Categories
K. MAG

K. MAG 1

Amfanin Karin Magana

1 Karin maganar Sulemanu, ɗan Dawuda, Sarkin Isra’ila.

2 Ga Karin magana da za su taimake ka ka rarrabe da hikima, da kyakkyawar shawara, da fahimtar ma’anar zurfafan karin magana,

3 da yadda za ka karɓi koyarwa ta hanyar hikima, da adalci, da gaskiya, da sanin abin da yake daidai.

4 Sukan sa marar sani ya zama masani, sukan koya wa samari yadda za su zama masu amfani.

5 Waɗannan karin magana sukan ƙara wa masu ilimi hikima, sukan zama jagora ga masana,

6 don su fahimci ɓoyayyiyar ma’anar da take cikin karin magana, da mawuyatan al’amura waɗanda masu hikima suka ƙago.

7 In kana so ilimi dole ne ka fara da tsoron Ubangiji. Jahilai ba su san darajar hikima ba, sun kuwa ƙi su koya.

Gargaɗi da Faɗaka

8 Ɗana, ka kasa kunne ga koyarwar mahaifinka, ka mai da hankali ga abin da mahaifiyarka take faɗa.

9 Koyarwarsu za ta inganta halinka, ta zama kayan ado kamar kyakkyawan rawani a kanka, ko kyakkyawan abin wuya a wuyanka, don su ƙara maka kyau.

10 Ɗana sa’ad da masu zunubi suka jarabce ka, kada ka yarda

11 in suka ce maka, “Zo mu tafi mu nemi wani mutum mu kashe, mu je, mu fāɗa wa marasa laifi mu ji daɗi!

12 Ba mu damu da ransu da lafiyarsu ba, mu dai mu tafi mu kashe su, mu hallaka su ɗungum.

13 Za mu sami dukiya iri iri, mu cika gidajenmu da ganima!

14 Ka zo ka haɗa kai da mu, dukanmu kuwa za mu raba abin da muka sato.”

15 Ɗana, kada ka gama kanka da irin waɗannan mutane, ka yi nesa da su.

16 Ba su kasalar aikata mugunta, kullum a shirye suke su yi kisankai.

17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idon tsuntsun da ake so a kama.

18 Amma waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko. Ba za su kama kome ba, sai rayukansu.

19 Yin fashi yakan zama sanadin mutuwar ɗan fashi a koyaushe. Wannan shi ne abin da yakan sami kowane mutum da ya kama sana’ar sata.

Hikima Tana Kira

20 Ku kasa kunne! Hikima tana kira a tituna da a kasuwoyi.

21 Tana kira da ƙarfi a ƙofofin birni, a duk inda mutane suke tattaruwa.

22 Ta ce, “Wawayen mutane! Har yaushe za ku yi ta kasancewa haka? Har yaushe za ku daina jin daɗin yi wa mai ilimi ba’a? Faufau ba za ku taɓa koya ba?

23 Ku kasa kunne lokacin da nake tsauta muku, zan ba ku shawara mai kyau, mu yi tarayya cikin ilimina.

24 Ina ta kiranku ina gayyatarku ku zo, amma ba ku kula ba, ba ku mai da hankali gare ni ba.

25 Kun ƙi bin shawarwarina duka, ba ku yarda in gyara kuskurenku ba.

26 Saboda haka, lokacin da kuke shan wahala, zan yi muku dariya. Zan yi muku ba’a lokacin da razana ta auka muku,

27 sa’ad da ta zo muku kamar hadiri mai ƙaƙƙarfar iska mai wahalarwa, sa’ad da kuke shan azaba da damuwa.

28 Sa’an nan za ku kira gare ni, amma ba za ku same ni ba. Za ku neme ni a ko’ina, amma ba za ku same ni ba.

29 Domin ba ku taɓa sanin amfanin ilimi ba, kun ƙi tsoron Ubangiji a kullum.

30 Ba ku taɓa yarda da shawarata ba, ko ku yarda in gyara kuskurenku.

31 Saboda haka za ku karɓi sakayyarku, ayyukanku za su cuce ku.

32 Marasa sani sukan mutu saboda ba su yarda da hikima ba. Wawaye kuwa sukan hallaka saboda rashin kulawarsu.

33 Amma duk wanda ya kasa kunne gare ni, zai zauna lafiya. Ba abin da zai same shi, ba abin da zai tsorata shi.”

Categories
K. MAG

K. MAG 2

Sakamakon Neman Hikima

1 Ɗana, ka koyi abin da nake koya maka, sam kada ka manta da abin da na faɗa maka ka yi.

