Categories
MAR

MAR 11

Mutanen Urushalima Sun Marabci Yesu

1 Da suka kusato Urushalima, da Betafaji, da Betanya, wajen Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa biyu,

2 ya ce musu, “Ku shiga ƙauyen can da yake gabanku. Da shigarku za ku ga wani aholaki a ɗaure, wanda ba a taɓa hawa ba. Ku kwanto shi.

3 Kowa ya ce muku, ‘Don me kuke haka?’ ku ce, ‘Ubangiji ne yake bukatarsa, Zai kuma komo da shi nan da nan.’ ”

4 Sai suka tafi, suka tarar da aholakin a ɗaure a ƙofar gida a bakin hanya, suka kwance shi.

5 Sai waɗanda suke tsaitsaye a gun suka ce musu, “Don me kuke kwance aholakin nan?”

6 Suka faɗa musu abin da Yesu ya ce. Su kuwa suka ƙyale su suka tafi.

7 Suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfiɗa mayafansu a kai, ya hau.

8 Sai mutane da yawa suka shisshimfiɗa mayafansu a hanya, waɗansu kuma suka baza ganyen da suka kakkaryo a saura.

9 Da na gaba da na baya suka riƙa sowa suna cewa, “Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji!

10 Albarka ta tabbata ga mulkin nan mai zuwa na ubanmu Dawuda! Hosanna ga Allah!”

11 Sai ya shiga Urushalima, ya shiga Haikalin. Da dai ya dudduba kome, da yake magariba ta yi, ya fita ya tafi Betanya tare da goma sha biyun nan.

La’antar da Itacen Ɓaure

12 Kashegari da suka tashi daga Betanya, ya ji yunwa.

13 Da ya hango wani itacen ɓaure mai ganye kore shar, sai ya je ya ga ko ya sami ‘ya’ya. Da ya isa wurinsa bai ga kome ba sai ganye, don ba lokacin ‘ya’yan ɓaure ba ne.

14 Sai ya ce wa ɓauren, “Kada kowa ya ƙara cin ‘ya’yanka har abada!” Almajiransa kuwa suna ji.

Yesu Ya Tsabtace Haikalin

15 Suka iso Urushalima. Ya shiga Haikalin ya fara korar masu saye da sayarwa daga ciki, ya kuma birkice teburorin ‘yan canjin kuɗi da kujerun masu sayar da tattabarai,

16 ya kuma hana kowa ratsa Haikalin ɗauke da wani abu.

17 Sai ya yi musu gargaɗi ya ce, “Ashe, ba a rubuce yake ba cewa, ‘Za a kira masujadata ɗakin addu’a na dukkan al’ummai’? Amma ku kun maishe shi kogon ‘yan fashi.”

18 Da manyan firistoci da malaman Attaura suka ji wannan magana suka kuma nemi hanyar hallaka shi, saboda sun tsorata da shi, don duk jama’a na mamaki da koyarwa tasa.

19 Kowace yamma kuwa Yesu yakan fita gari.

Aya a kan Bushewar Itacen Ɓaure

20 Suna wucewa da safe, sai suka ga ɓauren nan ya bushe har saiwarsa.

21 Bitrus kuwa ya tuna, sai ya ce masa, “Ya Shugaba, dubi! Ɓauren nan da ka la’anta ya bushe!”

22 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku gaskata da Allah.

23 Hakika, ina gaya muku, kowa ya ce wa dutsen nan, ‘Ka ciru, ka faɗa teku’, bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata abin da ya faɗa zai auku, sai a yi masa shi.

24 Don haka ina dai gaya muku, kome kuka roƙa da addu’a, ku gaskata cewa samamme ne, za ku kuwa samu.

25 Koyaushe kuka tsaya yin addu’a, in akwai wanda kuke jin haushinsa, ku yafe masa, domin Ubanku da yake Sama shi ma yă yafe muku laifofinku. [

26 Amma in ba kwa yafewa, haka Ubanku da yake Sama ma ba zai yafe muku laifofinku ba.]”

Ana Shakkar Iznin Yesu

27 Suka koma Urushalima. Yana zaga cikin Haikalin sai manyan firistoci, da malaman Attaura, da shugabannin jama’a suka zo wurinsa,

28 suka ce masa, “Da wane izni kake yin waɗannan abubuwa, ko kuwa wa ya ba ka iznin yin haka?”

29 Sai Yesu ya ce musu, “Zan yi muku wata tambaya. Ku ba ni amsa, ni kuwa in gaya muku ko da wane izni nake yin abubuwan nan.

