Categories
M. SH

M. SH 21

Yadda za a yi da Laifin Kisankai da ba a San wanda ya yi Ba

1 “Idan aka iske gawar mutum wanda wani ya kashe a fili a ƙasar da Ubangiji Allahnku ya ba ku, ku mallaka, ba a kuwa san wanda ya kashe shi ba,

2 sai dattawanku da alƙalanku su fito su auna nisan wurin daga gawar zuwa garuruwan da yake kewaye da gawar.

3 Dattawan garin da ya fi kusa da gawar za su ɗauki karsana wadda ba a taɓa aiki da ita ba, ba a kuma taɓa sa mata karkiya ba.

4 Sai dattawan garin nan su kai karsanar kwari inda ruwa yake gudu, inda ba a taɓa noma ko shuka ba. A can cikin kwarin za a karya wuyan karsanar.

5 Sa’an nan sai firistoci, ‘ya’yan Lawiyawa, su fito gaba, gama su ne Ubangiji Allahnku ya zaɓa don su yi masa aiki, su sa albarka da sunansa, su ne kuma masu daidaita kowace gardama da cin mutunci.

6 Sai dukan dattawan garin da ya fi kusa da gawar su wanke hannuwansu a bisa karsanar da aka karya wuyanta a kwarin.

7 Sa’an nan su ce, ‘Hannuwanmu ba su zub da wannan jini ba, idanunmu kuma ba su ga wanda ya zubar da shi ba.

8 Ya Ubangiji, ka kuɓutar da jama’arka, Isra’ila, wadda ka fansa, kada ka bar alhakin jinin marar laifin nan ya kama jama’arka, Isra’ila. Ka gafarta musu alhakin wannan jini.’

9 Ta haka za ku kawar da alhakin jinin marar laifi daga cikinku, sa’ad da kuka yi abin da yake daidai a wurin Ubangiji.”

Yadda Za a Yi da Matan da Aka Kama Wurin Yaƙi

10 “Sa’ad da kuka tafi yaƙi da magabtanku, Ubangiji Allahnku kuwa ya bashe su a hannunku, kun kuwa kama su bayi,

11 in a cikinsu ka ga wata kyakkyawar mace wadda ka yi sha’awarta, to, ka iya aurenta.

12 Sai ka kawo ta gidanka, ta aske kanta, ta yanke farcenta,

13 ta tuɓe tufafin bauta. Sa’an nan sai ta zauna a gida tana makokin mahaifinta da mahaifiyarta har wata ɗaya cif. Bayan haka ka iya shiga wurinta, ka zama mijinta, ita kuma ta zama matarka.

14 In ka ji ba ka bukatarta, sai ka sake ta ta tafi inda take so, amma kada ka sayar da ita, kada kuma ka wahalshe ta, tun da yake ka riga ka ƙasƙantar da ita.”

Ka’ida a kan Gādon Ɗan Fari

15 “Idan mutum yana da mata biyu, amma ya fi ƙaunar ɗayar, idan kuwa dukansu biyu, wato mowar da borar, suka haifi ‘ya’ya, idan bora ce ta haifi ɗan fari,

16 to, a ranar da zai yi wa ‘ya’yansa wasiyya a kan gādon da zai bar musu, kada ya sa ɗan mowa ya zama kamar shi ne ɗan fari, a maimakon ɗan borar wanda shi ne ɗan farin,

17 Amma sai ya yarda ya ba ɗan farin, wato ɗan borar, za a ba shi riɓi biyu na dukan abin da yake da shi gama shi ne mafarin ƙarfinsa, yana da hakkin ɗan fari.”

Gagararren Ɗa

18 “Idan mutum yana da gagararren ɗa wanda ba ya jin maganar mahaifinsa da ta mahaifiyarsa, sun kuma hore shi, duk da haka bai ji ba,

19 sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su kama shi, su kawo shi wurin dattawan garin a dandalin ƙofar gari.

20 Sai su faɗa wa dattawan garinsu, su ce, ‘Wannan ɗanmu ne, gagararre, ba ya yi mana biyayya. Shi mai zari ne, mashayi!’

21 Sa’an nan, sai mutanen garin su jajjefe shi da duwatsu har ya mutu. Ta haka za ku kawar da mugunta daga cikinku. Dukan Isra’ilawa za su ji, su ji tsoro.”

Waɗansu Dokoki

22 “Idan mutum ya yi laifin da ya isa mutuwa, aka rataye shi a itace har ya mutu,

23 kada a bar gawarsa ta kwana a kan itacen. Sai ku binne shi a ranar da aka rataye shi, gama wanda aka rataye shi la’ananne ne ga Ubangiji. Ku binne shi don kada ku ƙazantar da ƙasar da Ubangiji Allah yake ba ku, ku gāda.”

Categories
M. SH

M. SH 22

1 “Idan kun ga ɓataccen san wani, ko tunkiyarsa, to, kada ku ƙyale shi, amma lalle sai ku komar da shi ga mai shi.

2 Idan mutumin ba kusa da ku yake zaune ba, ko kuma ba ku san shi ba, to, sai ku kawo dabbar a gidanku, ta zauna a wurinku, har lokacin da mutumin ya zo ya shaida ta, sa’an nan ku ba shi.

3 Haka nan kuma za ku yi da jakinsa, da riga, da kowane abin wani da ya ɓace, ku kuwa kuka tsinta. Faufau, kada ku ƙyale su.

4 “Idan kun ga jakin wani ko sansa ya faɗi a hanya, kada ku ƙyale shi, sai ku taimake shi ku tashe shi.

5 “Kada mace ta sa suturar maza, kada kuma namiji ya sa suturar mata. Duk mai yin haka, abin ƙyama ne ga Ubangiji Allahnku.

6 “Idan kuna tafiya a hanya, kun ga sheƙar tsuntsu a itace, ko a ƙasa, da ‘ya’yanta, ko da ƙwayaye a ciki, uwar kuma tana kwance bisa ‘ya’yan ko ƙwayayen, kada ku kama uwar duk da ‘ya’yan.

7 Sai ku bar uwar ta tafi, amma kun iya kwashe ‘ya’yan. Yin haka zai sa ku sami zaman lafiya da tsawon rai.

8 “Sa’ad da kuka gina sabon gida, sai ku ja masa rawani don kada ku jawo wa gidanku alhakin jini idan wani ya fāɗi daga bisa.

9 “Kada ku shuka iri biyu a gonar inabinku don kada abin da kuka shuka da amfanin gonar inabinku su zama haramiyarku.

