Categories
NEH

NEH 1

Addu’ar Nehemiya domin Urushalima

1 Labarin Nehemiya ɗan Hakaliya ke nan. Ya zama fa a watan Kisle a shekara ta ashirin, sa’ad da ni Nehemiya nake a fādar Shushan, wato alkarya,

2 sai Hanani, ɗaya daga cikin ‘yan’uwana, ya zo tare da waɗansu mutanen Yahuza. Na kuwa tambaye shi labarin Yahudawan da suka tsira, suka koma daga zaman talala, da labarin Urushalima.

3 Sai suka ce mini, “Waɗanda suka tsira, suka koma daga zaman talala, da suke can lardin, suna cikin wahala ƙwarai, suna kuma shan kunya. Garun Urushalima kuma ya rushe, ƙofofi sun ƙone.”

4 Da na ji wannan labari, sai na zauna, na yi kuka. Na yi kwanaki ina baƙin ciki, na yi ta azumi da addu’a a gaban Allah na Sama.

5 Na ce, “Ya Ubangiji Allah na Sama, Allah mai girma, mai banrazana, mai cika alkawari, mai nuna madawwamiyar ƙauna ga waɗanda suke ƙaunarka, wato masu kiyaye umarnanka,

6 ina roƙonka ka kasa kunne, ka kuma buɗe idanunka, ka ji addu’ar bawanka, wadda nake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra’ila. Ina hurta zunubanmu, mu mutanen Isra’ila, da muka yi maka. Ni da gidan ubana mun yi zunubi.

7 Mun kangare maka, ba mu kiyaye umarnai, da dokoki, da ka’idodi waɗanda ka ba bawanka Musa ba.

8 Ka tuna da maganar da ka umarci bawanka Musa cewa, ‘Idan kun yi rashin aminci, zan warwatsa ku cikin al’ummai.

9 Amma idan kun juyo wurina, kun kiyaye umarnaina, kun aikata su, ko da yake an warsatsar da ku can nesa, zan tattaro ku, in kawo ku wurin da na zaɓa domin in sa sunana ya kahu a wurin.’

10 “Su bayinka ne, mutanenka ne kuma, waɗanda ka fansa da ikonka.

11 Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu’ar bawanka, da addu’o’in bayinka, waɗanda suke jin daɗin girmama sunanka. Ka ba bawanka nasara yau ka sa ya sami tagomashi a gaban mutumin nan.”

Categories
NEH

NEH 2

An Aika da Nehemiya Ya Tafi Urushalima

1 Ni kuwa ina riƙe da finjalin sarki. Wata rana a watan Nisan, a shekara ta ashirin ta sarautar sarki Artashate, sa’ad da na kai masa ruwan inabi, sai na ɗauki ruwan inabin, na ba shi. Ni ban taɓa ɓata fuskata a gabansa a dā ba, sai wannan karo.

2 Sai sarki ya tambaye ni, ya ce, “Me ya sa fuskarka ta ɓaci, ga shi, ba ciwo kake yi ba. Ba abin da ya kawo wannan, sai lalle kana baƙin ciki.”

Sai na tsorata ƙwarai,

3 na ce wa sarki, “Ranka ya daɗe, me zai hana fuskata ta ɓaci, da yake birni inda makabartar kakannina take ya zama kango, an kuma ƙone ƙofofinsa da wuta?”

4 Sa’an nan sarki ya ce mini, “To, me kake so?”

Sai na yi addu’a ga Allah na Sama,

5 sa’an nan na ce wa sarki, “Idan ka yarda, idan kuma na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, ka yardar mini in tafi Yahuza, birnin kakannina, inda makabartarsu take domin in sāke gina shi.”

6 Sarki kuwa, a sa’an nan sarauniya tana zaune kusa da shi, ya ce mini, “Kwana nawa za ka yi, yaushe kuma za ka dawo?” Sai na faɗa masa, ya kuwa yardar mini in tafi, ni kuwa na yanka masa kwanakin da zan yi.

7 Sa’an nan na ce wa sarki, “Idan sarki ya yarda, sai a ba ni takarda zuwa ga masu mulki da suke a lardin Yammacin Kogin Yufiretis domin su yardar mini in wuce zuwa Yahuza.

8 A kuma ba ni takarda zuwa ga Asaf, sarkin daji, domin ya ba ni katakan da zan yi jigajigan ƙofofin kagarar Haikali, da na garun birnin, da na gidan da zan zauna.” Sarki kuwa ya ba ni abin da na roƙa, gama Allah yana tare da ni.

9 Da na zo wurin masu mulkin Yammacin Kogin Yufiretis, sai na miƙa musu takardar sarki. Sarki ya haɗa ni da sarkin yaƙi da mahayan dawakai.

10 Amma Sanballat Bahorone, da Tobiya, Ba’ammone, bawa, ba su ji daɗi ba ko kaɗan sa’ad da suka ji labari, cewa wani ya zo domin ya inganta zaman lafiyar mutanen Isra’ila.

Nehemiya Ya Ƙarfafa Maginan Garu

11 Da na iso Urushalima na yi kwana uku,

12 sai na fita da dare tare da waɗansu mutane kima,ban faɗa wa kowa abin da Allahna ya sa a zuciyata in yi wa Urushalima ba. Ba waɗansu dabbobi kuma tare da ni, sai dai dabbar da na hau.

13 Da na fita, sai na bi ta Ƙofar Kwari zuwa Rijiyar Dila da Ƙofar Juji, na dudduba garun Urushalima, wanda aka rushe, da ƙofofinsa da wuta ta cinye.

14 Na yi gaba zuwa Ƙofar Maɓuɓɓuga da Tafkin Sarki, amma dabbar da na hau ba ta sami wurin wucewa ba.

15 Haka kuwa na fita da dare ta hanyar kwari na dudduba garun, sa’an nan na koma ta Ƙofar Kwari.

16 Shugabanni ba su san inda na tafi, ko abin da na yi ba, gama ban riga na faɗa wa Yahudawa, da firistoci, da manyan gari, da shugabanni, da sauran waɗanda za su yi aikin ba.

17 Sa’an nan na ce musu, “Kun ga irin wahalar da muke ciki, yadda Urushalima ta zama kango, an kuma ƙone ƙofofinta. Ku zo, mu sāke gina garun Urushalima don mu fita kunya.”

18 Na kuma faɗa musu yadda Allah yana tare da ni, ya kuma taimake ni, da maganar da sarki ya faɗa mini.

Sai suka ce, “Mu tashi, mu kama gini.” Suka himmatu su yi wannan aiki nagari.

19 Amma sa’ad da Sanballat Bahorone, da Tobiya Ba’ammone, bawa, da Geshem Balarabe, suka ji labari, sai suka yi mana ba’a, suka raina mu, suka ce, “Me kuke yi? Kuna yi wa sarki tayarwa ne?”