30 To, baftismar da Yahaya ya yi, daga Sama take, ko kuwa ta mutum ce? Ku ba ni amsa.”

31 Sai suka yi muhawara da juna, suka ce, “In muka ce, ‘Daga Sama take,’ sai ya ce, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’

32 Ma kuwa ce, ‘Ta mutum ce’?” Suna kuwa jin tsoron jama’a, don duk kowa ya tabbata, cewa Yahaya annabi ne.

33 Sai suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Yesu ya ce musu, “Haka ni kuma ba zan faɗa muku ko da wane izni nake yin abubuwan nan ba.”

Categories
MAR

MAR 12

Misali na Manoman da Suka Yi Sufurin Garkar Inabi

1 Sai Yesu ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ne ya yi garkar inabi, ya shinge ta, ya haƙa ramin matse inabin, ya kuma gina wata ‘yar hasumiyar tsaro. Ya ba waɗansu manoma sufurin garkar, sa’an nan ya tafi wata ƙasa.

2 Da kakar inabin ta yi, sai ya aiki wani bawansa wurin manoman nan ya karɓo masa gallar garkar.

3 Manoman kuwa suka kama shi, suka yi masa dūka, suka kore shi hanu banza.

4 Sai ya sāke aika musu wani bawa. Shi kuma suka yi masa rotsi, suka wulakanta shi.

5 Ya sāke aiken wani, shi kam, sai suka kashe shi. Haka fa aka yi ta yi da waɗansu da yawa, ana dūkan waɗansu, ana kashe waɗansu.

6 Har yanzu dai yana da sauran ɗaya tak, shi ne makaɗaicin ɗansa. Daga ƙarshe ya aike shi wurinsu, yana cewa, ‘Sā ga girman ɗana.’

7 Amma manoman nan suka ce wa juna, ‘Ai, wannan shi ne magajin. Ku zo mu kashe shi, gādon yă zama namu.’

8 Sai suka kama shi, suka kashe shi, suka jefar da shi bayan shinge.

9 To, me ubangijin garkan nan zai yi? Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba waɗansu garkar.

10 Ashe, ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba? cewa,

‘Dutsen da magina suka ƙi,

Shi ne ya zama mafificin dutsen gini.

11 Wannan aikin Ubangiji ne,

A gare mu kuwa abin al’ajabi ne.’ ”

12 Sai suka nemi su kama shi, don sun lura a kansu ne ya yi misalin, amma suna jin tsoron jama’a. Don haka suka ƙyale shi, suka tafi.

Biyan Haraji ga Kaisar

13 Suka aiko masa da waɗansu Farisiyawa da mutanen Hirudus, don su burma shi cikin magana tasa.

14 Da suka zo, suka ce masa, “Malam, ai, mun sani kai mai gaskiya ne, ba ka kuma zaɓen kowa, domin ka ɗauki kowa da kowa daidai, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi. Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa?

15 Mu biya, ko kada mu biya?” Shi kuwa da ya gane makircinsu, ya ce musu, “Don me kuke jarraba ni? Ku kawo mini dinari in gani.”

16 Suka kawo masa. Ya ce musu, “Suran nan da sunan nan na wane ne?” Suka ce masa, “Na Kaisar ne.”

17 Sai Yesu ya ce musu, “To, ku ba Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah.” Sai suka yi mamakinsa ƙwarai.

Tambaya a kan Tashin Matattu

18 Sai Sadukiyawa (su da suke cewa, wai ba tashin matattu) suka zo wurinsa, suka tambaye shi suka ce,

19 “Malam, Musa dai ya rubuta mana, cewa idan ɗan’uwan mutum ya mutu, ya bar mata tasa ba ɗa, sai lalle mutumin ya auri matar, ya haifa wa ɗan’uwansa ‘ya’ya.

20 To, an yi waɗansu ‘yan’uwa maza guda bakwai. Na farkon ya yi aure, ya mutu bai bar baya ba.

21 Na biyun kuma ya aure ta, shi ma ya mutu, ba ɗa. Na ukun ma haka.

22 Haka dai duk bakwai ɗin, ba wanda ya bar ɗa. Daga ƙarshe kuma ita matar ta mutu.

23 To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu? Don duk bakwai ɗin sun aure ta.”

24 Sai Yesu ya ce musu, “Ba saboda wannan ne ya sa kuka ɓata ba? Wato don ba ku san Littattafai ba, ba ku kuma san ikon Allah ba.

25 Domin in an tashi daga matattu, ba a aure, ba a aurarwa, amma kamar mala’ikun da suke Sama ake.

26 Game da tashin matattu kuma, ashe, ba ku taɓa karantawa a Littafin Musa ba, yadda Allah ya ce masa, ‘Ni ne Allahn Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu’?

27 Ai, waɗanda Allah shi ne Allahnsu rayayyu ne, ba matattu ba. Kun ɓata da gaske.”

Umarni Mafi Girma

28 Sai wani malamin Attaura ya zo ya ji suna muhawara da juna. Da dai ya ga Yesu ya ba su kyakkyawar amsa, sai ya tambaye shi, “Wane umarni ne mafi girma duka?”