10 “Kada ku haɗa sa da jaki su yi huɗa tare.

11 “Kada ku sa rigar da aka saƙa da ulu garwaye da lilin.

12 “Sai ku yi wa rigar da kukan sa tuntu huɗu, tuntu ɗaya a kowace kusurwa.

Dokoki a kan Hana Lalata

13 “Idan mutum ya auri mace, ya shiga wurinta, sa’an nan ya ƙi ta,

14 yana zarginta da cewa ta yi abin kunya, yana ɓata mata suna a fili, yana cewa, ‘Na auri wannan mata, amma sa’ad da na kusace ta, sai na iske ita ba budurwa ba ce,’

15 sai mahaifinta da mahaifiyarta su kawo shaidar budurcin yarinyar a gaban dattawan garin a dandalin ƙofar garin.

16 Sai mahaifinta ya ce wa dattawan, ‘Na ba wannan mutum ‘yata aure, amma ya ƙi ta.

17 Yana zarginta da aikata abin kunya, ya ce, bai iske ‘yarmu budurwa ba. Amma ga shaidar budurcin ‘yata.’ Sai su shimfiɗa tsalala a gaban dattawan.

18 Sai dattawan garin su kama mutumin su yi masa bulala,

19 su ci shi tara shekel ɗari na azurfa, su ba mahaifin yarinyar, gama a fili mutumin ya ɓata sunan budurwar cikin Isra’ila. Za ta zama matarsa, ba shi da iko ya sake ta muddin ransa.

20 “Idan aka tabbatar zargin gaskiya ne, ba a kuma ga shaidar budurcinta ba,

21 sai a kai yarinyar a ƙofar gidan mahaifinta, sa’an nan mutanen garin su jajjefe ta da duwatsu har ta mutu, don ta yi aikin wauta cikin Isra’ila, gama ta yi karuwanci a gidan mahaifinta. Ta haka za ku kawar da mugunta daga cikinku.

22 “Idan aka iske wani yana kwance da matar wani, sai a kashe dukansu biyu, wato mutumin da matar. Haka za ku kawar da mugunta daga Isra’ila.

23 “Idan a cikin gari wani ya iske budurwar da ake tashinta, ya kwana da ita,

24 sai a kawo su, su biyu ɗin, a dandalin ƙofar gari, ku jajjefe su da duwatsu har su mutu, don yarinyar tana cikin gari, amma ba ta yi kururuwa a taimake ta ba, don kuma mutumin ya ɓata budurwar maƙwabcinsa. Da haka za ku kawar da mugunta daga cikinku.

25 “Amma idan a saura wani ya fāɗa wa yarinyar da ake tashinta, har ya kwana da ita ƙarfi da yaji, sai a kashe wannan mutum.

26 Amma ita yarinyar ba za a yi mata kome ba, domin ba ta yi laifin da ya isa mutuwa ba, gama wannan shari’a daidai take da ta mutumin da ya faɗa wa maƙwabcinsa ya kashe shi.

27 Gama sa’ad da ya same ta a saura, ita wadda ake tashinta ta yi kururuwa, amma ba wanda zai cece ta.

28 “Idan wani ya iske yarinyar da ba a tashinta, ya kama ta, ya kwana da ita, aka kuwa same su,

29 to, sai wanda ya kwana da ita ya ba mahaifinta shekel hamsin na azurfa, ita kuwa za ta zama matarsa, gama ya ci mutuncinta. Ba zai sake ta ba muddin ransa.

30 “Kada mutum ya auri matar mahaifinsa, kada kuma ya kware fatarinta, gama na mahaifinsa ne.”

Categories
M. SH

M. SH 23

Waɗanda Za a Ware daga Cikin Taron Jama’a

1 “Duk wanda aka dandaƙe ko wanda aka yanke gabansa ba zai shiga taron jama’ar Ubangiji ba.

2 “Shege ba zai shiga taron jama’ar Ubangiji ba. Har tsara ta goma zuriyarsa ba za su shiga taron jama’ar Ubangiji ba.

3 “Kada Ba’ammone ko Bamowabe ya shiga taron jama’ar Ubangiji. Har tsara ta goma ta zuriyarsu ba za su shiga taron jama’ar Ubangiji ba.

4 domin ba su zo sun tarye ku, su kawo muku abinci da ruwa ba sa’ad da kuke a hanyarku, lokacin da kuka fito daga Masar. Ga shi kuma, sun yi ijara da Bal’amu ɗan Beyor daga Fetor ta Mesofatamiya ya zo ya la’anta ku.

5 Amma Ubangiji Allahnku ya ƙi saurarar Bal’amu, sai Ubangiji ya juyar da la’anar ta zama muku albarka saboda Ubangiji Allahnku yana ƙaunarku.

6 Har abada kada ku nemar musu zaman lafiya ko wadata.

7 “Kada ku ji ƙyamar Ba’edome gama shi danginku ne. Kada kuma ku ji ƙyamar Bamasare don kun yi baƙunci a ƙasarsa.

8 ‘Ya’yansu tsara ta uku, za su iya shiga taron jama’ar Ubangiji.”

Kiyaye Sansanin Yaƙi da Tsabta

9 “Sa’ad da kuka kafa sansani don ku yi yaƙi da magabtanku, sai ku kiyaye kanku daga kowane mugun abu.

10 Idan wani a cikinku ya ƙazantu saboda ya zubar da maniyyi da dare, to, sai ya fita daga sansanin, kada ya koma sansanin.

11 Amma da maraice, sai ya yi wanka da ruwa, ya koma sansani sa’ad da rana ta faɗi.

12 “Za ku keɓe wani wuri a bayan sansani inda za ku riƙa zagayawa.

13 Sai ku ɗauki abin tona ƙasa tare da makamanku. Lokacin da za ku zagaya garin yin najasa, sai ku tsuguna ku tona rami da abin tona ƙasa sa’an nan ku rufe najasar da kuka yi.

14 Gama Ubangiji Allahnku yakan yi yawo cikin sansaninku don ya cece ku, ya ba da magabtanku cikin hannunku. Saboda haka dole ku tsabtace sansaninku don kada Ubangiji ya iske wata ƙazanta a cikinku, ya rabu da ku.”

Waɗansu Dokoki

15 “Kada ku ba da bawan da ya tsere, ya zo gare ku, ga ubangijinsa.

