Categories
NAH

NAH 1

Fushin Ubangiji a kan Nineba

1 Jawabi a kan Nineba ke nan, a littafin wahayin Nahum na Elkosh.

2 Ubangiji Allah mai kishi ne, mai

sakayya,

Ubangiji mai sakayya ne, mai

hasala.

Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan

maƙiyansa.

Yana tanada wa maƙiyansa fushi.

3 Ubangiji mai jinkirin fushi ne,

Mai Iko Dukka.

Ubangiji ba zai kuɓutar da mai laifi

ba.

Hanyarsa tana cikin guguwa da cikin

hadiri,

Gizagizai su ne ƙurar ƙafafunsa.

4 Yakan tsauta wa teku, sai teku ta

ƙafe.

Yakan busar da koguna duka.

Bashan da Karmel sukan bushe,

Tohon Lebanon yakan yanƙwane.

5 Duwatsu sukan girgiza a gabansa,

Tuddai kuma su narke.

Duniya ta murtsuke a gabansa,

Da dukan mazauna a cikinta.

6 Wa zai iya tsaya wa fushinsa?

Wa kuma zai iya daurewa da

hasalarsa?

Yana zuba hasalarsa mai kama da

wuta,

Duwatsu sukan farfasu a gabansa.

7 Ubangiji mai alheri ne,

Shi mafaka ne a ranar wahala.

Ya san waɗanda suke fakewa a gare

shi.

8 Zai shafe maƙiyansa da ambaliyar

ruwa,

Zai kuma runtumi maƙiyansa zuwa

cikin duhu.

9 Me kuke ƙullawa game da Ubangiji?

Ubangiji zai wofintar da abin nan da

kuke ƙullawa,

Sau ɗaya kawai zai hallaka ku.

10 Suna maye da abin shansu,

Za su ƙone kamar sarƙaƙƙiyar ƙaya,

Da busasshiyar ciyawa.

11 Daga cikinki wani ya fito,

Wanda ya ƙulla wa Ubangiji

makirci,

Ya ƙulla shawara marar amfani.

12 Ni Ubangiji na ce,

“Ko da yake suna da ƙarfi, suna

kuma da yawa,

Za a datse su, su ƙare.

Ko da yake na wahalar da kai,

Ba zan ƙara wahalar da kai ba.

13 Yanzu zan karya karkiyarsa daga

wuyanka,

Zan kuma tsinke sarƙarta.”

14 Ubangiji ya riga ya yi umarni a

kanka cewa,

“Sunanka ba zai ci gaba ba,

Zan farfashe sassaƙaƙƙun siffofi

Da siffofi na zubi daga gidan

gumakanka.

Zan shirya maka kabari, gama kai

rainanne ne.”

Labarin Fāɗuwar Nineba

15 Duba a kan duwatsu, ƙafafun

wanda yake kawo albishir,

Wanda yake shelar salama!

Ya Yahuza, ka yi bikin idodinka,

Ka kuma cika wa’adodinka.

Gama mugun ba zai sāke zuwa ya yi

gāba da kai ba,

An datse shi ƙaƙaf.

Categories
NAH

NAH 2

1 Wanda yake farfashewa ya auko

maka,

Sai ka sa mutane a kagara, a yi

tsaron hanya,

Ka yi ɗamara, ka tattaro ƙarfinka

duka.

2 Gama Ubangiji zai mayar wa

Yakubu da darajarsa kamar ta

Isra’ila.

Ko da masu washewa sun washe su,

Sun kuma lalatar da rassan inabinsu.

3 Garkuwoyin jarumawansa jajaye ne,

Sojojinsa kuma suna saye da mulufi.

Da ya shirya tafiya,

Karusai suna walƙiya kamar

harshen wuta,

Ana kaɗa mashi da bantsoro.

4 Karusai sun zabura a tituna a

haukace.

Suna kai da kawowa a dandali,

Suna walwal kamar jiniya,

Suna sheƙawa a guje kamar

walƙiya.

5 Sai aka kira shugabanni,

Suka zo a guje suna tuntuɓe,

Suka gaggauta zuwa garu,

Suka kafa kagara.

6 An buɗe ƙofofin kogi,

Fāda ta rikice.

7 An tsiraita sarauniya, an tafi da ita,

‘Yan matanta suna makoki, suna

kuka kamar kurciyoyi,

Suna bugun ƙirjinsu.

8 Nineba tana kama da tafki wanda

ruwansa yake zurarewa,

Suna cewa, “Tsaya, tsaya,”

Amma ba wanda ya waiga.

9 A washe azurfa!

A washe zinariya!

Dukiyar ba ta da adadi,

Akwai dukiya ta kowane iri.

10 Nineba ta halaka! ta lalace, ta zama

kufai!

