Categories
K. MAG

K. MAG 21

1 Ubangiji ne yake mallakar tunanin sarki a sawwaƙe kamar yadda yake yi da ruwan rafi.

2 Ko da a ce dukan abin da kake yi daidai ne, ka tuna fa Ubangiji ya san manufarka.

3 Ubangiji ya fi so ka yi abin da yake daidai, mai kyau kuma, fiye da ka miƙa masa hadayu.

4 Girmankai da fāriya suke bi da mugaye, wannan kuwa zunubi ne.

5 Yin shiri a tsanaki zai kai ka ga biyan bukatarka, idan kuwa ka cika gaggawa ba za ka sami abin da zai ishe ka ba.

6 Dukiyar da aka tara ta hanyar rashin gaskiya takan ƙare nan da nan, takan kuma kai ga mutuwa.

7 Mugaye, tasu ta ƙare saboda muguntarsu, gama sun ƙi yin abin da yake daidai.

8 Mutane masu laifi sukan bi ta karkatacciyar hanya, marasa laifi kuwa suna aikata abin da yake daidai.

9 Gara zama a saƙo da zama a gida ɗaya tare da mace mai mita.

10 Mugaye sun zaƙu su aikata mugunta, ba su yi wa kowa jinƙai.

11 Sa’ad da aka hukunta mai girmankai, ko marar tunani yakan koyi wani abu, mutum mai hikima yakan koyi abin da ake koya masa.

12 Adali ya san tunanin mugaye, yakan kuwa zama sanadin lalacewarsu.

13 Idan ka ƙi jin kukan matalauci, naka kukan da kake yi na neman taimako, ba za a ji ba.

14 Kyauta a asirce takan kwantar da zuciyar wanda yake fushi da kai.

15 Sa’ad da aka yi adalci mutanen kirki sukan yi murna, amma mugaye sukan yi baƙin ciki.

16 Mutuwa tana jiran wanda ya ƙi bin hanyar hankali.

17 Sa kai cikin nishaɗi, wato shan ruwan inabi, da cin abinci mai tsada, ba zai bar ka ka tara dukiya ba.

18 Wahalar da mugaye suke so su jawo wa mutanen kirki, za ta koma kansu.

19 Gara ka zauna a hamada, da ka zauna tare da mace mai mita, mai yawan kai ƙara.

20 Mutane masu hikima suna zaune da wadata da nishaɗi, amma wawaye da zarar sun sami kuɗi sukan kashe su nan da nan.

21 Ka yi alheri ka yi aminci, za ka yi tsawon rai waɗansu kuma za su girmama ka, su yi maka abin da yake daidai.

22 Sarkin yaƙi mai wayo yakan ci birnin da jarumawa suke tsaro, ya rushe garun da suke taƙama da shi.

23 Idan ba ka so ka shiga wahala, ka lura da abin da kake faɗa.

24 Ba kalmar da ta fi “fāɗin rai” dacewa ga mutum mai girmankai, mai fāriya marar tunani.

25 Malalacin mutumin da ya ƙi yin aiki, kansa yake kashewa.

26 Duk abin da yake tunani dukan yini, shi ne a kan abin da yake so ya samu. Amma adali ko ta ƙaƙa yakan bayar da hannu sake.

27 Ubangiji yana ƙin hadayar da mugaye suka miƙa masa, tun ba wadda suka miƙa ta da mugun nufi ba.

28 Ba a gaskata shaidar maƙaryaci, amma mutumin da yakan yi tunani a kan al’amura, akan karɓi tasa.

29 Adali ya tabbatar da kansa, haka ma mugun mutum yakan yi da’awa, cewa shi ma ya tabbatar da kansa.

30 Hikima, da haziƙanci, da basira, ba kome suke ba gāba da Ubangiji.

31 Kana iya shirya dawakai don zuwa yaƙi, amma nasara ta Ubangiji ce.

Categories
K. MAG

K. MAG 22

1 Idan ya zama dole ne ka zaɓa tsakanin kyakkyawan suna ko dukiya, to, ka zaɓi kyakkyawan suna, tagomashi kuma ya fi azurfa da zinariya.

2 Ba bambanci tsakanin mawadaci da matalauci, gama Ubangiji ne ya halicce su duka.

3 Mutum mai hankali, in ya ga wahala tana zuwa yakan kauce mata, amma shashasha yakan kutsa kai ciki, daga baya ya yi da na sani.