2 Ka kasa kunne ga abin da yake na hikima, ka yi ƙoƙari ka fahimce shi.

3 I, ka roƙi ilimi da tsinkaya.

4 Ka nema da iyakar ƙoƙarinka kamar yadda za ka nemi azurfa, ko kowace irin ɓoyayyiyar dukiya.

5 Idan ka yi za ka san abin da ake nufi da tsoron Ubangiji. Za ka yi nasara a kan koyon sanin Allah.

6 Ubangiji ne yake ba da hikima. Ilimi da fahimi kuwa suna cikin kalmominsa.

7 Shi yake tanada wa adalai taimako da kiyayewa, wato mutane masu aminci.

8 Yakan kiyaye waɗanda suke lura da kyau, ya kiyaye waɗanda suke dogara gare shi.

9 Idan ka kasa kunne gare ni za ka san abin da yake daidai, da abin da yake gaskiya, da abin da yake na kirki. Za ka san abin da za ka yi.

10 Za ka zama mai hikima, iliminka zai faranta maka rai.

11 Tsinkayarka da fahiminka za su tsare ka.

12 Za su hana ka aikata mugayen ayyuka, za su nisantar da kai daga mutane masu ta da hargitsi da irin maganganunsu,

13 mutane waɗanda suka bar zaman adalci don su zauna cikin duhun zunubi,

14 waɗanda suke jin daɗin yin laifi, suna nishaɗi cikin mugunta.

15 Ba za a dogara da su ba, ba kuwa za a iya amincewa da su ba.

16 Za a nisantar da kai daga mazinaciya, wadda take ƙoƙari ta lalatar da kai da daɗin bakinta,

17 marar aminci ga mijinta, wadda ta manta da tsarkakan alkawaran da ta ɗauka.

18 Idan ka tafi gidanta ka kama hanyar mutuwa. Tafiya can kama hanyar zuwa lahira ne.

19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa. Ba zai ƙara komowa ga hanyar rai ba.

20 Saboda haka dole ka bi hanyar da mutanen kirki suka bi, ka bi gurbin adalai.

21 Mutane adalai, masu kamewa, su ne za su zauna ƙasarmu.

22 Amma Allah zai fizge mugaye daga ƙasar, ya kuma tumɓuke masu zunubi kamar yadda ake tumɓuke shuke-shuke daga ƙasa.

Categories
K. MAG

K. MAG 3

Gargaɗin Yin Biyayya

1 Ɗana kada ka manta da abin da na koya maka. Kullum ka tuna da abin da na faɗa maka ka yi.

2 Koyarwata za ta ba ka tsawon rai da wadata.

3 Kada ka yarda ka rabu da biyayya da aminci, ka ɗaura su a wuyanka, ka rubuta su kuma a zuciyarka.

4 Idan ka yi wannan kuwa, Allah zai yi murna da kai. Za ka yi nasara cikin hulɗar da kake yi da mutane.

5 Ka dogara ga Ubangiji da zuciya ɗaya, kada ka dogara ga abin da kake tsammani ka sani.

6 A cikin dukan abin da kake yi, ka tuna da Ubangiji, shi kuma zai nuna maka hanyar da take daidai.

7 Sam, kada ka yarda ka ɗauki kanka kai mai hikima ne fiye da yadda kake, kai dai ka ji tsoron Ubangiji, ka rabu da aikata mugunta.

8 Idan ka kiyaye wannan, zai zama maka kamar magani mai kyau, ya warkar da raunukanka, ya kuma sawwaƙe maka azabar da kake sha.

9 Ka girmama Ubangiji ta wurin miƙa masa hadaya daga mafi kyau na amfanin gonarka.

10 Idan ka yi haka rumbunanka za su cika da hatsi. Za ka sami ruwan inabi mai yawa, har ka rasa wurin da za ka zuba shi duka.

11 Ɗana, sa’ad da Ubangiji ya tsauta maka ka mai da hankali sosai, ka kuma yarda da gargaɗinsa.