20 Ni kuwa sai na amsa musu, na ce, “Allah na Sama zai ba mu nasara, saboda haka mu mutanensa za mu tashe, mu kama gini, amma ba ruwanku, ba hakkinku, ba ku da wani abin tunawa a Urushalima.”

Categories
NEH

NEH 3

An Raba wa Mutane Wuraren da Za su Gina

1 Eliyashib, babban firist kuwa, tare da ‘yan’uwansa firistoci, suka tashi suka gina Ƙofar Tumaki. Suka tsarkake ta, suka sa mata ƙyamarenta. Suka tsarkake garun zuwa Hasumiyar Ɗari da Hasumiyar Hananel.

2 Mutanen Yariko suka kama gini kusa da shi.

Sai kuma Zakkur ɗan Imri ya kama gini kusa da na mutanen Yariko.

3 Iyalin Hassenaya suka gina Ƙofar Kifi, suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta.

4 Kusa da su kuma, sai Meremot ɗan Uriya, wato jīkan Hakkoz ya yi gyare-gyare.

Kusa da shi kuma sai Meshullam ɗan Berikiya jikan Meshezabel ya yi gyare-gyare.

Kusa da shi kuma sai Zadok ɗan Ba’ana ya yi gyare-gyare.

5 Kusa da Zadok kuwa mutanen Tekowa suka yi nasu gyare-gyare, amma manyansu ba su sa hannu ga aikin shugabanninsu ba.

6 Yoyada ɗan Faseya, da Meshullam ɗan Besodeya, suka gyara Tsohuwar Ƙofa, suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta.

7 Kusa da su kuma sai Melatiya Bagibeyone, da Yadon Bameronote, da mutanen Gibeyon, da na Mizfa waɗanda suke a ƙarƙashin mulkin Yammacin Kogin Yufiretis suka yi gyare-gyare.

8 Kusa da su kuma sai Uzziyel ɗan Harhaya, maƙerin zinariya, ya yi gyare-gyare.

Kusa da Uzziyel kuma sai Hananiya, ɗaya daga cikin masu yin turare, ya yi gyare-gyare. Suka gyare Urushalima har zuwa Garu Mai Faɗi.

9 Kusa da su kuma sai Refaya ɗan Hur, mai mulkin rabin yankin Urushalima, ya yi gyare-gyare.

10 Kusa da Refaya kuma, sai Yedaiya ɗan Harumaf ya yi gyare-gyare daura da gidansa.

Kusa da Yedaiya sai Hattush ɗan Hashabnaiya ya yi gyare-gyare.

11 Malkiya ɗan Harim, da Hasshub ɗan Fahat-mowab suka gyara wani sashi da kuma Hasumiyar Tanderu.

12 Kusa da su kuma, sai Shallum ɗan Hallohesh mai mulkin rabin yankin Urushalima ya yi gyare-gyare tare da ‘ya’yansa mata.

13 Hanun da mazaunan Zanowa suka gyara Ƙofar Kwari. Sun gina ta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta, da ƙyamarenta, suka gyara garun kamu dubu, har zuwa Ƙofar Juji.

14 Malkiya ɗan Rekab, mai mulkin yankin Bet-akkerem, ya gyara Ƙofar Juji. Ya gina ta, ya sa ƙyamarenta da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta.

15 Sai Shallum ɗan Kolhoze, mai mulkin yankin Mizfa ya gyara Ƙofar Maɓuɓɓuga, ya gina ta, ya rufe ta, ya sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta. Ya kuma gina garun Tafkin Siluwam na gonar sarki, har zuwa matakan da suka gangaro daga Birnin Dawuda.

16 Bayansa kuma Nehemiya, ɗan Azbuk, mai mulkin yankin Bet-zur ya yi gyare-gyare, har zuwa wani wuri daura da kabarin Dawuda, har zuwa haƙaƙƙen tafki da gidan masu tsaro.

Lawiyawan da Suka Yi Aikin Garu

17 Waɗannan Lawiyawa sun yi gyare-gyare a ƙarƙashin shugabancin Rehum ɗan Bani.

Kusa da su kuma, sai Hashabiya mai mulkin rabin yankin Kaila, ya yi gyare-gyare domin yankinsa.

18 Bayansa kuma, sai ‘yan’uwansu suka yi gyare-gyare a ƙarƙashin shugabancin Bawwai ɗan Henadad, mai mulkin rabin yankin Kaila.

19 Kusa da su kuma sai Ezer ɗan Yeshuwa, mai mulkin Mizfa, ya gyara wani sashi a gaban gidan makamai a wajen kusurwa.

20 Bayansa kuma, Baruk ɗan Zabbai, ya gyara wani sashi daga wajen kusurwar, har ya zuwa ƙofar gidan Eliyashib babban firist.

21 Bayansa kuma Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz, ya gyara wani sashi daga ƙofar gidan Eliyashib, zuwa ƙarshen gidan.

Firistocin da Suka Yi Aikin Garu

22 Bayansa kuma sai firistoci, mutanen filin kwari, suka yi gyare-gyare.

23 Bayansu kuma Biliyaminu da Hasshub suka yi gyara daura da gidansu. Bayansu kuma Azariya, ɗan Ma’aseya, wato jikan Ananiya, ya yi gyara kusa da gidansa.

24 Bayansa kuma Binnuyi, ɗan Henadad, ya gyara wani sashi daga gidan Azariya zuwa kusurwar garun.

25 Falal ɗan Uzai, ya gyara wani sashi daga kusurwar da hasumiyar benen gidan sarki a wajen shirayin matsara.

Bayansa kuma sai Fedaiya ɗan Farosh ya yi gyare-gyare.

26 Ma’aikatan Haikali da suke zaune a Ofel suka yi gyare-gyare zuwa wani wuri daura da Ƙofar Ruwa wajen gabas, har zuwa wata doguwar hasumiya.

Sauran Masu Gini

27 Bayansu kuma mutanen Tekowa suka gyara wani sashi daura da babbar doguwar hasumiya, har zuwa garun Ofel.

28 Daga Ƙofar Dawaki, firistoci suka yi gyare-gyare, kowa ya yi gyara daura da gidansa.

29 Bayansu kuma Zadok, ɗan Immer, ya gyara wani sashi daura da gidansa.

Bayansa kuma Shemaiya, ɗan Shekaniya, mai tsaron Ƙofar Gabas ya yi gyare-gyare.

30 Bayansa kuma Hananiya ɗan Shelemiya, da Hanun, ɗa na shida na Zalaf, suka gyara wani sashi, kashi na biyu.

Bayansu kuma Meshullam, ɗan Berikiya, ya gyara wani sashi daura da gidansa.