29 Yesu ya amsa masa ya ce, “Mafi girma shi ne, ‘Ku saurara, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.

30 Sai ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka, da kuma dukkan ƙarfinka.’

31 Mabiyinsa shi ne, ‘Ka ƙaunaci ɗan’uwanka kamar kanka.’ Ba fa sauran wani umarni da ya fi waɗannan girma.”

32 Sai malamin Attaura ya ce masa, “Hakika gaskiyarka Malam, Ubangiji ɗaya ne, ba kuwa wani sai shi.

33 A ƙaunace shi kuma da dukkan zuciya, da dukan hankali, da dukkan ƙarfi, a kuma ƙaunaci ɗan’uwa kamar kai, ai, ya fi dukkan hadayar ƙone-ƙone da yanke-yanke nesa.”

34 Da Yesu ya ga ya yi masa magana da fasaha, sai ya ce masa, “Ba ka nesa da Mulkin Allah.” Bayan wannan kuma ba wanda ya yi ƙarfin halin sāke tambayarsa wani abu.

Tambaya a kan Ɗan Dawuda

35 Sa’ad da Yesu yake koyarwa a Haikalin sai ya ce, “Ƙaƙa malaman Attaura za su ce Almasihu ɗan Dawuda ne?

36 Domin Dawuda kansa, ta ikon Ruhu Mai Tsarki ya ce,

‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,

Zauna a damana,

Sai na ɗora ka a kan maƙiyanka.’

37 Dawuda da kansa ya kira shi Ubangiji. To, ƙaƙa zai zama ɗansa?” Babban taron mutane kuwa sun saurare shi da murna.

Yesu Ya Fallashi Malaman Attaura

38 A koyarwa tasa har ya ce, “Ku yi hankali da malaman Attaura, masu son yawo da manyan riguna, suna so a gaishe su a kasuwa,

39 da kuma mafifitan mazaunai a majami’u, da mazaunan alfarma a wurin biki.

40 Su ne masu cin kayan matan da mazansu suka mutu, da yin doguwar addu’a don ɓad da sawu. Su za a yi wa hukunci mafi tsanani.”

Baiko Wadda aka Zuba

41 Sai ya zauna gaban baitulmalin Haikalin, yana duban yadda jama’a suke zuba kuɗi a ciki. Waɗansu masu arziki da yawa suna zuba kuɗi masu tsoka.

42 Sai ga wata gajiyayyiya da mijinta ya mutu ta zo, ta zuba rabin kobo biyu a ciki, wato kobo ke nan.

43 Sai ya kira almajiransa, ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, abin da gajiyayyiya gwauruwan nan ta zuba cikin baitulmalin nan ya fi na sauran duka.

44 Su duk sun bayar daga yalwa tasu ne, ita kuwa daga cikin rashinta ta ba da duk abin da take da shi, duk ma da kuɗinta na abinci.”

Categories
MAR

MAR 13

Yesu Ya Faɗi irin Rushewar da za Ta Sami Haikalin

1 Yesu na fita daga Haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam, dubi irin duwatsun nan da gine-ginen nan!”

2 Sai Yesu ya ce masa, “Ka ga manyan gine-ginen nan? Ba wani dutsen da za a bari nan a kan ɗan’uwansa, da ba za a baje shi ba.”

Farkon Azaba

3 Yana zaune a kan Dutsen Zaitun wanda yake kallon Haikalin sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawas suka tambaye shi a keɓe suka ce.

4 “Gaya mana yaushe za a yi waɗannan abubuwa? Wace alama kuma za a gani sa’ad da suke shirin aukuwa?”

5 Sai Yesu ya fara ce musu, “Ku kula fa kada kowa ya ɓad da ku.

6 Mutane da yawa za su zo da sunana, suna cewa su ne ni, har su ɓad da mutane da yawa.

7 In kuma kun jin labarin yaƙe-yaƙe da jita-jitarsu, kada hankalinku ya tashi. Lalle ne wannan ya auku, amma ƙarshen tukuna.

8 Al’umma za ta tasar wa al’umma, mulki ya tasar wa mulki. Za a yi ta raurawar ƙasa a wurare dabam dabam, da kuma yunwa. Amma fa duk wannan masomin azaba ne tukuna.

9 “Amma ku kula da kanku, don za su kai ku gaban majalisa, a kuma yi muku dūka a majami’u. Za a kuma kai ku gaban mahukunta da sarakuna saboda sunana, domin ku ba da shaida a gabansu.

10 Amma lalle sai an fara yi wa dukan al’ummai bishara.

11 Sa’ad da suka kai ku gaban shari’a suka miƙa ku, kada ku damu kan abin da za ku faɗa. Amma duk abin da aka yi muku baiwa da shi a lokacin nan, shi za ku faɗa, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne.