12 Ubangiji yana tsauta wa waɗanda yake ƙauna. Kamar yadda mahaifi yakan tsauta wa ɗan da yake fāriya da shi.

13 Mai farin ciki ne mutumin da ya zama mai hikima, ya kuma sami fahimi.

14 Yana da riba mai yawan gaske fiye da ta azurfa, tamaninta a gare ka ya fi na zinariya.

15 Tamanin hikima ya fi na lu’ulu’ai, ya kuma fi kowane irin abin da kake so tamani.

16 Hikima takan tsawanta ranka, ta kuma ba ka dukiya da daraja.

17 Hikima takan sa ka ji daɗin zama, ta kuma bi da kai lafiya a zamanka.

18 Masu farin ciki ne waɗanda suka sami hikima, hikima za ta ba su rai kamar yadda itace yakan ba da ‘ya’ya.

19 Ubangiji ya halicci duniya ta wurin hikimarsa,

Ya shimfiɗa sararin sama a inda yake ta wurin saninsa.

20 Hikimarsa ta sa ruwan koguna ya yi gudu,

Gizagizai kuwa su zubo da ruwa bisa duniya.

21 Ɗana ka riƙe hikimarka da basirarka. Ko kusa kada ka bari su rabu da kai.

22 Za su tanada maka rai, rai mai daɗi da farin ciki.

23 Za ka bi hanyarka lafiya lau, ba ko tuntuɓe.

24 Ba za ka ji tsoro, sa’ad da kake kwance a gadonka ba, za ka yi ta sharar barci a dukan dare.

25 Ba za ka damu da masifar da za ta auko farat ɗaya ba, irin wadda takan auka wa mugaye kamar hadiri.

26 Ubangiji zai kiyaye ka. Ba zai bari ka fāɗa cikin tarko ba.

27 Ka yi wa masu bukata alheri a duk lokacin da kake iyawa.

28 Sam, kada ka ce wa maƙwabcinka ya dakata sai gobe, idan dai kana iya taimakonsa yanzu.

29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, gama yana zaune kusa da kai, yana kuwa amincewa da kai.

30 Kada ka yi jayayya ba dalili da wanda bai taɓa cutarka ba.

31 Kada ka ji kishin masu ta da zaune tsaye, ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu,

32 gama Ubangiji yana ƙin mutanen da suke aikata mugunta, amma yakan rungumi adalai ya amince da su.

33 Ubangiji yakan la’antar da gidajen masu mugunta, amma yakan sa wa gidajen adalai albarka.

34 Ba ruwansa da masu girmankai, amma masu tawali’u sukan sami tagomashi a wurinsa.

35 Mutane masu hikima za su sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.

Categories
K. MAG

K. MAG 4

Fa’idodin Hikima

1 ‘Ya’yana ku kasa kunne ga koyarwar mahaifinku. Ku mai da hankali, za ku zama haziƙai.

2 Abin da nake koya muku, abu mai kyau ne, saboda haka ku tuna da shi duka.

3 Sa’ad da nake ɗan yaro tilo a wurin iyayena,

4 mahaifina yakan koya mini, yakan ce, “Ka tuna da abin da nake faɗa maka, kada ka manta. Ka yi abin da na faɗa maka za ka rayu.

5 Ka nemi hikima da basira! Kada ka manta ko ka ƙyale abin da na faɗa.

6 Kada ka rabu da hikima, gama za ta kiyaye ka, ka ƙaunace ta, za ta kiyaye lafiyarka.

7 Samun hikima shi ne mafificin abin da za ka yi. Kome za ka samu dai, ka sami basira.

8 Ka ƙaunaci hikima, za ta girmama ka. Ka rungume ta, za ta kawo maka daraja.

9 Za ta zamar maka rawanin daraja.”

10 Ɗana, ka kasa kunne gare ni. Ka ɗauki abin da nake faɗa maka, muhimmin abu ne, za ka yi tsawon rai.

11 Gama na koya maka hikima da hanyar zama mai kyau.

12 Idan ka yi tafiya da hikima ba abin da zai tsare maka hanya, sa’ad da kake gudu ba za ka yi tuntuɓe ba.

13 Kullum ka tuna da abin da ka koya, iliminka shi ne ranka, ka lura da shi da kyau.

14 Kada ka tafi inda mugaye suke tafiya, kada ka bi gurbin mugaye.

15 Kada ka yi mugunta! Ka nisance ta! Ka ƙi ta, yi tafiyarka.

16 Mugaye ba su iya yin barci, sai sun aikata ɓarna. Ba su barci sai sun cuci wani.

17 Mugunta da ta’adi kamar ci da sha suke a gare su.

18 Hanyar da adalai suke bi kamar fitowar rana ce, sai ta yi ta ƙara haske, har ta take tsaka.

19 Hanyar mugaye kuwa duhu ne baƙi ƙirin, kamar duhun dare. Sukan fāɗi, amma ba su san abin da ya sa suka yi tuntuɓe ba.

20 Ɗana, ka kula da abin da nake faɗa. Ka kasa kunne ga kalmomina.

