Categories
MAT

MAT 11

‘Yan Saƙo daga Yahaya Maibaftisma

1 Da Yesu ya gama yi wa almajiransa sha biyun nan umarni, sai ya ci gaba daga nan domin ya koyar, yă kuma yi wa’azi a garuruwansu.

2 To, da Yahaya ya ji a kurkuku labarin ayyukan Almasihu, sai ya aiki almajiransa,

3 su ce masa, “Kai ne mai zuwan nan, ko kuwa mu sa ido ga wani?”

4 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da kuka ji, da abin da kuka gani.

5 Makafi suna samun gani, guragu suna tafiya, ana tsarkake kutare, kurame suna ji, ana ta da matattu, ana kuma yi wa matalauta bishara.

6 Albarka tā tabbata ga wanda ba ya tuntuɓe sabili da ni.”

7 Sun tafi ke nan, sai Yesu ya fara yi wa taro maganar Yahaya, ya ce, “Kallon me kuka je yi a jeji? Kyauron da iska take kaɗawa?

8 To, kallon me kuka fita? Wani mai adon alharini? Ai kuwa, masu adon alharini a fada suke.

9 To, don me kuka fita? Ku ga wani annabi? I, lalle kuwa, har ya fi annabi nesa.

10 Wannan shi ne wanda labarinsa yake rubuce cewa,

‘Ga shi, na aiko manzona ya riga ka gaba,

Wanda zai shirya maka hanya gabanninka.’

11 Hakika ina gaya muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya bayyana da ya fi Yahaya Maibaftisma girma. Duk da haka, wanda ya fi ƙanƙanta a Mulkin Sama ya fi shi.

12 Tun daga zamanin Yahaya Maibaftisma har ya zuwa yanzu, Mulkin Sama yana shan kutse, masu kutsawa kuwa sukan riske shi.

13 Domin dukan annabawa da Attaura sun yi annabci har ya zuwa kan Yahaya.

14 In kuma za ku karɓa, shi ne Iliya da dā ma zai zo.

15 Duk mai kunnen ji, yă ji.

16 “To, da me zan kwatanta zamanin nan? Kamar yara ne da suke zaune a kasuwa, suna kiran abokan wasansu, suna cewa,

17 ‘Mun busa muku sarewa, ba ku yi rawa ba,

Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba!’

18 “Ga shi, Yahaya ya zo, ya ƙi ciye-ciye da shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ai, yana da iska.’

19 Ga Ɗan Mutum ya zo, yana ci yana sha, sai suka ce, ‘Ga mai haɗama, mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi!’ Duk da haka hikimar Allah, ta aikinta ne ake tabbatar da gaskiyarta.”

Tsawata wa Garuruwan da Ba Su Tuba Ba

20 Sai ya fara tsawata wa garuruwan da ya yi yawancin ayyukansa na al’ajabi a cikinsu, don ba su tuba ba.

21 “Kaitonki, Korasinu! Kaitonki, Betsaida! Da mu’ujizan da aka yi a cikinku, su aka yi a Taya da Sidon, da tuni sun tuba, suna sanye da tsumma, suna hurwa da toka.

22 Amma ina gaya muku, a Ranar Shari’a, za a fi haƙurce wa Taya da Sidon a kanku.

23 Ke kuma Kafarnahum, ɗaukaka ki sama za a yi? A’a, ƙasƙantar da ke za a yi, har Hades. Da mu’ujizan da aka yi a cikinki, su aka yi a Saduma, da ta wanzu har ya zuwa yau.

24 Amma ina gaya muku, a Ranar Shari’a, za a fi haƙurce wa Saduma a kanki.”

Ku Zo Gare Ni, Ku Huta

25 A wannan lokaci sai Yesu ya ce, “Na gode maka ya Uba, Ubangijin Sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan al’amura ga masu hikima da masu basira, ka kuma bayyana su ga jahilai.

26 Hakika na gode maka ya Uba, domin wannan shi ne nufinka na alheri.

27 Kowane abu Ubana ne ya mallakar mini. Ba kuwa wanda ya san Ɗan sai dai Uban, ba kuma wanda ya san Uban sai Ɗan, da kuma wanda Ɗan ya so ya bayyana wa.

28 Ku zo gare ni dukanku masu wahala, masu fama da kaya, ni kuwa zan hutasshe ku.

29 Ku shiga bautata, ku kuma koya a gare ni, domin ni mai tawali’u ne, marar girmankai, za ku kuwa sami kwanciyar rai.

30 Domin bautata sassauƙa ce, kayana kuma marar nauyi ne.”

Categories
MAT

MAT 12

Almajirai Na Zagar Alkama Ran Asabar

1 A lokacin nan a ran Asabar, Yesu yana ratsa gonakin alkama. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara zagar alkamar suna ci.

2 Amma da Farisiyawa suka ga haka, suka ce masa, “Ka ga! Almajiranka suna yin abin da bai halatta a yi ran Asabar ba.”

3 Sai ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba sa’ad da ya ji yunwa, shi da abokan tafiyarsa?

4 Yadda ya shiga Ɗakin Allah ya ci keɓaɓɓiyar gurasar nan, wadda bai halatta ya ci ba, ko abokan tafiyarsa ma su ci ba, sai dai firistoci kaɗai?

5 Ko kuwa ba ku taɓa karantawa a Attaura ba, yadda a ran Asabar, firistoci a Haikalin sukan keta dokar Asabar, ba tare da yin wani laifi ba kuwa?

6 Ina dai gaya muku, ga wanda ya fi Haikali a nan.

7 Da kun san ma’anar wannan cewa, ‘Ni kam, zaman jinƙai nake nema a gare ku, ba hadaya ba’, da ba ku ga laifin marasa laifi ba.

8 Domin Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabar.”

Mai Shanyayyen Hannu

9 Sai ya ci gaba daga nan ya shiga majami’arsu.

10 Akwai wani mutum a nan kuwa mai shanyayyen hannu. Sai suka tambayi Yesu, suka ce, “Ya halatta a warkar a ran Asabar?” Wannan kuwa don su samu su kai ƙararsa ne.

11 Ya ce musu, “Misali, wane ne a cikinku in yana da tunkiya, ta faɗa a rami ran Asabar, ba zai kama ta ya fitar da ita ba?

12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja? Domin haka ya halatta a yi alheri a ran Asabar.”

13 Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Ya miƙa. Sai ya koma lafiyayye kamar ɗayan.

14 Amma Farisiyawa suka fita, suka yi shawara a kansa, yadda za su hallaka shi.

Zaɓaɓɓen Bara

15 Da Yesu ya gane haka, ya tashi daga nan. Sai jama’a da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su duka.

16 Sai ya kwaɓe su, kada su bayyana shi.

17 Wannan kuwa domin a cika faɗar Annabi Ishaya ne cewa,

18 “Ga barana wanda na zaɓa!

Ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi ƙwarai.

Zan sa masa Ruhuna, zai kuma sanar da al’ummai hanyar gaskiya.

19 Ba zai yi husuma ko magana sama sama ba,

Ba kuma wanda zai ji muryarsa tasa a titi.