12 Ɗan’uwa zai ba da ɗan’uwansa a kashe shi, uba kuwa ɗansa. ‘Ya’ya kuma za su tayar wa iyayensu har su sa a kashe su.

13 Kowa kuma zai ƙi ku saboda sunana. Amma duk wanda ya jure har ƙarshe zai cetu.”

Matsananciyar Wahala

14 “Sa’ad da kuka ga an kafa mummunan aikin saɓo mai banƙyama a wurin da bai kamata ba (mai karatu fa yă fahimta), to, sai waɗanda suke ƙasar Yahudiya su gudu su shiga duwatsu.

15 Wanda yake kan soro kuma kada yă sauko yă shiga gida garin ɗaukar wani abu.

16 Wanda yake gona kuma kada ya koma garin ɗaukar mayafinsa.

17 Kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokaci!

18 Ku yi addu’a kada abin nan ya auku da damuna.

19 A lokacin nan za a yi wata matsananciyar wahala, irin wadda ba a taɓa yi ba tun farkon halittar da Allah ya yi, har ya zuwa yanzu, ba kuwa za a ƙara yi ba har abada.

20 Da ba don Ubangiji ya taƙaita kwanakin nan ba, da ba ɗan adam ɗin da zai tsira. Amma sabili da zaɓaɓɓun nan da ya zaɓa, sai ya taƙaita kwanakin.

21 To, a lokacin nan kowa ya ce muku, ‘Kun ga, ga Almasihu nan!’ ko, ‘Kun ga, ga shi can!’ kada ku yarda.

22 Don almasihan ƙarya da annabawan ƙarya za su firfito, su nuna alamu da abubuwan al’ajabi, don su ɓad da ko da zaɓaɓɓu ma, in zai yiwu.

23 Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.”

Komowar Ɗan Mutum

24 “Amma lokacin nan, wato bayan tsabar wahalan nan, za a duhunta rana, wata kuma ba zai yi haske ba.

25 Taurari za su riƙa faɗawa daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.

26 A sa’an nan ne za a ga Ɗan Mutum na zuwa cikin gajimare, da iko mai girma da ɗaukaka.

27 Sa’an nan zai aiko mala’ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga gabas da yamma, kudu da arewa, wato daga iyakar duniya har ya zuwa iyakar sama.”

Aya a kan Itacen Ɓaure

28 “Ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa sun fara sakuwa, suna toho, kun san damuna ta yi kusa ke nan.

29 Haka kuma sa’ad da kuka ga waɗannan abubuwa na aukuwa, ku sani ya kusato, a bakin ƙofa ma yake,

30 Hakika, ina gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun auku.

31 Sararin sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za ta shuɗe ba.”

Ba Wanda Ya San Ranar ko Sa’ar

32 “Amma fa wannan rana ko wannan sa’a ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke Sama, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.

33 Ku kula, ku zauna a faɗake, kuna addu’a, domin ba ku san sa’ar da lokacin zai yi ba.

34 Kamar mutum ne mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta yaransa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai jiran ƙofa ya zauna a faɗake.

35 To, ku zauna a faɗake fa, don ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne,

36 kada ya zo kwaram, ya samu kuna barci.

37 Abin kuwa da na gaya muku, ina gaya wa kowa ne, shi ne ku zauna a faɗake.”

Categories
MAR

MAR 14

Shugabanni sun Ƙulla Shawara Gāba da Yesu

1 Sauran kwana biyu a yi Idin Ƙetarewa da idin abinci marar yisti, sai manyan firistoci da malaman Attaura suka nemi hanyar kama Yesu da makirci, su kashe shi,

2 don sun ce, “Ba dai a lokacin idi ba, don kaɗa jama’a su yi hargitsi.”

An Shafi Yesu da Man Ƙanshi a Betanya

3 Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana cin abinci ke nan, sai ga wata mace ta zo da wani ɗan tulu na man ƙanshi na nardi tsantsa, mai tsadar gaske. Sai ta fasa ulun, ta tsiyaye masa man a kā.

4 Waɗansu kuwa da suka ji haushi, suka ce wa juna, “Mene ne na ɓata mai haka?

5 Gama da ma an sayar da shi fiye da dinari ɗari uku, an ba gajiyayyu!” Sai suka hasala da ita, suna gunaguni.

6 Amma Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta. Don me kuke damunta? Ai, alheri ta yi mini, na gaske kuwa.

7 Kullum kuna tare da gajiyayyu, ko yaushe kuma kuke so, kwa iya yi musu alheri, amma ba kullum ne kuke tare da ni ba.

8 Ta yi iyakacin ƙoƙarinta. Ta shafe jikina da mai gabannin jana’izata.

9 Hakika kuwa ina gaya muku, duk inda za a yi bishara a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa domin tunawa da ita.”