21 Kada ka kuskura su rabu da kai, ka tuna da su, ka ƙaunace su.

22 Za su ba da rai da lafiya ga dukan wanda ya fahimce su.

23 Tunane-tunanenka mafarin rai ne kansa, ka kiyaye su abin mallakarka ne mafi daraja.

24 Kada ka faɗi kowane abu da yake ba na gaskiya ba, kada wani abu ya haɗa ka da ƙarya, ko maganganun ruɗawa.

25 Ka duba gaba sosai gabanka gaɗi, ba tsoro.

26 Ka tabbata ka san abin da kake yi, duk abin da kake yi kuma zai zama daidai.

27 Ka rabu da mugunta ka yi tafiyarka sosai, kada ka kauce ko da taki ɗaya daga hanyar da take daidai.

Categories
K. MAG

K. MAG 5

Faɗakarwa a kan Fasikanci

1 Ɗana, ka mai da hankali, ka kasa kunne ga hikimata da basirata.

2 Sa’an nan ne za ka san yadda za ka yi kome daidai, kalmominka za su nuna kana da ilimi.

3 Leɓunan matar wani, mai yiwuwa ne, su yi zaƙi kamar zuma, sumbace-sumbacenta kuma su fi man zaitun taushi.

4 Amma bayan an gama duka, ba abin da za ta bar maka sai baƙin ciki, da azaba.

5 Za ta gangara da kai zuwa lahira, hanyar da take bi hanyar mutuwa ce.

6 Ba a kan hanyar rai take ba, tana ragaita nesa da hanyar, amma kai ba ka ankara ba.

7 ‘Ya’yana, ku kasa kunne gare ni yanzu, kada ko kusa ku manta da abin da nake faɗa.

8 Ku yi nesa da irin wannan mace! Kada ku yarda ku yi ko kusa da ƙofarta!

9 Idan kuwa kun yi, girmamawar da ake yi muku za ta zama ta waɗansu. Za ku yi mutuwar ƙuruciya ta hannun mutane marasa imani.

10 Hakika, baƙi za su kwashe dukan dukiyarku, abin da kuka sha wahalar samu kuma zai zama rabon wani dabam.

11 Za ku kwanta kuna nishi a kan gadon mutuwa, namanku da tsokokinku za su zagwanye.

12 Sa’an nan za ku ce, “Me ya sa ban taɓa koyo ba? Me ya sa ban yarda wani ya kwaɓe ni ba?

13 Ban kasa kunne ga malamaina ba. Ban mai da hankalina gare su ba.

14 Farat ɗaya sai aka kunyatar da ni a bainar jama’a.”

15 Ka yi aminci ga matarka, ka ƙaunace ta ita kaɗai.

16 Idan kuma waɗansu mata sun haifa maka ‘ya’ya, ‘ya’yan nan ba za su yi maka wani amfani ba.

17 ‘Ya’yanka za su yi girma su taimake ka, ba na baƙi ba.

18 Saboda haka ka yi farin ciki tare da matarka, ka yi murna da budurwa da ka auro,

19 kyakkyawa mai kyan gani kamar barewa. Bari kyanta ya ɗau hankalinka. Bari ƙaunarta ta kewaye ka.

20 Ɗana, don me za ka fi son matar wani? Don me za ka bar matar wani ta lallame ka da daɗin bakinta?

21 Ubangiji yana ganin dukan abin da kake yi. Inda ka shiga duk yana kallonka.

22 Zunuban mutum tarko ne, komar zunubinsa ce take kama shi.

23 Yakan mutu saboda rashin kamewarsa, cikakkiyar wautarsa za ta kai shi kabarinsa.

Categories
K. MAG

K. MAG 6

Faɗakarwa a kan Ragwanci da Ƙarya

1 Ɗana, ka taɓa yin alkawari ka ɗaukar wa wani lamuni?