31 Bayansa kuma, Malkiya, ɗaya daga cikin maƙeran zinariya ya yi gyare-gyare, har zuwa gidan ma’aikatan Haikali da na ‘yan kasuwa, daura da Ƙofar Taruwa, har zuwa soron bene a wajen kusurwa.

32 Maƙeran zinariya da ‘yan kasuwa suka gyara wani sashi tsakanin soron bene daga kusurwa da Ƙofar Tumaki.

Categories
NEH

NEH 4

Ma’aikata sun Tsare Kansu

1 Sa’ad da Sanballat ya ji muna ginin garun, sai ya husata ƙwarai, ya yi wa Yahudawa ba’a.

2 Ya yi magana a gaban ‘yan’uwansa da sojojin Samariya ya ce, “Mene ne waɗannan Yahudawa kumamai suke yi? Za su mai da abubuwa yadda suka a dā ne? Za su miƙa hadayu ne? Za su gama ginin a rana ɗaya ne? Za su iya samun duwatsun gini daga tsibin matattun duwatsu?”

3 Tobiya Ba’ammone yana kusa da shi, ya ce, “Ai, garun da suke ginawa da duwatsu, ko dila ya hau, sai ya rushe shi!”

4 Sai ni, Nehemiya, na yi addu’a, na ce, “Ka ji, ya Allahnmu, gama ana raina mu, ka sa ba’arsu ta koma kansu, ka sa a washe su a kai su ƙasar bauta.

5 Kada ka shafe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.”

6 Muka gina garun, har ya kai rabin tsayinta, domin mutane sun himmatu da aikin.

7 Amma sa’ad da Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Ammonawa, da mutanen Ashdod, suka ji yadda ginin garun Urushalima yake ci gaba, ana kuma tattoshe tsattsaguwa, sai suka husata.

8 Dukansu suka ƙulla za su zo, su yi yaƙi da Urushalima, su ta da hankali a cikinta.

9 Sai muka yi addu’a ga Allahnmu, muka sa masu tsaro su yi mana tsaro dare da rana saboda su.

10 Mutanen Yahuza kuwa suka ce,

“Ƙarfin ma’aikata yana kāsawa,

Akwai komatsai da yawa da za a kwashe,

Yaya za mu iya gina garun yau?”

11 Abokan gābanmu kuma suka ce, “Ba za su sani ba, ba kuwa za su gan mu ba, sai dai kawai su gan mu a cikinsu, za mu karkashe su, mu tsai da aikin.”

12 Da Yahudawan da suke zaune kusa da su suka zo, suka yi ta nanata mana irin shirin abokan gabanmu, wato za su zo su fāɗa mana.

13 Saboda haka na sa jama’a su ja ɗamara bisa ga iyalinsu a bayan garu, a wuraren da ba a gina ba. Suna riƙe da takuba, da māsu, da bakuna.

14 Da na ga mutane sun damu, sai na tashi na yi magana da shugabanni, da sauran jama’a, na ce, “Kada ku ji tsoro, ku tuna da Ubangiji mai iko, mai banrazana, ku yi yaƙi domin ‘yan’uwanku, da ‘ya’yanku mata da maza, da matanku, da gidajenku.”

15 Da abokan gābanmu suka ji mun san shirinsu, Ubangiji kuwa ya wargaje shirinsu, sai dukanmu muka koma wurin garun, kowa ya kama aikinsa.

16 Daga wannan rana, sai rabin barorina suka yi ta gini, rabi kuwa suna riƙe da māsu, da garkuwoyi, da bakuna, da sulke. Shugabannin kuwa suka goyi bayan dukan Yahudawa sosai.

17 Masu ginin garun da masu ɗaukan kaya suna yi da hannu ɗaya, hannu ɗaya kuma na riƙe da makami.

18 Kowane magini yana rataye da takobinsa sa’ad da yake gini. Mai busa ƙaho yana kusa da ni.

19 Sai na ce wa manya da shugabanni, da sauran jama’a, “Aikin nan babba ne, mai yawa kuma, ga shikuwa, muna rarrabe a kan garun nesa da juna.

20 Duk inda kuka ji an busa ƙaho, sai ku taru a wurin. Allahnmu zai yi yaƙi dominmu.”

21 Haka kuwa muka yi aikin, rabinmu na riƙe da māsu tun daga wayewar gari har zuwa fitowar taurari.

22 A wannan lokaci kuma na ce wa jama’a, kowane mutum tare da baransa ya kwana a Urushalima domin a yi tsaro da dare, da safe kuma a kama aiki.

23 Saboda haka ni, da ‘yan’uwana, da barorina, da matsaran da suke tare da ni, ba wanda ya tuɓe tufafinsa. Kowa yana riƙe da makami.

Categories
NEH

NEH 5

An Hana Ba da Kuɗi da Ruwa

1 Sai mata da maza suka yi ta kuka ƙwarai saboda ‘yan’uwansu Yahudawa.

2 Akwai waɗanda suka ce, “Mu da ‘ya’yanmu mata da maza muna da yawa, sai mu sami hatsi don mu ci mu rayu.”

3 Waɗansu kuma suka ce, “Saboda yunwa mun jinginar da gonakinmu, da gonakin inabinmu, da gidajenmu don mu sami hatsi.”

4 Akwai waɗansu kuma da suka ce, “Mun ci bashin kuɗi don mu biya haraji a kan gonakinmu, da gonakin inabinmu.

5 Ga shi kuwa, mu da su dangin juna ne, ‘ya’yanmu da nasu kuma ɗaya ne, duka da haka muna tilasta wa ‘ya’yanmu mata da maza su zama bayi. Har ma waɗansu daga cikin ‘ya’yanmu mata an riga an bautar da su, amma ba mu da iko mu ce kome, domin gonakinmu da gonakin inabinmu suna a hannun waɗansu mutane.”

6 Ni Nehemiya na husata ƙwarai, sa’ad da na ji kukansu da wannan magana.

7 Sai na yi shawara a zuciyata, na yi wa manya da shugabanni faɗa, na ce musu, “Kuna musguna wa ‘yan’uwanku da yake kuna ba su rance da ruwa.”

Sa’an nan na kira babban taro saboda su.

8 Na ce musu, “Da iyakacin ƙoƙarinmu mun fanshi ‘yan’uwanmu Yahudawa waɗanda aka sayar wa al’ummai, amma ga shi, kuna tilasta wa ‘yan’uwanku su sayar da kansu ga ‘yan’uwansu.” Sai suka yi tsit, suka rasa abin da za su ce.

9 Na kuma ce musu, “Abin da kuke yi ba shi da kyau. Ya kamata ku yi tsoron Allah don ku hana al’ummai, abokan gabanmu, yi mana ba’a.