4 Kana da tsoron Ubangiji, ka yi tawali’u, za ka arzuta, ka ɗaukaka, ka sami tsawon rai.

5 Idan kana ƙaunar ranka ka nisanci tarkunan da aka kafa a hanya don su kama mugaye.

6 Ka koya wa yaro yadda zai yi zamansa, zai kuwa tuna da ita dukan kwanakinsa.

7 Matalauta su ne bayin attajirai, bawa ne kai ga wanda ka ci bashi a gare shi.

8 In ka shuka rashin gaskiya masifa ce za ta tsiro, wato hukunci mai tsanani wanda zai hallakar da kai.

9 Ka zama mai hannu sake, ka riƙa ba matalauta abincinka, za a sa maka albarka saboda haka.

10 Ka rabu da mutum mai fāriya, mai gardama, mafaɗaci, hatsaniya za ta ƙare.

11 In ka yi ladabi za ka zama aminin sarki, gama yana ƙaunar amintaccen mutum.

12 Ubangiji yana lura ya ga an riƙe gaskiya sosai ta wurin ƙin yarda da maganganun ƙarya.

13 Malalaci yakan yi zamansa a gida, yakan ce, “Zaki zai kama ni in na fita waje.”

14 Zina tarko ce, takan kama waɗannan waɗanda Ubangiji yake fushi da su.

15 Halin yara ne su yi wauta da waɗansu abubuwa na rashin kula, amma tsumagiya za ta koya musu abin da ya fi kyau.

16 Idan attajirai kake yi wa kyauta, kana kuma zaluntar matalauta don ka arzuta, kai kanka za ka talauce.

Umarnai da Dokoki

17 Ka kasa kunne zan koya maka abin da masu hikima suka faɗa, yi nazari a kan koyarwarsu.

18 Za ka yi murna in ka tuna da su, ka iya faɗarsu.

19 Ina so ka dogara ga Ubangiji, don haka zan faɗa maka su yanzu.

20 Na rubuta maka karin magana, suna ƙunshe da ilimi da kyakkyawar shawara.

21 Zan koya maka ainihin gaskiya, domin sa’ad da aka aike ka ka nemo ta, za ka iya kawo amsa daidai.

22 Kada ka ƙwari matalauci don ka fi shi, kada ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a.

23 Ubangiji zai yi magana dominsu a kan shari’ar da suke yi, ya nemi ran duk wanda yake neman rayukansu.

24 Kada ka yi abuta da mutane masu zafin fushi, ko masu zafin rai.

25 Mai yiwuwa ne ka koyi irin ɗabi’unsu, har ka kasa sākewa.

26 Kada ka yi alkawarin ɗaukar wa wani lamuni,

27 gama idan ka kāsa biya har gadonka ma za su ɗauke.

28 Kada ka kawar da shidar kan iyaka wadda kakanninka suka kafa.

29 Ka nuna mini mutumin da yake aiki mai kyau, ni kuwa in nuna maka mutumin da ya fi duka, wanda ya cancanci ya zauna tare da sarakuna.

Categories
K. MAG

K. MAG 23

1 Sa’ad da ka zauna cin abinci tare da babban mutum, ka tuna da yadda yake.

2 Idan kai mai son ci da yawa ne sai ka kanne.

3 Kada ka yi haɗamar kyakkyawan abincin da yake gabanku, zai yiwu wayo yake so ya yi maka.

4 Ka zama mai isasshiyar hikima, kada ka gajiyar da kanka garin ƙoƙarin neman dukiya.

5 Kuɗinka sun iya ƙarewa kamar ƙyiftawar ido, kamar suna da fikafikai su tashi kamar gaggafa.

6 Kada ka ci abincin marowaci, ko ka yi haɗamar kyakkyawan abincin da ya sa a gabanka.

7 Zai ce, “Bari a ƙara maka,” amma ba haka yake nufi ba. Kamar gashi yake a cikin maƙogwaronka.

8 Za ka harar da abin da ka ci, dukan daɗin bakinka zai tafi a banza.

9 Kada ka yi wa wawa magana irin ta haziƙai, gama ba zai yaba da maganarka ba.

10 Kada ka kuskura ka kawar da shaidar iyaka, ko ka ƙwace gonar marayu.

11 Ubangiji Mai Iko shi ne kāriyarsu, shi zai yi magana dominsu.

12 Ka mai da hankali ga malaminka, ka koyi dukan abin da kake iyawa.

13 Kada ka bar yaro ba horo, gama ko ka duke shi ba za a kashe shi ba.

14 Lalle ne za ka ceci ransa.

15 Ɗana, idan ka zama mai hikima zan yi murna ƙwarai.

16 Zan yi murna idan na ji kana faɗar magana da hikima.

17 Kada ka yi ƙyashin masu aikata zunubi tsoron Ubangiji kaɗai za ka sa a gaba.

18 Idan haka ta samu za ka yi farin ciki nan gaba.

19 Ka saurara, ya ɗana, ka zama mai hikima. Ka yi tunani mai zurfi a kan hanyarka.

20 Kada ka zauna da mashayan ruwan inabi, ko masu haɗama.

21 Gama bugaggu da ruwan inabi da masu zarin ci za su zama matalauta. Idan iyakar abin da kake yi daga ci sai barci ne, nan da nan za ka ga kana saye da tsummoki.

22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, gama da ba dominsa ba, da ba ka, sa’ad da mahaifiyarka ta tsufa ka nuna mata godiyarka.