20 Kyauron da ya tanƙwasa ba zai kakkarye shi ba,

Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba,

Har ya sa gaskiya ta ci nasara.

21 Al’ummai kuma za su sa zuciya ga sunansa.”

Yesu da Ba’alzabul

22 Sai aka kawo masa wani beben makaho mai aljan, ya kuwa warkar da shi, har beben ya yi magana, ya kuma gani.

23 Mutane duk suka yi al’ajabi, suka ce, “Shin, ko wannan shi ne Ɗan Dawuda?”

24 Amma da Farisiyawa suka ji haka sai suka ce, “Ai, da ikon Ba’alzabul sarkin aljannu kawai, wannan yake fitar da aljannu.”

25 Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ce musu, “Duk mulkin da ya rabu a kan gāba, zai lalace. Ba kuma gari ko gidan da ya rabu a kan gāba, yă ɗore.

26 In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, yā rabu a kan gāba ke nan. To, ta yaya mulkinsa zai ɗore?

27 In kuwa da ikon Ba’alzabul nake fitar da aljannu, to, ‘ya’yanku fa, da ikon wa suke fitarwa? Saboda haka su ne za su zama alƙalanku.

28 Ni kuwa in da ikon Ruhun Allah nake fitar da aljannu, ashe, Mulkin Allah ya zo muku ke nan.

29 Yaya za a iya shiga gidan ƙaƙƙarfan mutum a washe kayansa, in ba an fara ɗaure ƙaƙƙarfan mutumin ba? Sa’an nan ne za a iya washe gidansa.

30 Wanda ba nawa ba ne, gāba yake da ni. Wanda kuma ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.

31 “Don haka ina gaya muku, ā gafarta wa mutane kowane zunubi da saɓo, amma wanda ya saɓi Ruhun, ba za a gafarta masa ba.

32 Kowa ya aibata Ɗan Mutum, ā gafarta masa. Amma wanda ya aibata Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, duniya da lahira.”

Itace da ‘Ya’yansa

33 “Ko dai ku ce itace kyakkyawa ne, ‘ya’yansa kuma kyawawa, ko kuwa ku ce itace mummuna ne, ‘ya’yansa kuma munana. Don itace, da ‘ya’yansa ake gane shi.

34 Ku macizai! Yaya za ku iya yin maganar kirki, alhali kuwa ku mugaye ne? Don abin da ya ci rai, shi mutum yake faɗa.

35 Mutumin kirki kam, ta kyakkyawar taskar zuciya tasa yakan yi abin kirki, mugu kuwa, ta mummunar taskar zuciya tasa yakan yi mugun abu.

36 Ina dai gaya muku, a Ranar Shari’a duk hululun da mutum ya yi, za a bincike shi.

37 Maganarka ce za ta kuɓutar da kai, ko kuma ta hukunta ka.”

‘Yan Zamani Suna Neman Alama

38 Waɗansu malaman Attaura da Farisiyawa suka amsa masa suka ce, “Malam, muna so mu ga wata alama daga gare ka.”

39 Sai ya amsa musu ya ce, “’Yan zamani, mugaye, maciya amana, suke nema su ga wata alama! Amma ba wata alama da za a nuna musu sai dai ta Annabi Yunusa.

40 Wato, kamar yadda Yunusa ya yi kwana uku dare da rana cikin wani babban kifi, haka kuma Ɗan Mutum zai yi kwana uku dare da rana a cikin ƙasa.

41 A Ranar Shari’a mutanen Nineba za su tashi tare da mutanen zamanin nan, su kā da su, don sun tuba saboda wa’azin Yunusa. Ga kuma wanda ya fi Yunusa a nan.

42 A Ranar Shari’a Sarauniyar Kudu za ta tashi tare da mutanen zamanin nan, ta kā da su, don ta zo ne daga bangon duniya ta ji hikimar Sulemanu. Ga kuma wanda ya fi Sulemanu a nan.

Komawar Baƙin Aljan

43 “Baƙin aljan in ya rabu da mutum, sai ya bi ta wurare marasa ruwa neman hutu, amma ba ya samu.

44 Sa’an nan sai ya ce, ‘Zan koma gidana da na fito.’ Sa’ad da kuwa ya koma, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, ƙawatacce.

45 Daga nan ya je ya ɗebo waɗansu aljannu bakwai da suka fi shi mugunta. Sai su shiga su zauna a wurin. Wannan mutum ƙarshen zamansa ya fi na fari lalacewa. Haka zai zamar wa wannan mugun zamani.”

Uwar Yesu da ‘Yan’uwansa

46 Yana cikin magana da taro, sai ga Uwa tasa da ‘yan’uwansa suna tsaye a waje, suna nema su yi magana da shi.

47 Wani ya ce masa, “Ga tsohuwarka da ‘yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”

48 Sai ya amsa wa wanda ya gaya masa, ya ce, “Wace ce tsohuwata, su wane ne kuma ‘yan’uwana?”

49 Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa, ya ce, “Ga nan tsohuwata da ‘yan’uwana nan!

50 Ai, kowa ya yi abin da Ubana da yake cikin Sama yake so, shi ne ɗan’uwana, shi ne ‘yar’uwata, shi ne kuma tsohuwata.”

Categories
MAT

MAT 13

Misali da Mai Shuka

1 A ran nan Yesu ya fita daga gidan, ya je ya zauna a bakin teku.

2 Taro masu yawan gaske suka haɗu a wurinsa, har ya kai shi ga shiga jirgi, ya zauna. Duk taron kuwa suka tsaya a bakin gaci.

3 Sai ya gaggaya musu abubuwa da yawa da misalai, ya ce, “Wani mai shuka ya je shuka.

4 Yana cikin yafa iri sai waɗansu ƙwayoyi suka faɗa a hanya, sai tsuntsaye suka zo suka tsince su.

5 Waɗansu kuma suka faɗa a wuri mai duwatsu inda ba ƙasa da yawa. Nan da nan sai suka tsiro saboda rashin zurfin ƙasa.

6 Da rana fa ta ɗaga, sai suka yanƙwane, da yake ba su da saiwa sosai, suka bushe.

7 Waɗansu kuma suka faɗa cikin ƙaya, sai ƙaya ta tashi ta sarƙe su.

8 Waɗansu kuma suka faɗa a ƙasa mai kyau, suka yi tsaba, waɗansu riɓi ɗari ɗari, waɗansu sittin sittin, waɗansu kuma talatin talatin.

9 Duk mai kunnen ji, yă ji.”

Manufar Misalan

10 Sai almajiran suka zo, suka ce masa, “Me ya sa kake musu magana da misalai?”

11 Ya amsa musu ya ce, “Ku kam, an yarda muku ku san asiran Mulkin Sama, amma su ba a ba su ba.

12 Domin mai abu akan ƙara wa, har ya yalwata. Marar abu kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa.

13 Shi ya sa nake musu magana da misalai, don ko sun duba ba sa gani, ko sun saurara ba sa ji, ba sa kuma fahimta.

14 Lalle a kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa,

‘Za ku ji kam, amma ba za ku fahimta ba faufau,

Za ku kuma gani, amma ba za ku gane ba faufau,

15 Don zuciyar jama’ar nan ta yi kanta,

Sun toshe kunnuwansu,

Sun kuma runtse idanunsu,

Don kada su gani da idanunsu,

Su kuma ji da kunnuwansu,

Su kuma fahimta a zuciyarsu,

Har su juyo gare ni in warkar da su.’