Yahuza Ya Yarda Ya Ba da Yesu

10 Sai Yahuza Iskariyoti, ɗaya daga cikin sha biyun nan, ya je wurin manyan firistoci don ya bashe shi a gare su.

11 Da suka ji haka suka yi murna, har suka yi alkawarin su ba shi kuɗi. Shi kuwa ya riƙa neman hanyar bashe shi.

Yesu Ya Ci Idin Ƙetarewa tare da Almajiransa

12 A ranar farko ta idin abinci marar yisti, wato ran da aka saba yanka ɗan ragon Idin Ƙetarewa, sai almajiransa suka ce masa, “Ina kake so mu je mu shirya maka cin Idin Ƙetarewa?”

13 Sai ya aiki almajiransa biyu, ya ce musu, “Ku shiga gari, can za ku gamu da wani mutum ɗauke da tulun ruwa, ku bi shi.

14 Duk gidan da ya shiga, ku ce wa maigidan, ‘In ji Malam, ina masaukin da zai ci Idin Ƙetarewa da almajiransa?’

15 Shi kuwa zai nuna muku wani babban soron bene mai kaya a shirye. A nan za ku shirya mana.”

16 Sai almajiran suka tashi, suka shiga gari, suka kuwa tarar kamar yadda ya faɗa musu, suka shirya Idin Ƙetarewa.

17 Da magariba ta yi, sai ya zo tare da sha biyun nan.

18 Suna cin abinci ke nan, sai Yesu ya ce, “Hakika, ina gaya muku, ɗayanku zai bashe ni, wanda muke ci tare.”

19 Suka fara baƙin ciki, suna ce masa da ɗaya ɗaya, “Ni ne?”

20 Sai ya ce musu, “Ɗaya daga cikin sha biyun nan ne dai, wanda muke ci ƙwarya ɗaya.

21 Ga shi, Ɗan Mutum zai tafi ne, yadda labarinsa yake a rubuce, duk da haka kuwa, kaiton mutumin nan da yake ba da Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da zai fiye masa.”

Cin Jibin Ubangiji

22 Suna cikin cin abinci, sai ya ɗauki gurasa, ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya ba su, ya ce, “Ungo, wannan jikina ne.”

23 Sai ya ɗauki ƙoƙo kuma, bayan ya yi godiya ga Allah, ya ba su, dukkansu kuwa suka shassha.

24 Sa’an nan ya ce musu, “Wannan jinina ne na tabbatar da alkawari, wanda za a bayar saboda mutane da yawa.

25 Hakika, ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabi ba, sai dai a ranan nan da zan sha wani sabo a Mulkin Allah.”

26 Da suka yi waƙar yabon Allah, sai suka fita suka tafi Dutsen Zaitun.

Bitrus Zai Yi Musun Sanin Yesu

27 Yesu ya ce musu, “Duk za ku yi tuntuɓe ne, domin a rubuce yake cewa, ‘Zan bugi makiyayi, tumaki kuwa su fasu.’

28 Amma fa bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa ƙasar Galili.”

29 Bitrus ya ce masa, “Ko duk sun yi tuntuɓe, ni kam, ba zan yi ba.”

30 Sai Yesu ya ce masa, “Hakika, ina gaya maka, ko a wannan dare, kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sanina sau uku.”

31 Amma Bitrus ya yi ta nanatawa da ƙarfi yana cewa, “Ko da za a kashe ni tare da kai, ba zan yi musun saninka ba.” Dukansu ma haka suka ce.

Yesu Ya Yi Addu’a a Gatsemani

32 Sai suka isa wani wuri, wai shi Getsamani. Ya ce wa almajiransa, “Ku zauna nan har in yi addu’a.”

33 Sai ya ɗauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, ya kuma fara jin wahala gaya, yana damuwa ƙwarai.

34 Sai ya ce musu, “Raina na shan wahala matuƙa, har ma kamar na mutu. Ku dakata nan, ku zauna a faɗake.”

35 Da ya ci gaba kaɗan, sai ya faɗi ƙasa, ya yi addu’a ko ya yiwu a ɗauke masa wannan lokaci.

36 Sa’an nan ya ce, “Ya Abba, Uba, kowane abu mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini ƙoƙon wahalan nan. Duk da haka dai ba nufina ba, sai naka.”

37 Ya komo ya samu suna barci, sai ya ce wa Bitrus, “Bitrus, barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a faɗake ko da sa’a ɗaya ba?

38 Ku zauna a faɗake, ku yi addu’a kada ku faɗa ga gwaji. Lalle ruhu ya ɗauka, amma jiki rarrauna ne.”

39 Sai ya sāke komawa, ya yi addu’a, yana maimaita maganar dā.

40 Har wa yau kuma ya sāke dawowa, ya samu suna barci, don duk barci ya cika musu ido ƙwarai, sun kuwa rasa abin da za su ce masa.