23 Gaskiya, da hikima, da ilimi, da hankali, sun cancanta a saye su, kome tamaninsu.

24 Mahaifin adali yana da dalilin yin murna. Zai yi fāriya a kan ɗa mai hikima.

25 Ka sa mahaifinka da mahaifiyarka su yi fāriya da kai, ka sa mahaifiyarka farin ciki.

26 Ɗana ka mai da hankali sosai, irin zamana ya zamar maka kyakkyawan misali.

27 Karuwa, da mata mazinata, tarkon mutuwa ne su.

28 Sukan laɓe su jira ka kamar mafasa, suna sa mutane da yawa su zama marasa aminci.

29 Wa ake yi wa kaito? Wa yake da baƙin ciki? Wane ne mafaɗaci? Wa yake yin gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan ido?

30 Sai riƙaƙƙen mashayi wanda yake gaurayar ruwan inabi.

31 Kada ka bar ruwan inabi ya jarabce ka, ko da yake ja wur yake, har kana iya ganin kanka a cikin ƙoƙon, yana kuwa da kyan gani sa’ad da kake motsa shi.

32 Kashegari za ka ji kamar maciji mai dafi ne ya sare ka.

33 Idanunka za su riƙa gane-gane, ba za ka iya tunani ko ka faɗi magana sosai ba.

34 Za ka ji kamar kana can cikin teku, jirin teku na ɗibarka kana lilo a kan rufin jirgin ruwa da yake tangaɗi.

35 Za ka ce, “Lalle an doke ni, sosai an daddoke ni amma ban san lokacin ba, me ya sa ban farka ba? Ina bukatar in ƙara sha.”

Categories
K. MAG

K. MAG 24

1 Kada ka ji ƙyashin mugaye, kada ka yi ƙoƙarin yin abuta da su.

2 Duk tunaninsu na yin mugunta ne, a duk lokacin da suka buɗe bakinsu sai sun cuci wani.

3 An gina gidaje a kan harsashin hikima da fahimi.

4 Ta wurin ilimi a kan ƙawata ɗakuna da kyawawan kayayyaki masu tamani.

5 Mai hikima ƙaƙƙarfa ne, i, mai ilimi yana daɗa ƙarfi.

6 Banda wannan ma, dole ne ka shisshirya a natse kafin ka kama yaƙi. Bisa ga shawarwarin da za ka samu ne za ka yi nasara.

7 Kalmomi masu hikima sun yi wa wawa zurfin ganewa ƙwarai, ba shi da ta cewa sa’ad da ake magana a kan muhimman abubuwa.

8 Idan a ko yaushe shirye-shiryen mugunta kake, za ka yi suna a kan kuta tashin hankali.

9 Kowace irin dabarar da wawa yake tunani a kanta zunubi ne. Jama’a suna ƙin mutum mai rainako.

10 Idan ba ka da ƙarfi a lokacin hargitsi, hakika ka tabbata marar ƙarfi.

11 Kada ka ji nauyin ceton wanda ake janye da shi zuwa inda za a kashe shi.

12 Mai yiwuwa ne ka ce kai ba ruwanka, amma Allah ya sani, yana kuwa auna manufofinka. Yana lura da kai, ya kuwa sani. Yakan sāka wa mutane a kan abin da suke aikatawa.

13 Ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau. Kamar yadda kakin zuma yake da zaƙi a harshenka,

14 haka ilimi da hikima suke da amfani ga ranka. Ka same su, a gaba za ka yi farin ciki.

15 Kada ka shirya dabarun yi wa amintacce ƙwace, ko ka ƙwace masa gidansa, wannan mugunta ce.

16 Ko sau nawa amintaccen mutum ya faɗi, ba abin damuwa ba ne, gama a ko yaushe zai sāke tashi, amma masifa takan hallaka mugaye.

17 Kada ka yi murna sa’ad da bala’i ya aukar wa maƙiyinka.

18 Ubangiji zai sani in kana murna, ba kuwa zai so haka ba, mai yiwuwa ne ba zai hukunta shi ba.

19 Kada ka damu saboda mugaye, kada ka yi ƙyashin masu aikata abin da ba daidai ba.

20 Gama mugun mutum ba shi da sa zuciya, ba abin da zai sa zuciya a kansa nan gaba.

21 Ɗana, ka yi tsoron Ubangiji, ka kuma ji tsoron sarki, kada ka yi harkar kome da mutanen da suka tayar musu.

22 Irin waɗannan mutane sukan hallaka farat ɗaya. Ka taɓa yin tunani a kan bala’in da Allah ko sarki sukan aukar?

Waɗansu sauran Karin Magana na Hikima

23 Masu hikima kuma sun faɗi waɗannan abu.

Kuskure ne alƙali ya yi son zuciya.