16 Albarka tā tabbata ga idanunku domin suna gani, da kuma kunnuwanku domin suna ji.

17 Hakika, ina gaya muku, annabawa da adalai da yawa sun yi ɗokin ganin abin da kuke gani, amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.

Yesu Ya Ba Da Bayanin Misalin Mai Shuka

18 “To, ga ma’anar misalin mai shukar nan.

19 Wanda duk ya ji Maganar Mulki bai kuma fahimce ta ba, sai Mugun ya zo ya zăre abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya faɗa a hanya.

20 Wanda ya faɗa a wuri mai duwatsu kuwa, shi ne wanda da zarar ya ji Maganar Allah, sai ya karɓa da farin ciki.

21 Amma kuwa ba shi da tushe, rashin ƙarƙo gare shi kuma, har in wani ƙunci ko tsanani ya faru saboda Maganar, sai ya yi tuntuɓe.

22 Wanda ya faɗa cikin ƙaya kuwa, shi ne wanda ya ji Maganar, amma taraddadin duniya da jarabar dukiya sukan sarƙe Maganar, har ta zama marar amfani.

23 Wanda aka shuka a ƙasa mai kyau kuwa, shi ne wanda yake jin Maganar, ya kuma fahimce ta. Hakika shi ne mai yin amfani har ya yi albarka, wani riɓi ɗari, wani sittin, wani kuma talatin.”

Ciyayi a Cikin Alkama

24 Ya kawo musu wani misali kuma, ya ce, “Za a kwatanta Mulkin Sama da mutumin da ya yafa iri mai kyau a gonarsa.

25 Sa’ad da mutane suke barci, sai anokin gābansa ya je ya yafa irin wata ciyawa a cikin alkamar, ya tafi abinsa.

26 Da shukar ta tashi, ta yi ƙwaya, sai ciyawar ta bayyana.

27 Sai bayin maigidan suka zo, suka ce masa, ‘Maigida, ashe, ba kyakkyawan iri ka yafa a gonarka ba? To, ta yaya ke nan ta yi ciyawa?’

28 Sai ya ce musu, ‘Wani magabci ne ya yi wannan aiki.’ Bayin suka ce masa, ‘To, kana so mu je mu cire mu tara ta?’

29 Amma ya ce, ‘A’a, kada garin cire ciyawar ku tumɓuke har da alkamar ma.

30 Ku bari su zauna tare har lokacin yanka. A lokacin yanka kuma zan gaya wa masu yankan su fara yanke ciyawar su tara, su ɗaure dami dami a ƙone, alkamar kuwa su taro ta su sa a taskata.’ ”

Misali da Ƙwayar Mastad

31 Ya kawo musu wani misali, ya ce, “Mulkin Sama kamar ƙwayar mastad yake, wadda wani mutum ya je ya shuka a lambunsa.

32 Ita ce mafi ƙanƙanta a cikin ƙwayoyi, amma in ta girma, sai ta fi duk sauran ganyaye, har ta zama itace, har ma tsuntsaye su zo su yi sheƙarsu a rassanta.”

Misali na Yisti

33 Ya kuma ba su wani misali, ya ce, “Mulkin Sama kamar yisti yake, wanda wata mace ta ɗauka ta cuɗe da mudu uku na garin alkama, har duk garin ya game da yistin.”

Yesu Ya Yi Amfani da Misalai

34 Yesu ya gaya wa taro duk waɗannan abubuwa da misalai. Ba ya faɗa musu kome sai da misali.

35 Wannan kuwa domin a cika faɗar Annabi Ishaya ne cewa,

“Zan yi magana da misalai,

Zan sanar da abin da yake ɓoye tun farkon duniya.”

Yesu Ya Ba Da Bayanin Misalin Ciyayi a Cikin Alkama

36 Sai ya bar taron, ya shiga gida. Almajiransa kuma suka zo gare shi, suka ce, “Ka fassara mana misalin nan na ciyawa a gonar.”

37 Ya amsa ya ce, “Mai yafa kyakkyawan irin nan, shi ne Ɗan Mutum.

38 Gonar kuwa ita ce duniya, kyakkyawan irin nan, su ne ‘ya’yan Mulkin Allah, ciyawar kuwa, ‘ya’yan Mugun ne.

39 Magabcin nan da ya yafa ta kuwa, Iblis ne. Lokacin yankan kuwa, ƙarshen duniya ne, masu yankan kuma, mala’iku ne.

40 Kamar yadda ake tara ciyawa a ƙone ta, haka zai kasance a ƙarshen duniya.

41 Ɗan Mutum zai aiko mala’ikunsa, za su tattaro duk masu sa mutane laifi, da kuma duk masu yin mugun aiki, su fitar da su daga Mulkinsa,

42 su kuma jefa su cikin wuta mai ruruwa. Nan za su yi kuka da cizon haƙora.

43 Sa’an nan ne masu adalci za su haskaka kamar rana a Mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”

Dukiyar da Take Binne

44 “Mulkin Sama kamar dukiya yake da take binne a gona, wadda wani ya samu, ya sāke binnewa. Yana tsaka da murna tasa, sai ya je ya sayar da dukan mallaka tasa, ya sayi gonar.”

Lu’ulu’u Mai Tamanin Gaske

45 “Har wa yau kuma Mulkin Sama kamar attajiri yake, mai neman lu’ulu’u masu daraja.

46 Da ya sami lu’ulu’u ɗaya mai tamanin gaske, sai ya je ya sai da dukan mallaka tasa, ya saye shi.”

Taru

47 “Har wa yau kuma Mulkin Sama kamar taru yake da aka jefa a teku, ya kamo kifi iri iri.

48 Da ya cika, aka jawo shi gaci, aka zauna, aka tsince kyawawan kifi, aka zuba a goruna, munanan kuwa aka watsar.

49 Haka zai kasance a ƙarshen duniya. Mala’iku za su fito, su ware mugaye daga masu adalci,

50 su jefa su cikin wuta mai ruruwa. Nan za su yi kuka da cizon hakora.”

Sabuwar Dukiya da Tsohuwa

51 “Kun fahimci duk wannan?” Suka ce masa, “I.”

52 Sai ya ce musu, “To, duk malamin Attaura da ya zama almajirin Mulkin Sama, kamar maigida yake, wanda ya ɗebo dukiya sabuwa da tsohuwa daga taskarsa.”

An Ƙi Yesu a Nazarat

53 Da Yesu ya gama waɗannan misalai, sai ya tashi daga nan.

54 Da ya zo garinsu, ya koya musu a majami’arsu, har suka yi mamaki, suka ce, “Daga ina mutumin nan ya sami wannan hikima haka, da kuma mu’ujizan nan?