41 Ya sāke komowa zuwa na uku, ya ce musu, “Har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka. Lokaci ya yi. An ba da Ɗan Mutum ga masu zunubi.

42 Ku tashi mu tafi. Kun ga, ga mai bashe ni ɗin nan ya matso!”

An Ba da Yesu, an Kama Shi

43 Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, ɗaya daga cikin sha biyun nan, da taron mutane riƙe da takuba da kulake, manyan firistoci, da malaman Attaura, da shugabanni ne suka turosu.

44 To, mai bashe shi ɗin nan ya riga ya ƙulla da su cewa, “Wanda zan yi wa sumba, shi ne mutumin. Ku kama shi, ku tafi da shi a rirriƙe.”

45 Da zuwansa kuwa ya zo wurin Yesu, ya ce masa, “Ya shugaba!” sai ya yi ta sumbantarsa.

46 Su kuwa suka danƙe Yesu, suka kama shi.

47 Amma ɗaya daga cikin na tsaye, ya zaro takobinsa, ya kai wa bawan babban firist sara, ya dauke masa kunne.

48 Sai Yesu ya ce musu, “Kun fito ne da takuba da kulake ku kama ni kamar ɗan fashi?

49 Kowace rana ina tare da ku a Haikalin ina koyarwa, amma ba ku kama ni ba. Amma an yi haka ne fa domin a cika Littattafai.”

50 Daga nan duk almajiran suka yashe shi, suka yi ta kansu.

Saurayin da Ya Gudu

51 Sai wani saurayi, daga shi sai mayafi, ya bi shi. Suka kai masa cafka,

52 shi kuwa ya bar musu mayafin, ya gudu huntu.

Yesu a gaban ‘Yan Majalisa

53 Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. Duk manyan firistoci da shugabanni da malaman Attaura suka taru a wurinsa.

54 Bitrus kuma ya bi shi daga nesa nesa, har cikin gidan babban firist ɗin, ya zauna cikin dogaran Haikali, yana jin wuta.

55 To, manyan firistoci da ‘yan majalisa duka suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi, amma ba su samu ba.

56 Da yawa kam, sun yi masa shaidar zur, amma bakinsu bai zo ɗaya ba.

57 Daga baya kuma waɗansu suka taso, suka yi masa shaidar zur suka ce,

58 “Mun ji ya ce, wai zai rushe Haikalin nan da mutane suka gina, ya gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba.”

59 Duk da haka dai shaida tasu ba ta zo ɗaya ba.

60 Sai babban firist ya miƙe a tsakiyarsu ya tambayi Yesu ya ce, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”

61 Amma yana shiru abinsa, bai amsa kome ba. Sai babban firist ɗin ya sāke tambayarsa, “To, ashe, kai ɗin nan ne Almasihu Ɗan Maɗaukaki?”

62 Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum zaune dama ga Mai Iko, yana kuma zuwa cikin gajimare.”

63 Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa, ya ce, “Wace shaida kuma za mu nema?

64 Kun dai ji saɓon da ya yi! Me kuka gani?” Duk suka yanke masa shari’a a kan ya cancanci kisa.

65 Waɗansu ma suka fara tattofa masa yau, suka ɗaure masa idanu, suka bubbuge shi, suna ce masa, “Yi annabci!” Dogaran Haikali kuma suka yi ta marinsa.

Bitrus Ya Yi Musun Sanin Yesu

66 Bitrus kuwa na ƙasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo.

67 Da ta ga Bitrus na jin wuta, ta zura masa ido, ta ce, “Kai ma, ai, tare kake da Banazaren nan Yesu!”

68 Amma ya musa ya ce, “Ni ban ma san abin da kike faɗa ba, balle in fahimta.” Sai ya fito zaure. Zakara kuwa ya yi cara.

69 Sai baranyar ta gan shi, ta sāke ce wa waɗanda suke tsaitsaye a wurin, “Wannan ma nasu ne.”

70 Amma ya sāke musawa. Jim kaɗan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus, “Lalle kai ma ɗayansu ne, don Bagalile ne kai.”

71 Sai ya fara la’antar kansa, yana ta rantserantse, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan da kuke faɗa ba.”

72 Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu. Bitrus kuwa ya tuna da maganar da Yesu ya faɗa masa cewa, “Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sanina sau uku.” Ko da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.

Categories
MAR

MAR 15

Yesu a gaban Bilatus

1 Da wayewar gari sai manyan firistoci da shugabanni, da malaman Attaura, da dukkan ‘yan majalisa suka yi shawara. Sai suka ɗaure Yesu, suka tafi da shi, suka ba da shi ga Bilatus.

2 Bilatus ya tambaye shi, “Ashe, kai ɗin nan kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa masa ya ce, “Yadda ka faɗa.”

