Categories
ROM

ROM 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, bawan Yesu Almasihu, manzo kirayayye, keɓaɓɓe domin yin bisharar Allah,

2 wadda Allah ya yi alkawari tun dā, ta bakin annabawansa a cikin Littattafai masu tsarki.

3 Bishara ɗin nan a kan Ɗansa ce, Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ga jiki shi zuriyar Dawuda ne,

4 amma ga tsarkinsa na ruhu shi Ɗan Allah ne, da iko aka ayyana shi haka ta wurin tashinsa daga matattu.

5 Ta wurinsa ne muka sami alheri da kuma manzanci, saboda sunansa dukan al’ummai su gaskata su yi biyayya,

6 a cikinsu kuma har da ku da kuke kirayayyun Yesu Almasihu.

7 Daga Bulus zuwa ga dukan ƙaunatattun Allah da kuke a Roma, tsarkaka kirayayyu.

Alheri da salama na Allah Ubanmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu su tabbata a gare ku.

Nufin Bulus Ya Ziyarci Roma

8 Da farko dai ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Almasihu saboda ku duka, domin ana baza labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.

9 Domin kuwa Allah, wanda nake bauta wa a ruhuna ta yin bisharar Ɗansa, shi ne mashaidina a kan yadda kullum ba na fasa ambatonku a cikin addu’ata,

10 ina addu’a, ko ta ƙaƙa, da yardar Allah, a yanzu kam, in sami arzikin zuwa wurinku.

11 Domin ina ɗokin ganinku, in ni’imta ku da wata baiwa ta ruhu, domin ku ƙarfafa.

12 Wato ni da ku, mu ƙarfafa juna ta bangaskiyarmu, tawa da taku.

13 Ina so ku sani ‘yan’uwa, na sha ɗaura niyyar zuwa wurinku, ko da yake har yanzu ba a yardar mini ba, domin ku ma in sami amfani a gare ku, kamar yadda na samu a cikin al’ummai.

14 Akwai hakkin Helenawa, da na bare, da na masu ilimi, da na jahilai duka a kaina.

15 Saboda haka a gwargwadon iyawata, ina da himma ku ma in yi muku bisharar, ku da kuke a Roma.

Ikon Bishara

16 Gama ba na jin kunyar bishara, domin ita ce ikon Allah mai kai kowane mai ba da gaskiya ga samun ceto, Yahudawa da fari, sa’an nan kuma al’ummai.

17 Gama bishara ɗin ta bayyana wata hanyar samun adalci a gaban Allah, hanyar nan kuwa ta bangaskiya ce, tun daga farko har zuwa ƙarshe, yadda yake a rubuce cewa, “Wanda yake da adalci ta wurin bangaskiya zai rayu.”

Laifin ‘Yan Adam

18 Gama ana bayyana fushin Allah daga Sama, a kan dukan rashin bin Allah, da aikin mugunta na mutanen da suke danne gaskiya, ta aikin muguntarsu,

19 Domin abin da za a iya sani a game da Allah a bayyane yake a gare su, gama Allah ne ya bayyana musu shi.

20 Gama tun daga halittar duniya al’amuran Allah marasa gănuwa, wato ikonsa madawwami, da allahntakarsa, sun fahimtu sarai, ta hanyar abubuwan da aka halitta kuma ake gane su. Saboda haka mutane sun rasa hanzari.

21 Domin kuwa ko da yake sun san da Allah, duk da haka ba su ɗaukaka shi a kan shi Allah ne ba, ba su kuma gode masa ba. Sai tunaninsu ya wofince, zuciyarsu marar fahimta kuma ta duhunta.

22 Suna da’awa cewa, su masu hikima ne, sai suka zama wawaye.

23 Sun sauya ɗaukakar Allah marar mutuwa da misalin siffar mutum mai mutuwa, da ta tsuntsaye, da ta dabbobi, da kuma ta masu jan ciki.

24 Saboda haka Allah ya sallama su ga rashin tsarkaka ta mugayen sha’awace-sha’awacensu, har su wulakanta jikinsu a junansu,

25 saboda sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, har yi wa halitta ibada, sun kuma bauta mata, sun ƙi su yi wa Mahalicci, shi wanda yabo ya tabbata a gare shi har abada. Amin.

26 Don haka Allah ya sallama su ga mugayen sha’awace-sha’awace masu banƙyama, har matansu suka sauya ɗabi’arsu ta halal, da wadda take ta haram.

27 Haka kuma maza suka bar ma’amalarsu ta halal da mata, jarabar juna ta ɗebe su, maza da maza suna aikata rashin kunya, suna jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.

28 Tun da yake sun ƙi su yarda su san Allah, Allah ya sallama su ga halin banza, su aikata abin kunya.

29 Su masu aikata rashin adalci ne ƙwarai, da mugunta, da kwaɗayi, da ƙeta. Masu hassada ne, da kisankai, da jayayya, da ha’inci, da kuma nukura gaya matuƙa. Macizan ƙaiƙayi ne,

30 da masu yanke, da maƙiyan Allah, da masu cin mutunci, da masu girmankai, da masu ruba, da masu haddasa mugunta, da marasa bin iyaye,

31 da marasa fahimta, da masu ta da alkawari, da marasa ƙauna, da marasa tausayi.

32 Waɗannan kuwa ko da yake sun san shari’ar Allah cewa masu yin irin waɗannan abubuwa, sun cancanci mutuwa, duk da haka, ba aikata su kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon masu yinsu.

