Categories
IRM

IRM 51

Hukuncin Ubangiji a kan Babila

1 Ubangiji ya ce,

“Ga shi, zan kawo iskar ɓarna a

kan Babila

Da mazaunan Kaldiya.

2 Zan aika da masu casawa zuwa

Babila, za su casa ta,

Su bar ƙasarta kango.

Za su kewaye ta a kowane sashi

A wannan ranar masifa.

3 Kada ku bar maharbi ya yi harbi da

bakansa,

Kada kuma ya sa kayan yaƙinsa,

Kada ku rage samarinta,

Ku hallaka dukan sojojinta.

4 Za su fāɗi matattu a ƙasar

Kaldiyawa,

Za a sassoke su a titunansu.”

5 Allah na Isra’ila da Yahuza,

Ubangiji Mai Runduna, bai yashe

su ba,

Ko da yake sun yi wa Mai Tsarki na

Isra’ila zunubi.

6 Ku gudu daga cikin Babila,

Bari kowa ya ceci ransa,

Kada a hallaka ku tare da ita,

Gama a wannan lokaci Ubangiji zai

sāka mata,

Zai sāka mata bisa ga alhakinta.

7 Babila ta zama ƙoƙon zinariya a

hannun Ubangiji,

Ta sa dukan duniya ta yi maye.

Ƙasashen duniya sun sha ruwan

inabinta, suka haukace.

8 Farat ɗaya, Babila ta fāɗi, ta

kakkarye,

Ku yi kuka dominta!

Ku samo mata magani domin azabar

da take sha, watakila ta warke.

9 Mun ba Babila magani, amma ba ta

warke ba.

Bari mu ƙyale ta, kowannenmu ya

koma garinsu,

Gama hukuncinta ya kai sammai, ya

yi tsawo har samaniya.

10 Ubangiji ya baratar da mu a fili,

Bari mu tafi mu yi shelar aikin

Ubangiji Allahnmu a cikin

Sihiyona.

11 Ku wasa kibau, ku cika

kwaruruwanku!

Ubangiji ya ta da ruhun sarakunan

Mediyawa,

Domin yana niyyar hallaka Babila.

Gama Ubangiji zai yi ramuwa

saboda Haikalinsa.

12 Ku ta da tuta don a faɗa wa garun

Babila,

Ku ƙarfafa matsara,

Ku sa su su yi tsaro,

Ku kuma sa ‘yan kwanto!

Ga shi, Ubangiji ya yi niyya, ya kuwa

aikata

Abin da ya faɗa a kan mazaunan

Babila.

13 Ƙarshenki ya zo,

Ke mai zama kusa da ruwa mai yawa,

Mai yawan dukiya.

Ajalinki ya auka.

14 Ubangiji Mai Runduna ya rantse da

zatinsa, ya ce,

“Hakika zan cika Babila da mutane

kamar fāra,

Za su kuwa raira waƙar nasara a

kanta.”

15 Ubangiji ne ya halicci ƙasa da

ikonsa,

Ya kafa duniya da hikimarsa,

Ya kuma shimfiɗa sammai da

fahiminsa.

16 Bisa ga umarninsa ruwan da yake

samaniya yakan yi ruri,

Yakan sa gajimare su tashi daga

ƙarshen duniya,

Yakan sa walƙiya ta walƙata cikin

ruwan sama,

Yakan sa iska ta haura daga cikin

taskokinsa.

17 Kowane ɗan adam wawa ne, marar

ilimi,

Kowane maƙerin zinariya kuma zai

sha kunya daga wurin gumakansa,

Gama siffofinsa na ƙarya ne, ba

numfashi a cikinsu.

18 Su marasa amfani ne, aikin ruɗarwa

ne kawai,

Za su lalace a lokacin da za a

hukunta su.

19 Amma wanda yake wajen Yakubu ba

haka yake ba,

Domin shi ne ya halicci dukan

abu,

Isra’ila kuwa abin mallakarsa ne,

Ubangiji Mai Runduna ne sunansa.

20 Ubangiji ya ce,

“Kai ne guduma da kayan yaƙina,

Da kai ne na farfasa ƙasashen

duniya,

Da kai ne na hallaka mulkoki.

21 Da kai ne na karya doki da

mahayinsa,

22 Da kai ne na farfasa karusa da

mahayinsa.

Da kai ne na kakkarya mace da

namiji,

Da kai ne na kakkarya tsoho da

saurayi,

Da kai ne na kakkarya saurayi da

budurwa,

23 Da kai ne na kakkarya makiyayi da

garkensa,

Da kai ne na kakkarya manoma da

dawakan nomansa,

Da kai ne na kakkarya masu mulki

da shugabanni.”

24 Ubangiji ya ce, “Zan sāka wa Babila da dukan mazaunan Kaldiya a ganin idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona.

25 Ga shi, ina gaba da kai, ya dutse mai

hallakarwa,

Wanda ya hallaka duniya duka.

Zan miƙa hannuna gāba da kai,

Zan mirgino da ƙasa daga

ƙwanƙolin dutse,

Zan maishe ka ƙonannen dutse.