10 Ni ma da ‘yan’uwana da barorina muna ba da rancen kuɗi da hatsi. Sai mu daina sha’anin ba da rance da ruwa.

11 Yau sai ku mayar musu da gonakinsu, da gonakin inabinsu, da na zaitunsu, da gidajensu, da kashi ɗaya bisa ɗari na kuɗi, da na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai, waɗanda kuka karɓa a wurinsu.”

12 Sa’an nan suka ce, “Za mu mayar musu da waɗannan abubuwa, ba kuwa za mu bukaci wani abu a gare su ba. Za mu yi abin da ka faɗa.”

Sai na kira firistoci su rantsar da su, cewa za su yi yadda suka alkawarta.

13 Sai kuma na kakkaɓe hannuna, na ce, “Duk wanda ya karya wannan alkawari, haka Allah zai kakkaɓe shi daga gidansa da aikinsa. Allah zai kakkaɓe shi, ya wofintar da shi.”

Sai dukan taron suka amsa, “Amin, amin.” Suka kuma yabi Ubangiji. Suka kuwa cika alkawarin da suka yi.

Rashin Sonkan Nehemiya

14 Tun kuma lokacin da na yi mulkin ƙasar Yahuza, a shekara ta ashirin zuwa shekara ta talatin da biyu ta sarautar sarki Artashate, shekara goma sha biyu ke nan, ni ko ‘yan’uwana, ba wanda ya karɓi albashin da akan ba mai mulki.

15 Waɗanda suka riga ni mulki sun nawaita wa mutane. Sun yi ta karɓar abinci da ruwan inabi daga gare su, banda shekel arba’in kowace rana domin abinci da ruwan inabi. Har ma barorin masu mulki sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah.

16 Na mai da hankali ga aikin garu, ban samar wa kaina gonaki ba. Barorina duka suka haɗa kai da ni a kan aikin gini.

17 Duk da haka akwai Yahudawa da shugabanni ɗari da hamsin waɗanda suke cin abinci a teburina, banda waɗanda sukan zo wurinmu daga al’umman da suke kewaye da mu.

18 Ga abincin da ake shiryawa kowace rana, sa ɗaya, da tumaki shida kyawawa, da kuma kaji. A kowace rana ta goma akan kawo salkunan ruwan inabi masu yawa, amma duk da haka ban karɓi albashin da akan ba mai mulki ba, domin wahala ta yi wa mutane yawa.

19 Ya Allahna, ka tuna da alherin da na yi wa mutanen nan.

Categories
NEH

NEH 6

Sharrin ‘Yan Hammayya

1 Sa’ad da fa aka sanar da Sanballat, da Tobiya, da Geshem Balarabe, da sauran abokan gābanmu, cewa na gina garun, har ba sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake a lokacin ban riga na sa wa ƙofofi ƙyamare ba,

2 sai Sanballat da Geshem suka aika wurina cewa, “Ka zo mu sadu a wani ƙauye a filin Ono,” amma da nufin su cuce ni.

3 Sai na aika musu da manzanni, na ce, “Ina fama da babban aiki, ba ni da damar zuwa wurinku. Don me zan bar aiki in gangaro zuwa wurinku?”

4 Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.

5 A karo na biyar sai Sanballat ya aiko da buɗaɗɗiyar wasiƙa ta hannun baransa, da irin maganar dā.

6 Ga abin da yake cikin wasiƙar, “Geshem ya faɗa mini, ana ta ji jita jita wurin maƙwabta, cewa kai da Yahuduwa kuna niyyar tayarwar, don haka kake ginin garun, kana so kuma ka naɗa kanka sarki.

7 Ga shi, ka sa annabawa su yi shelarka a Urushalima cewa, ‘Akwai sarki a Yahuza.’ To, za a faɗa wa sarki wannan magana, sai ka zo mu yi shawara tare a kan wannan al’amari.”

8 Sai na mayar masa da amsa cewa, “Faufau, ba a yi wani abu haka kamar yadda ka faɗa ba, kai ne ka ƙaga wannan a zuciyarka.”

9 Gama dukansu so suke su tsoratar da mu, suna cewa, “Za su daina aikin.” Amma na yi addu’a, na ce, “Ya Allah, ka ƙarfafa ni.”

10 Sa’ad da na ziyarci Shemaiya ɗan Delaiya, wato jikan wanda aka hana shi fita, sai ya ce mini, “Bari mu tafi cikin Haikalin Allah, mu rufe ƙofofin Haikalin, gama suna zuwa su kashe ka, za su iya zuwa a wani dare su kashe ka.”

11 Sai na ce, “Mutum kamata ne, zai gudu? Mutum irina zai shiga Haikali don ya tsere? To, ba zan tafi ba.”

12 Na gane Allah bai aike shi wurina ba. Ya yi mini wannan magana domin Tobiya da Sanballat sun haɗa baki da shi.

13 Gama da wannan nufi ne suka haɗa baki, don in ji tsoro, in yi yadda suke so, in yi zunubi, da haka za su ba ni mugun suna, su yi mini ba’a.

14 “Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat bisa ga abubuwan nan da suka yi, da annabiya Nowadiya, da sauran annabawa waɗanda suka so su tsoratar da ni.”

Gamawar Aikin

15 A cikin kwana hamsin da biyu aka gama garun, ran ashirin da biyar ga watan Elul.

16 Sa’ad da abokan gābanmu da dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji, sai suka ji tsoro, gabansu kuma ya faɗi, gama sun gane, da taimakon Allahnmu muka yi wannan aiki.

17 A kwanakin nan kuma shugabannin Yahuza suka yi ta aika wa Tobiya da wasiƙu, shi kuma Tobiya yana ta aika musu da nasa wasiƙu.

18 Mutane da yawa a Yahuza sun rantse za su goyi bayan Tobiya, domin ya auri ‘yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato Yohenan, ya auri ‘yar Meshullam, ɗan Berikiya.

19 Mutane suka yi magana a kan ayyukan kirki na Tobiya a gabana. Suka kuma kai maganata a wurinsa, sai Tobiya ya yi ta aika mini da wasiƙu don ya tsoratar da ni.

Categories
NEH

NEH 7

Nehemiya Ya Zaɓi Masarautan Urushalima

1 Sa’ad da aka gina garun, aka sa ƙofofinsa, aka kuma sa matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da Lawiyawa,

2 sai na ba ɗan’uwana, Hanani, da Hananiya, shugaban kagara, aikin riƙon Urushalima. Shi Hananiya mai aminci ne, mai tsoron Allah, fiye da sauran mutane.

3 Sa’an nan na ce musu, kada su buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe, sai rana ta cira sosai, su kuma kulle ƙofofin da ƙarfe kafin matsara su tashi wajen faɗuwar rana. Su samo matsara daga mazaunan Urushalima, su sa su tsaye a muhimman wurare, waɗansunsu kuma suna zaga gidaje.