Categories
ROM

ROM 2

Hukuncin Allah Daidai Ne

1 Saboda haka ba ka da wata hujja, kai mutum, ko kai wane ne da kake ganin laifin wani. A yayin da kake ganin laifin wani, ai, kanka kake hukunta wa, don ga shi, kai mai ganin laifin wani, kai ma haka kake yi.

2 Mun dai san hukuncin Allah a kan masu yin haka daidai ne.

3 Ya kai mutum, kai da kake ganin laifin masu yin haka, alhali kuwa kai kanka, kana yinsu, kana tsammani za ka tsere wa hukuncin Allah ne?

4 Ko kuwa kana raina yalwar alherinsa, da jimirinsa, da kuma haƙurinsa ne? Ashe, ba ka sani ba alherin Allah yana jawo ka zuwa ga tuba?

5 Amma ga shi, saboda ƙeƙasasshiyar zuciyarka marar tuba, kana nema wa kanka fushin Allah a ranar fushi, sa’ad da za a bayyana hukuncin Allah macancani.

6 Allah ne zai saka wa kowa gwargwadon aikinsa.

7 Waɗanda suke neman daraja da ɗaukaka da kuma dawwama ta wurin naciyarsu ga aikata nagarta, zai saka musu da rai madawwami.

8 Waɗanda suke masu sonkai, da waɗanda suke ƙin bin gaskiya, da masu bin rashin adalci, zai saka musu da fushi da hasala.

9 Duk waɗanda suke aikata mugunta za su sha wahala da masifa, da fari Yahudawa, sa’an nan kuma al’ummai.

10 Amma Allah zai ba da daraja, da ɗaukaka, da salama ga dukan waɗanda suke aikata nagarta, da fari ga Yahudawa, sa’an nan ga al’ummai.

11 Domin kuwa, Allah ba ya nuna tara.

12 Ɗaukacin waɗanda suka yi zunubi a rashin sanin Shari’a, za su hallaka ne ba tare da Shari’a ba. Ɗaukacin waɗanda suka yi zunubi a ƙarƙashin Shari’a kuwa, za a hukunta su ta hanyar Shari’a.

13 Don ba ta jin shari’ar kawai mutum yake samun kuɓuta ga Allah ba, sai dai masu aikata ta, su ne za su kuɓuta.

14 In al’ummai, su da ba su da Shari’a, jikinsu ya ba su suka bi umarnin Shari’a, ko da yake ba su da Shari’ar, ashe kuwa, suna da shari’a ke nan.

15 Ayyukansu sun nuna, cewa abin da Shari’a ta umarta a rubuce yake a cikin zukatansu, lamirinsu kuwa yana shaidawa, tunaninsu kuwa yana zarginsu, ko kuma yana kāre su.

16 A wannan rana Allah zai yi wa ‘yan adam shari’a a kan asiransu, ta wurin Yesu Almasihu, bisa ga bishara da nake wa’azinta.

Yahudawa da Shari’a

17 To, in ka ce kai Bayahude ne, cewa ka dogara da Shari’a, har kana taƙama da Allah,

18 ka san abin da yake so, da yake kuma ka karantu da Shari’a, ka iya bambancewa da abubuwa mafifita,

19 har ka amince kai kanka jagoran makafi ne, haske ga waɗanda suke a cikin duhu,

20 mai horon marasa azanci, mai koya wa sababbin shiga, don a cikin Shari’ar kana da ainihin sani da ainihin gaskiya,

21 to, kai mai koya wa wani, ba ka koya wa kanka? Kai mai wa’azin kada a yi sata, shin, kai ba ka yi ne?

22 Kai mai cewa kada a yi zina, kai ba ka yi ne? Kai mai ƙyamar gumaka, ba ka sata a ɗakin gunki ne?

23 Kai mai taƙama da Shari’a, ashe, ba wulakanta Allah kake yi ba ta keta Shari’ar?

24 Yadda yake a rubuce cewa, “A sanadinku ne al’ummai suke saɓon sunan Allah.”

25 Lalle yin kaciya yana da amfani, in dai kana bin Shari’ar. Amma in kai mai keta shari’ar ne, kaciyarka ba a bakin kome take ba.

26 In kuwa marar kaciya yana kiyaye farillan Shari’a, ashe, ba sai a lasafta rashin kaciyarsa a kan kaciya ba?

27 Ashe, wanda rashin kaciya al’adarsa ce, ga shi kuwa, yana bin Shari’ar daidai, ba sai yă kāshe ka ba, kai da kake da Shari’a a rubuce da kuma kaciya, amma kana keta Shari’ar?

28 Gama Bayahude na ainihi ba mutum ne wanda yake Bayahude bisa siffar jikinsa na fili ba, kaciya ta ainihi kuwa ba kaciya ce ta fili ta fatar jiki ba.

29 Wanda yake Bayahude a zuci, ai, shi ne Bayahude. Kaciyar ainihi kuwa a zuci take, wato ta ruhu, ba ta zahiri ba. Irin wannan mutum, Allah ne yake yaba masa, ba ɗan adam ba.

Categories
ROM

ROM 3

1 To, ina fifikon Bayahude? Ko kuma ina fa’idar kaciya?

2 Ai kuwa, akwai ƙwarai, ta kowace hanya. Da farko dai, Yahudawa su ne aka amince wa a game da zantuttukan Allah.

3 To, ƙaƙa ke nan in waɗansu sun ci amanar nan? Sai cin amanarsu ya shafe cikar alkawarin Allah?

4 A’a, ko kusa! A dai tabbata Allah mai gaskiya ne, ko da yake kowane mutum maƙaryaci ne, yadda yake a rubuce cewa,

“Don maganarka tă tabbatar da adalcinka,

Ka kuma yi rinjaye in an binciki al’amarinka.”