55 Ashe, wannan ba ɗan masassaƙin nan ba ne? Uwa tasa ba sunanta Maryamu ba? ‘Yan’uwansa kuwa ba su ne Yakubu, da Yusufu, da Saminu, da kuma Yahuza ba?

56 ‘Yan’uwansa mata ba duk tare da mu suke ba? To a ina ne mutumin nan ya sami waɗannan abu duka?”

57 Sai suka yi tuntuɓe sabili da shi. Amma Yesu ya ce musu, “Ai, annabi ba ya rasa girma sai dai a garinsu da kuma a gidansu.”

58 Bai kuma yi mu’ujizai masu yawa a can ba, saboda rashin bangaskiyarsu.

Categories
MAT

MAT 14

Mutuwar Yahaya Maibaftisma

1 A lokacin nan sarki Hirudus ya ji labarin shaharar Yesu.

2 Sai ya ce wa barorinsa, “Wannan, ai, Yahaya Maibaftisma ne, shi aka tasa daga matattu, shi ya sa mu’ujizan nan suke aiki ta wurinsa.”

3 Don dā ma Hirudus ya kama Yahaya ya ɗaure shi, ya sa shi kurkuku saboda Hirudiya, matar ɗan’uwansa Filibus.

4 Don dā ma Yahaya ya ce masa bai halatta ya zauna da ita ba.

5 Ko da yake yana son kashe shi, yana jin tsoron jama’a, don sun ɗauka shi annabi ne.

6 To, da ranar haihuwar Hirudus ta kewayo, sai ‘yar Hirudiya ta yi rawa a gaban taron, har ta gamshi Hirudus,

7 har ma ya yi mata rantsuwa zai ba ta duk abin da ta roƙa.

8 Amma da uwa tasa ta zuga ta, sai ta ce, “A ba ni kan Yahaya Maibaftisma a cikin akushi yanzu yanzu.”

9 Sai sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwa tasa da kuma baƙinsa, ya yi umarni a ba ta.

10 Ya aika aka fille wa Yahaya kai a kurkuku,

11 aka kuwa kawo kan a cikin akushi, aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa uwa tasa.

12 Almajiransa suka zo suka ɗauki gangar jikin, suka binne, suka kuma je suka gaya wa Yesu.

Ciyar da Mutum Dubu Biyar

13 Da Yesu ya ji haka sai ya tashi daga nan, ya shiga jirgi zuwa wani wuri inda ba kowa, domin ya kaɗaita. Amma da taron jama’a suka ji haka, suka fito daga garuruwa suka bi shi da ƙafa.

14 Da ya fita daga jirgin ya ga babban taron mutane. Sai ya ji tausayinsu, ya kuma warkar da marasa lafiya a cikinsu.

15 Da maraice ya yi, almajiransa suka zo gare shi, suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuwa, rana ta sunkuya. Sai ka sallami taron, su tafi ƙauyuka su saya wa kansu abinci.”

16 Yesu ya ce, “Ba lalle su tafi ba. Ku ku ba su abinci mana.”

17 Sai suka ce masa, “Ai, gurasa biyar da kifi biyu kawai muke da su a nan.”

18 Sai ya ce, “Ku kawo mini su.”

19 Sa’an nan ya umarci taron su zazzauna a ɗanyar ciyawa. Da ya ɗauki gurasa biyar ɗin da kifi biyun, sai ya ɗaga kai sama, ya yi wa Allah godiya, ya gutsuttsura gurasar, ya yi ta ba almajiransa, almajiran kuma suna bai wa jama’a.

20 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi, har suka kwashe ragowar gutsattsarin, cike da kwando goma sha biyu.

21 Waɗanda suka ci kuwa misalin maza dubu biyar ne banda mata da yara.

Yesu Yana Tafiya a kan Ruwan Teku

22 Sai ya sa almajiransa suka shiga jirgi su riga shi hayewa kafin ya sallami taron.

23 Bayan ya sallami taron, ya hau dutse shi kaɗai domin ya yi addu’a. Har magariba ta yi yana can shi kaɗai.

24 Sa’an nan kuwa jirgin yana tsakiyar teku, raƙuman ruwa mangara tasa, gama iska tana gāba da su.

25 Wajen ƙarfe uku na dare sai Yesu ya nufo su, yana tafe a kan ruwan tekun.

26 Sa’ad da kuwa almajiran suka gan shi yana tafiya a kan ruwan, sai suka firgita suka ce, “Fatalwa ce!” Suka yi kururuwa don tsoro.

27 Sai nan da nan ya yi musu magana ya ce, “Ba kome, Ni ne, kada ku ji tsoro.”

28 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ya Ubangiji, in kai ne, to, ka umarce ni in zo gare ka a kan ruwan.”

29 Ya ce, “Zo mana.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin, ya taka ruwa ya nufi gun Yesu.

30 Amma da ya ga iska ta yi ƙarfi sai ya ji tsoro. Da ya fara nutsewa sai ya yi kururuwa, ya ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”

31 Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi, ya ce masa, “Ya kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”

32 Da shigarsu jirgin iska ta kwanta.

33 Na cikin jirgin suka yi masa sujada, suka ce, “Hakika kai Ɗan Allah ne.”

Yesu Ya Warkar da Marasa Lafiya a Janisarata

34 Da suka haye, suka sauka a ƙasar Janisarata.

35 Da mutanen garin suka shaida shi, sai suka aika ko’ina a duk karkarar, aka kakkawo masa dukan marasa lafiya,

36 suka roƙe shi su taɓa ko da gezar mayafinsa ma, iyakar waɗanda suka taɓa kuwa suka warke.

Categories
MAT

MAT 15

Al’adun Shugabanni

1 Waɗansu Farisiyawa da malaman Attaura suka zo wurin Yesu daga Urushalima, suka ce,

2 “Don me almajiranka suke keta al’adun shugabanni? Domin ba sa wanke hannu kafin su ci abinci.”

3 Sai ya amsa musu ya ce, “Ku kuma don me kuke keta umarnin Allah saboda al’adunku?

4 Domin Allah ya yi umarni ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ kuma ‘Wanda ya zagi ubansa ko uwa tasa lalle a kashe shi.’

5 Amma ku kukan ce, ‘Kowa ya ce wa ubansa ko uwa tasa, “Duk abin da dā za ku samu a gare ni an ba Allah,” to, ba lalle ya girmama ubansa ba ke nan.’

6 Wato, saboda al’adunku kun bazanta Maganar Allah.

7 Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku, da ya ce,

8 ‘Al’ummar nan a baka kawai suke girmama ni,

Amma a zuci nesa suke da ni.

9 A banza suke bauta mini,

Don ka’idodin da suke koyarwa umarnin ɗan adam ne.’ ”

Abubuwan da Suke Ƙazantarwa

10 Ya kira taro ya ce musu, “Ku saurara, ku fahimta.

11 Ba abin da yake shiga mutum ta baka ne yake ƙazanta shi ba, abin da yake fita ta baka yake ƙazanta mutum.”

12 Sai almajiran suka zo suka ce masa, “Ka san Farisiyawa sun ji haushi da suka ji maganan nan?”

13 Ya amsa ya ce, “Duk dashen da ba Ubana da yake Sama ne ya dasa ba, za a tumɓuke shi.

14 Ƙyale su kawai, makafin jagora ne. In kuwa makaho ya yi wa makaho jagora, ai, duk biyu sai su faɗa a rami.”

