifi

ba,’

Gama sun yi wa Ubangiji laifi,

wanda yake tushen gaskiya,

Ubangiji wanda kakanninsu suka

dogara gare shi.

8 “Ku gudu daga cikin Babila,

Ku fita kuma daga cikin ƙasar

Kaldiyawa,

Ku zama kamar bunsurai waɗanda

suke ja gaban garke.

9 Ga shi, zan kuta manyan ƙasashe

daga arewa

Su faɗa wa Babila da yaƙi.

Za su ja dāgar yaƙi gāba da ita, su

cinye ta.

Kibansu kamar na gwanayen

mayaƙa ne

Waɗanda ba su komowa banza.

10 Za a washe Kaldiyawa,

Waɗanda suka washe su kuwa za su

ƙoshi,

Ni Ubangiji na faɗa.

11 “Saboda kuna murna, kuna farin

ciki,

Ku da kuka washe gādona,

Saboda kuma kuna tsalle kamar

karsana a cikin ciyawa,

Kuna haniniya kamar ingarmu,

12 Domin haka za a kunyatar da Babila

sosai, inda kuka fito.

Za ta zama ta baya duka a cikin

sauran al’umma,

Za ta zama hamada, busasshiyar

ƙasa.

13 Saboda fushin Ubangiji, ba wanda

zai zauna a cikinta,

Za ta zama kufai,

Duk wanda ya bi ta wajen Babila, zai

ji tsoro,

Zai kuma yi tsaki saboda

lalacewarta.

14 “Dukanku ‘yan baka, ku ja dāga, ku

kewaye Babila,

Ku harbe ta, kada ku rage kibanku,

Gama ta yi wa Ubangiji zunubi.

15 Ku kewaye ta da kuwwar yaƙi!

Ta ba da gari,

Ginshiƙanta sun fāɗi.

An rushe garunta,

Gama wannan sakayya ce ta

Ubangiji.

Ku sāka mata, ku yi mata kamar

yadda ta yi.

16 Ku datse wa Babila mai shuka,

Da mai yanka da lauje a lokacin

girbi.

Saboda takobin azzalumi,

Kowa zai koma wurin mutanensa,

Kowa kuma zai gudu zuwa

ƙasarsa.”

17 “Isra’ilawa kamar tumaki ne waɗanda zakuna suka bi su suna kora. Da farko dai Sarkin Assuriya ne ya cinye su. Yanzu kuwa Sarkin Babila, wato Nebukadnezzar, shi ne yake gaigayi ƙasusuwansu.

18 Saboda haka ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila na ce, zan yi wa Sarkin Babila da ƙasarsa hukunci, kamar yadda na hukunta Sarkin Assuriya.

19 Zan komar da Isra’ila a makiyayarsa, zai yi kiwo a Karmel da Bashan. Zai sami biyan bukatarsa a tsaunukan Ifraimu da na Gileyad.

20 Ni Ubangiji na ce sa’ad da lokacin nan ya yi za a nemi laifi da zunubi a cikin Isra’ila da Yahuza, amma ba za a samu ba, gama zan gafarta wa sauran da suka ragu.

21 “Ku haura ku fāɗa wa ƙasar

Meratayim da mazaunan Fekod.

Ku kashe, ku hallaka su sarai,

Ku aikata dukan abin da na umarce

ku,

Ni Ubangiji na faɗa.

22 Hargowar yaƙi tana cikin ƙasar,

Da kuma babbar hallakarwa!

23 Ga yadda aka karya gudumar dukan

duniya!

Ga yadda Babila ta zama abar

ƙyama ga sauran al’umma!

24 Na kafa miki tarko, ya kuwa kama

ki, ya Babila,

Ke kuwa ba ki sani ba.

An same ki, an kama,

Domin kin yi gāba da ni.”

25 Ubangiji ya buɗe taskar

makamansa,

Ya fito da makaman hasalarsa,

Gama Ubangiji Allah Mai Runduna

yana da aikin da zai yi a ƙasar

Kaldiyawa.

26 Ku zo, ku fāɗa mata daga kowane

sashi.