5 In kuwa rashin adalcinmu shi ne yake nuna adalcin Allah a fili, me za mu ce? in Allah ya hore mu, ya yi rashin adalci ke nan? (Misali nake yi kawai.)

6 A’a, ko kusa! To, in da haka ne, ta ƙaƙa Allah zai yi wa duniya shari’a?

7 In kuwa, a dalilin ƙaryata, gaskiyar Allah ta ƙara bayyana, har aka kara ɗaukaka shi, to, don me har yanzu ake hukunta ni a kan ni mai zunubi ne?

8 In haka ne, ba sai mu yi ta yin mugun aiki don ya zama sanadin nagarta ba? Kamar yadda dai waɗansu suke mana yanke, cewa haka muke faɗa. Hukuncin da za a yi wa irin waɗannan kuwa daidai ne.

Babu Mai Adalci

9 To, ƙaƙa? Mu Yahudawa mun fi sauran ne? A’a, ko kaɗan! Don dā ma mun ɗora wa Yahudawa da al’ummai laifi, cewa dukkansu zunubi yana iko da su.

10 Kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Babu wani mai adalci, babu, ko ɗaya,

11 Babu wani mai fahimta, babu wani mai neman Allah.

12 Duk sun bauɗe, sun zama marasa amfani baki ɗaya,

Babu wani mai aiki nagari, babu kam, ko da guda ɗaya.”

13 “Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗen kabari ne,

Maganarsu ta yaudara ce.”

“Masu ciwon baki ne.”

14 “Yawan zage-zage da ɗacin baki gare su.”

15 “Masu hanzarin zub da jini ne,

16 Ta ko’ina suka bi sai hallaka da baƙin ciki,

17 Ba su kuma san hanyar salama ba.”

18 “Babu tsoron Allah a cikin sha’aninsu sam.”

19 To, mun sani duk abin da Shari’a ta ce, ya shafi waɗanda suke ƙarƙashinta ne, don a tuƙe hanzarin kowa, duk duniya kuma tă sani ƙarƙashin hukuncin Allah take.

20 Ai, ba wani ɗan adam da zai sami kuɓuta ga Allah ta kiyaye ayyukan Shari’a, tun da yake ta Shari’a ne mutum yake ganin laifinsa.

Adalci ta Wurin Bangaskiya

21 A yanzu, ba kuwa a game da shari’a ba, an bayyana wata hanyar samun adalcin Allah, wadda ma Attaura da littattafan annabawa suke yi wa shaida.

22 Adalcin nan na Allah, wanda yake samuwa ta wurin bangaskiya ga Yesu Almasihu, na masu ba da gaskiya ne dukka, ba kuwa wani bambamci,

23 gama ‘yan adam duka sun yi zunubi, sun kasa kuma ga ɗaukakar Allah.

24 Amma ta wurin alherin da Allah ya yi musu kyauta, sun sami kuɓuta ta wurin fansar da Almasihu Yesu ya yi.

25 Allah kuwa ya ayyana Yesu Almasihu ya zama hadayar sulhu, ta wurin ba da gaskiya ga jininsa. Allah kuwa ya yi haka domin yă nuna adalcinsa ne, domin dā saboda haƙurinsa ya jingine zunuban da aka gabatar,

26 domin a nuna adalcinsa a wannan zamani, wato a bayyana shi kansa mai adalci ne, mai kuɓutar da duk mai gaskatawa da Yesu kuma.

27 To, ina kuma fariyarmu ta shiga? Ina kuwa! Ta wace hanya aka kawar da ita? Ta aikin lada? A’a, sai dai ta hanyar bangaskiya.

28 Domin mun amince, cewa ta bangaskiya ne mutum yake kuɓuta, ba ta kiyaye ayyukan Shari’a ba.

29 Wato Allah, Allahn Yahudawa ne kurum? Ashe, ba na al’ummai ba ne kuma? Hakika na al’ummai ne ma,

30 tun da yake Allah ɗaya ne, zai kuwa kuɓutar da masu kaciya ta wurin bangaskiya, marasa kaciya ma ta wannan bangaskiya.

31 Wato mun soke Shari’a ke nan ta bangaskiyar nan? A’a, ko kusa! Sai tabbatar da ita muka yi.

Categories
ROM

ROM 4

Misali na Ibrahim

1 To, me ke nan za mu ce a game da Ibrahim, kakan kakanninmu?

2 Gama in da Ibrahim ya sami kuɓuta ta aikinsa na lada, ashe kuwa, yana da abin yin taƙama ke nan, amma fa ba a gaban Allah ba.

3 To, me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, bangaskiyar nan tasa kuma aka lasafta ta adalci ce a gare shi.”

4 Wanda yake aikin lada, ladarsa ba kyauta ba ce, sakamakon aikinsa ce.

5 Wanda ba ya aikin lada, amma yana dogararsa ga Allah, wanda yake kuɓutar da masu laifi, akan lasafta bangaskiyar nan tasa adalci ce.

6 Haka kuma Dawuda ya yi maganar albarkar da aka yi wa mutumin da Allah yake lasafta adalci a gare shi, ba don ya yi aikin lada ba,

7 da ya ce,

“Albarka tā tabbata ga waɗanda aka yafe wa laifofinsu,

Waɗanda kuma aka shafe zunubansu,

8 Albarka tā tabbata ga wanda faufau Ubangiji ba zai lasafta zunubansa ba.”

9 To, wannan albarka, masu kaciya ne kawai ake yi wa, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Gama abin da muke cewa shi ne, “Aka lasafta bangaskiyar Ibrahim adalci ce a gare shi.”