3 Sai manyan firistoci suka yi ta kai ƙararsa a kan abubuwa da yawa.

4 Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba ka da wata amsa? Dubi yawan maganganu da suke ba da shaida a kanka!”

5 Yesu dai har yanzu bai yi wata magana ba, har Bilatus ya yi mamaki.

An Hukunta wa Yesu Mutuwa

6 To, a lokacin idi kuwa Bilatus ya saba sakar musu kowane ɗan sarƙa guda da suka roƙa.

7 Akwai wani wai shi Barabbas da yake ɗaure, tare da waɗansu ‘yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin tawayen.

8 Jama’a fa suka matso, suka fara roƙon Bilatus ya yi musu abin da ya saba yi.

9 Sai ya amsa musu, ya ce, “Wato kuna so ne in sakar muku Sarkin Yahudawa?”

10 Don ya gane, saboda hassada ne manyan firistoci suka bashe shi.

11 Amma manyan firistocin suka zuga jama’a, gwamma ya sakar musu Barabbas.

12 Sai Bilatus ya sāke ce musu, “To, ƙaƙa zan yi da wanda kuke kira Sarkin Yahudawa?”

13 Sai suka sāke yin ihu suka ce, “A gicciye shi!”

14 Bilatus ya ce musu, “Ta wane hali? Wane mugun abu ne ya yi?” Amma su, sai ƙara ɗaga murya suke yi, suna cewa, “A gicciye shi!”

15 Bilatus kuwa da yake yana son ƙayatar da jama’a, ya sakar musu Barabbas. Bayan ya yi wa Yesu bulala, ya ba da shi a gicciye shi.

Sojoji Sun Yi wa Yesu Ba’a

16 Sai soja suka tafi da shi cikin fada, wato fadar mai mulkin, suka tara dukkan rundunar soja.

17 Suka yafa masa wata alkyabba mai ruwan jar garura, suka kuma yi wani kambi na ƙaya, suka sa masa a kā.

18 Sai suka fara gaishe shi, “Ranka ya daɗe, Sarkin Yahudawa!”

19 Suka riƙa ƙwala masa sanda a ka, suna tattofa masa yau, sa’an nan suka durƙusa, wai suna masa ladabi.

20 Da suka gama yi masa ba’a haka, suka yaye masa alkyabba mai ruwan jar garura, suka sa masa nasa tufafi, suka kai shi waje don su gicciye shi.

An Gicciye Yesu

21 Sai ga wani mai wucewa, wai shi Saminu Bakurane, uban Iskandari da Rufas, yana zuwa daga ƙauye. Suka fa tilasta masa ya ɗauki gicciyen Yesu.

22 Suka kai Yesu wani wuri wai shi Golgota, wato wurin ƙoƙon kai.

23 Suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, amma ya ƙi sha.

24 Sa’an nan suka gicciye shi, suka rarraba tufafinsa a junansu, suna kuri’a a kansu, su ga abin da kowa zai samu.

25 Da ƙarfe tara na safe suka gicciye shi.

26 Aka kuma rubuta sanarwar laifinsa sama da shi, wato “Sarkin Yahudawa.”

27 Suka kuma gicciye ‘yan fashi biyu tare da shi, ɗaya dama da shi, ɗaya kuma a hagun. [

28 Wannan shi ne cikar Nassin nan da ya ce, “An lasafta shi a cikin masu laifi.”]

29 Masu wucewa suka yi ta yi masa baƙar magana, suna kaɗa kai, suna cewa, “Ahaf! kai da za ka rushe Haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku,

30 to, sauko daga gicciyen, ka ceci kanka mana!”

31 Haka kuma manyan firistoci da malaman Attaura suka riƙa yi masa ba’a a junansu suna cewa, “Ya ceci waɗansu, ya kuwa kasa ceton kansa,

32 Almasihun nan, Sarkin Isra’ila, yă sauko mana daga gicciyen yanzu, mu kuwa mu gani mu ba da gaskiya.” Waɗanda aka gicciye tare da shi su ma suka zazzage shi.

Mutuwar Yesu

33 Daidai rana tsaka, sai duhu ya rufe ƙasa duka, har zuwa ƙarfe uku na yamma.

34 Da ƙarfe ukun sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktāna?” wato “Ya Allahna, Ya Allahna, don me ka yashe ni?”

35 Da waɗansu na tsaitsayen suka ji haka, suka ce, “Kun ji yana kiran Iliya.”

36 Sai ɗayansu ya yiwo gudu, ya jiƙo wani soso da ruwan tsami, ya soka a sanda, ya miƙa masa yă sha, yana cewa, “Bari mu gani ko Iliya zai zo ya sauko da shi.”

37 Sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi, kana ya cika.

38 Sa’an nan labulen da yake cikin Haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa.

39 Sa’ad da jarumi ɗin da yake tsaye yana kallon Yesu, ya ga yadda ya mutu haka, sai ya ce, “Hakika mutumin nan Ɗan Allah ne!”