15 Amma Bitrus ya ce masa, “A yi mana fassarar misalin nan.”

16 Yesu ya ce, “Ku ma, ashe, har yanzu ba ku fahimta?

17 Ashe, ba ku gane ba, kome ya shiga mutum ta baka, cikinsa ya shiga, ta haka kuma zai fice?

18 Amma abin da ya fito ta baka, daga zuci yake, shi ne kuwa yake ƙazantar da mutum.

19 Don daga zuci mugayen tunani suke fitowa, kamar su kisankai, da zina, da fasikanci, da sata, da shaidar zur, da yanke.

20 Waɗannan suke ƙazantar da mutum. Amma a ci da hannu marar wanki ba ya ƙazantar da mutum.”

Bangaskiyar Mace Bakan’aniya

21 Yesu ya tashi daga nan, ya tafi zuwa ƙasar Taya da Sidon.

22 Ga wata Bakan’aniya mutuniyar ƙasar, ta zo, ta ɗaga murya ta ce, “Ya Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayina. Wani aljani ya bugi ‘yata, ba yadda take.”

23 Amma bai ce da ita kanzil ba. Sai almajiransa suka zo suka roƙe shi, suka ce, “Sallame ta mana, tana binmu tana cika mana kunne da kuka.”

24 Ya amsa ya ce, “Ni wurin ɓatattun tumakin jama’ar Isra’ila kaɗai aka aiko ni.”

25 Amma ta zo ta durƙusa a gabansa, ta ce, “Ya Ubangiji, ka taimake ni mana!”

26 Ya amsa ya ce, “Ai, bai kyautu a bai wa karnuka abincin ‘ya’ya ba.”

27 Sai ta ce, “I, haka ne, ya Ubangiji, amma ai, karnuka sukan ci suɗin ‘ya’ya.”

28 Sai Yesu ya amsa mata ya ce, “Kai, uwargida, bangaskiyarki da yawa take! Yă zamar miki yadda kike so.” Nan take ‘ya tata ta warke.

Yesu Ya Warkar da Mutane Masu Yawa

29 Yesu ya tashi daga nan, ya bi ta bakin Tekun Galili. Sai ya hau dutse ya zauna a can.

30 Taro masu yawan gaske suka zo wurinsa, suka zazzo da guragu, da masu dungu, da makafi, da bebaye, da kuma waɗansu da yawa, suka ajiye su a gabansa, ya kuwa warkar da su.

31 Har jama’ar suka yi ta al’ajabi da ganin bebaye suna magana, masu dungu sun sami gaɓoɓinsu, guragu na tafiya, makafi kuma suna gani, duk suka ɗaukaka Allah na Isra’ila.

Ciyar da Mutum Dubu Huɗu

32 Yesu ya kira almajiransa, ya ce, “Ina jin tausayin wannan taro, don yau kwanansu uku ke nan a guna ba su da wani abinci. Ba na kuwa so in sallame su da yunwa haka, kada su kasa a hanya.”

33 Sai almajiran suka ce masa, “Ina za mu samo gurasa a jeji haka da za ta isa ciyar da ƙasaitaccen taro haka?”

34 Yesu ya ce musu, “Gurasa nawa suke gare ku?” Suka ce, “Bakwai, da ƙananan kifaye kaɗan.”

35 Sai ya umarci taron su zauna a ƙasa.

36 Da ya ɗauki gurasa bakwai ɗin da kifayen nan, ya yi godiya ga Allah, sai ya gutsuttsura, ya yi ta ba almajiran, almajiran kuma na, bai wa jama’a.

37 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi, har suka kwashe ragowar gutsattsarin, cike da manyan kwanduna bakwai.

38 Waɗanda suka ci kuwa maza dubu huɗu ne, banda mata da yara.

39 Da ya sallami taron ya shiga jirgi ya tafi ƙasar Magadan.

Categories
MAT

MAT 16

Neman Alama

1 Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo suka roƙe shi ya nuna musu wata alama daga Sama, domin su gwada shi.

2 Ya amsa musu ya ce, “In magariba ta yi, kuka ga sama ta yi ja, kukan ce, ‘Aha, gari zai yi sarari.’

3 Da safe kuma in kun ga sama ta yi ja, ta kuma gama gari, kukan ce, ‘Yau kam, za a yi hadiri.’ Kuna iya gane yanayin sararin sama, amma ba kwa iya gane alamun zamanin nan.

4 ‘Yan zamani, mugaye, maciya amana, suke nema su ga wata alama, amma ba wata alamar da za a nuna musu, sai dai ta Yunusa.” Sai ya bar su ya tafi.

Yistin Farisiyawa da Sadukiyawa

5 Da almajiran suka isa wancan ƙetare, ashe, sun manta ba su kawo gurasa ba.

6 Sai Yesu ya ce musu, “Ku kula, ku yi hankali da yistin Farisiyawa da na Sadukiyawa.”

7 Sai suka yi magana da juna suka ce, “Ba mu kawo gurasa ba fa!”

8 Da Yesu ya lura da haka sai ya ce, “Ya ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da juna a kan ba ku zo da gurasa ba?

9 Ashe, har yanzu ba ku gane ba? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka ɗauka?

10 Ko kuma gurasan nan bakwai na mutum dubu huɗu, manyan kwanduna nawa kuka ɗauka?

11 Yaya kuka kasa ganewa? Ba zancen gurasa na yi ba, sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da na Sadukiyawa.”

12 Sa’an nan ne fa suka fahimta cewa, ba ce musu ya yi, su yi hankali da yistin gurasa ba, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da ta Sadukiyawa.

Hurcin Bitrus a kan Yesu

13 To, da Yesu ya shiga ƙasar Kaisariya Filibi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke cewa, Ɗan Mutum yake?”

14 Sai suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yahaya Maibaftisma, waɗansu kuwa Iliya, waɗansu kuma Irmiya, ko kuwa ɗaya daga cikin annabawa.”

15 Ya ce musu, “Amma ku fa, wa kuke cewa, nake?”

16 Sai Bitrus ya amsa, ya ce, “Kai ne Almasihu, Ɗan Allah Rayayye.”

17 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai mai albarka ne, Saminu, ɗan Yunusa! Domin ba ɗan adam ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin Sama.

18 Ina dai gaya maka, kai ne Bitrus, a kan dutsen nan ne zan gina ikilisiyata, wadda ikon Hades ba zai rinjaye ta ba.

19 Zan ba ka mabuɗan Mulkin Sama. Kome ka ƙulla a duniya, zai zama abin da aka riga ƙullewa a Sama ne. Kome ka warware a duniya, zai zama abin da aka riga warwarewa a Sama ne.”

20 Sai ya kwaɓi almajiransa ƙwarai kada su gaya wa kowa shi ne Almasihu.

Yesu Ya Faɗi Irin Mutuwar da Zai Yi

21 Tun daga lokacin nan Yesu ya fara bayyana wa almajiransa, lalle ne ya tafi Urushalima, ya sha wuya iri iri a hannun shugabanni da manyan firistoci da malaman Attaura, har a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.