24 Idan ya kuɓutar da mugu, kowane mutum da yake a duniya zai la’anta shi ya ƙi shi.

25 Alƙalan da suke hukunta wa mai laifi kuwa, za su arzuta, su ji daɗin kyakkyawan suna.

26 Amsar gaskiya ita ce alamar abuta ta ainihi.

27 Kada ka gina gidanka ka kafa shi, sai ka gyara gonakinka, ka tabbata za ka sami abin zaman gari.

28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isasshen dalili ba, ko ka faɗi ƙarya a kansa.

29 Kada ka ce, “Zan yi masa daidai da yadda ya yi mini, zan rama masa!”

30 Na ratsa ta gonakin inabin wani malalaci, dakiki,

31 suna cike da ƙayayuwa, ciyayi sun sha kansu, katangar dutse da take kewaye da su ta faɗi.

32 Da na dubi wannan, na yi tunani a kansa, ya zamar mini ishara.

33 “Yi ta ruruminka, ci gaba da barcinka, rungume hannuwanka don ka shaƙata.”

34 Amma sa’ad da kake ta sharar barci fatara za ta auka maka kamar ƙungiyar ‘yan fashi.

Categories
K. MAG

K. MAG 25

Waɗansu sauran Karin Magana na Sulemanu

1 Ga waɗansu sauran karin maganar Sulemanu waɗanda magatakardan Hezekiya Sarkin Yahuza suka juya.

2 Muna girmama Allah saboda abin da ya rufe, muna girmama sarakuna saboda abin da suka ba da bayaninsa.

3 Ba ku taɓa sanin abin da sarki yake tunani ba, gama tunaninsa sun fi ƙarfinmu. Kamar nisan sararin sama suke ko zurfafan teku.

4 Ka tace azurfa, gwani kuwa zai yi wani kyakkyawan abu da ita.

5 A kawar da mugayen mashawarta daga gaban sarki, hukumarsa za ta shahara a kan adalci.

6 Sa’ad da kake tsaye a gaban sarki, kada ka nuna kai wani abu ne, kana kai kanka inda Allah bai kai ka ba.

7 Gara a roƙe ka ka hau zuwa babban matsayi, da a faɗa maka ka ba da wurin da kake ga wanda ya fi ka maƙami.

8 Kada ka yi garajen kai ƙara a majalisa. Idan wani mashaidi ya nuna kai kake da kuskure, me za ka yi?

9 Idan kai da maƙwabcinka kun saɓa, ku daidaita a tsakaninku, kada a tona asiri.

10 Mai yiwuwa ne wani ya ji ya zarge ku, ba za ku taɓa rabuwa da wannan kunya ba.

11 Manufar da aka bayyana sosai kamar zubin zinariya take wanda aka yi a kan azurfa.

12 Faɗakarwar da mutumin da ya gogu da al’amuran duniya ya yi ga wanda yake da niyya ya kasa kunne, tamaninta ya fi na zoben zinariya, ko kayan ado da aka yi da zinariya tsantsa.

13 Amintaccen manzo yakan wartsakar da wanda ya aike shi, kamar ruwan sanyi yake a lokacin zafi.

14 Mutanen da suke yin alkawari, ba su cikawa, kamar holoƙo suke, hadirin kaka.

15 Rinjayen da aka yi cikin haƙuri yakan rushe ƙaƙƙarfar tsayayya, har ma yakan i wa masu ƙarfin gaske.

16 Kada ka kuskura ka sha zuma gaba da kima, in ya yi maka yawa za ka yi hararwa.

17 Kada ka cika ziyartar maƙwabcinka, ko zai gaji da kai har ya ƙi ka.

18 Mutumin da yakan faɗi ƙarairayi a kan maƙwabcinsa, shi kamar kakkaifan takobi ne, ko kulki, ko kibiya mai tsini.

19 Dogara ga marar aminci a lokacin hargitsi, kamar ƙoƙarin yin tauna da ruɓaɓɓun haƙora ne, ko yin tafiya da mai gurguwar ƙafa,

20 ko kuma ka yi ƙoƙarin jin ɗumi ta wurin tuɓe tufafinka a ranar da ake sanyi.

Raira waƙa ga mai baƙin ciki kamar marmasa gishiri a kan rauni ne.