10 To, a cikin wane hali aka lasafta masa ita? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa tun ba a yi ba? Ai, tun ba a yi ba ne, ba bayan da aka yi ba.

11 Kaciyar da aka yi masa alama ce, wato tabbatacciyar shaida ce ta samun adalci, albarkacin bangaskiyar da yake da ita tun ba a yi masa kaciya ba. Wannan kuwa, domin yă zama uban dukkan masu ba da gaskiya ne, domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba,

12 haka kuma yă zama uban masu kaciya, waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba, har ma suna bin hanyar bangaskiyar nan ta kakanmu Ibrahim, wadda shi ma ya bi, tun ba a yi masa kaciya ba.

Tabbatar da Alkawari ta Wurin Bangaskiya

13 Alkawarin nan da aka yi wa Ibrahim da zuriyarsa, cewa zai zama magājin duniya, ba ta Shari’a aka yi masa ba, amma domin ya ba da gaskiya ne, shi ya sa Allah ya karɓe shi mai adalci ne.

14 In dai masu bin Shari’a su ne magāda, ashe, bangaskiya ta zama banza ke nan, alkawarin nan kuma ya wofinta,

15 don Shari’a tana jawo fushin Allah. A inda ba Shari’a kuwa, ba keta umarni ke nan.

16 Saboda haka al’amarin ya dogara ga bangaskiya, domin yă zama bisa ga alheri, don kuma a tabbatar da alkawarin nan ga dukkan zuriyar Ibrahim, ba ga masu bin Shari’a kaɗai a cikinsu ba, har ma ga waɗanda suke da bangaskiya irin Ibrahim, shi da yake ubanmu duka.

17 kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na sa ka uban al’ummai da yawa.” Shi ne kuwa ubanmu a gaban Allah, wannan da ya gaskata, wato mai raya matattu, shi ne kuma mai kiran marasa kasancewa kamar sun kasance.

18 Ibrahim kuwa ko da yake ba halin sa zuciya a gare shi, sai ya yi ta sawa, ya gaskata zai zama uban al’ummai da yawa, kamar yadda aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za ta yawaita.”

19 Bangaskiyarsa kuwa ba ta raunana ba, bai dubi gajiyawar jikinsa ba, don yana da shekara wajen ɗari a lokacin, ko kuma cewa Saratu ta wuce haihuwa.

20 Ba kuwa wata rashin bangaskiyar da ta sa shi shakkar cikar alkawarin Allah, sai ma ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa ya yi, yana ɗaukaka Allah,

21 yana haƙƙaƙewa, cewa Allah na da ikon yin abin da ya yi alkawari.

22 Shi ya sa aka lasafta bangaskiyarsa adalci ce a gare shi.

23 To, “lasafta masa” ɗin nan da aka rubuta kuwa, ba saboda Ibrahim kaɗai aka rubuta ba,

24 har saboda mu ma, za a lasafta mana, wato mu da muke gaskatawa da wannan da ya ta da Yesu Ubangijinmu daga matattu,

25 wanda aka bayar a kashe saboda laifofinmu, aka kuma tashe shi, domin mu sami kuɓuta ga Allah.

Categories
ROM

ROM 5

Abubuwan da Kuɓutarwa Take Kawowa

1 To, da yake mu kuɓutattu ne ta wurin bangaskiya, muna da salama ke nan a gun Allah, ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu.

2 Ta wurinsa kuma muka sami shiga alherin nan da muke a ciki, saboda bangaskiyarmu, muna kuma taƙama da sa zuciyarmu ga samun ɗaukakar nan ta Allah.

3 Banda haka ma, har muna taƙama da shan wuyarmu, da yake mun sani shan wuya take sa jimiri,

4 jimiri kuma yake sa ingataccen hali, ingataccen hali kuma yake sa sa zuciya,

5 ita sa zuciyar nan kuwa ba ta sāce iska faufau, domin Allah ya kwarara ƙaunarsa a zukatanmu, ta wurin Ruhu Mai Tsarki da aka ba mu.

6 Tun muna raunana tukuna, Almasihu ya mutu a daidaitaccen lokaci, domin marasa bin Allah.

7 Da ƙyar za a sami wanda zai ba da ransa, saboda mutum mai adalci, ko da yake watakila saboda mutum mai nagarta wani ma sai yă yi kasai da ransa.

8 Amma kuwa Allah yana tabbatar mana da ƙaunar da yake yi mana, wato tun muna masu zunubi, Almasihu ya mutu dominmu.

9 To, tun da yake a yanzu an kuɓutar da mu ta wurin jininsa, ashe kuwa, ta wurinsa za mu fi samun kārewa daga fushin Allah ke nan.

10 In kuwa tun muna maƙiyan Allah aka sulhunta mu da shi ta mutuwar Ɗansa, to, da yake an sulhunta mu, ashe kuwa, za a fi kāre mu ta wurin rayuwarsa ke nan.

11 Banda haka ma, har muna fariya da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ta wurinsa ne muka sami sulhun nan a yanzu.

Adamu da Almasihu

12 To, kamar yadda zunubi ya shigo duniya ta dalilin mutum ɗaya, zunubi kuwa shi ya jawo mutuwa, ta haka mutuwa ta zama gādo ga kowa, don kowa ya yi zunubi.