Zukata sun narke, gwiwoyi suna

kaɗuwa!

Kwankwaso yana ciwo,

Fuskoki duka sun kwantsare!

11 Ina kogon nan na zakoki,

Inda aka ciyar da ‘ya’yan zaki,

Inda zaki da zakanya da

kwiyakwiyansu sukan tafi,

Su tsere daga fitina?

12 Zaki ya kashe abin da ya ishi

kwiyakwiyansa.

Ya kaso wa zakanyarsa abin da ya

ishe ta.

Ya cika kogonsa da ganima.

Ragargajewar Nineba

13 “Ga shi, ina gāba da ke. Ni Ubangiji

Allah Mai Runduna na faɗa.

Zan ƙone karusanki,

Takobi kuwa zai karkashe sagarun

zakokinki,

Zan hana miki ganima a duniya.

Ba za a ƙara jin muryoyin jakadunki

ba.”

Categories
NAH

NAH 3

1 Kaiton birnin jini,

Wanda yake cike da ƙarairayi da

ganima,

Da waso kuma ba iyaka!

2 Ku ji amon bulala da kwaramniyar

ƙafafu,

Da sukuwar doki da girgizar karusai!

3 Sojojin dawakai suna kai sura,

Takuba suna walƙiya, māsu suna

ƙyalƙyali.

Ga ɗumbun kisassu, da tsibin

gawawwaki,

Matattu ba su ƙidayuwa,

Suna tuntuɓe a kan gawawwaki!

4 Ya faru saboda yawan karuwancin

Nineba kyakkyawa mai daɗin

baki,

Wadda ta ɓad da al’umman duniya

da karuwancinta,

Ta kuma ɓad da mutane da daɗin

bakinta.

5 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ina

gāba da ke,

Zan kware fatarinki a idonki,

Zan sa al’ummai da mulkoki su dubi

tsiraicinki.

6 Zan watsa miki ƙazanta,

In yi miki wulakanci,

In maishe ki abin raini.

7 Dukan waɗanda za su dube ki

Za su ja da baya su ce,

‘Nineba ta lalace, wa zai yi kuka

dominta?’

A ina zan samo miki waɗanda za su

ta’azantar da ke?”

8 Kin fi No ne?

Wadda take a bakin Nilu,

Wadda ruwa ya kewaye ta?

Teku ce kagararta.

Ruwa ne kuma garunta.

9 Habasha da Masar su ne ƙarfinta

marar iyaka,

Fut da Libiya su ne kuma

mataimakanta.

10 Duk da haka an tafi da ita, an kai ta

cikin bauta.

An fyaɗa ƙanananta a ƙasa,

An yi kacakaca da su a kowace

mararraba.

An jefa kuri’a a kan manyan

mutanenta,

Aka ɗaure dukan manyan mutanenta

da sarƙoƙi.

11 Ke Nineba kuma za ki bugu,

Za a ɓoye ki.

Za ki nemi mafaka a wurin maƙiyinki.

12 Dukan kagaranki suna kama da

itatuwan ɓaure,

Waɗanda ‘ya’yansu suka harba.

Da an girgiza sai su faɗo a bakin mai

sha.

13 Sojojinki kamar mata suke a

tsakiyarki!

An buɗe wa maƙiyanki ƙofofin

ƙasarki.

Wuta za ta cinye madogaran

ƙofofinki.

14 Ki tanada ruwa domin za a kewaye

ki da yaƙi!

Ki ƙara ƙarfin kagaranki!

Ki tafi kududdufi, ki kwaɓa laka!

Ki ɗauki abin yin tubali!

15 A can wuta za ta cinye ki,

Takobi zai sare ki,

Zai cinye ki kamar fara.

Ki riɓaɓɓanya kamar fara.

Ki kuma riɓaɓɓanya kamar ɗango.

16 Kin yawaita ‘yan kasuwanki suna da

yawa fiye da taurari,

Amma sun tafi kamar fara waɗanda

sukan buɗe fikafikansu su tashi, su

tafi.

17 Shugabanninki kamar ɗango suke,

Manyan mutanenki kamar

cincirindon fāra ne,

Suna zaune a kan shinge a kwanakin

sanyi,

Sa’ad da rana ta fito, sukan tashi su

tafi,

Ba wanda ya san inda suke.

18 Ya Sarkin Assuriya, masu tsaronka

suna barci,

Manyan mutanenka suna

kwankwance,

Mutanenka sun watse cikin

duwatsu,

Ba wanda zai tattaro su.

19 Ba abin da zai rage zafin rauninka,

Rauninka ba ya warkuwa.

Duk wanda ya ji labarinka, zai tafa

hannuwansa

Gama wane ne ba ka musguna wa

ba?