22 Sai Bitrus ya ja shi waje ɗaya, ya fara tsawata masa, ya ce, “Allah ya sawwaƙe, ya Ubangiji! Wannan har abada ba zai same ka ba!”

23 Amma Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Ka yi nesa da ni, ya Shaiɗan! Tarko kake a gare ni. Ba ka tattalin al’amuran Allah, sai dai na mutane.”

24 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, sai ya ƙi kansa, ya ɗauki gicciyensa, ya bi ni.

25 Duk mai son tattalin ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi.

26 Me mutum ya amfana in ya sami duniya duka a bakin ransa? Me kuma mutum zai iya bayarwa ya fanshi ransa?

27 Domin Ɗan Mutum zai zo da ɗaukakar Ubansa tare da mala’ikunsa. A sa’an nan ne zai sāka wa kowane mutum gwargwadon aikinsa.

28 Hakika, ina gaya muku, akwai waɗansu tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba, sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin Mulkinsa.”

Categories
MAT

MAT 17

Sākewar Kamanninsa

1 Bayan kwana shida sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yakubu, da ɗan’uwansa Yahaya, ya kai su a kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai.

2 Sai kamanninsa suka sāke a gabansu, fuskarsa ta yi annuri kamar hasken rana, tufafinsa kuma suka yi fari fat suna haske.

3 Ga shi, Musa da Iliya sun bayyana a gare su, suna magana da Yesu.

4 Sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Ya Ubangiji, ya kyautu da muke nan wurin. In kana so, sai in kafa bukkoki uku a nan, ɗaya taka, ɗaya ta Musa, ɗaya kuma ta Iliya.”

5 Yana magana ke nan sai ga wani gajimare mai haske ya zo ya rufe su. Aka kuma ji wata murya daga cikin gajimaren, ta ce, “Wannan shi ne Ɗana ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi ƙwarai. Ku saurare shi.”

6 Da almajiran suka ji haka, sai suka faɗi ƙasa, tsoro ya kama su.

7 Sai Yesu ya zo ya taɓa su, ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”

8 Da suka ɗaga kai ba su ga kowa ba, sai Yesu kaɗai.

9 Suna cikin gangarowa daga dutsen, sai Yesu ya kwaɓe su ya ce, “Kada ku gaya wa kowa abin da kuka gani, sai an ta da Ɗan Mutum daga matattu.”

10 Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, yaya malaman Attaura suke cewa, lalle ne Iliya ya riga zuwa?”

11 Ya amsa ya ce, “Lalle Iliya zai zo ne, zai kuwa raya dukan abubuwa.

12 Amma ina gaya muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa san shi ne ba, har ma suka yi masa abin da suka ga dama. Haka kuma Ɗan Mutum zai sha wuya a hannunsu.”

13 Sa’an nan ne almajiran suka gane, ashe, zancen Yahaya Maibaftisma yake yi musu.

Yesu Ya Warkar da Yaro Mai Beben Aljan

14 Da suka isa wurin taro, sai wani mutum ya zo gare shi, ya durƙusa a gabansa, ya ce,

15 “Ya Ubangiji, ka ji tausayin ɗana, yana farfaɗiya, yana shan wuya ƙwarai, sau da yawa yakan faɗa wuta da kuma ruwa.

16 Na kuwa kai shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”

17 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku marasa bangaskiya, kangararru na wannan zamani! Har yaushe zan zama da ku? Har yaushe kuma zan jure muku? Ku kawo mini shi nan.”

18 Sai Yesu ya tsawata masa, aljanin kuma ya rabu da shi. Nan take yaron ya warke.

19 Sa’an nan almajiran suka zo wurin Yesu a keɓe, suka ce, “Me ya sa mu muka kasa fitar da shi?

20 Ya ce musu, “Saboda ƙarancin bangaskiyarku. Domin hakika ina gaya muku, da kuna da bangaskiya, ko misalin ƙwayar mustad, da za ku ce wa dutsen nan, ‘Kawu daga nan, ka koma can!’, sai kuwa ya kawu. Ba kuwa abin da zai gagare ku. [

21 Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu’a da azumi.]”

Yesu Ya Sāke Faɗar Irin Mutuwar da Zai Yi

22 Tun suna ƙasar Galili, sai Yesu ya ce musu, “Za a ba da Ɗan Mutum ga mutane,

23 za su kuwa kashe shi, a rana ta uku kuma za a tashe shi.” Sai duk tsananin baƙin ciki ya rufe su.

Ba Da Gudunmawar Haikali

24 Da suka zo Kafarnahum masu karɓar rabin shekel na gudunmawar Haikali suka je wurin Bitrus, suka ce, “Malaminku yana ba da gudunmawar?”

25 Ya ce, “I, yakan bayar.” Da ya dawo gida kuma, sai Yesu ya fara yi masa magana ya ce, “Me ka gani, Bitrus? Wurin wa sarakunan duniya suke karɓar kuɗin fito ko haraji, a wurin ‘ya’yansu, ko kuwa daga wurin waɗansu?”

26 Sa’ad da kuma ya ce, “Daga wurin waɗansu,” sai Yesu ya ce masa, “Wato, ‘ya’yan an ɗauke musu ke nan.

27 Duk da haka, don kada mu ba su haushi, ka je teku ka yi fatsa, kifin da ka fara kamawa kuwa shi za ka ɗauka. In ka buɗe bakinsa za ka sami shekel guda a ciki. To, sai ka ɗauki shekel ɗin nan ka kai musu, wato, nawa da naka.”

Categories
MAT

MAT 18

Wane ne Mafi Girma?

1 A lokacin nan almajirai suka zo wurin Yesu, suka ce, “Wa ya fi girma duka a Mulkin Sama?”

2 Sai ya kira wani ƙaramin yaro, ya sa shi a tsakiyarsu,

3 ya ce, “Hakika, ina gaya muku, in ba kun juyo kun zama kamar ƙananan yara ba, har abada ba za ku shiga Mulkin Sama ba.

4 Duk wanda ya ƙasƙantar da kansa kamar ɗan yaron nan, ai, shi ne mafi girma a Mulkin Sama.

5 “Wanda duk ya karɓi ƙaramin yaro ɗaya kamar wannan saboda sunana, Ni ya karɓa.

6 Amma fa duk wanda ya sa ɗaya daga cikin waɗannan ‘yan yara masu gaskatawa da ni ya yi laifi, zai fiye masa a rataya babban dutsen niƙa a wuyarsa, a kuma nutsar da shi a zurfin teku.”

Sanadodin Yin Zunubi

7 “Kaiton duniya saboda sanadodin tuntuɓe! Lalle sanadodin tuntuɓe ba su da makawa, duk da haka kaiton wanda shi ne sanadin!

8 In kuwa hannunka ko ƙafarka suna sa ka laifi, to, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai dungu ko da gurguntaka, da a jefa ka madawwamiyar wuta da hannu biyu ko ƙafa biyu.