16 Zai zauna a wurinku. Sai ya zauna tare da ku, a wurin da ya zaɓa cikin garuruwanku inda ya fi so. Kada ku dame shi.

17 “Kada Isra’ilawa mata da maza su shiga ƙungiyar karuwanci na addini.

18 Kada ku kawo kuɗin da aka samu ta wurin karuwanci, ko kuɗin da aka samu ta wurin yin luɗu a Haikalin Ubangiji don biyan wa’adin da kuka riga kuka yi, gama wannan abin ƙyama ne ga Ubangiji Allahnku.

19 “Kada ku ba danginku rance da ruwa, ko rancen kuɗi ne, ko na abinci, ko na kowane irin abu da akan ba da shi da ruwa.

20 Kun iya ba baƙo rance da ruwa, amma kada ku ba danginku rance da ruwa don Ubangiji Allahnku ya sa muku albarka a kan dukan abin da za ku yi a ƙasar da kuke shiga, ku kuma mallake ta.

21 “Idan kun yi wa Ubangiji Allahnku wa’adi, to, kada ku yi jinkirin cikawa, gama Ubangiji Allahnku zai neme shi a gare ku, ba kuwa zai zama zunubi a gare ku ba.

22 Idan kun nisanci yin wa’adi, ba zai zama zunubi gare ku ba.

23 Sai ku cika duk abin da kuka faɗa da bakinku, gama da yardarku ne kuka yi wa Ubangiji Allahnku wa’adi wanda kuka alkawarta.

24 “Sa’ad da kuka shiga gonar inabin maƙwabcinku, kuna iya cin ‘ya’yan inabin, har ku ƙoshi yadda kuke so, amma kada ku sa wani a jakarku.

25 Sa’ad da kuka shiga hatsin maƙwabcinku da yake tsaye, kun iya ku yi murmuren tsabar da hannunku, amma kada ku sa wa hatsin maƙwabcinku lauje.”

Categories
M. SH

M. SH 24

Dokar Kisan Aure

1 “Idan mutum ya sami wata mata ya aura, amma idan ba ta gamshe shi ba saboda ya iske wani abu marar kyau game da ita, har ya ba ta takardar saki a hannunta, ya sallame ta daga gidansa,

2 ta kuwa fita gidansa, idan ta je ta auri wani mutum dabam,

3 idan shi kuma ya ƙi ta, ya ba ta takardar saki a hannunta, ya sallame ta daga gidansa, ko kuma idan ya mutu ne,

4 to, kada mijinta na fari wanda ya sake ta, ya sāke aurenta, tun da yake ta ƙazantu. Gama wannan abar ƙyama ce a wurin Ubangiji. Kada ku jawo alhaki a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku gāda.

5 “Idan mutum ya yi sabon aure, kada ya tafi yaƙi tare da sojoji, ko kuma a sa shi kowane irin aiki. Sai ya huta a gida har shekara ɗaya saboda gidansa, don ya faranta wa matar da ya auro zuciya.”

Waɗansu Dokoki

6 “Kada mutum ya karɓi jinginar dutsen niƙa ko ɗan dutsen niƙa, gama yin haka karɓar jinginar rai ne.

7 “Idan aka iske mutum yana satar danginsa Ba’isra’ile don ya maishe shi bawansa, ko ya sayar da shi, sai a kashe ɓarawon. Ta haka za ku kawar da mugunta daga tsakiyarku.

8 “Game da ciwon kuturta, sai ku lura ku bi daidai da yadda firistoci na Lawiyawa suka umarce ku, ku yi. Sai ku kiyaye, ku aikata yadda na umarce su.

9 Ku tuna da abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Maryamu a lokacin da kuka fito daga Masar.

10 “Idan kun ba maƙwabcinku rance na kowane iri, kada ku shiga gidansa don ku ɗauki jingina.

11 Sai ku tsaya a waje, mutumin da kuka ba shi rancen zai kawo muku jinginar.

12 Amma kada ku yarda abin da aka jinginar ya kwana a wurinku idan mutumin matalauci ne.

13 Sai ku mayar masa da shi a faɗuwar rana domin ya yi barci yafe da rigarsa ya gode muku. Yin haka zai zama muku adalci a wurin Ubangiji Allahnku.

14 “Kada ku zalunci ɗan ƙodago wanda yake matalauci, ko shi danginku ne, ko kuwa baƙon da yake zaune a garuruwan ƙasarku.

15 Sai ku biya shi hakkinsa a ranar da ya yi aikin, kafin faɗuwar rana, gama shi matalauci ne, zuciyarsa tana kan abin hakkinsa, don kada ya yi wa Ubangiji kuka a kanku, har ya zama laifi a gare ku.

16 “Kada a kashe ubanni maimakon ‘ya’ya, kada kuma a kashe ‘ya’ya maimakon ubanni. Amma za a kashe mutum saboda laifin da ya aikata.

17 “Kada ku karkatar da shari’ar baƙo ko maraya. Kada kuma ku karɓi mayafin matar da mijinta ya rasu abin jingina.

18 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku ya fanshe ku daga can, saboda haka ina umartarku ku yi wannan.

19 “Idan kun manta da wani dami a gona lokacin girbin amfanin gona, kada ku koma ku ɗauko. Ku bar wa baƙo, da maraya, da gwauruwa ta gaske, domin Ubangiji Allahnku ya sa muku albarka a kan dukan aikin hannuwanku.

20 Sa’ad da kuka kakkaɓe ‘ya’yan zaitunku, kada ku sāke bin rassan kuna kakkaɓewa, sai ku bar wa baƙo, da maraya, da gwauruwa ta gaske.

21 Sa’ad da kuka girbe gonar inabinku kada kuma ku yi kala, sai ku bar wa baƙo, da maraya, da gwauruwa ta gaske.

22 Sai ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, don haka nake umartarku ku yi wannan.”

Categories
M. SH

M. SH 25

1 “Idan wata gardama ta tashi tsakanin mutane, suka je gaban shari’a, alƙalai kuwa suka yanke musu maganar, suka kuɓutar da marar laifi, suka kā da mai laifin,

2 idan mai laifin ya cancanci bulala, sai alƙali ya sa shi ya kwanta ƙasa, a bulale shi a gabansa daidai yawan bulalar da ta dace da irin laifin da ya yi.

3 Za a iya yi masa bulala arba’in, amma kada ta fi haka, don kada a ci gaba da bugunsa fiye da haka, har ya zama rainanne a idonku.