13 Lalle fa zunubi yana nan a duniya tun ba a ba da Shari’a ba, sai dai inda ba shari’a, ba a lasafta zunubi.

14 Duk da haka kuwa mutuwa ta mallaka tun daga Adamu har ya zuwa Musa, har ma a kan waɗanda ba su yi zunubi irin na keta umarnin da adamu ya yi ba, wanda yake shi ne kwatancin mai zuwan nan.

15 Amma fa baiwar nan dabam take ƙwarai da laifin nan. Ai, in laifin mutum ɗayan nan ya jawo wa masu ɗumbun yawa mutuwa, ashe ma, alherin Allah, da kuma baiwar nan, albarkacin alherin Mutum ɗaya, Yesu Almasihu, sai su yalwata ga masu ɗumbun yawa fin haka ƙwarai.

16 Baiwar nan kuwa dabam take ƙwarai da hakkokin zunubin mutum ɗayan nan. Don kuwa hukuncin da aka yi a kan laifin mutum ɗayan nan, shi ya jawo hukuncin hallaka. Amma baiwar nan da aka yi a sanadin laifofi da yawa, ita take sa kuɓuta ga Allah.

17 In kuwa saboda laifin mutum ɗayan nan ne mutuwa ta yi mallaka ta wurinsa, ashe kuwa, waɗanda suke samun alherin nan mayalwaci, da kuma baiwar nan ta adalcin Allah, sai su yi mallaka fin haka ƙwarai a cikin rai, ta wurin ɗayan nan, wato Yesu Almasihu.

18 To, kamar yadda laifin mutum ɗayan nan ya jawo wa dukan mutane hukunci, haka kuma aikin adalci na Mutum ɗayan nan ya zama wa dukan mutane sanadin kuɓuta zuwa rai.

19 Kamar yadda masu ɗumbun yawa suka zama masu zunubi ta wurin rashin biyayyar mutum ɗaya, haka kuma ta wurin biyayyar Mutum ɗaya za a mai da masu ɗumbun yawa masu adalci.

20 Shari’a fa, an shigo da ita ne, don laifi yă haɓaka. Amma a inda zunubi ya haɓaka, alherin Allah ma ya fi haɓaka ƙwarai da gaske.

21 Wato kamar yadda mallakar zunubi mutuwa ce, haka mallakar Allah ta wurin alheri adalci ce, da take bi da mu zuwa rai madawwami ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu.

Categories
ROM

ROM 6

Mutuwa ga Zunubi, Rayuwa ga Almasihu

1 To, me kuma za mu ce? Ma ci gaba da yin zunubi ne domin alherin Allah yă haɓaka?

2 A’a, ko kusa! Mu da muka mutu ga zunubi, ƙaƙa za mu ƙara rayuwa a cikinsa har yanzu?

3 Ashe, ba ku sani ba duk ɗaukacinmu da aka yi wa baftisma a cikin Almasihu Yesu, a cikin mutuwarsa aka yi mana baftismar ba?

4 Saboda haka, an binne mu da shi ke nan, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa, domin kamar yadda aka ta da Almasihu daga matattu ta wurin ɗaukakar Uba, haka mu ma mu yi zaman sabuwar rayuwa.

5 Tun da yake mun zama ɗaya da shi wajen kwatancin mutuwarsa, ashe kuwa, za mu zama ɗaya ma a wajen tashinsa.

6 Wato, mun sani an gicciye halayenmu na dā tare da shi, domin a hallakar da ikon nan namu mai zunnubi, kada mu ƙara bauta wa zunubi.

7 Wanda ya yi irin wannan mutuwa kuwa, an kuɓutar da shi daga zunubi ke nan.

8 Amma idan muka mutu tare da Almasihu, mun gaskata za mu rayu tare da shi kuma.

9 Mun sani tun da yake an ta da Almasihu daga matattu, ba zai sāke mutuwa ba ke nan, mutuwa ba ta da sauran wani iko a kansa.

10 Mutuwar nan da ya yi kuwa, ya mutu ne sau ɗaya tak ba ƙari, saboda shafe zunubanmu, amma rayuwar da yake yi, yana rayuwa ne, rayuwa ga Allah.

11 Haka ku ma sai ku lasafta kanku kamar ku matattu ne ga zunubi, amma kuna a raye rayuwa ga Allah, ta wurin Almasihu Yesu.

12 Saboda haka, kada ku yarda zunubi yă mallaki jikin nan naku mai mutuwa har da za ku biye wa muguwar sha’awarsa.

13 Kada kuma ku miƙa gaɓoɓinku su zama kayan aikin mugunta, don yin zunubi. Amma ku miƙa kanku ga Allah, kamar waɗanda aka raya bayan mutuwa, kuna miƙa gaɓoɓinku ga Allah kayan aikin adalci.

14 Domin zunubi ba zai mallake ku ba, tun da yake ba shari’a take iko da ku ba alherin Allah ne.

Bayin Adalci

15 To, ƙaƙa? Wato, sai mu yi zunubi don shari’a ba ta iko da mu, sai alherin Allah? A’a, ko kusa!

16 Ba ku sani ba, shi wanda kuke miƙa kanku a gare shi domin yi wa biyayya, lalle ku bayi ne na wanda kuke yi wa biyayya ɗin (ko bautar zunubi wanda ƙarshensa mutuwa ne, ko bautar biyayya wadda ƙarshenta adalci ce)?

17 Amma godiya tā tabbata ga Allah, ko da yake dā can ku bayin zunubi ne, a yanzu kam kuna biyayya da zuciya ɗaya ga irin koyarwar nan da aka yi muku.