9 In kuwa idonka yana sa ka laifi, to ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da a jefa ka Gidan Wuta da ido biyu.”

Misali na Ɓatacciyar Tunkiya

10 “Ku dai lura, kada ku raina ɗaya daga cikin waɗannan ‘yan yara. Ina gaya muku, mala’ikunsu a Sama kullum suna duban fuskar Ubana da yake cikin Sama.[

11 Domin Ɗan Mutum ya zo ne musamman ceton abin da ya ɓata.]

12 To, me kuka gani? In wani na da tumaki ɗari, ɗayarsu ta băce, ashe, ba zai bar tasa’in da taran nan a gindin dutse, ya je neman wadda ta ɓăce ba?

13 In kuwa ya samo ta, labudda, ina gaya muku, ai, farin cikin da yake yi a kanta ya fi na tasa’in da taran nan da ba su taɓa ɓăcewa ba.

14 Haka ma, ba nufin Ubanku da yake cikin Sama ba ne ɗaya daga cikin waɗannan ‘yan yara ya hallaka.”

Ɗan’uwan da Ya Yi Laifi

15 “In ɗan’uwanka ya yi maka laifi, sai ka je, ka gaya masa laifinsa, kai da shi, ku kaɗai. In ya saurare ka, to, kā maido da ɗan’uwanka ke nan.

16 In kuwa bai saurare ka ba, sai ka tafi da mutum ɗaya ko biyu, don a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku.

17 In kuma ya ƙi sauraronsu, sai ka shaida wa ikilisiya. In kuma har ya ƙi sauraron ikilisiyar, ka maishe shi kamar bare, ko mai karɓar haraji.”

Kullewa da Warwarewa

18 “Hakika, ina gaya muku, kome kuka ƙulla a duniya, zai zama abin da aka riga ƙullewa a Sama ne. Kome kuka warware a duniya, zai zama abin da aka riga warwarewa a Sama ne.

19 Har wa yau dai ina gaya muku, in mutum biyu daga cikinku, ra’ayinsu ya zo ɗaya a nan duniya a kan wani abin da za su roƙa, Ubana kuwa da yake Sama zai yi musu shi.

20 Gama kuwa inda mutum biyu ko uku suka taru saboda sunana, ni ma ina nan a tsakiyarsu.”

Misali na Bawa Wanda Bai Yafe Ba

21 Sai Bitrus ya matso ya ce masa, “Ya Ubangiji, sau nawa ɗan’uwana zai yi mini laifi in yafe masa? Har sau bakwai?”

22 Yesu ya ce masa, “Ba sau bakwai kawai na ce maka ba, sai dai bakwai har saba’in.

23 “Saboda haka za a misalta Mulkin Sama da wani sarkin da yake so ya yi ƙididdigar dukiyarsa da yake hannun bayinsa.

24 Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wanda yake bi talanti dubu goma bashi.

25 Da yake ya gagara biya, sai ubangidansa ya yi umarni a sayar da shi da mata tasa da ‘ya’yansa da kuma duk abin da ya mallaka, a biya kuɗin.

26 Sai bawan ya faɗi a gabansa ya yi masa ladabi, ya ce, ‘Ya ubangida, ka yi mini haƙuri, zan biya ka tsaf.’

27 Saboda tausayin bawan nan ubangidansa ya sake shi, ya yafe masa bashin.

28 Amma wannan bawa, da fitarsa sai ya tarar da wani abokin bautarsa, wanda yake bi dinari ɗari bashi. Ya cafi wuyarsa, ya ce, ‘Biya ni abin da nake binka.’

29 Sai abokin bautarsa ya faɗi a gabansa, ya yi ta roƙonsa ya ce, ‘Ka yi mini haƙuri, ai, zan biya ka.’

30 Amma ya ƙi, ya kuma je ya sa shi a kurkuku, har yā biya bashin.

31 Da abokan bautarsa suka ga abin da ya faru, suka yi baƙin ciki gaya, har suka je suka gaya wa ubangidansu duk abin da ya gudana.

32 Sai ubangiji nasa ya kira shi, ya ce masa, ‘Kai mugun bawa ne! Na yafe maka duk bashin nan saboda ka roƙe ni,

33 ashe, bai kyautu kai ma ka ji tausayin abokin bautarka, kamar yadda na ji tausayinka ba?’

34 Ubangijinsa ya yi fushi, ya ba da shi ga masu azabtarwa har yă biya duk bashin da ake binsa.

35 Haka kuma Ubana da yake Sama zai yi da ko wannenku, in ba ku yafe wa ‘yan’uwanku da zuciya ɗaya ba.”

Categories
MAT

MAT 19

Koyarwar Yesu a kan Kisan Aure

1 To, da Yesu ya gama duk wannan magana, sai ya bar ƙasar Galili, ya shiga ta Yahudiya, wadda take ƙetaren Kogin Urdun.

2 Taro mai yawan gaske suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can.

3 Sai waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa su gwada shi, suka ce, “Halal ne mutum ya saki mata tasa a kan kowane dalili?”

4 Ya amsa ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karantawa ba, cewa, wanda ya halicce su tun farko, dā ma ya yi su, namiji da tamata?”

5 Ya kuma ce, “Don haka fa sai mutum ya bar uwa tasa da ubansa, ya manne wa mata tasa. Haka su biyun nan su zama jiki guda.

6 Har nan gaba su zama ba jiki biyu ba ne, ɗaya ne. Abin da Allah fa ya gama, kada mutum ya raba.”

7 Sai suka ce masa, “To, don me Musa ya yi umarni a ba da takardar kisan aure, a kuma saki matar?”

8 Ya ce musu, “Don taurinkanku ne Musa ya yardar muku ku saki matanku, amma ba haka yake ba tun farko.

9 Ina kuma gaya muku, kowa ya saki mata tasa, in ba a kan laifin zina ba, ya kuma auri wata, ya yi zina ke nan. Wanda ma ya auri sakakkiya, ya yi zina.”

10 Sai almajiran suka ce masa, “In ko haka tsakanin mutum da mata tasa yake, ashe ma, rashin yin aure ya fi amfani.”

11 Amma ya ce musu, “Ba duk mutum ne zai iya ɗaukar maganar nan ba, sai dai waɗanda aka yardar wa.

12 Akwai waɗanda aka haifa babanni, akwai waɗanda mutane ne suka mai da su babanni. Akwai kuma waɗanda suka mai da kansu babanni domin ƙaunar Mulkin Sama. Duk mai iya ɗaukar maganar nan, yă ɗauka.”

Yesu Ya Sa wa ‘Yan Yara Albarka

13 Sa’an nan aka kawo masa yara ƙanana domin ya ɗora musu hannu, ya yi musu addu’a, amma almajiran suka kwaɓe su.

14 Yesu kuwa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai, Mulkin Sama na irinsu ne.”

15 Sai ya ɗora musu hannu ya yi tafiyarsa.

Saurayi Mai Dukiya

16 Sai ga wani ya matso wurinsa, ya ce, “Malam, wane aiki nagari ne da lalle zan yi in sami rai madawwami?”

17 Sai ya ce masa, “Don me kake tambayata a kan abin da yake nagari? Ai, Managarci ɗaya ne. In kuwa kana so ka sami wannan rai, to, ka kiyaye umarnan nan.”