Lissafin Mutane

4 Birnin yana da faɗi da girma, amma mutanen da suke ciki kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje ba tukuna.

5 Allahna kuwa ya sa a zuciyata in tara manya da shugabanni, da sauran jama’a don a rubuta su bisa ga asalinsu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara komowa. Ga abin da na tarar aka rubuta ciki.

6 Waɗannan su ne mutanen lardin Yahuza, waɗanda suka komo daga zaman talala da Nebukadnezzar Sarkin Babila ya kai mutane. Sun komo Urushalima da Yahuza. Kowa ya tafi garinsu.

7 Sun komo tare da Zarubabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Seraiya, da Re’elaya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Rehum, da Ba’ana.

8-25 Ga jerin iyalan Isra’ila da adadin waɗanda suka komo daga zaman dole

iyalin Farosh, dubu biyu da ɗari da saba’in da biyu (2,172)

iyalin Shefatiya, ɗari uku da saba’in da biyu

iyalin Ara, ɗari shida da hamsin da biyu

iyalin Fahat-mowab, wato zuriyar Yeshuwa da Yowab, dubu biyu da ɗari takwas da goma sha takwas (2,818)

iyalin Elam, dubu da ɗari biyu da hamsin da huɗu (1,254)

iyalin Zattu, ɗari takwas da arba’in da biyar

iyalin Zakkai, ɗari bakwai da sittin

iyalin Bani, ɗari shida da arba’in da takwas

iyalin Bebai, ɗari shida da ashirin da takwas

iyalin Azgad, dubu biyu da ɗari uku da ashirin da biyu (2,322)

iyalin Adonikam, ɗari shida da sittin da bakwai

iyalin Bigwai, dubu biyu da sittin da bakwai (2,067)

iyalin Adin, ɗari shida da hamsin da biyar

iyalin Ater (na Hezekiya), tasa’in da takwas

iyalin Hashum, ɗari uku da ashirin da takwas

iyalin Bezai, ɗari uku da ashirin da huɗu

iyalin Yora, ɗari da goma sha biyu

iyalin Gibeyon, tasa’in da biyar

26-38 Mutanen da kakanninsu suka zauna a waɗannan garuruwa, su ma sun komo daga zaman talala.

Baitalami da Netofa, ɗari da tamanin da takwas

Anatot, ɗari da ashirin da takwas

Azmawet, arba’in da biyu

Kiriyat-yeyarim da Kefira, da Biyerot, ɗari bakwai da arba’in da uku

Rama da Geba, ɗari shida da ashirin da ɗaya

Mikmash, ɗari da ashirin da biyu

Betel da Ai, ɗari da ashirin da uku

Da wani Nebo, hamsin da biyu

Da wani Elam, dubu da ɗari biyu da hamsin da huɗu (1,254)

Harim, ɗari uku da ashirin

Yariko, ɗari uku da arba’in da biyar

Lod, da Hadid, da Ono, ɗari bakwai da ashirin da ɗaya

Senaya, dubu uku da ɗari tara da talatin (3,930)

39-42 Ga lissafin iyalin firistoci da suka komo daga zaman talala.

Yedaiya, na zuriyar Yeshuwa, ɗari tara da saba’in da uku

Immer, dubu ɗaya da hamsin da biyu (1,052)

Fashur, dubu da ɗari biyu da arba’in da bakwai (1,247)

Harim, dubu ɗaya da goma sha bakwai (1,017)

43 Lawiyawan da suka komo daga zaman talala, Yeshuwa da Kadmiyel na zuriyar Hodawiya, saba’in da huɗu.

44 Mawaƙa, na zuriyar Asaf, ɗari da arba’in da takwas.

45 Masu tsaron Haikali su ne zuriyar Shallum, da Ater, da Talmon, da Akkub, da Hatita, da Shobai, ɗari da talatin da takwas.

46-56 Ma’aikatan Haikali da suka komo daga zaman talala, su ne

Zuriyar Ziha, da Hasufa, da Tabbawot,

Keros, da Siyaha, da Fadon,

Lebana, da Hagaba, da Shamlai,

Hanan, da Giddel, da Gahar,

Rewaiya, da Rezin, da Nekoda,

Gazam, da Uzza, da Faseya,

Besai, da Me’uniyawa, da Nefushiyawa,

Bakbuk, da Hakufa, da Harkur,

Bazlut, da Mehida, da Harsha,

Barkos, da Sisera, da Tema,

Neziya, da Hatifa.

57-59 Iyalan barorin Sulemanu da suka komo daga zaman talala, su ne

na Sotai, da Hassoferet, da Feruda,

Yawala, da Darkon, da Giddel,

Shefatiya, da Hattil, da Fokeret-hazzebayim, da Ami.

60 Jimillar zuriyar ma’aikatan Haikali da na Sulemanu, su ɗari uku da tasa’in da biyu ne.

61-62 Waɗannan su ne daga zuriyar Delaiya, da Tobiya, da Nekoda, waɗanda suka zo daga garuruwan Telmela, da Tel-harsha, da Kerub, da Addan, da Immer, amma ba su iya nuna gidajen kakanninsu, ko zuriyarsu a cikin Isra’ilawa ba, su ɗari shida ne da arba’in da biyu.

63 Na wajen firistoci kuma su ne zuriyar Habaya, da na Hakkoz, da na Barzillai, wanda ya auri ‘yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kira shi da sunan zuriyar surukinsa.

64 Waɗannan suka nema a rubuta su tare da waɗanda aka rubuta jerin sunayen asalinsu, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.

65 Sai mai mulki ya faɗa musu kada su ci abinci mafi tsarki, sai an sami firist wanda zai yi tambaya ta wurin Urim da Tummin tukuna.

66-69 Jimillar waɗanda suka komo duka su dubu arba’in da dubu biyu da ɗari uku da sittin ne (42,360)

barorinsu mata da maza, waɗanda yawansu ya kai dubu bakwai da ɗari uku da talatin da bakwai (7,337)

mawaƙa ɗari biyu da arba’in da biyar mata da maza

dawakansu kuma ɗari bakwai da talatin da shida ne

alfadaransu kuma ɗari biyu da arba’in da biyar ne

raƙumansu ɗari huɗu da talatin da biyar ne

jakunansu dubu shida da ɗari bakwai da ashirin (6,720)

70-72 Da yawa daga cikin jama’a suka ba da taimako domin biyan aikin gyaran Haikali.