2 Maganganunka sun taɓa kama ka, ko alkawaranka sun taɓa zamar maka tarko?

3 To, ɗana, kana cikin ikon wannan mutum, amma ga yadda za ka yi ka fita, sheƙa zuwa wurinsa, ka roƙe shi ya sake ka.

4 Kada ka yarda ka yi barci ko ka huta.

5 Ka fita daga cikin tarkon kamar tsuntsu ko barewar da ta tsere wa maharbi.

6 Bari ragwaye su yi koyi da tururuwa.

7 Ba su da shugaba, ba su da sarki, ko mai mulki,

8 amma da kaka sukan tanada wa kansu abinci, domin kwanakin bazara.

9 Har yaushe rago zai yi ta ɓalɓalcewa? Yaushe zai farka?

10 Yakan ce, “Bari in ɗan ruruma, in naɗa hannuwana in shaƙata.”

11 Amma lokacin da yake sharar barci, tsiya za ta auka masa kamar ɗan fashi da makamai.

12 Sakarkari, wato mugaye sukan yi ta baza jita-jita.

13 Sukan yi ƙyifce, ko su yi nuni don su yaudare ka.

14 A kowane lokaci suna shirya mugunta a kangararren hankalinsu, suna kuta tashin hankali ko’ina.

15 Saboda wannan masifa za ta fāɗa musu farat ɗaya ba makawa, za a yi musu mummunan raini.

16-19 Akwai abu shida, i, har bakwai ma, waɗanda Ubangiji yake ƙi, waɗanda ba zai haƙura da su ba,

duban raini,

harshe mai faɗar ƙarya,

hannuwan da suke kashe marasa laifi,

kwanyar da take tunane-tunanen mugayen dabaru,

mutum mai gaggawar aikata mugunta,

mai yawan shaidar zur,

mutum mai ta da fitina a tsakanin abokai.

Faɗakarwa a kan Zina

20 Ɗana, ka yi abin da mahaifinka ya faɗa maka, kada ka manta da koyarwar mahaifiyarka.

21 Kullum ka kiyaye abin da suke faɗa maka, ka kulle su kuma a zuciyarka.

22 Koyarwarsu za ta bi da kai sa’ad da kake tafiya, ta kiyaye ka da dare, ta kuma ba ka shawara da rana.

23 Doka da abubuwan da take koyarwa haske ne mai haskakawa. Tsautawa tana iya koya maka zaman duniya.

24 Za ta tsare ka daga mugayen mata, daga kalmomin alfasha da suke fitowa daga bakin matan waɗansu.

25 Kada kyansu ya jarabce ka, kada ka faɗa cikin tarkon feleƙensu.

26 Mutum ta dalilin karuwa zai sha hasarar abin da ya mallaka duka ta wurin zina.

27 Ka iya rungumar wuta a ƙirjinka sa’an nan ka ce ba za ta ƙone tufafinka ba?

28 Ka iya tafiya a kan garwashi sa’an nan ka ce ƙafafunka ba za su ƙone ba?

29 Haka yake da mutumin da ya kwana da matar wani. Duk wanda ya aikata wannan, zai sha wahala.

30 Mutane ba sukan raina wanda ya saci abinci don yana jin yunwa ba,

31 duk da haka in an kama shi, sai ya biya diyya sau bakwai, tilas kuwa ya ba da dukan abin da yake da shi.

32 Amma mazinaci marar hankali ne, gama hallaka kansa yake yi.

33 Zai sha dūka, a wulakanta shi, zai dawwama cikin kunya.

34 Hasalar miji mai kishi babu irinta, ramawarsa ba dama.

35 Ba zai karɓi biya ba, ba kyautar da za a yi masa wadda za ta kwantar da fushinsa.

Categories
K. MAG

K. MAG 7

Wayon Mazinaciya

1 Ɗana, ka tuna da abin da na faɗa, kada ka manta da abin da na ce maka ka yi.

2 Ka yi abin da na faɗa maka, za ka rayu. Ka natsu, ka bi koyarwata, ka tsare ta kamar ƙwayar idonka.

3 Kullayaumi ka riƙe koyarwata tare da kai, ka rubuta ta a zuciyarka.

4 Ka mai da hikima ‘yar’uwarka, basira kuwa ta zama ƙawarka ta jikinka.

5 Za su nisanta ka da matan mutane, daga kuma mata masu maganganun alfasha.

6 Wata rana ina leƙawa ta tagar ɗakina,

7 sai na ga waɗansu samari masu yawa waɗanda ba su gogu da duniya ba, musamman sai na lura da wani dolo a cikinsu.