26 Ba za a sami dutsen yin kusurwa, ko

na kafa harsashen gini a cikinka

ba,

Amma za ka zama marar amfani har

abada.”

27 Ku ta da tuta a duniya,

Ku busa wa ƙasashen duniya ƙaho,

Ku shirya ƙasashe don su yi yaƙi

da ita,

Ku kirawo mulkokin Ararat, da na

Minni, da na Ashkenaz, su yi yaƙi

da ita.

Ku naɗa sarkin yaƙi wanda zai

shugabanci yaƙin da za a yi da ita,

Ku kawo dawakai kamar fāra.

28 Ku shirya ƙasashe su yi yaƙi da ita,

Sarakunan Mediyawa, da masu

mulkinsu, da shugabanninsu,

Da kowace ƙasar da take ƙarƙashin

mulkinsu.

29 Duniya ta girgiza, tana makyarkyata

saboda azaba,

Gama nufin Ubangiji na gāba da

Babila ya tabbata,

Nufinsa na mai da ƙasar Babila

kufai, inda ba kowa.

30 Sojojin Babila sun daina yaƙi, suna

zaune a cikin kagaransu.

Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata,

An sa wa wuraren zamanta wuta,

An karya ƙyamaren ƙofofin

garinta.

31 Maguji yana biye da maguji a guje,

Jakada yana biye da jakada,

Don su faɗa wa Sarkin Babila, cewa

an ci birninsa a kowane gefe.

32 An ƙwace mashigai

An ƙone fadamu da wuta,

Sojoji sun gigice.

33 Ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na

Isra’ila na ce,

“Mutanen Babila sun zama kamar

daɓen masussuka

A lokacin da ake sussuka,

Ba kuwa da daɗewa ba lokacin girbe

ta zai zo.”

34 Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya

cinye Urushalima,

Ya ragargaza ta,

Ya maishe ta kufai,

Ya haɗiye ta kamar yadda dodon

ruwa yakan yi,

Ya cika cikinsa da kayan

marmarinta,

Ya tatse ta sarai.

35 Bari mutanen Sihiyona su ce,

“Allah ya sa muguntar da mutanen

Babila suka yi mana ta koma

kansu!”

Bari kuma mutanen Urushalima su

ce,

“Allah ya sa hakkin jininmu ya koma

kan Kaldiyawa!”

36 Ubangiji ya ce,

“Zan tsaya muku,

Zan ɗaukar muku fansa,

Zan sa tekunsu da maɓuɓɓugarsu su

ƙafe.

37 Babila za ta zama tarin juji, wurin

zaman diloli,

Abar ƙyama da abar ba’a, inda ba

kowa.

38 Mutanen Babila za su yi ruri kamar

zakuna,

Su yi gurnani kamar ‘ya’yan zaki.

39 Sa’ad da suke cike da haɗama zan yi

musu biki,

In sa su sha, su yi maye, su yi

murna.

Za su shiga barcin da ba za su farka

ba.

40 Zan kai su mayanka kamar ‘yan

raguna, da raguna, da bunsurai.

41 “An ci Babila,

Ita wadda duniya duka take yabo an

cinye ta da yaƙi,

Ta zama abar ƙyama ga sauran

al’umma!

42 Teku ta malalo a kan Babila,

Raƙuman ruwa masu hauka sun

rufe ta.

43 Garuruwanta sun zama abin

ƙyama,

Ta zama hamada, inda ba ruwa,

Ƙasar da ba mazauna,

Ba kuma mutumin da zai ratsa ta

cikinta.

44 Zan hukunta Bel, gunkin Babila,

Zan sa ya yi aman abin da ya

haɗiye,

Ƙasashen duniya ba za su ƙara

bumbuntowa wurinsa ba.

Garun Babila ya rushe!”

45 “Ku fito daga cikinta, ya jama’ata,

Kowa ya tsere da ransa daga zafin

fushin Ubangiji.

46 Kada zuciyarku ta yi suwu,

Kada kuma ku ji tsoro saboda

labarin da ake ji a ƙasar,

Labari na wannan shekara dabam,

na wancan kuma dabam,

A kan hargitsin da yake a ƙasar,

Mai mulki ya tasar wa mai mulki.

47 Saboda haka kwanaki suna zuwa,

Sa’ad da zan hukunta gumakan

Babila,

Za a kunyatar da dukan ƙasar

Babila,

Dukan matattunta za su faɗi a

tsakiyarta.

48 Sa’an nan sama da duniya, da dukan

abin da take cikinsu,

Za su raira waƙar farin ciki,

Domin masu hallakarwa daga arewa

da za su auko mata,

Ni Ubangiji na faɗa.”

49 Babila za ta fāɗi,

Saboda mutanen Isra’ila da dukan

mutanen duniya waɗanda ta

kashe.

50 Ku waɗanda kuka tsere wa takobi!

Ku gudu! Kada ku tsaya!

Ku tuna da Ubangiji a can nesa inda

kuke,

Ku kuma yi ta tunawa da

Urushalima.