21 Idan maƙiyinka yana jin yunwa ka cishe shi, idan yana jin ƙishi ka ba shi abin sha.

22 Za ka sa ya sha kunya, Ubangiji kuma zai sāka maka.

23 Iskar arewa takan kawo ruwan sama, haka kuma jita-jita takan kawo fushi.

24 Gara zama a saƙo da zama a gida ɗaya tare da mata mai mita.

25 Jin labari mai daɗi wanda ba ka zato, yana kamar shan ruwan sanyi ne a sa’ad da ka sha rana kana jin ƙishi.

26 Mutumin kirki wanda yakan yarda da mugun yana tunasshe ka da ƙazantattun maɓuɓɓuga ko rijiya mai dafi.

27 Kamar yadda shan zuma da yawa ba shi da kyau a gare ka, haka kuma ƙoƙarin neman yabo mai yawa yake.

28 Idan ba ka iya danne fushinka ba, ka zama mai kasala kamar birnin da ba shi da garuka, yana buɗe don a faɗa masa.

Categories
K. MAG

K. MAG 26

1 Yabo bai dace da wawa ba, kamar yadda dusar ƙanƙara ba ta dace da lokacin zafi ba, ko ruwan sama a lokacin girbi.

2 La’ana ba za ta kama ka ba, sai dai in ka cancance ta. Tana kamar tsuntsayen da suke firiya da dare ba za su sauka ba.

3 Sai ka fyaɗi doki, ka sa wa jaki linzami, wawa kuma sai ka doke shi.

4 Idan ka amsa tambayar wauta, ka zama wawa daidai da mutumin da ya yi tambayar.

5 Ka amsa wauta ga tambayar wauta, wanda ya yi tambayar zai gane wawancinsa.

6 Mutumin da ya sa wawa ya isar masa da saƙo ya datse ƙafafunsa, yana nemar wa kansa wahala.

7 Wawa yakan yi amfani da karin magana kamar yadda tauyayyen mutum yake amfani da ƙafafunsa.

8 Wanda ya yabi wawa yana kama da wanda ya ɗaura dutse a majajjawa.

9 Karin magana a bakin wawa kamar sukar ƙaya ce a hannun mai maye.

10 Wanda ya ɗauki wawa aiki yana cutar duk wanda aikin ya shafa.

11 Wawan da yake maimaita aikin wautarsa yana kama da kare mai yin amai ya koma ya tanɗe.

12 Gwamma riƙaƙƙen wawa da mutum mai ganin kansa mai hikima ne.

13 Don me malalaci yakan kasa fita daga gida? Zaki yake tsoro?

14 Malalaci yana ta jujjuyawa a gadonsa kamar yadda ƙyauren ƙofa take juyawa.

15 Malalaci yana sa hannu cikin ƙwaryar abinci, amma ya kāsa kaiwa bakinsa.

16 Malalaci yana ganin kansa mai hikima ne fiye da mutum bakwai waɗanda suke da dalilai a kan ra’ayinsu.

17 Mutumin da ya tsoma baki cikin jayayyar da ba ta shafe shi ba sa’ad da yake wucewa, yana kama da mutum wanda yake kama kare a kunne.

18-19 Mutum wanda yakan ruɗi maƙwabcinsa sa’an nan ya ce, wasa yake yi kawai, yana kama da mahaukaci wanda yake wasa da wuta, da kibau, da mutuwa.

20 Idan ba itace wuta takan mutu, haka kuma idan ba mai gulma ba za a yi jayayya ba.

21 Kamar yadda gawayi yake ga garwashin wuta, itace kuma ga wuta, haka mai gardama yake ga jayayya.

22 Kamar yadda lomar abinci mai daɗi takan gangara can cikin ciki haka maganar mai gulma take.

23 Bakin da ba ya faɗar gaskiya, da zuciya mai ƙiyayya suna kama da kaskon da aka dalaye da azurfar da ba a tace ba.

24 Mai yin ƙiyayya yakan ɓoye ta da maganar bakinsa, yana kuma ƙunshe da munafunci.

25 Sa’ad da yake magana mai kyau kada ka gaskata shi, domin zuciyarsa tana cike da mugunta.

26 Ko da yake kila zai ɓoye ƙiyayyarsa, duk da haka muguntarsa za ta bayyana ga mutane.

27 Wanda ya haƙa ramin mugunta shi zai faɗa ciki, wanda kuma ya mirgino dutse, zai fāɗo a kansa.

28 Maƙaryaci yana ƙin wanda ya yi wa ƙarya, mai daɗin baki kuma yakan aikata ɓarna.

Categories
K. MAG

K. MAG 27

1 Kada ka yi fāriya a kan abin da za ka yi gobe domin ba ka san abin da zai faru daga yanzu zuwa gobe ba.

2 Bari waɗansu su yabe ka ko da baƙi ne, faufau kada ka yabi kanka.

3 Dutse da yashi suna da nauyi ƙwarai, amma nauyin wahalar da wawa zai haddasa ya fi nasu duka.

4 Fushi mugun abu ne mai hallakarwa, amma duk da haka bai kai ga kishi ba.

5 Gara ka tsauta wa mutum a fili da ka bar shi ya zaci ba ka kula da shi ba sam.

6 Aboki aboki ne ko da ya cuce ka, amma maƙiyi ko ya rungume ka kada ka sake!

7 Wanda ya ƙoshi ba zai ko kula da zuma ba, amma wanda yake jin yunwa abinci mai ɗaci zaƙinsa yake ji.

8 Mutumin da ya bar gida yana kama da tsuntsun da ya bar sheƙarsa.

9 Turare da man ƙanshi sukan sa ka ji daɗi, haka abuta ta ainihi takan ƙara maka ƙarfi.

10 Kada ka manta da abokanka, ko abokan mahaifinka. Idan kana shan wahala kada ka nemi taimako wurin ɗan’uwanka. Maƙwabci na kusa yana iya taimakonka fiye da ɗan’uwan da yake nesa.