18 Da aka ‘yanta ku kuma daga bautar zunubi, kun zama bayin aikin adalci.

19 Mai da magana nake yi irin ta yau da kullum, saboda rarraunar ɗabi’arku. Wato, kamar yadda dā can kuka miƙa gaɓoɓinku ga bautar rashin tsarki, da mugun aiki a kan mugun aiki, haka kuma a yanzu sai ku miƙa gaɓoɓinku ga bautar aikin adalci, domin aikata tsarkakan ayyuka.

20 Sa’ad da kuke bayin zunubi, ba ruwanku da aikin adalci.

21 To, wace fa’ida kuka samu a lokacin nan, a game da aikin da kuke jin kunya a yanzu? Lalle ƙarshen irin wannan aiki mutuwa ne.

22 Amma a yanzu da aka ‘yanta ku daga bautar zunubi, kun zama bayin Allah, sakamakonku shi ne tsarkakewa, ƙarshenta kuwa rai madawwami ne.

23 Gama sakamakon zunubi mutuwa ne, amma baiwar Allah ita ce rai madawwami a cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu.

Categories
ROM

ROM 7

Ƙiyasi da Aure

1 Ya ‘yan’uwa, ko ba ku sani ba, shari’a tana da iko da mutum, muddin yana raye ne kawai? Da waɗanda suka san shari’a fa nake.

2 Misali, mace mai aure, shari’a ta ɗaure ta ga mijinta muddin yana da rai. Amma in mijinta ya mutu, ta kuɓuta daga igiyar auren ke nan.

3 Don haka, muddin mijinta yana da rai, in ta auri wani, sai a kira ta mazinaciya. Amma in mijinta ya mutu, ta kuɓuta daga igiyar wannan aure, ko da ta auri wani kuwa, ita ba mazinaciya ba ce.

4 Haka kuma ‘yan’uwana, kun zama matattu ga Shari’a, ta wurin jikin Almasihu, domin ku zama mallakar wani, wato, wanda aka tashe shi daga matattu, domin mu ba da amfani ga Allah.

5 Ai, dā sa’ad da muke zaman halin mutuntaka, muguwar sha’awa wadda faɗakarwar Shari’a take sa a yi, ita take aiki a gaɓoɓinmu, tă wurin haddasa mutuwa.

6 Amma a yanzu mun ‘yantu daga Shari’a, mun mutu daga abin da dā ya ɗaure mu ke nan, har muna iya bauta wa Allah da sabon rai da Ruhu, ba da tsofaffin rubutattun ka’idodi ba.

Damuwa wadda Zunubin da Yake a Cikinmu Take Haddasawa

7 To, me kuma za mu ce? Shari’a zunubi ce? A’a, ko kusa! Amma kuwa duk da haka, da ba domin Shari’a ba, da ban san zunubi ba. Da ba domin Shari’a ta ce, “Kada ka yi ƙyashi” ba, da ban san ƙyashi ba.

8 Amma zunubi, da ya sami ƙofa ta hanyar umarni, sai ya haddasa ƙyashi iri iri a zuciyata. Gama da ba domin shari’a ba, da zunubi ba shi da wani tasiri.

9 Dā kam, sa’ad da ban san shari’a ba, ni rayayye ne, amma da na san umarnin, sai zunubi ya rayu, ni kuma sai na mutu.

10 Umarnin nan kuwa, wanda manufarsa a gare ni rai ne, sai ya jawo mini mutuwa.

11 Don kuwa zunubi ya sami ƙofa ta hanyar umarni, sai ya yaudare ni, ta wurinsa kuwa ya kashe ni.

12 Domin haka Shari’a da kanta mai tsarki ce, umarnin kuma mai tsarki ne, daidai ne, nagari ne.

13 Wato, abar nan da take tagari ta jawo mini mutuwa ke nan? A’a, ko kusa! Zunubi ne ya jawo, domin ya bayyana kansa shi zunubi ne, gama ta wurin abar nan tagari ya jawo mini mutuwa, ta dalilin umarnin nan kuma, zunubi ya bayyana matuƙar muninsa.

14 Mun dai san Shari’a aba ce ta ruhu, ni kuwa mai halin mutuntaka ne, bautar zunubi kawai nake yi.

15 Ban ma fahimci abin da nake yi ba. Don ba abin da nake niyya yi, ba shi nake aikatawa ba, abin da nake ƙi, shi nake yi.

16 To, idan abin da ba na niyya, shi nake yi, na yarda ke nan Shari’a aba ce mai kyau.

17 Ashe kuwa, ba ni nake yinsa ba ke nan, zunubin da ya zaune mini ne.

18 Don na sani ba wani abin kirki da ya zaune mini, wato a jikina. Niyyar yin abin da yake daidai kam, ina da ita, sai dai ikon zartarwar ne babu.

19 Nagarin abin da nake niyya yi kuwa, ba shi nake yi ba, sai dai mugun abin da ba na niyya, shi nake aikatawa.

20 To, idan abin da ba na niyya shi nake yi, ashe kuwa, ba ni nake yinsa ba ke nan, zunubin da ya zaune mini ne.

21 Sai na ga, ashe, ya zama mini ka’ida, in na so yin abin da yake daidai, sai in ga mugunta tare da ni.

22 Ni kam, a birnin zuciyata, na amince da shari’ar Allah.

23 Amma ina ganin wata ka’ida dabam a gaɓoɓina, wadda take yaƙi da ka’idar da hankalina ya ɗauka, har tana mai da ni bawan ƙa’idar nan ta zunubi wadda take zaune a gaɓoɓina.