51 Mun sha kunya saboda zargin da ake

yi mana,

Kunya ta rufe mu,

Gama baƙi sun shiga tsarkakan

wurare na Haikalin Ubangiji.

52 “Domin haka kwanaki suna zuwa,”

in ji Ubangiji,

“Sa’ad da zan hukunta gumakan

Babila, da dukan ƙasarta,

Waɗanda aka yi wa rauni, za su yi

nishi.

53 Ko da Babila za ta hau samaniya,

Ta gina kagara mai ƙarfi a can,

Duk da haka zan aiki masu

hallakarwa a kanta,

Ni Ubangiji na faɗa.”

54 Ku ji muryar kuka daga Babila,

Da hargowar babbar hallakarwa

daga ƙasar Kaldiyawa!

55 Gama Ubangiji yana lalatar da

Babila,

Yana kuma sa ta kame bakinta na

alfarma,

Sojoji suna kutsawa kamar raƙuman

ruwa,

Suna ta da muryoyinsu.

56 Gama mai hallakarwa ya auka wa

Babila,

An kama sojojinta,

An kuma kakkarya bakunansu,

Gama Ubangiji shi Allah ne, mai

sakayya,

Zai yi sakayya sosai.

57 “Zan sa mahukuntanta, da masu

hikimarta,

Da masu mulkinta, da

shugabanninta,

Da sojojinta su sha su yi maye.

Za su dinga yin barcin da ba za su

farka ba,”

In ji Sarkin, mai suna Ubangiji Mai

Runduna.

58 “Ni Ubangiji Mai Runduna, na ce,

Za a baje garun nan na Babila mai

fāɗi

Za a kuma ƙone dogayen

ƙyamarenta da wuta.

Mutane sun wahalar da kansu a

banza.

Sauran al’umma sun yi wahala kawai

domin wutar lalata.”

59 Jawabin da annabi Irmiya ya ba Seraiya, ɗan Neriya, wato jikan Ma’aseya, lokacin da ya tafi tare da Zadakiya, Sarkin Yahuza, zuwa Babila a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Seraiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.

60 Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babila, wato dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babila.

61 Irmiya kuwa ya ce wa Seraiya, “Lokacin da ka kai Babila, sai ka karanta dukan maganan nan.

62 Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’

63 Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yufiretis.

64 Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babila za ta nutse, ba za ta ƙara tashi ba saboda masifar da Ubangiji zai kawo mata.’ ”

Wannan shi ne ƙarshen maganar Irmiya.

Categories
IRM

IRM 52

Mulkin Zadakiya

1 Zadakiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal, ‘yar Irmiya, wanda yake zaune a Libna.

2 Sarki Zadakiya ya aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehoyakim ya yi.

3 Al’amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra’ila da Yahuza, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala.

Faɗuwar Urushalima

Zadakiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babila.

4 A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zadakiya, Sarkin Yahuza, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina garu kewaye da ita.

5 An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zadakiya.

6 A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci.

7 Sai aka huda garun birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa’ad da Kaldiyawan take kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba.

8 Amma sojojin Kaldiyawa suka runtumi sarki Zadakiya, suka ci masa a filayen Yariko. Dukan sojoji suka yashe shi.

9 Da aka kama Zadakiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babila a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babila ya yanke masa shari’a.

10 Ya kuwa kashe ‘ya’yan Zadakiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuza a Ribla.

11 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zadakiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babila inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.

Yahuza ya Je Zaman Talala

12 A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babila, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima.

13 Sai ya ƙone Haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan manyan gidajen da suke Urushalima.

14 Sojojin Kaldiyawa da suke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan garun Urushalima.

15 Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babila, da sauran masu sana’a, ya kai su bautar talala a Babila.

16 Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki.

17 Kaldiyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda suke a Haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babila.

18 Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar Haikali.

19 Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe.

20 Tagullar da sarki Sulemanu ya yi waɗannan abubuwa da ita, wato ginshiƙai biyu, da kwatarniyar tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda suke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.

21 Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma taƙi huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki.

22 A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman.

23 Akwai siffofin rumman tasa’in da shida da ake gani a gyaffan. Dukan siffofin rumman da suke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne.

24 Shugaban matsara kuma ya ɗauki Seraiya babban firist, da Zafaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar Haikali, ya tafi da su.

25 Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai ‘yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su.

26 Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babila a Ribla,

27 Sarkin Babila kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat.

Haka aka tafi da mutanen Yahuza bautar talala.

28 Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa dubu uku da ashirin da uku (3,023).

29 A shekara ta goma sha takwas ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima ɗari takwas da talatin da biyu.

30 A shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa kuma, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa ɗari bakwai da arba’in da biyar. Jimillarsu duka kuwa dubu huɗu da ɗari shida ne (4.600).

An saki Yekoniya an ba shi Girma a Babila

31 A shekarar da Ewil-merodak ya zama Sarkin Babila, sai ya nuna wa Yekoniya Sarkin Yahuza alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yekoniya bauta.

32 Ewil-merodak ya nuna wa Yekoniya alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babila tare da shi.

33 Yekoniya ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa.

34 Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarki, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.