4 “Kada ku yi wa takarkari takunkumi sa’ad da yake tattaka hatsinku.”

Gādon Aure

5 “Idan ‘yan’uwa suna zaune wuri ɗaya tare, in ɗayansu ya rasu bai haihu ba, to, kada matar marigayin ta auri wani baƙo wanda yake ba a cikin dangin mijin ba. Sai ɗan’uwan mijinta ya zo wurinta, ya aure ta, ya yi mata abin da ya kamaci ɗan’uwan miji ya yi.

6 Ɗan farin da za ta haifa, zai zama magajin marigayin don kada a manta da sunansa cikin Isra’ila.

7 Amma idan mutum ya ƙi ya auri matar ɗan’uwansa, marigayi, sai matar ta tafi wurin dattawa a dandalin ƙofar gari, ta ce, ‘Ɗan’uwan mijina, marigayi, ya ƙi wanzar da sunan ɗan’uwansa cikin Isra’ila, gama ya ƙi yi mini abin da ya kamaci ɗan’uwan marigayi, ya yi.’

8 Sai dattawan garin su kira mutumin, su yi masa magana. Idan ya nace, yana cewa, ‘Ba na so in aure ta,’

9 sai matar ɗan’uwansa, marigayi, ta tafi wurinsa a gaban dattawan, ta kwaɓe takalmin ƙafarsa, ta tofa masa yau a fuskarsa, ta ce, ‘Haka za a yi wa wanda ya ƙi kafa gidan ɗan’uwansa.’

10 Za a kira sunan gidansa cikin Isra’ila, ‘Gidan wanda aka kwaɓe masa takalmi.’ ”

Waɗansu Dokoki

11 “Idan mutane biyu suna faɗa da juna, idan matar mutum ɗaya daga cikinsu ta zo don ta taimaki mijinta, idan ta kama marainan wancan mutum da hannunta,

12 sai ku yanke hannunta, kada ku ji tausayi.

13 “Kada ku riƙe ma’aunin nauyi iri biyu a jakarku, wato babba da ƙarami.

14 Kada kuma ku ajiye mudu iri biyu a gidanku, wato babba da ƙarami.

15 Sai ku kasance da ma’aunin nauyi da mudu masu kyau don ku daɗe a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.

16 Gama duk wanda yake aikata irin waɗannan abubuwa, da dukan marasa gaskiya, abin ƙyama ne su ga Ubangiji Allahnku.”

A Karkashe dukan Amalekawa

17 “Ku tuna da abin da Amalekawa suka yi muku a hanya, lokacin da kuka fito daga Masar.

18 Yadda suka yi muku kwanto a hanya, suka fāɗa muku ta baya, suka karkashe waɗanda suka gaji tiɓis. Ba su ko ji tsoron Allah ba.

19 Domin haka sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa daga dukan magabtanku da suke kewaye da ku a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka, abar gādo, to, sai ku shafe Amalekawa daga duniya, don kada a ƙara tunawa da su. Kada fa ku manta.”

Categories
M. SH

M. SH 26

Abin da Za a Yi da Nunan Fari da Zaka

1 “Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku gāda, kuka mallake ta, kuka zauna cikinta,

2 to, sai ku keɓe nunan fari na dukan amfanin ƙasa wanda kuka shuka a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Ku sa cikin kwando, ku tafi inda Ubangiji Allahnku zai zaɓa don ya tabbatar da sunansa.

3 Ku je wurin firist wanda yake aiki a lokacin, ku ce, ‘Yau, na sakankance a gaban Ubangiji Allahnka, cewa na shiga ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninmu zai ba mu.’

4 “Sa’an nan firist ya karɓi kwandon daga gare ku ya sa shi kusa da bagaden Ubangiji Allahnku.

5 Sa’an nan kuma sai ku hurta waɗannan kalmomi a gaban Ubangiji Allahnku, ku ce, ‘Ubana Ba’aramiye ne, mayawaci a dā. Ya gangara zuwa Masar yana da jama’a kima, ya yi baƙunci a wurin. Amma a can ya zama al’umma mai girma, mai iko, mai yawa.

6 Masarawa suka wulakanta mu, suka tsananta mana, suka bautar da mu.

7 Amma muka yi kuka ga Ubangiji Allah na kakanninmu. Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya ga azabarmu, da wahalarmu, da zaluncin da ake yi mana.

8 Sai Ubangiji ya fisshe mu daga Masar da dantsensa mai ƙarfi, mai iko, tare da bantsoro, da alamu, da mu’ujizai.

9 Ubangiji ya kawo mu nan, ya ba mu ƙasar nan, ƙasar da take mai yalwar abinci.

10 Ga shi, yanzu mun kawo nunan fari na amfanin ƙasar, da kai, ya Ubangiji, ka ba mu.’

“Sai ku ajiye shi a gaban Ubangiji Allahnku, ku yi sujada a gaban Ubangiji Allahnku.

11 Ku yi murna kuma, ku da Lawiyawa, da baƙin da suke zaune tare da ku, saboda dukan alherin da Ubangiji Allah ya yi muku, ku da gidanku.

12 “Sa’ad da kuka gama fitar da zakarku ta amfanin gona a shekara ta uku, wadda take shekara ta fid da zaka, sai ku ba Balawe, da baƙo, da maraya, da matar da mijinta ya rasu, don su ci, su ƙoshi a cikin garuruwanku.

13 Sa’an nan za ku ce a gaban Ubangiji Allahnku, ‘Na fitar da tsattsarkan kashi daga cikin gidana na ba Balawe, da baƙo, da maraya, da matar da mijinta ya rasu bisa ga umarnin da ka yi mini. Ban karya wani umarninka ba, ban kuwa manta da su ba.

14 Ban ci kome daga cikin zakar sa’ad da nake baƙin ciki ba, ban kuma fitar da kome daga cikinta ba sa’ad da nake da ƙazanta, ban kuma miƙa wa matattu kome daga cikinta ba. Na yi biyayya da muryar Ubangiji Allahna, na aikata dukan abin da ka umarce ni.

15 Ka duba ƙasa daga Sama, daga wurin zamanka mai tsarki, ka sa wa jama’arka, Isra’ila, albarka duk da ƙasar da ka ba mu, ƙasar da take mai yalwar abinci, kamar yadda ka rantse wa kakanninmu.’ ”

Tsattsarkar Jama’a ta Ubangiji

16 “Yau Ubangiji Allahnku yana umartarku ku kiyaye waɗannan dokoki da farillai. Sai ku lura ku aikata su da dukan zuciyarku da dukan ranku.