11 Ɗana, ka zama mai hikima, ni kuwa zan yi farin ciki, zan iya amsa kowace irin sūkar da wani zai yi mini.

12 Mutum mai hankali yakan hango hatsari ya kauce masa, amma mutumin da ba shi da kula, yakan kutsa kai ciki, daga baya ya yi da na sani.

13 Ka karɓe tufar wanda ya zamar wa baƙo lamuni, da kuma wanda ya zama lamunin karuwa.

14 In ka farkar da abokinka da babbar murya tun da sassafe, daidai ne da zaginsa.

15 Mace mai mita kamar ɗiɗɗigar ruwa take ba ƙaƙƙautawa.

16 Kaƙa za ka iya sa ta ta kame bakinta? Ka taɓa ƙoƙarin tsai da iska? Ko kuwa ka taɓa ƙoƙarin dintsi mai a tafin hannunka?

17 Daga wurin mutane mutane suke koyo, kamar yadda a kan wasa ƙarfe da ƙarfe.

18 Ka lura da itacen ɓaure, zai yi ‘ya’ya ka ci. Baran da ya lura da maigidansa za a girmama shi.

19 Yadda kake ganin fuskarka a ruwa, haka kake ganin kanka a zuciyarka.

20 Muradin mutum kamar lahira yake, a kullum ba ya ƙoshi.

21 Da wuta ake gwada azurfa da zinariya, amma yabon da ake yi wa mutum shi ne magwajinsa.

22 Ko da za ka doki wawa ka bar shi tsakanin rai da mutuwa, duk da haka yana nan da wautarsa kamar yadda yake.

23 Ka lura da garkunan tumakinka da na shanunka da kyau iyakar iyawarka,

24 domin dukiya ba ta tabbata har abada, al’ummai ma haka ne.

25 Ka yanki ingirici, lokacin da yake toho kana iya yankar ciyawa a gefen tuddai.

26 Kana iya yin tufafi da ulun tumakinka, kana iya sayen gona da kuɗin awakinka.

27 Madarar awakinka za ta zama abincinka kai da iyalinka, da kuma barorinka ‘yan mata.

Categories
K. MAG

K. MAG 28

Mugaye da Adalai

1 Mugun mutum yakan gudu, alhali kuwa ba mai korarsa, amma amintaccen mutum kamar zaki yake, ba shi da tsoro.

2 Al’umma za ta ƙarfafa ta jure idan shugabanninta masu basira ne, masu hankali. Amma idan ƙasar mai aikata zunubi ce za ta sami shugabanni da yawa.

3 Mai mulki wanda yake zaluntar talakawa, ya zama kamar ruwa mai lalatar da amfanin gona.

4 Wanda ba ya bin doka tare da mugaye yake, amma idan kana bin doka kai abokin gāban mugaye ne.

5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada sun san ta sosai.

6 Gara ka zama matalauci mai aminci da ka zama mawadaci, marar aminci.

7 Saurayi wanda ya kiyaye doka mai basira ne shi, amma wanda yake abuta da ‘yan iska zai zama mai jawo wa mahaifinsa kunya.

8 Idan kana tara dukiya ta wurin ba da bashi da ruwa kana kuma ƙwarar jama’a, dukiyarka za ta koma ga wanda yake yi wa talakawa alheri.

9 Idan ka ƙi biyayya ga doka, Allah zai ƙi jin addu’o’inka.

10 Idan ka yaudari mutumin kirki don ya faɗa cikin mugunta, kai kanka ne za ka fāɗa cikin tarkon da ka haƙa. Marar laifi kuwa zai sami babban sakamako.

11 Attajirai, a ko yaushe, zato suke su masu hikima ne, amma matalauci mai tunani ya fi sanin abin da yake daidai.

12 Sa’ad da mutanen kirki suke sarauta, kowa da kowa yakan yi biki, amma sa’ad da mugaye suka kama mulki mutane sukan riƙa ɓuya.

13 Ba za ka taɓa cin nasara a zamanka ba muddin kana ɓoye laifofinka. Ka hurta zunubanka ka tuba, sa’an nan Allah zai yi maka jinƙai.

14 Mutumin da yake tsoron Ubangiji ko yaushe, zai yi farin ciki, amma idan ya taurare zai lalace.

15 Talakawa ba su da wani taimako sa’ad da suke ƙarƙashin mulkin mugun. Abin tsoro ne shi kamar zaki mai ruri, ko beyar mai sanɗa.

16 Mai mulki wanda ba shi da basira yakan zama mai mugun tsanani. Amma wanda yake ƙin rashin aminci, ko ta ƙaƙa zai daɗe yana mulki.