24 Kaitona! Wa zai cece ni daga jikin nan, wanda yake kai ni ga mutuwa?

25 Godiya tā tabbata ga Allah, akwai, ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu! Ashe kuwa, ni a kaina, da hankalina, hakika Shari’ar Allah nake bauta wa, amma da jikina ka’idar zunubi nake bauta wa.

Categories
ROM

ROM 8

Rayuwa a Cikin Ruhu

1 Saboda haka a yanzu, ba sauran kayarwa ga waɗanda suke na Almasihu Yesu.

2 Ka’idar nan ta Ruhu mai ba da rai da yake ga Almasihu Yesu ta ‘yanta ni daga ka’idar zunubi da ta mutuwa.

3 Abin da ba shi yiwuwa Shari’a ta yi domin ta kasa saboda halin ɗan adam, Allah ya yi shi, wato ya ka da zunubi a cikin jiki, da ya aiko da Ɗansa da kamannin jikin nan namu mai zunubi, domin kawar da zunubi.

4 Wannan kuwa domin a cika hakkokin Shari’a ne a gare mu, mu da ba zaman halin mutuntaka muke yi ba, sai dai na Ruhu.

5 Masu zaman halin mutuntaka, ai, ƙwallafa ransu ga al’amuran halin mutuntaka suke yi, masu zaman Ruhu kuwa ga al’amuran Ruhu.

6 Ƙwallafa rai ga al’amuran halin mutuntaka ƙarshensa mutuwa ne, ƙwallafa rai ga ala’muran Ruhu kuwa rai ne da salama.

7 Don ƙwallafa rai ga al’amuran halin mutuntaka gāba ne da Allah, gama ba ya bin Shari’ar Allah, ba kuwa zai iya ba.

8 Masu zaman halin mutuntaka, ba dama su faranta wa Allah rai.

9 Amma ku kam, ba masu zaman halin mutuntaka ba ne, masu zaman Ruhu ne, in dai har Ruhun Allah yana zaune a zuciyarku. Duk wanda ba shi da Ruhun Almasihu kuwa, ba na Almasihu ba ne.

10 In kuwa Almasihu yana a zuciyarku, ba ruwan jikinku da zunubi ke nan, Ruhu kuwa rai ne a gare ku saboda kun sami adalcin Allah.

11 In kuwa Ruhun wannan da ya ta da Yesu daga matattu yana zaune a zuciyarku, to, shi da ya ta da Almasihu Yesu daga matattu zai kuma raya jikin nan naku mai mutuwa, ta wurin Ruhunsa da yake a zaune a zuciyarku.

12 Domin haka, ‘yan’uwa, kun ga halin mutuntaka ba shi da wani hakki a kanmu har da za mu yi zamansa.

13 In kuna zaman halin mutuntaka, za ku mutu ke nan, amma in da ikon Ruhu kuka kashe ayyukan nan na halin mutuntaka, sai ku rayu.

14 Duk waɗanda Ruhun Allah yake bishe su, su ne ‘ya’yan Allah.

15 Ai, ruhun da kuka samu ba na bauta ba ne, har da za ku koma zaman tsoro. A’a, na zaman ‘ya’ya ne, har muna kira, “Ya Abba! Uba!”

16 Ruhu da Kansa ma, tare da namu ruhu suna yin shaida, cewa mu ‘ya’yan Allah ne.

17 In kuwa ‘ya’ya muke, ashe, magāda ne kuma, magādan Allah, abokan gādo kuma da Almasihu, in dai har muna shan wuya tare da shi, a kuwa ɗaukaka mu tare da shi.

18 Ai, a ganina, wuyar da muke sha a wannan zamani, ba ta isa a kwatanta ta da ɗaukakar da za a bayyana mana ba.

19 Ga shi, duk halitta tana marmari, tana ɗokin ganin bayyanar ‘ya’yan Allah.

20 An sarayar da halitta ta zama banza, ba da nufinta ba, amma da nufin wanda ya sarayar da ita. Duk da haka, akwai sa zuciya,

21 gama za a ‘yantar da halitta da kanta ma, daga bautar ruɓewa, domin ta sami ‘yancin nan, na ɗaukaka na ‘ya’yan Allah.

22 Mun dai san dukan halitta tana nishi, na shan azaba kuma irin ta mai naƙuda, har ya zuwa yanzu.

23 Banda haka ma, har mu kanmu da muka riga muka sami Ruhu Mai Tsarki, wanda yake shi ne nunan fari, a cikin abubuwan da za mu samu, muna nishi a ranmu, muna ɗokin cikar zamanmu na ‘ya’yan Allah, wato, fansar jikin nan namu ke nan.

24 Sa’ad da aka cece mu ne muka yi wannan sa zuciya. Amma kuwa, ai, sa zuciya ga abin da aka samu, ba sa zuciya ba ce. Wa yake sa zuciya ga abin da ya samu?

25 In kuwa muna sa zuciya ga abin da ba mu samu ba, da jimiri mukan yi sauraronsa.

26 Haka kuma Ruhu yake yi mana taimako a kan gajiyawarmu, domin ba mu ma san abin da ya kamata mu roƙa ba, amma Ruhu da kansa yana yi mana roƙo da nishe-nishen da ba su hurtuwa.

27 Amma shi mai fayyace zukatanmu ya san abin da Ruhu yake niyya, domin bisa ga nufin Allah ne Ruhu yake yi wa tsarkaka roƙo.