17 Yau kun shaida, cewa Ubangiji shi ne Allahnku, za ku yi tafiya cikin tafarkunsa, za ku kiyaye dokokinsa, da umarnansa, da farillansa, za ku kuma yi masa biyayya.

18 Yau kuma Ubangiji ya shaida, cewa ku ne jama’arsa ta musamman, kamar yadda ya alkawarta muku. Ku kuwa za ku kiyaye dukan umarnansa.

19 Shi kuwa zai ɗaukaka ku ku zama abin yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al’umman da ya yi. Za ku zama jama’a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku kamar yadda ya faɗa.”

Categories
M. SH

M. SH 27

Za a Rubuta Dokoki a Dutsen Ebal

1 Musa da dattawan Isra’ila suka umarci jama’a, suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai waɗanda na umarce ku da su yau.

2 Bayan da kuka haye Urdun, kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, sai ku kakkafa manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.

3 Sai ku rubuta kalmomin wannan shari’a a kansu daidai lokacin da kuka haye ku shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasar da take mai yalwar abinci, kamar yadda Ubangiji Allahnku ya alkawarta wa kakanninku.

4 Sa’ad da kuka haye Urdun ɗin sai ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal bisa ga umarnin da na yi muku yau. Ku yi musu shafe da farar ƙasa.

5 Can za ku gina wa Ubangiji Allahnku bagade da duwatsun da ba a taɓa sassaƙa su da baƙin ƙarfe ba.

6 Sai ku gina wa Ubangiji Allahnku bagade da duwatsun da ba a sassaƙa ba. A bisa wannan bagade za ku miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji Allahnku.

7 Za ku kuma miƙa hadayu na salama ku ci a wurin, ku yi ta murna a gaban Ubangiji Allahnku.

8 Sai ku rubuta dukan kalmomin waɗannan dokoki su fita sosai bisa duwatsun nan.”

9 Sai Musa da Lawiyawan da suke firistoci, suka ce wa Isra’ilawa, “Ku ji. Yau kun zama jama’ar Ubangiji Allahnku.

10 Sai ku saurari muryar Ubangiji Allahnku, ku kiyaye umarnansa, da dokokinsa waɗanda muke umartarku da su yau.”

La’ana a kan Dutsen Ebal

11 A wannan rana kuma Musa ya umarci jama’a, ya ce,

12 “Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato kabilar Saminu, da ta Lawi, da ta Yahuza, da ta Issaka, da ta Yusufu, da ta Biliyaminu.

13 Waɗannan za su tsaya a bisa kan Dutsen Ebal don su la’anta, wato kabilar Ra’ubainu, da ta Gad, da ta Ashiru, da ta Zabaluna, da ta Dan, da ta Naftali.

14 Sa’an nan Lawiyawa za su ta da murya, su ce wa dukan Isra’ilawa:

15 “ ‘La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa, ko ya ƙera gumaka, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannun mai sana’a, ya kafa ta a ɓoye.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’

16 “ ‘La’ananne ne wanda ya raina mahaifinsa ko mahaifiyarsa.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’

17 “ ‘La’ananne ne wanda ya ci iyakar maƙwabcinsa.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’

18 “ ‘La’ananne ne wanda ya karkatar da makaho daga hanya.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’

19 “ ‘La’ananne ne wanda ya yi wa baƙo, ko maraya, ko gwauruwa ta gaske shari’a ta rashin gaskiya.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’

20 “ ‘La’ananne ne wanda ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya buɗe fatarin matar mahaifinsa.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’

21 “ ‘La’ananne ne wanda ya kwana da dabba.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’

22 “ ‘La’ananne ne wanda ya kwana da ‘yar’uwarsa, wato ‘yar mahaifinsa, ko ‘yar mahaifiyarsa.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’

23 “ ‘La’ananne ne wanda ya kwana da surukarsa.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’

24 “ ‘La’ananne ne wanda ya buge maƙwabcinsa daga ɓoye.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!”

25 “ ‘La’ananne ne wanda aka yi ijara da shi don ya kashe marar laifi.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’

26 “ ‘La’ananne ne wanda bai yi na’am da kalmomin dokokin nan don ya yi aiki da su ba.’

“Sai dukan jama’a su amsa, ‘Amin, Amin!’ ”

Categories
M. SH

M. SH 28

Albarkun Biyayya

1 “Idan kun yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, kuna aikata dukan umarnansa waɗanda nake umartarku da su yau, to, Ubangiji Allahnku zai fifita ku fiye da dukan sauran al’umma.

2 Idan kun yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, dukan albarkun nan za su sauko muku, su zama naku.

3 “Za ku zama masu albarka, ko kuna cikin gari, ko kuna cikin karkara.

4 “’Ya’yanku za su zama masu albarka, haka nan kuma amfanin gonakinku, da ‘ya’yan dabbobinku, da ‘ya’yan shanunku, da ‘ya’yan tumakinku da awakinku.

5 “Kwandunanku da makwaɓan za su yalwata ƙullunku.

6 “Da albarka za ku shiga, da albarka kuma za ku fita.

7 “Ubangiji zai sa ku fatattaki abokan gābanku a gabanku waɗanda suke tasar muku. Ta hanya guda za su auka muku, amma ta hanyoyi bakwai za su gudu daga gabanku.

8 “Ubangiji zai sa wa abin da yake cikin rumbunanku albarka da dukan aikin hannuwanku. Zai sa muku albarka a ƙasar da yake ba ku.

9 “Ubangiji zai sa ku zama tsattsarkar jama’arsa kamar yadda ya rantse muku, idan za ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin tafarkunsa.

10 Dukan mutanen duniya za su gane ku na Ubangiji ne, za su ji tsoronku.

11 Ubangiji zai arzuta ku ƙwarai da ‘ya’ya, da ‘ya’yan dabbobi, da amfanin gona, a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba ku.

12 Ubangiji zai buɗe muku taskarsa ta sammai, don ya ba ƙasarku ruwa a kan kari, zai kuma sa albarka a kan dukan aikin hannuwanku. Al’ummai da yawa za su karɓi rance a wurinku, amma ku, ba za ku karɓi rance ba.

13 Ubangiji zai sa ku zama kai, ba wutsiya ba. Kullum ci gaba za ku yi, ba baya ba, idan kuka yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku waɗanda nake umartarku da su yau, in kun lura, kun yi aiki da su,

14 idan kuma ba ku kauce zuwa dama ko hagu daga maganar da na umarce ku da ita yau ba, wato don ku bi waɗansu gumaka, ku bauta musu.”