Ku buɗe rumbunanta,

Ku tsittsiba ta kamar tsibin hatsi,

Ku hallakar da ita ɗungum,

Kada wani abu nata ya ragu.

27 Ku kashe dukan bijimanta, a kai su

mayanka!

Kaitonsu, gama kwanansu ya ƙare,

Lokacin hukuncinsu ya yi.

28 Ku ji, sun gudu sun tsere daga ƙasar

Babila,

Don su faɗa cikin Sihiyona,

Sakayyar Ubangiji Allahnmu domin

Haikalinsa.

29 “Ku kirawo ‘yan baka, dukan

waɗanda sukan ja baka, su faɗa

wa Babila.

Ku kafa sansani kewaye da ita, kada

ku bar kowa ya tsira.

Ku sāka mata bisa ga dukan

ayyukanta, gama ta raina Ubangiji

Mai Tsarki na Isra’ila.

30 Domin haka samarinta za su fāɗi a

tituna.

Za a hallaka sojojinta duka a wannan

rana,

Ni Ubangiji na faɗa.

31 “Ga shi, ina gāba da ke, ke Babila,

mai girmankai.

Gama ranar da zan hukunta ki, ta zo,

Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.

32 Mai girmankai za ta yi tuntuɓe ta

fāɗi,

Ba kuwa wanda zai tashe ta,

Zan ƙone garuruwanta da wuta,

Zan kuma hallaka dukan abin da yake

kewaye da ita.

33 “Ni Ubangiji Mai Runduna na ce,

An danne mutanen Isra’ila da na

Yahuza,

Duk waɗanda suka kama su bayi sun

riƙe su da ƙarfi.

Sun ƙi su sake su.

34 Mai fansarsu mai ƙarfi ne,

Ubangiji Mai Runduna ne sunansa.

Hakika zai tsaya musu don ya kawo

wa duniya salama,

Amma zai kawo wa mazaunan Babila

fitina.

35 Ni Ubangiji na ce,

Akwai takobi a kan Kaldiyawa,

Da a kan mazaunan Babila,

Da a kan ma’aikatanta da masu

hikimarta,

36 Akwai takobi a kan masu sihiri

Don su zama wawaye.

Akwai takobi a kan jarumawanta

Don a hallaka su.

37 Akwai takobi a kan mahayan

dawakanta, da a kan karusanta,

Da a kan sojojin da ta yi ijara da su

Don su zama kamar mata,

Akwai takobi a kan dukan dukiyarta

domin a washe ta.

38 Fari zai sa ruwanta ya ƙafe,

Gama ƙasa tana cike da gumaka

waɗanda suka ɗauke hankalin

mutane.

39 “Domin haka namomin jeji da diloli

za su zauna a Babila,

Haka kuma jiminai.

Ba za a ƙara samun mazauna a

cikinta ba har dukan zamanai.

40 Abin da ya faru da Saduma da

Gwamrata,

Da biranen da suke kewaye da su,

Shi ne zai faru da Babila.

Ba mutumin da zai zauna cikinta.

41 “Ga mutane suna zuwa daga arewa,

Babbar al’umma da sarakuna

Suna tahowa daga wurare masu nisa

na duniya.

42 Suna riƙe da baka da māshi,

Mugaye ne marasa tausayi.

Amonsu yana kama da rurin teku,

Suna shirya don yin yaƙi da ke, ya

Babila.

43 Sarkin Babila ya ji labarinsu,

Hannuwansa suka yi suwu.

Wahala da azaba sun kama shi

kamar mace mai naƙuda.

44 “Ni Ubangiji ina zuwa kamar zakin da yake fitowa daga kurmin Urdun zuwa makiyaya. Nan da nan zan sa su gudu daga gare ta. Sa’an nan zan naɗa mata wanda na zaɓa. Wa yake kama da ni? Wa zai yi ƙarata? Wane shugaba zai yi gāba da ni?

45 Saboda haka ku ji shirin da Ubangiji ya yi gāba da Babila, da nufin ya yi gaba da ƙasar Kaldiyawa. Hakika za a tafi da ƙananansu, garke zai zama kango.

46 Duniya za ta girgiza sa’ad da ta ji an ci Babila da yaƙi. Za a ji kukanta cikin sauran al’umma.”