8 Yana tafe a kan titi kusa da kusurwar da take a zaune, yana wucewa kusa da gidanta,

9 da magariba cikin duhu.

10 Sai ta tarye shi, ta ci ado kamar karuwa, tana shirya yadda za ta yaudare shi.

11 (Ba ta jin tsoro, ba ta kuma jin kunya, ko yaushe tana ta gantali a tituna.

12 Takan tsaya tana jira a kowace kusurwa, wani lokaci a tituna, wani lokaci kuma a kasuwa.)

13 Ta rungumi saurayin, ta sumbace shi, ta dubi tsabar idonsa ta ce,

14 “Na miƙa hadayu yau, ina da nama na hadayu.

15 Shi ya sa na fito ina nemanka, ina so in gan ka, ga shi kuwa, na gan ka!

16 Na lulluɓe gadona da zannuwan lilin masu launi iri iri daga Masar.

17 Na yayyafa musu turaren mur da na aloyes da na kirfa.

18 Ka zo mu sha daɗin ƙauna, mu more dukan dare, mu yi farin ciki rungume da juna.

19 Mijina ba ya gida, ya yi tafiya mai nisa.

20 Ya tafi da kuɗi masu yawa, ba zai komo ba sai bayan mako biyu.”

21 Ta jarabce shi da kwarkwasarta, sai ya ba da kai ga daɗin bakinta.

22 Nan da nan ya bi ta kamar sā zuwa mayanka, kamar barewa tana tsalle zuwa cikin tarko,

23 inda kibiya za ta soke zuciyarta. Yana kama da tsuntsun da yake zuwa cikin tarko, bai kuwa sani ransa yana cikin hatsari ba.

24 Yanzu fa ‘ya’yana, ku kasa kunne gare ni, ku mai da hankali ga abin da nake faɗa.

25 Kada ku yarda irin wannan mace ta rinjayi zuciyarku, kada ku yi ta yawon nemanta.

26 Ita ce sanadin hallakar mutane da yawa, ta sa mutane da yawa mutuwa, har ba su ƙidayuwa.

27 Tafiya gidanta kuna kan hanya zuwa mutuwa ke nan, gajeruwar hanya ce zuwa lahira.

Categories
K. MAG

K. MAG 8

Yabon Hikima

1 Ku kasa kunne! Hikima tana kira.

Tana so a ji ta.

2 Tana tsaye bisa kan tuddai a bakin hanya

Da a mararraban hanyoyi.

3 A ƙofofin shiga birni, tana kira,

4 “Ina roƙonku, ya ku, ‘yan adam,

Ina kiran kowane mutum da yake a duniya.

5 Ba ku balaga ba? To, ku balaga.

Ku wawaye ne? Ku koyi hankali.

6 Ku kasa kunne ga jawabina mafi kyau,

Dukan abin da na faɗa muku daidai ne.

7 Abin da na faɗa gaskiya ne,

Ƙarairayi abin ƙi ne a gare ni.

8 Kowane abu da na faɗa gaskiya ne,

Ba wani abu da yake na laifi ko na ruɗawa.

9 Ga mutum mai basira, dukan abu ne a sarari,

Ga wanda aka sanar da shi sosai, abu ne a sawwaƙe.

10 Ka zaɓi koyarwata fiye da azurfa,

Ka zaɓi ilimi fiye da zinariya tsantsa.

11 “Ni ce hikima, na fi lu’ulu’ai,

Cikin dukan abin da kake so, ba kamata.

12 Ni ce hikima, ina da basira,

Ina da ilimi da faɗar daidai.

13 Ƙin mugunta shi ne tsoron Ubangiji,

Na ƙi girmankai, da fāriya, da mugayen hanyoyi,

Da maganganu na ƙarya.

14 Nakan shirya abin da zan yi, in kuwa yi shi.

Ina da fahimi, ina da ƙarfi.

15 Nakan taimaki sarakuna su yi mulki,

Mahukunta kuma su tsara dokoki masu kyau.

16 Kowane mai mulki a duniya, da taimakona yake mulki,

Ƙusoshin hukumomi da dattawan gari duka ɗaya.