Sakamakon Rashin Biyayya

15 “Amma idan ba za ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku ba, ko kuwa ba ku lura kuka aikata umarnansa da dokokinsa waɗanda nake umartar da su yau ba, to, dukan waɗannan la’ana za su auko muku, su same ku.

16 “La’anannu za ku zama a gari da karkara.

17 “La’anannu ne kwandunanku da makwaɓan ƙullunku.

18 “La’anannu ne ‘ya’yanku, da amfanin gonakinku, da ‘ya’yan shanunku, da ‘ya’yan tumakinku da na awakinku.

19 “Da la’ana za ku shiga, da la’ana kuma za ku fita.

20 “Ubangiji zai aiko muku da la’ana, da ruɗewa, da damuwa cikin dukan abin da za ku yi, har ya hallaka ku, ku lalace da sauri saboda mugayen ayyukanku, domin kuma kuka rabu da ni.

21 Ubangiji zai aiko muku da annoba wadda za ta manne muku, ta cinye ku cikin ƙasar da za ku shiga, ku mallake ta.

22 Ubangiji zai buge ku da ciwon fuka, da zazzaɓi, da ciwon kumburi, da zafi mai tsanani, da fari, da burtuntuna, da fumfuna. Waɗannan za su yi ta damunku har ku lalace.

23 Samaniya da take bisa kanku za ta zama tagulla, ƙasar kuma da kuke a bisa kanta ta zama baƙin ƙarfe.

24 Ubangiji zai mai da ruwan sama na ƙasarku gāri da ƙura, zai zubo muku da shi daga sama har ku hallaka.

25 “Ubangiji zai sa abokan gabanku su rinjaye ku cikin yaƙi. Ta hanya guda za ku auka musu, amma ta hanyoyi bakwai za ku gudu daga gabansu. Za ku zama abin ƙi ga dukan mulkokin duniya.

26 Gawawwakinku za su zama abinci ga dukan tsuntsayen sama, da namomin duniya. Ba wanda zai kore su.

27 Ubangiji zai buge ku da marurai irin na Masar, da basur, da ƙazwa, da ƙaiƙayi waɗanda ba za su warke ba.

28 Ubangiji kuma zai buge ku da ciwon hauka, da makanta, da rikicewar hankali.

29 Da tsakar rana za ku riƙa lalubawa kamar makaho, ba za ku yi arziki cikin ayyukanku ba. Za a riƙa zaluntarku, ana yi muku ƙwace kullum, ba wanda zai cece ku.

30 “Za ku yi tashin yarinya, wani ne zai kwana da ita. Za ku gina gida, wani ne zai zauna a ciki. Za ku dasa inabinku, wani ne zai girbe amfanin.

31 Za a yanka sanku a idonku, amma ba za ku ci ba. Za a ƙwace jakinku ƙiri ƙiri a idonku, ba za a mayar muku da shi ba. Za a ba magabtanku tumakinku, ba wanda zai cece ku.

32 A idonku za a ba da ‘ya’yanku mata da maza ga wata al’umma dabam, za ku yi ta jin kewarsu, amma a banza, gama ba ku da ikon yin kome.

33 Mutanen da ba ku sani ba, su za su ci amfanin gonakinku da dukan amfanin wahalarku. Za a zalunce ku, a murƙushe ku kullum.

34 Abubuwan da idanunku za su gani za su sa ku zama mahaukata.

35 Ubangiji zai bugi gwiwoyinku da ƙafafunku da marurai tun daga tafin ƙafarku har zuwa ƙoƙwan kanku.

36 “Ubangiji zai bashe ku, ku da sarkin da kuka naɗa wa kanku ga wata al’ummar da ku da kakanninku ba ku sani ba. Can za ku bauta wa gumakan itace da na duwatsu.

37 Za ku zama abin ƙi, da abin karin magana, da abin habaici a cikin dukan mutane inda Ubangiji zai kora ku.

38 “Za ku shuka iri da yawa a gonakinku, amma kaɗan za ku girbe gama fara za su cinye.

39 Za ku dasa gonakin inabi, ku nome su, amma ba za ku sha ruwan inabin, ko ku tsinke ‘ya’yan inabin ba, gama tsutsa za ta cinye shi.

40 Za ku sami itatuwan zaitun ko’ina cikin ƙasarku, amma ba za ku sami man da za ku shafa ba, gama ‘ya’yan za su kakkaɓe.

41 Za ku haifi ‘ya’ya mata da maza, amma ba za su zama naku ba, gama za a kai su bauta.

42 Ƙwari za su cinye dukan itatuwanku da dukan amfanin ƙasarku.

43 “Baƙin da suke tare da ku za su yi ta ƙaruwa, ku kuwa za ku yi ta komawa baya baya.

44 Za ku karɓi rance a wurinsu, su ba za su karɓi rance a wurinku ba. Su za su zama kai, ku kuwa za ku zama wutsiya.

45 “Dukan waɗannan la’anoni za su auko muku, su bi ku, su same ku, har ku hallaka, domin ba ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku ba, ba ku kiyaye umarnai da dokoki da ya umarce ku da su ba.

46 Za su zama alama da abin mamaki a kanku da zuriyarku har abada.

47 Ba ku bauta wa Ubangiji Allahnku da murna da farin ciki ba, saboda dukan abin da ya ba ku a yalwace,

48 domin haka za ku bauta wa magabtanku waɗanda Ubangiji zai turo muku. Za ku bauta musu da yunwa, da ƙishirwa, da tsiraici, da talauci. Za su sa karkiyar ƙarfe a wuyanka har su hallaka ku.

49 Ubangiji zai kawo wata al’umma daga nesa, wato daga bangon duniya, mai kai sura kamar gaggafa, wadda za ta yi gāba da ku. Al’ummar da ba ku san harshenta ba,

50 al’umma mai zafin hali, wadda ba ta kula da tsofaffi, ba ta kuma jin tausayin yara.

51 Za ta ci shanunku da amfanin ƙasarku har ku hallaka. Ba za ta bar muku hatsi ko ruwan inabi, ko mai, ko ‘ya’yan shanunku, ko na tumaki da na awakinku ba, har ta lalatar da ku.