40 Akwai kuma waɗansu mata da suke hange daga nesa, cikinsu da Maryamu Magadaliya, da Maryamu uwar Yakubu ƙarami da Yusufu, da kuma Salome,

41 su ne waɗanda suka biyo shi, sa’ad da yake ƙasar Galili, suna yi masa hidima, da kuma mata da yawa da suka rako shi Urushalima.

Jana’izar Yesu

42 La’asar lis, da yake ranar shiri ce, wato gobe Asabar,

43 Yusufu ya zo, mutumin Arimatiya, wani ɗan majalisa mai mutunci, wanda shi ma yake sauraron bayyanar Mulkin Allah, ya yi ƙarfin hali ya shiga wurin Bilatus, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.

44 Bilatus ya yi mamaki ko ya mutu. Sai ya kira jarumin ɗin, ya tambaye shi ko Yesu ya jima da mutuwa.

45 Da ya san haka daga bakin jarumin ɗin sai ya bai wa Yusufu jikin.

46 Sai Yusufu ya sayi likkafanin lilin. Da ya sauko da Yesu, ya sa shi a likkafanin lilin ɗin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe dutse aka yi, ya kuma mirgina wani dutse a bakin kabarin.

47 Maryamu Magadaliya da Maryamu uwar Yusufu sun ga inda aka sa shi.

Categories
MAR

MAR 16

Tashin Yesu daga Matattu

1 Da Asabar ta wuce, Maryamu Magadaliya, da Maryamu uwar Yakubu, da kuma Salome, suka sayo kayan ƙanshi, domin su je su shafa masa.

2 A ranar farko ta mako, da assussuba suka tafi kabarin, da fitowar rana sai suka isa.

3 Suna ce wa juna, “Wa zai mirgine mana dutsen nan daga bakin kabarin?”

4 Da suka ɗaga kai, suka ga, ashe, an mirgine dutsen waje ɗaya, ga shi kuwa, ƙato ne ƙwarai.

5 Suna shiga kabarin, sai suka ga wani saurayi a zaune daga dama, saye da farar riga. Sai suka firgita.

6 Shi kuwa ya ce musu, “Kada ku firgita. Yesu Banazare kuke nema, wanda aka gicciye. Ai, ya tashi, ba ya nan. Kun ga ma wurin da suka sa shi!

7 Amma ku tafi ku gaya wa almajiransa, duk da Bitrus, cewa zai riga ku zuwa ƙasar Galili, a can ne za ku gan shi, kamar yadda ya faɗa muku.”

8 Sai suka fita, suka ruga a guje daga kabarin, suna rawar jiki a ruɗe. Ba su kuma ce wa kowa kome ba, domin suna tsoro.

Yesu Ya Bayyana ga Maryamu Magadaliya

[

9 Da ya tashi da rai da wuri ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magadaliya, wadda ya fitar wa da aljannu bakwai.

10 Ita kuwa ta tafi ta faɗa wa waɗanda dā suke tare da shi, ta tarar suna baƙin ciki, suna kuka.

11 Amma da suka ji yana da rai, har ma ta gan shi, sai suka ƙi gaskatawa.

Yesu Ya Bayyana ga Almajirai Biyu

12 Bayan haka ya bayyana da wata kama ga waɗansu biyu daga cikinsu, sa’ad da suke tafiya ƙauye.

13 Suka koma suka gaya wa sauran, su ma kuwa ba su gaskata su ba.

Umarnin Yesu ga Goma Sha Ɗayan

14 Daga baya ya bayyana ga sha ɗayan nan, su kansu, sa’ad da suke cin abinci. Sai ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu da taurinkansu, domin ba su gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi ba.

15 Sai ya ce musu, “Ku tafi ko’ina a duniya, ku yi wa dukkan ‘yan adam bishara.

16 Duk wanda ya ba da gaskiya, aka kuma yi masa baftisma, zai sami ceto. Amma wanda ya ƙi ba da gaskiya za a hukunta shi.

17 Za a ga waɗannan mu’ujizai wurin masu ba da gaskiya, wato da sunana za su fitar da aljannu, za su yi magana da waɗansu baƙin harsuna,

18 za su iya ɗaukar maciji, kowace irin guba kuma suka sha, ba za ta cuce su ba ko kaɗan, za su kuma ɗora wa marasa lafiya hannu, su warke.”

An Ɗauke Yesu zuwa Sama

19 To, bayan da Ubangiji Yesu ya yi musu jawabi, aka ɗauke shi aka kai shi Sama, ya zauna dama ga Allah.

20 Su kuwa suka tafi, suka yi ta wa’azi ko’ina, Ubangiji yana taimakonsu, yana kuma tabbatar da maganarsu ta mu’ujizan nan da suke biye da maganar.]