18 Sai ya ce masa, “Waɗanne?” Yesu ya ce, “Kada ka yi kisankai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi shaidar zur.

19 Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, ka kuma ƙaunaci ɗan’uwanka kamar kanka.”

20 Saurayin ya ce masa, “Ai, duk na kiyaye waɗannan, me kuma ya rage mini?”

21 Yesu ya ce masa, “In kana so ka zama kammalalle, sai ka je ka sayar da duk mallakarka, ka bai wa gajiyayyu, ka sami wadata a Sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”

22 Da saurayin nan ya ji haka, sai ya tafi, yana baƙin ciki, don yana da arziki ƙwarai.

23 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Hakika, ina gaya muku, da wuya mai arziki ya sami shiga Mulkin Sama.

24 Har wa yau ina gaya muku, zai fiye wa raƙumi sauƙi ya bi ta kafar allura, da mai arziki ya shiga Mulkin Allah.”

25 Da almajiran suka ji haka, sai suka yi mamaki ƙwarai da gaske, suka ce, “To, in haka ne, wa zai sami ceto ke nan?”

26 Amma Yesu ya dube su, ya ce musu, “Ga mutane kam, ba mai yiwuwa ba ne, amma gun Allah kowane abu mai yiwuwa ne.”

27 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “To, ai, ga shi mun bar kome, mun bi ka. Me za mu samu ke nan?”

28 Yesu ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, a sabon zamani, sa’ad da Ɗan Mutum ya zauna a maɗaukakin kursiyinsa, ku da kuka bi ni, ku ne kuma za ku zauna a kursiyi goma sha biyu, kuna hukunta kabilan nan goma sha biyu na Isra’ila.

29 Kowa ya bar gidaje, ko ‘yan’uwa mata, ko ‘yan’uwa maza, ko uwa, ko uba, ko ‘ya’ya, ko gonaki, saboda sunana, zai sami ninkinsu ɗari, ya kuma gāji rai madawwami.

30 Da yawa na farko za su koma na ƙarshe, na ƙarshe kuma za su zama na farko.”

Categories
MAT

MAT 20

Ma’aikata a Garkar Inabi

1 “Mulkin Sama kamar wani maigida yake, wanda ya fita da sassafe ya ɗauki ma’aikata don aikin garkarsa ta inabi.

2 Da ya yi lada da su a kan dinari guda a yini, sai ya tura su garkarsa.

3 Wajen ƙarfe tara kuma da ya fita, sai ya ga waɗansu suna zaman banza a bakin kasuwa.

4 Sai ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi garkata, zan kuwa biya ku abin da yake daidai.’ Sai suka tafi.

5 Da ya sāke fita wajen tsakar rana, da kuma azahar, ya sāke yin haka dai.

6 Wajen la’asar kuma ya fita ya sami waɗansu a tsaitsaye, ya ce musu, ‘Don me kuke zaman banza yini zubur?’

7 Sai suka ce masa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’ Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi garkata.’

8 Da magariba ta yi, mai garkar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kirawo ma’aikatan, ka biya su hakkinsu, ka fara daga na ƙarshe har zuwa na farko.’

9 Da waɗanda aka ɗauka wajen la’asar suka zo, sai ko wannensu ya sami dinari guda.

10 To, da na farkon suka zo suka zaci za su sami fiye da haka. Amma su ma aka ba ko wannensu dinari guda.

11 Da suka karɓa sai suka yi ta yi wa maigidan gunaguni,

12 suna cewa, ‘Na bayan nan, ai, aikin sa’a guda kawai suka yi, ka kuwa daidaita mu, mu da muka yini zubur muna shan wahala da zafin rana.’

13 Sai ya amsa wa ɗayansu ya ce, ‘Abokina, ai, ban cuce ka ba. Ashe, ba mu yi lada da kai a kan dinari guda ba?

14 Sai ka karɓi halalinka ka tafi. Ni ne na ga damar ba waɗannan na ƙarshe daidai da yadda na ba ka.

15 Ashe, ba ni da ikon yin abin da na ga dama da abin da yake mallakata? Ko kuwa kana jin haushin alherina ne?’

16 Saboda haka na ƙarshe za su zama na farko, na farko kuma za su koma na ƙarshe.”

Yesu kuma Ya Sāke Faɗar Irin Mutuwar da Zai Yi

17 Yesu na tafiya Urushalima, ya ɗauki almajiran nan goma sha biyu waje ɗaya. Suna tafiya ke nan sai ya ce musu,

18 “To, ga shi, za mu Urushalima, za a kuma ba da Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman Attaura, za su kuwa yi masa hukuncin kisa,

19 su bashe shi ga al’ummai, su yi masa ba’a, su yi masa bulala, su kuma gicciye shi. A rana ta uku kuma za a tashe shi.”

Roƙon da Mahaifiyar Yakubu da Yahaya ta Yi

20 Sa’an nan uwar ‘ya’yan Zabadi ta matso wurinsa tare da ‘ya’yanta, ta durƙusa a gabansa, ta roƙe shi wani abu.

21 Sai ya ce mata, “Me kike bukata?” Ta ce masa, “Ka yi umarni waɗannan ‘ya’yana biyu su zauna, ɗaya a damanka, ɗaya a hagunka, a mulkinka.”

22 Amma Yesu ya amsa ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Kwa iya shan ƙoƙon da ni zan sha?” Suka ce masa, “Ma iya.”

23 Sai ya ce musu, “Lalle kwa sha ƙoƙona, amma zama a damana da haguna, ba nawa ba ne da zan bayar, ai, na waɗanda Ubana ya riga ya shirya wa ne.”

24 Da almajiran nan goma suka ji haka, sai suka ji haushin ‘yan’uwan nan biyu.

25 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani sarakunan al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.

26 Ba haka zai zama a tsakaninku ba. Amma duk wanda yake son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku.

27 Wanda duk kuma yake so ya shugabance ku, lalle ne ya zama bawanku,

28 kamar yadda Ɗan Mutum ma ya zo ba domin a bauta masa ba sai dai domin shi ya yi bautar, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”

Makafi Biyu Sun Sami Ganin Gari

29 Suna fita daga Yariko ke nan, sai wani babban taro ya bi shi.

30 Ga mutum biyu makafi zaune a bakin hanya. Da suka ji dai Yesu ne yake wucewa, sai suka ɗaga murya suka ce, “Ya Ubangiji, ka ji tausayinmu, ya Ɗan Dawuda!”

31 Jama’a suka kwaɓe su su yi shiru. Amma sai ƙara ɗaga murya suke yi ƙwarai da gaske, suna cewa, “Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai, ya Ɗan Dawuda!”

32 Sai Yesu ya tsaya, ya yi kiransu ya ce, “Me kuke so in yi muku?”

33 Suka ce masa, “Ya Ubangiji, mu dai mu sami gani!”

34 Domin tausayi, sai Yesu ya taɓa idanunsu, nan take suka gani, suka bi shi.