52 Za su kewaye garuruwanku da yaƙi, har dogayen garukanku, da kagaranku waɗanda kuke dogara gare su, su rurrushe. Za su kewaye garuruwan ƙasarku da yaƙi a ƙasar da Ubangiji Allahnku ya ba ku.

53 Za ku ci naman ‘ya’yanku, mata da maza, waɗanda Ubangiji Allahnku ya ba ku, saboda irin tsananin kewayewar da magabtanku suka yi muku da yaƙi.

54 Nagarin mutum mai taushin zuciya wanda yake tare da ku, zai ƙi ɗan’uwansa, da matarsa, da ‘ya’yansa da suka ragu,

55 domin kada ya ba wani daga cikinsu naman ‘ya’yansa wanda yake ci, gama ba abin da ya rage masa saboda irin tsananin kewayewar garuruwanku da yaƙi wanda abokan gabanku suka kawo muku.

56 Matar kirki mai taushin zuciya wadda take tare da ku wadda ba za ta sa tafin ƙafarta a ƙasa ba saboda taushin zuciyarta da kyakkyawan halinta, za ta ƙi ƙaunataccen mijinta, da ɗanta, da ‘yarta.

57 A ɓoye za ta ci mahaifar da take biyo bayan ta haihu, da ‘ya’yan da za ta haifa, saboda ba ta da wani abinci lokacin da magabtanku za su kewaye garuruwanku da yaƙi mai tsanani.

58 “Idan ba ku lura, ku aikata dukan maganar dokokin nan da aka rubuta a wannan littafi ba, domin ku ji tsoron sunan nan mai ɗaukaka, mai kwarjini, wato sunan Ubangiji Allahnku,

59 to, Ubangiji zai aukar muku, ku da zuriyarku, da munanan masifu waɗanda ba su kawuwa, da mugayen cuce-cuce marasa warkewa.

60 Sai ya sāke kawo muku cuce-cuce irin na Masar, waɗanda kuka ji tsoronsu, za su kuwa manne muku.

61 Har yanzu kuma Ubangiji zai kawo muku kowace irin cuta, da kowace irin annoba, waɗanda ba a ambace su a littafin dokokin nan ba, har ku hallaka.

62 Ko da yake kuna da yawa kamar taurarin sama, za ku zama ‘yan kaɗan, domin ba ku yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku ba.

63 Kamar yadda Ubangiji ya ji daɗi ya arzuta ku, ya riɓaɓɓanya ku, haka nan kuma zai ji daɗi ya lalatar da ku, ya hallaka ku. Za a fitar da ku daga ƙasar da za ku shiga, ku mallaka.

64 “Ubangiji zai warwatsa ku cikin dukan al’ummai daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Can za ku bauta wa gumakan itace da na dutse waɗanda ku da kakanninku ba ku san su ba.

65 Ba za ku sami zaman lafiya wurin waɗannan al’ummai ba, ko tafin ƙafarku ma ba zai sami wurin hutawa ba. Ubangiji kuma zai sa fargaba a zuciyarku, ya sa idanunku su lalace, ranku zai yi suwu.

66 Kullum ranku zai kasance da damuwa, za ku zauna da tsoro dare da rana, kuna tsoron abin da zai sami ranku.

67 Da safe za ku ce, ‘Da ma maraice ne.’ Da maraice kuma za ku ce, ‘Da ma safiya ce,’ saboda tsoron da yake a zuciyarku, da abubuwan da idanunku suke gani.

68 Ubangiji zai komar da ku Masar cikin jiragen ruwa, ko da yake na ce ba za ku ƙara tafiya can ba. Can za ku sayar da kanku bayi mata da maza, amma ba wanda zai saye ku.”

Categories
M. SH

M. SH 29

Alkawarin Ubangiji da Isra’ilawa a Ƙasar Mowab

1 Waɗannan ne zantuttukan alkawari da Ubangiji ya umarci Musa ya faɗa wa Isra’ilawa a ƙasar Mowab, wato banda alkawarin da ya yi da su a bisa Dutsen Horeb.

2 Sai Musa ya kira dukan Isra’ilawa ya ce musu, “Ai, kun ga dukan abin da Ubangiji ya yi wa Fir’auna da barorinsa a dukan ƙasar Masar.

3 Idanunku sun ga manyan wahalai, da alamu, da mu’ujizai masu girma.

4 Duk da haka har wa yau Ubangiji bai ba ku zuciyar ganewa, ko idanun gani, ko kunnuwan ji ba.

5 Shekara arba’in na bi da ku cikin jeji. Rigunanku da takalmanku ba su tsufa ba.

6 Ba ku ci hatsi ba, ba ku kuma sha ruwan inabi ba, ko barasa, don ku sani shi ne Ubangiji Allahnku.

7 Sa’ad da kuka isa wannan wuri, sai Sihon Sarkin Heshbon, da Og, Sarkin Bashan, suka fito su yi yaƙi da mu, amma muka ci su.

8 Muku ƙwace ƙasarsu, muka ba Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa, su gāda.

9 Saboda haka sai ku kiyaye, ku aikata dukan zantuttukan wannan alkawari don ku arzuta a cikin dukan abin da za ku yi.

10 “Yau, ga ku nan tsaye, dukanku a gaban Ubangiji Allahnku, shugabannin kabilanku, da dattawanku, da shugabannin sojojinku, da dukan mazajen Isra’ila,

11 da ‘ya’yanku, da matanku, da baƙin da suke a zangonku, da mai yi muku faskare ko mai ɗebo muku ruwa.

12 Don ku ƙulla alkawari da Ubangiji Allahnku, alkawarin da Ubangiji Allahnku yake yi da ku yau.

13 Don ya mai da ku jama’arsa yau, shi kuma ya zama Allahnku kamar yadda ya yi muku magana, da yadda kuma ya rantse wa kakanninku, wato Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.

14 Ba da ku kaɗai nake yin wannan alkawari ba,

15 amma da wanda ba ya nan tare da mu yau, da shi wanda yake tare da mu a nan yau, a gaban Ubangiji Allahnmu.

16 “Kun sani dai yadda muka zauna a ƙasar Masar, da yadda muka yi ta ratsawa ta tsakiyar al’ummai muka wuce.

17 Kun ga abubuwan da suke da su masu banƙyama, wato gumakansu na itace, da na dutse, da na azurfa, da na zinariya.

18 Kada zuciyar wani mutum, ko ta wata mata ko na wani iyali, ko wata kabila cikinku yau, ta bar bin Ubangiji Allahnku, ta koma ga bauta wa gumakan al’umman nan. Kada a iske wani tushe a cikinku mai ba da ‘ya’ya masu dafi, masu ɗaci.