17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata,

Dukan wanda yake nemana kuma zai same ni.

18 Ina da dukiya da daraja da zan bayar,

Da wadata da nasara kuma.

19 Abin da za ka samu daga gare ni

Ya fi zinariya kyau, da azurfa tsantsa.

20 A kan hanyar adalci nake tafiya,

Rankai a kan hanyoyin gaskiya.

21 Ina ba da dukiya ga waɗanda suke ƙaunata,

Ina kuma cika gidajensu da wadata.

22 “Ni ce halittar farko da Ubangiji

Ya fara halittawa daga cikin ayyukansa tuntuni.

23 Da farkon farawa ni aka fara halittawa

Kafin a yi duniya.

24 Ni aka fara yi kafin tekuna,

A sa’ad da ba maɓuɓɓugan ruwa.

25 Ni aka fara yi kafin a yi duwatsu,

Kafin a kafa tuddai a wurarensu,

26 Kafin Allah ya halicci duniya da filayenta,

Ko ɗan ɓarɓashin ƙasa.

27 A can nake sa’ad da ya shata sararin sama,

Da sa’ad da ya shimfiɗa al’arshi a hayin tekuna,

28 Da sa’ad da ya sa gizagizai a sararin sama,

Ya buɗe maɓuɓɓugan teku,

29 Ya kuma umarci ruwan teku, kada ya zarce wurin da ya sa.

Ina can sa’ad da ya kafa harsashin ginin duniya.

30 Ina kusa da shi kamar mai tsara fasalin gini,

Ni ce abar murnarsa kowace rana,

A ko yaushe ina farin ciki a gabansa.

31 Ina farin ciki da duniya,

Ina murna da ‘yan adam.

32 “Yanzu ku matasa, ku kasa kunne gare ni,

Ku yi abin da na ce, za ku yi farin ciki.

33 Ku saurari abin da aka koya muku,

Ku zama masu hikima, kada ku yi sakaci da ita.

34 Mutumin da ya kasa kunne gare ni, zai yi farin ciki haka nan,

Wato yakan tsaya a ƙofata ko yaushe,

Yana kuma jira a ƙofar shiga gidana.

35 Mutumin da ya same ni ya sami rai,

Ubangiji zai ji daɗinsa.

36 Mutumin da bai same ni ba ya cuci kansa,

Duk wanda yake ƙina mutuwa yake ƙauna.”

Categories
K. MAG

K. MAG 9

Hikima da Dakikanci

1 Hikima ta gina gidanta, ta yi masa ginshiƙai bakwai.

2 Ta sa an yanka dabba don biki, ta gauraya ruwan inabi da kayan yaji, ta shirya tebur.

3 Ta aiki barorinta ‘yan mata su je su hau wuri mafi tsayi a birni su yi kira.

4 “Ku shigo, ku jahilai!” Ga dolo kuwa ta ce,

5 “Zo ka ci abincina ka sha ruwan inabin da na gauraya.

6 Ka rabu da ƙungiyar jahilai, ka rayu, ka bi hanyar ilimi.”

7 Idan ka kwaɓi mai fāriya, za ka gamu da cin mutunci, idan ka tsauta wa mugu, kai ne za ka cutu.

8 Faufau kada ka kuskura ka kwaɓi mai fāriya, zai ƙi ka saboda wannan, amma idan ka kwaɓi mai hikima zai girmama ka.

9 Dukan abin da ka faɗa wa mutum mai hikima, zai ƙara masa hikima. Dukan abin da ka faɗa wa adali zai ƙara masa ilimi.

10 Domin ka zama mai hikima dole ka fara da tsoron Ubangiji. Idan ka san Mai Tsarki, ka sami ganewa.

11 Hikima za ta ƙara shekarunka.

12 Kai ne da riba in ka sami hikima. Kai za ka sha hasara in ka ƙi ta.

13 Wawanci kamar mace ce mai kwakwazo, jahila, marar kunya.

14 Takan zauna a ƙofar gidanta, ko a wurin da ya fi duka bisa a cikin gari.

15 Takan yi ta kiran masu wucewa waɗanda hankalinsu yake a kan ayyukansu, ta ce,

16 “Ku shigo, ku jahilai!” Takan ce wa dolo,

17 “Ruwan da aka sata ya fi daɗi, haka nan kuma abincin da ake satar ya fi daɗi.”