17 Mutumin da yake da laifin kisankai, yana haƙa wa kansa kabari da gaggawa. Kada ka yi ƙoƙarin hana shi.

18 Ka yi aminci za ka zauna lafiya, idan kuwa ka yi rashin aminci za ka fāɗi.

19 Manomin da yake aiki sosai, zai sami wadataccen abinci, amma mutanen da suke zaman banza ko yaushe, za su zama matalauta.

20 Amintaccen mutum zai cika kwanakinsa lafiya, amma idan kana so ka sami dukiya dare ɗaya, za a hukunta ka.

21 Nuna sonkai mugun abu ne, waɗansu alƙalai sukan aikata mugunta saboda ‘yar ƙaramar rashawa.

22 Mutum mai haɗama yana gaggawar samun dukiya, bai kuwa sani ba, ashe, fatara ce za ta same shi.

23 Wanda ya tsauta wa mutum zai sami yabo daga baya, fiye da wanda ya yi masa daɗin baki.

24 Wanda yake yi wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa sata, yana kuwa tsammani ba laifi ba ne, daidai da ɓarawo yake.

25 Mutum mai haɗama yana haddasa tashin hankali, amma wanda ya dogara ga Ubangiji zai sami wadar zuci.

26 Wanda yake dogara ga son zuciyarsa, wawa ne, amma wanda yake tafiya cikin hikima zai kuɓuta.

27 Wanda yake bayarwa ga matalauta, ba zai talauce ba, amma wanda bai kula da su ba, mutane da yawa za su la’ance shi.

28 Mutane sukan ɓuya sa’ad da mugaye suka sami iko, amma sa’ad da iko ya fita daga hannunsu adalai sukan ƙaru.

Categories
K. MAG

K. MAG 29

1 Wanda ake ta tsauta wa a kai a kai, amma ya taurare, ba makawa tasa ta ƙare farat ɗaya.

2 Sa’ad da masu adalci suke mulki, jama’a sukan yi murna, amma sa’ad da mugaye suke mulki, jama’a sukan yi nishi.

3 Wanda yake ƙaunar hikima yana faranta zuciyar mahaifinsa.

Amma wanda yake abuta da karuwai zai lalatar da dukiyarsa.

4 Sarkin da yake aikata adalci ƙasarsa za ta yi ƙarƙo, amma wanda yake karɓar rashawa zai lalatar da ƙasar.

5 Mutum wanda yake yi wa maƙwabcinsa daɗin baƙi yana kafa wa kansa tarko.

6 Laifin mugun zai zama tarko a gare shi, amma adali zai raira waƙa, ya yi farin ciki.

7 Adali yana sane da hakkin matalauta, amma mugun bai san wannan ba.

8 Ashararai sukan sa wa birni wuta, amma masu hikima sukan kwantar da hasala.

9 Idan gardama ta shiga tsakanin mai hikima da wawa, sai wawa ya yi ta fushi, ko kuwa ya yi ta dariya, gardamar dai ba za ta ƙare ba.

10 Mutane masu kisankai suna ƙin amintaccen mutum, amma adalai za su kiyaye ransa.

11 Wawa yakan nuna fushinsa ko yaushe, amma mutum mai hikima yakan kanne fushinsa.

12 Idan mai mulki yana kasa kunne ga maganganun ƙarya, dukan ma’aikatansa za su zama maƙaryata.

13 Matalauci da azzalumi suna tarayya a abu ɗaya, wato dukansu Ubangiji ne yake ba su ganin gari.

14 Idan sarki yana yi wa talakawa shari’ar gaskiya, zai daɗe yana mulki.

15 Horo da tsautawa suna ba da hikima, amma yaron da aka sangarta zai jawo wa mahaifiyarsa kunya.

16 Sa’ad da mugaye suke mulki, laifofi suka ƙaru, amma adalai za su ga faɗuwar waɗannan mutane.

17 Ka hori ɗanka zai daɗaɗa maka rai, ya kuma faranta maka zuciya.

18 Inda ba a bin faɗar Allah, jama’a za su kangare, amma mai farin ciki ne wanda yake kiyaye dokar Allah.

19 Bara ba ya horuwa ta wurin magana kawai, gama ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba.

20 Ka ga mutum mai garajen yin magana? To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi.

21 Baran da aka shagwaɓa tun yana yaro, a ƙarshe zai ɗauki kansa tankar magājin gida.

22 Mutum mai saurin fushi yakan ta da faɗa, mai zafin rai kuma yakan aikata laifi da yawa.

23 Girmankan mutum zai jawo masa ƙasƙanci, amma za a girmama mai tawali’u.

24 Abokin ɓarawo mugun maƙiyin kansa ne, yana jinsa yana ta rantsuwa, amma ba zai ce kome ba.

25 Jin tsoron mutane tarko ne, amma wanda ya dogara ga Ubangiji za a ɗaukaka shi.

26 Mutane da yawa sukan nemi farin jini daga wurin mai mulki, amma Ubangiji ne yake yi wa mutum adalci.

27 Mutum marar gaskiya abin ƙyama ne ga adali, adali kuma abin ƙyama ne ga mugun.

Categories
K. MAG

K. MAG 30

Hikimar Agur

1 Waɗannan su ne maganar Agur ɗan Yake, da ya yi wa Etiyel da Yukal,

2 “Hakika wautata ta sa na zama kamar dabba ba mutum ba,

Ba ni kuwa da fahimi irin na mutum.