Mai mulki ya ba da

zinariya darik dubu (1,000)

kwanonin wanke hannu guda hamsin

rigunan firistoci ɗari biyar da talatin

Shugabannin iyali suka ba da

zinariya darik dubu ashirin (20,000)

azurfa maina dubu biyu da ɗari biyu (2,200)

Sauran jama’a suka ba da

zinariya darik dubu ashirin (20,000)

azurfa maina dubu biyu (2,000)

rigunan firistoci guda sittin da bakwai

73 Sa’an nan firistoci, da Lawiyawa, da masu tsaron Haikali, da mawaƙa da waɗansu da dama daga cikin jama’a, da ma’aikatan Haikali, da dukan Isra’ilawa suka zauna a garuruwansu.

Categories
NEH

NEH 8

Ezra Ya Karanta wa Jama’a Attaura

Da amaryar watan bakwai mutanen Isra’ila duk sun riga sun zauna a garuruwansu.

1 Dukan jama’a suka taru wuri ɗaya a filin Ƙofar Ruwa, suka faɗa wa Ezra, magatakarda, ya kawo Attaura ta Musa wanda Ubangiji ya ba Isra’ilawa.

2 A ran ɗaya ga watan bakwai, sai Ezra, firist, ya kawo Attaura a gaban taron jama’a, mata da maza, da dukan waɗanda za su ji, su fahimta.

3 Ya karanta Littafin, yana fuskantar filin Ƙofar Ruwa, a gaban mata da maza, da waɗanda za su iya fahimta. Mutane duka kuwa suka kasa kunne ga karatun Attaura, tun da sassafe har zuwa rana tsaka.

4 Sai Ezra, magatakarda, ya tsaya a wani dakali na itace, wanda suka shirya musamman domin wannan hidima. Sai Mattitiya, da Shema, da Anaya, da Uriya, da Hilkaya, da Ma’aseya, suka tsaya a wajen damansa, a wajen hagunsa kuwa Fedaiya, da Mishayel, da Malkiya, da Hashum, da Hashbaddana, da Zakariya, da Meshullam suka tsaya.

5 Ezra kuwa ya buɗe Littafin a gaban jama’a duka, domin yana sama da jama’a. Sa’ad da ya buɗe Littafin, sai jama’a duka suka miƙe tsaye.

6 Sai Ezra ya yabi Ubangiji Allah Maɗaukaki.

Jama’a duka suka amsa, “Amin, amin!” suna ɗaga hannuwansu. Suka sunkuyar da kansu har ƙasa, suka yi wa Ubangiji sujada.

7 Sa’ad da jama’a suke tsaye a wurarensu, sai Lawiyawa, wato su Yeshuwa, da Bani, da Sherebiya, da Yamin, da Akkub, da Shabbetai, da Hodiya, da Ma’aseya, da Kelita, da Azariya, da Yozabad, da Hanan, da Felaya, suka fassara musu dokokin.

8 Suka karanta daga littafin dokokin Allah sosai, suka fassara musu, saboda haka jama’a suka fahimci karatun.

9 Nehemiya kuwa wanda yake mai mulki, da Ezra, firist da magatakarda, da Lawiyawa waɗanda suka fassara wa jama’a dokokin, suka ce wa dukan jama’a, “Wannan rana tsattsarka ce, ta Ubangiji Allahnku, kada ku yi baƙin ciki ko kuka.” Gama mutane duka sai kuka suke sa’ad da aka karanta musu dokokin.

10 Sa’an nan ya ce musu, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha ruwan inabi mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi, gama wannan rana tsattsarka ce ta Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin da Ubangiji ya ba ku shi ne ƙarfinku.”

11 Lawiyawa kuma suka bi suna rarrashin jama’a, suna cewa, “Ku yi shiru, gama wannan rana tsattsarka ce, kada ku yi baƙin ciki.”

12 Sai jama’a duka suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci. Suka yi murna ƙwarai domin sun fahimta dokokin da aka karanta musu.

Idin Bukkoki

13 Kashegari kuma sai shugabannin kakannin gidajen jama’a duka, tare da firistoci, da Lawiyawa, suka je wurin Ezra, magatakarda, domin su yi nazarin dokokin.

14 Sai suka iske an rubuta a cikin dokokin da Ubangiji ya umarta ta hannun Musa, cewa sai jama’ar Isra’ila su zauna a bukkoki a lokacin idi na watan bakwai.

15 Saboda haka sai suka yi shela a garuruwansu duka da a Urushalima cewa, “Ku fita zuwa tuddai ku kawo rassan zaitun, da na kadanya, da na dargaza, da na dabino, da sauran rassan itatuwa masu gazari, domin a yi bukkoki kamar yadda aka rubuta.”

16 Sai suka tafi suka kawo rassan, suka yi wa kansu bukkoki a kan rufin sorayensu, da a dandalinsu, da cikin harabar Haikalin Allah, da a dandalin Ƙofar Ruwa, da a dandalin Ƙofar Ifraimu.

17 Dukan taron jama’ar da suka komo daga zaman talala suka yi wa kansu bakkoki, suka zauna cikinsu, gama tun daga kwanakin Joshuwa ɗan Nun, har zuwa wannan rana, jama’ar Isra’ila ba su yin haka. Aka kuwa yi farin ciki mai yawa.

18 Kowace rana, tun daga rana ta fari zuwa rana ta ƙarshe, Ezra yakan karanta musu daga cikin littafin dokokin Allah. Suka kiyaye idin har kwana bakwai. A rana ta takwas kuma suka muhimmin taro bisa ga ka’ida.

Categories
NEH

NEH 9

Jama’a Sun Hurta Laifofinsu

1 A rana ta ashirin da huɗu ga watan nan, sai jama’ar Isra’ila suka taru, suna azumi, suna saye da tufafin makoki, suna zuba toka a kansu.

2 Suka ware kansu daga bāre duka, suka tsaya, suna hurta laifofinsu da na kakanninsu.

3 Sa’ad da suke tsaye a inda suke, sai suka ɗauki kashi ɗaya daga cikin huɗu na yini, suna karanta littafin dokokin Ubangiji Allahnsu. Suka kuma ɗauki kashi ɗaya daga cikin huɗu ɗin na yinin, suna ta hurta laifofi suna kuma yi wa Ubangiji Allahnsu sujada.

4 Sai Yeshuwa, da Bani, da Kadmiyel, da Shebaniya, da Bunni, da Sherebiya, da Bani, da Kenani suka tsaya a kan dakalin Lawiyawa, suka ta da murya da ƙarfi ga Ubangiji Allahnsu.

5 Waɗannan Lawiyawa kuma, wato Yeshuwa, da Kadmiyel, da Bani, da Hashabnaiya, da Sherebiya, da Hodiya, da Shebaniya, da Fetahiya su ne suka yi kiran sujada, suka ce,

“Ku miƙe tsaye, ku yabi Ubangiji Allahnku,

Ku yabe shi har abada abadin.