18 Waɗanda suka fāɗa a hannunta ba su sani mutuwa za su yi ba, waɗanda suka riga sun shiga kuwa suna can sun nutse cikin lahira.

Categories
K. MAG

K. MAG 10

Adali da Mugu Dabam Suke

1 Karin maganar Sulemanu ke nan. Ɗa mai hikima abin fāriya ne ga mahaifinsa, amma wawa yakan jawo wa mahaifiyarsa baƙin ciki.

2 Abin da ka samu ta hanyar zamba ba zai yi albarka ba, amma gaskiya za ta cece ka.

3 Ubangiji ba zai bar mutumin kirki da yunwa ba, amma zai hana mugu ya kai ga biyan bukatarsa.

4 Ragwanci zai sa talauci, amma yin aiki sosai zai arzuta ka.

5 Mutum mai hankali yakan tattara amfanin gona da kaka, amma abin kunya ne a yi barci a lokacin girbi.

6 Mutumin kirki yakan karɓi albarka, maganganun mugun kuwa sukan ɓoye mugun halinsa.

7 Tunawa da mutumin kirki albarka ce, amma nan da nan za a manta da mugaye.

8 Mutane masu hankali sukan bi shawarar kirki, masu maganar wauta kuwa za su lalace.

9 Amintaccen mutum zai zauna lafiya ba abin da zai same shi, amma marasa aminci za a kama su.

10 Mutumin da ya ƙi faɗar gaskiya yana haddasa wahala, amma wanda ya bayyana gaskiya zai kawo salama.

11 Kalmomin mutumin kirki maɓuɓɓugan rai ne, amma kalmar mugun takan ɓoye makircinsa.

12 Ƙiyayya takan haddasa wahala, amma ƙauna takan ƙyale dukan laifofi.

13 Mutane masu fasaha sukan yi magana mai ma’ana, amma wawaye suna bukatar horo.

14 Mutane masu hikima sukan nemi ilimi iyakar iyawarsu, amma sa’ad da wawa ya yi magana, wahala tana kusa.

15 Wadata takan kiyaye attajiri, amma tsiya takan hallaka matalauci.

16 Sakayyar da za a yi wa mutumin kirki ta rai ce, amma zunubi yakan sa a ƙara yin wani zunubi.

17 Mutumin da yake kasa kunne sa’ad da ake kwaɓarsa zai rayu, amma duk wanda bai yarda da kuskurensa ba yana cikin hatsari.

18 Mutumin da yake faɗar ƙarairayi maƙiyi ne, dukan wanda yake baza jitajita wawa ne.

19 Bisa ga yawan surutunka, mai yiwuwa ne ƙwarai ka yi zunubi, amma idan kai mai la’akari ne, sai ka yi shiru.

20 Kalmomin mutumin kirki suna kama da azurfa tsantsa, amma shawarwarin mugu ba su da wani amfani.

21 Kalmomin mutumin kirki za su amfani mutane da yawa, amma kana iya hallaka kanka da wauta.

22 Albarkar Ubangiji takan arzuta mutum, amma yawan aiki ba shi yake kawo arziki ba.

23 Wawa ne yake jin daɗin aikata mugunta, amma mai fasaha yana jin daɗin hikima.

24 Abin da mugun yake tsoro, shi yakan auko masa, amma adali yakan sami biyan bukatarsa.

25 Hadiri yakan taso ya wargaza mugaye, amma amintattu lafiya lau suke a ko yaushe.

26 Sam, kada ka sa malalaci ya yi maka wani abu, zai sa ka ka yi fushi, idanunka su cika da hawaye mai zafi.

27 Ka yi tsoron Ubangiji za ka rayu, ka yi tsawon rai, amma mugaye sukan mutu tun kwanansu bai ƙare ba.

28 Abin da mutanen kirki suke sa zuciya yakan kai su ga murna, amma mugaye ba su da wani abu da za su sa zuciya a kai.

29 Ubangiji yana kiyaye marasa laifi, amma yakan hallaka masu mugunta.

30 Kullayaumi adalai sukan yi zamansu lafiya, amma mugaye ba za su zauna a ƙasar ba.

31 Maganar adalai ta hikima ce, amma harshen da yake hurta mugunta, za a dakatar da shi.

32 Adalai sun san irin maganar da ta cancanta su faɗa, amma mugaye, kullum sukan faɗi maganar da za ta cutar.