3 Ban koyi hikima ba,

Ban kuwa san kome game da Allah ba.

4 Wa ya taɓa hawa cikin Sama ya sauko?

Wa ya taɓa kama iska cikin tafin hannunsa?

Wa ya taɓa ƙunshe ruwa cikin rigarsa?

Wa kuma ya kafa iyakar duniya?

Ina sunansa, ina kuma sunan ɗansa?

Hakika ka sani!

5 “Kowace maganar Allah takan tabbata. Shi garkuwa ne ga waɗanda suke fakewa a wurinsa.

6 Kada ka yi ƙari a kan maganarsa, don kada ya tsauta maka, a kuma bayyana kai maƙaryaci ne.”

Waɗansu Karin Magana kuma

7 Abu biyu na roƙe ka, kada ka hana mini su kafin in mutu.

8 Ka kawar da ƙarya nesa da ni. Kada ka ba ni talauci ko dukiya, sai dai ka ba ni abinci daidai da bukatata,

9 don kada in wadata, har in yi musunka, in ce, “Wane ne Ubangiji?” Kada kuwa in yi talauci har in yi sata in saɓi sunan Allahna.

10 Kada ka kushe bara a wurin maigidansa domin kada ka yi laifin da zai sa a la’ance ka.

11 Akwai waɗansu mutane da sukan zagi iyayensu maza, ba sukan kuma nuna godiya ga iyayensu mata ba.

12 Akwai waɗansu mutanen da suke ganin kansu tsarkaka ne, alhali kuwa ƙazamai ne su.

13 Akwai waɗansu mutane da suke yi wa jama’a ƙallon raini suna ɗaurin gira.

14 Akwai waɗansu mutane waɗanda haƙoransu takuba ne, mataunansu kuma wuƙaƙe ne, don su cinye matalauta da masu fatara daga duniya.

15-16 Matsattsaku tana da ‘ya’ya mata biyu, ana kiransu, “Ba ni, Ba ni.”

Akwai abu uku da ba su ƙoshi, i, har huɗu ma da ba su cewa, “Ya isa,” wato

lahira,

macen da ba ta haihuwa,

ƙasa wadda ba ta ƙoshi da ruwa,

wuta wadda ba ta cewa, “Ya isa.”

17 Idan ɗa ya raina mahaifi, ya kuma yi wa mahaifiya ba’a hankakin kwari za su ƙwaƙule masa idanu, ‘ya’yan mikiya za su cinye.

18-19 Akwai abu uku, i, har huɗu ma, waɗanda ban iya fahimtar su ba, wato

yadda gaggafa take tashi a sararin sama,

yadda maciji yake jan ciki a kan dutse,

yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku,

Sha’anin namiji da ‘ya mace.

20 Ga yadda al’amarin mazinaciya yake, takan yi sha’aninta sa’an nan ta yi wanka ta ce, “Ban yi laifin kome ba!”

21-23 Akwai abu uku, i, har huɗu ma waɗanda duniya ba ta jurewa da su, wato

bara da ya zama sarki,

wawa da ya ƙoshi da abinci,

mummunar mace da ta sami miji,

baiwar da ta gāji uwargijiyarta.

24-28 Akwai ƙananan abubuwa huɗu a duniya, amma suna da hikima ƙwarai, wato

tururuwa talikai ne marasa ƙarfi, amma duk da haka sukan tanadi abincinsu da rani,

remaye ba ƙarfafa ba ne, duk da haka suna yi wa kansu gidaje a cikin duwatsu,

fara ba su da sarki, amma duk da haka suna tafiya sahu-sahu.

ƙadangare ma wanda ka iya kama shi a hannu, amma yana zama a cikin fādodin sarakuna.

29-31 Akwai abu uku, i, har huɗu ma da suke da kwarjini da taƙama a tafiyarsu, wato

Zaki wanda ya fi dukan dabbobi ƙarfi, ba ya ratse wa kowa daga cikinsu,

bunsuru da zakara mai taƙama,

sarkin da yake tafiya gaban jama’arsa.

32 Idan ka yi wauta kana ta ɗaukaka kanka, ko kuwa kana shirya mugunta, ka tsaya ka yi tunani!

33 Gama kaɗa madara takan kawo mai, murɗa hanci takan sa a yi haɓo, tsokanar fushi takan kawo jayayya.