Bari kowa ya yabi maɗaukakin sunanka, ya Ubangijii,

Ko da yake ba yabon da ɗan adam zai yi har ya isa.”

Addu’ar Hurta Laifi

6 Sa’an nan suka yi wannan addu’a, suka ce,

“Kai kaɗai ne Ubangiji, ya Ubangiji,

Kai ne ka yi samaniya da taurari da sararin sama.

Kai ne ka yi ƙasa, da teku, da kowane abu da yake cikinsu,

Ka ba dukansu rai,

Ikokin samaniya sun rusuna suna maka sujada.

7 Kai ne, ya Ubangiji Allah, ka zaɓi Abram,

Ka fito da shi daga Ur ta Kaldiyawa,

Ka sāke sunansa ya zama Ibrahim.

8 Ka iske shi amintacce a gare ka,

Ka kuwa yi masa alkawari.

Ka yi alkawari za ka ba shi ƙasar Kan’ana,

Da ta Hittiyawa, da ta Amoriyawa, da ta Ferizziyawa,

Da ta Yebusiyawa, da ta Girgashiyawa,

Ta zama inda zuriyarsa za su zauna.

Ka kuwa cika alkawarinka, gama kai mai aminci ne.

9 Ka ga wahalar kakanninmu a Masar,

Ka ji kukansu a Bahar Maliya.

10 Ka kuma aikata alamu da al’ajabai a kan Fir’auna,

Da fadawansa duka, da mutanen ƙasarsa,

Gama ka san yadda suka yi wa jama’arka danniya.

Ta haka ka yi wa kanka suna kamar yadda yake a yau.

11 Ka yi hanya ta cikin teku domin jama’arka,

Ka sa su bi ta ciki a kan sandararriyar ƙasa.

Ka sa waɗanda suke fafararsu suka hallaka cikin zurfin teku,

Suka nutse kamar dutse.

12 Da rana ka bishe su da al’amudin girgije,

Da dare ka bishe su da al’amudin wuta.

13 Ka kuma sauka a bisa Dutsen Sinai,

Ka yi magana da jama’arka a can,

Ka ba su ka’idodin da suka dace,

Da dokoki, da kyakkyawar koyarwa.

14 Ka koya musu su kiyaye Asabar ɗinka tsattsarka,

Ka kuma ba su dokokinka ta hannun Musa bawanka.

15 Ka ba su abinci daga sama sa’ad da suka ji yunwa,

Ruwa kuma daga dutse sa’ad da suka ji ƙishi,

Ka faɗa musu su shiga su mallaki ƙasar da ka yi alkawari za ka ba su.

16 Amma kakanninmu suka yi fāriya, suka taurare,

Suka ƙi yin biyayya da umarnanka.

17 Suka ƙi yin biyayya,

Suka manta da dukan abin da ka yi,

Suka manta da al’ajaban da ka aikata.

Cikin fāriyarsu suka zaɓi shugaba,

Don su koma cikin bauta a Masar.

Amma kai Allah ne mai gafartawa,

Kai mai alheri ne, mai ƙauna,

Jinƙanka da girma yake, ba ka yashe su ba.

18 Ko sa’ad da suka yi wa kansu ɗan marakin zubi,

Suka ce shi ne allahn da ya fisshe su daga Masar,

Ai, sun yi maka ɓatanci, ya Ubangiji.

19 Amma ba ka rabu da su a hamada ba,

Saboda jinƙanka mai girma ne.

Ba ka kuwa kawar da girgije da wuta ba,

Waɗanda suke nuna musu hanya dare da rana.

20 Ta wurin alherinka ka faɗa musu abin da ya kamata su yi,

Ka ciyar da su da manna, ka ba su ruwa su sha.

21 Ka taimake su a jeji shekara arba’in,

Ka ba su dukan abin da suke bukata,

Ƙafafunsu ba su kumbura su yi musu ciwo ba.

22 “Ka sa sun ci al’ummai da mulkoki da yaƙi,

Ƙasashen da suke maƙwabtaka da tasu.

Suka ci ƙasar Sihon, Sarkin Heshbon,

Da ƙasar Bashan, inda Og yake sarki.

23 Ka riɓaɓɓanya zuriyarsu kamar taurarin sararin sama,

Ka sa suka ci ƙasar, suka zauna cikinta,

Ƙasar da aka yi wa kakanninsu alkawari za ka ba su.

24 Saboda haka zuriyarsu suka shiga, suka mallaki ƙasar Kan’ana.

Ka rinjayi mutanen da suke zama a can.

Ka ba jama’arka iko su yi yadda suke so

Da mutane, da sarakunan ƙasar Kan’ana.

25 Sun ci birane masu garu, da ƙasa mai dausayi,

Da gidaje cike da dukiya, da rijiyoyi, da gonakin inabi,

Da itatuwan zaitun, da itatuwa masu ‘ya’ya.

Suka ci dukan abin da suke so, suka yi taiɓa,

Suka mori dukan kyawawan abubuwan da ka ba su.

26 “Amma suka yi maka rashin biyayya, suka tayar maka,

Suka juya wa dokokinka baya,

Suka karkashe anna bawan da suka faɗakar da su,

Waɗanda suka faɗa musu su juyo gare ka.

Suka yi ta saɓa maka lokaci lokaci.

27 Saboda haka ka bar abokan gābansu su ci su, mallake su.

A wahalarsu sun yi kira gare ka domin taimako,

Ka kuwa amsa musu daga Sama.

Ta wurin jinƙanka mai yawa ka aiko musu da shugabanni,

Waɗanda suka kuɓutar da su daga maƙiyansu.

28 Sa’ad da zaman salama ya komo, sai kuma su yi zunubi,

Kai kuma sai ka bar abokan gabansu su ci su.

Duk da haka idan sun tuba, suka roƙe ka ka cece su,

Kakan ji daga Sama,sau da yawa,

Ka cece su da jinƙanka mai yawa.

29 Ka gargaɗe su su yi biyayya da koyarwarka,

Amma sun bijire wa dokoki saboda girmankai,

Ko da yake kiyaye dokarka ita ce hanyar rai.

Masu taurinkai sun taurare, sun ƙi yin biyayya.

30 “Ka yi haƙuri da su shekaru da yawa, ka gargaɗe su,

Annabawanka sun yi musu magana, amma sun toshe kunne.

Saboda haka ka sa waɗansu al’ummai su mallaki jama’arka.

31 Duk da haka, saboda yawan jinƙanka,

Ba ka yashe su ko ka hallaka su ba.

Kai Allah mai alheri ne mai jinƙai!

32 “Ya Allah, Allahnmu, da girma kake!

Kai mai banrazana ne, cike da iko!

Da aminci ka cika alkawaranka da ka alkawarta.