19 Idan wani mutum ya ji zantuttukan la’anan nan sa’an nan ya sa wa kansa albarka a zuciyarsa, yana cewa, ‘Ba abin da zai same ni ko na bi taurin zuciyata,’ wannan zai haddasa lalacewar ɗanye da busasshe gaba ɗaya.

20 Ubangiji ba zai gafarce shi ba, amma fushin Ubangiji da kishinsa za su auko a kan wannan mutum, dukan la’anar kuma da aka rubuta a littafin nan za ta bi ta kansa, Ubangiji kuma zai shafe sunansa daga duniya.

21 Ubangiji zai ware mutumin nan daga dukan kabilan Isra’ila, don ya hukunta shi bisa ga dukan la’anar da aka rubuta a wannan littafin dokoki.

22 “Tsararraki masu zuwa nan gaba, wato ‘ya’yan da za su gaje ku, da baƙon da ya zo daga ƙasa mai nisa, za su ga annobar ƙasar, da cuce-cucen da Ubangiji zai ɗora mata.

23 Dukan ƙasa za ta zama kibritu da gishiri, ba shuka, ba amfani, ciyawa kuma ba ta tsirowa, kamar yadda Ubangiji ya kabantar da Saduma da Gwamrata, da Adam da Zeboyim, da zafin fushinsa.

24 Dukan al’ummai za su ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan ƙasa? Me ya sa ya yi fushi mai tsanani haka?’

25 Sa’an nan jama’a za su ce, ‘Saboda sun yi watsi da alkawarin Ubangiji Allah na kakanninsu, wato alkawarin da ya yi da su sa’ad da ya fisshe su daga ƙasar Masar.

26 Suka tafi suka bauta wa gumaka, suka yi musu sujada, gumakan da ba su san su ba, ba Ubangiji ne ya ba su ba.

27 Saboda haka Ubangiji ya husata da wannan ƙasa, ya kawo mata kowace irin la’anar da aka rubuta a wannan littafin.

28 Ubangiji ya tumɓuke su da zafin fushinsa, da babbar hasala, daga ƙasarsu, ya watsa su cikin wata ƙasa dabam kamar yadda suke a yau.’

29 “Sanin gaibu na Ubangiji Allahnmu ne, amma abubuwan da aka bayyana namu ne, mu da ‘ya’yanmu har abada, don mu kiyaye dukan maganar dokokin nan.”

Categories
M. SH

M. SH 30

Sharuɗan Komar da Mutane, da kuma Sa musu Albarka

1 “Sa’ad da duk waɗannan abubuwa suka same ku, wato albarka da la’ana waɗanda na sa a gabanku, in kun tuna da su a zuciyarku a duk inda kuke cikin al’ummai inda Ubangiji Allahnku ya kora ku,

2 kuka sāke komowa wurin Ubangiji Allahnku, ku da ‘ya’yanku kuka yi biyayya da maganarsa da zuciya ɗaya, da dukan ranku, bisa ga yadda na umarce ku yau,

3 sa’an nan Ubangiji Allahnku zai komo da ku daga bauta, ya yi muku jinƙai. Zai tattaro ku daga cikin al’ummai inda ya warwatsa ku.

4 Idan korarrunku suna can ƙurewar duniya, Ubangiji Allahnku zai tattaro ku daga can, ya dawo da ku.

5 Ubangiji Allahnku kuma zai komo da ku cikin ƙasar da kakanninku suka mallaka, za ku mallake ta. Ubangiji zai arzuta ku, ya riɓaɓɓanya ku fiye da kakanninku.

6 Ubangiji Allahnku kuma zai tausasa zuciyarku da ta ‘ya’yanku domin ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da zuciya ɗaya da dukan ranku, domin ku rayu.

7 Ubangiji Allahnku kuwa zai ɗora wa magabtanku da maƙiyanku waɗanda suka tsananta muku waɗannan la’ana.

8 Sa’an nan za ku yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, ku kiyaye dukan umarnan nan waɗanda na umarce ku da su yau.

9 Ubangiji Allahnku zai arzuta dukan aikin hannuwanku ƙwarai, ya kuma arzutar da ‘ya’yanku da ‘ya’yan shanu, da amfanin gona, gama Ubangiji zai ji daɗi ya arzuta ku kuma yadda ya ji daɗin kakanninku,

10 idan za ku yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, ku kiyaye umarnansa da dokokinsa waɗanda suke rubuce a littafin dokokin nan, idan kuma kun juyo wurin Ubangiji Allahnku da zuciya ɗaya da dukan ranku.

11 “Gama wannan umarni da na yi muku yau, bai fi ƙarfinku ba, bai kuma yi nisa da ku ba.

12 Ba cikin Sama yake ba, balle ku ce, ‘Wa zai hau zuwa sama, ya sauko mana da shi don mu ji, mu kiyaye?’

13 Ba kuma a hayin teku yake ba, balle ku ce, ‘Wa zai haye mana wannan teku don ya kawo mana shi don mu ji, mu kiyaye?’

14 Amma umarnin yana kurkusa da ku, yana cikin bakinku da zuciyarku don ku kiyaye shi.

15 “Ga shi yau, na sa rai da nagarta a gabanku, da mutuwa da mugunta.

16 Idan kuka kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku waɗanda nake umartarku da su yau, idan kuma kun ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna yin tafiya cikin tafarkunsa, kuna kiyaye umarnansa, da dokokinsa, da farillansa, to, za ku rayu, ku riɓaɓɓanya, Ubangiji Allahnku kuwa zai sa muku albarka cikin ƙasar da za ku shiga, ku mallake ta.

17 Amma idan zuciyarku ta kangare kun ƙi ku saurara, amma zuciyarku ta janye ku kun yi wa gumaka sujada, kuka bauta musu,

18 to, ina faɗa muku yau, lalle za ku hallaka. Ba za ku yi tsawon rai a ƙasar da za ku haye Urdun ku shiga ciki don ku mallake ta ba.

19 Ina kiran sama da duniya su zama shaidu a kanku yau, cewa na sa rai da mutuwa a gabanku, da albarka da la’ana. Ku zaɓi rai fa, don ku rayu, ku da zuriyarku.

20 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi biyayya da maganarsa, ku manne masa, gama wannan shi ne ranku da tsawon kwanakinku, don ku zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku ya rantse zai ba kakanninku, wato Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.”