Daga lokacin da Sarkin Assuriya ya danne mu,

Har yanzu ma, wace wahala ce ba mu sha ba!

Sarakunanmu, da shugabanninmu, da firistocinmu,

Da annabawanmu, da kakanninmu,

Da dukan sauran jama’arka sun sha wahala.

Ka san irin wahalar da muka sha.

33 Ka yi daidai da ka hukunta mu haka!

Kai mai aminci ne, mu kuwa mun yi zunubi.

34 Gama kakanninmu, da sarakunanmu,

Da shugabanninmu, da firistocinmu,

Ba su kiyaye dokarka ba.

Ba su kasakunne ga umarnanka da gargaɗinka ba.

Da waɗannan ne kake zarginsu.

35 Da albarkacinka sarakuna suke mulkin jama’arka,

Sa’ad da suke ƙasashen waje, ƙasa mai dausayi ka ba su,

Amma ba su juyo su bar zunubi, su bauta maka ba.

36 Ga shi, a yau mu bayi ne a ƙasar da ka ba mu,

Wannan ƙasa mai dausayi wadda take ba mu abinci.

37 Amfanin ƙasa duk yana tafiya ga sarakunan

Da ka ɗora su a kanmu saboda mun yi zunubi.

Suna yi mana yadda suka ga dama, mu da dabbobinmu,

Muna cikin baƙin ciki.”

Jama’a Sun Sa Hannu a Yarjejeniya

38 “Saboda wannan duka muke yin alkawari mai ƙarfi a rubuce. Shugabanninmu kuwa, da Lawiyawanmu, da firistocinmu, suka buga hatimi, suka sa hannu.”

Categories
NEH

NEH 10

1 Waɗanda suka fara sa hannu a takardar alkawarin, su ne mai mulki, wato Nehemiya ɗan Hakaliya, da Zadakiya,

2-8 sa’an nan firistoci, wato

Seraiya, da Azariya, da Irmiya,

Fashur, da Amariya, da Malkiya,

Hattush, da Shebaniya, da Malluki,

Harim, da Meremot, da Obadiya,

Daniyel, da Ginneton, da Baruk,

Meshullam, da Abaija, da Miyamin,

Mawaziya, da Bilgai, da Shemaiya.

9-13 Wajen Lawiyawa kuwa, su ne

Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi daga zuriyar Henadad da Kadmiyel.

‘Yan’uwansu kuwa su ne Shebaniya, da Hodiya,

Kelita, da Felaya, da Hanan,

Mika, da Rehob, da Hashabiya,

Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,

Hodiya, da Bani, da Beninu.

14-27 Shugabannin jama’a kuwa, su ne Farosh, da Fahat-mowab,

Elam, da Zattu, da Bani,

Bunni, da Azgad, da Bebai,

Adonaija, da Bigwai, da Adin,

Ater, da Hezekiya, da Azzur,

Hodiya, da Hashum, da Bezai,

Harif, da Anatot, da Nebai,

Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,

Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa,

Felatiya, da Hanan, da Anaya,

Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,

Hallohesh, da Filha, da Shobek,

Rehum, da Hashabna, da Ma’aseya,

Ahaija, da Hanan, da Anan,

Malluki, da Harim, da Ba’ana.

Alkawarin da Aka Yi

28 Jama’ar Isra’ila, da firistoci, da Lawiyawa, da masu tsaron ƙofofi, da mawaƙa, da ma’aikatan Haikali, da dukan waɗanda suka ware kansu daga sauran al’umman waɗansu ƙasashe, domin su bi dokokin Allah, su da matansu, da ‘ya’yansu mata da maza, da dai duk waɗanda suke da sani da fahimta,

29 suka haɗa kai da ‘yan’uwansu, da shugabanninsu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye dokokin Allah waɗanda ya ba bawansa Musa ba. Suka rantse za su kiyaye, su aikata umarnai, da ka’idodi, da dokokin Ubangijinmu.

30 Suka ce, “Ba za mu aurar wa mutanen ƙasar da ‘ya’yanmu mata ba. Ba kuma za mu auro wa ‘ya’yanmu maza ‘ya’yansu mata ba.

31 “Idan kuma mutanen ƙasar sun kawo kayayyaki da hatsi don sayarwa a ranar Asabar, ba za mu saya ba, ko kuma a wata tsattsarkar rana.

“A kowace shekara ta bakwai ba za mu girbe amfanin gonakinmu ba, za mu kuma yafe kowane irin bashi.

32 “Muka kuma anita kowannenmu zai riƙa ba da sulusin shekel a shekara domin aikin Haikalin Allahnmu.

33 “Za mu tanadi gurasar ajiyewa, da hadayar gāri ta kullum, da ta ranakun Asabar, da ta amaryar wata, da ta ƙayyadaddun idodi, da abubuwa masu tsarki, da hadaya don zunubi saboda yi wa jama’ar Isra’ila kafara, da dukan aiki na Haikalin Allahnmu.

34 “Muka kuma jefa kuri’a wato firistoci, da Lawiyawa, da jama’a a kan kawo itacen hadaya a Haikalin Allahnmu, bisa ga gidajen kakanninmu, a kan ƙayyadaddun lokatai a shekara, don a ƙona hadayu a bisa bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda aka rubuta a dokoki.

35 “Wajibi ne kuma mu kawo nunan fari na gonakinmu, da nunan fari na ‘ya’yan itatuwanmu kowace shekara zuwa Haikalin Ubangiji.

36 “Za mu kuma kawo ‘ya’yan farinmu maza, da na shanunmu, da na tumaki, da awaki, kamar dai yadda aka rubuta a dokoki, haka za mu kawo su a Haikalin Allahnmu, da gaban firistocin da suke hidima a Haikalin Allahnmu.

37 “Za mu kuma kawo hatsinmu na fari kullum, da sadakokinmu, da ‘ya’yan itatuwanmu, da sabon ruwan inabi, da mai, a gaban firistoci, a shirayin Haikalin Allahnmu.

“Za mu kuma ba Lawiyawa zakar amfanin gonakinmu, gama Lawiyawa ne suke tara zaka a garuruwanmu na karkara.

38 Firist kuwa daga zuriyar Haruna zai kasance tare da Lawiyawa sa’ad da suke karɓar zakar. Lawiyawa kuma za su fid da zaka daga cikin zakar da aka tara musu, su kawo ɗakin ajiya na Haikalin Allah.

39 Gama jama’ar Isra’ila da Lawiyawa za su kawo sadakoki na hatsi,da na ruwan inabi, da na mai, a ɗakin ajiya inda tasoshin Haikali suke, da gaban firistocin da suke hidima, da masu tsaron ƙofofi, da mawaƙa.

“Ba za mu ƙyale Haikalin Allahnmu ba.”