Mun Zarce A Ce da Mu Masu Nasara Ne

28 Mun kuma sani al’amura duka suna aikatawa tare, zuwa alheri ga waɗanda suke ƙaunar Allah, wato, waɗanda suke kirayayyu bisa ga nufinsa.

29 Waɗanda Allah ya riga ya zaɓa tun tuni, su ne ya ƙaddara su ɗauki kamannin Ɗansa, domin shi Ɗan yă zama na farko a cikin ‘yan’uwa masu yawa.

30 Waɗanda ya ƙaddarar nan kuwa, su ne ya kira. Waɗanda ya kira kuwa, su ne ya kuɓutar. Waɗanda ya kuɓutar ɗin kuwa, su ne ya ɗaukaka.

31 To, me kuma za mu ce a game da haka? Da yake Allah yana goyon bayanmu, wa kuwa zai iya gāba da mu?

32 Shi da bai hana Ɗansa ba, sai ma ya ba da shi saboda mu duka, ashe, ba zai ba mu kome tare da shi hannu sake ba?

33 Wa zai ɗora wa zaɓaɓɓun Allah laifi? Allah ne yake kuɓutar da su!

34 Wa zai hukunta su? Almasihu Yesu wanda ya mutu, ko kuwa a ce wanda ya tashi daga matattu, shi ne wanda yake zaune dama ga Allah, shi ne kuwa wanda yake roƙo saboda mu!

35 Wa zai iya raba mu da ƙaunar da Almasihu yake yi mana? Ƙunci ne? ko masifa? ko tsanani? ko yunwa? ko huntanci? ko hatsari? ko takobi?

36 Kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Saboda kai ne ake kashe mu yini zubur,

An lasafta mu kamar tumakin yanka.”

37 Duk da haka kuwa a cikin wannan hali duka, har mun zarce ma a ce mana masu nasara, ta wurin wannan da ya ƙaunace mu.

38 Domin na tabbata, ko mutuwa ce, ko rai, ko mala’iku, ko manyan mala’iku, ko al’amuran yanzu, ko al’amura masu zuwa, ko masu iko,

39 ko tsawo, ko zurfi, kai, ko kowace irin halitta ma, ba za su iya raba mu da ƙaunar da Allah yake yi mana ta wurin Almasihu Yesu Ubangijinmu ba.

Categories
ROM

ROM 9

Allah Ya Zaɓi Isra’ila

1 Gaskiya nake faɗa, ni na Almasihu ne, ba ƙarya nake yi ba. Lamirina, ta wurin Ruhu Mai Tsarki, yana ba da shaida,

2 cewa ina da matuƙar baƙin ciki da kuma takaici marar yankewa a zuciyata.

3 Da ma a la’ance ni, a raba ni da Almasihu saboda dangina, ‘yan’uwana na kabila!

4 Su ne Isra’ilawa. Da zama ‘ya’yan Allah, da ganin ɗaukakarsa, da alkawaran nan, da baiwar Shari’a, da ibada, da kuma sauran alkawarai, duk nasu ne.

5 Kakannin kakannin nan kuma nasu ne, Almasihu kuma, ta wurin zamansa mutum, na kabilarsu ne. Yabo yā tabbata ga Allah har abada, shi da yake bisa kome. Amin.

6 Ba cewa Maganar Allah ta fādi ba, don ba duk zuriyar Isra’ila ne suke Isra’ilawa na gaske ba.

7 Ba kuwa duk su ne ‘ya’yan Ibrahim ba, wai don suna zuriyarsa. Amma an ce, “Ta wurin Ishaku ne za a lasafta zuriyarka.”

8 Wato, zaman zuriyar Ibrahim, ba shi ne zama ‘ya’yan Allah ba, a’a, zuriya ta alkawarin nan su ne ake lasaftawa zuriyar Ibrahim.

9 Alkawarin kuwa shi ne, “Baɗi war haka zan dawo, Saratu kuma za ta haifi ɗa.”

10 Banda haka ma, sa’ad da Rifkatu ta yi ciki da mutumin nan ɗaya, wato, kakanmu Ishaku,

11 tun ba ta haifi ‘ya’yan ba, balle su yi wani abu mai kyau ko marar kyau–don nufin Allah bisa ga zaɓensa ya tabbata, ba ga aikin lada ba, sai dai ga kiransa–

12 aka ce mata, “Wan zai bauta wa ƙanen.”

13 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yakubu na so, Isuwa na ƙi.”

14 To, me kuma za mu ce? Allah ya yi rashin adalci ke nan? a’a, ko kusa!

15 Domin ya ce wa Musa, “Wanda zan yi wa jinƙai, zan yi masa jinƙan, wanda zan nuna wa tausayi kuwa, zan nuna masa tausayin.”

16 Ashe kuwa, abin bai danganta ga nufin mutum ko himma tasa ba, sai dai ga jinƙan Allah.

17 Don a Nassi an ce da Fir’auna, “Na girmama ka ne musamman, domin in nuna ikona a kanka, domin kuma a sanar da sunana a duniya duka.”

18 Wato, yana nuna jinƙai ga wanda ya so, yana kuma taurara zuciyar wanda ya so.

19 Kila ka ce mini, “To, don me har yanzu yake ganin laifi? Wa zai iya tsayayya da nufinsa?”

20 Ya kai ɗan adam! Wane ne kai har da za ka yi jayayya da Allah? Ashe, abin da aka gina zai iya ce wa magininsa, “Don me ka yi ni haka?”

21 Ashe, maginin tukwane ba ya iko da yumɓu, ya gina wata domin aiki mai martaba, wata kuma don kasasshen aiki, duk daga curi ɗaya?

22 To, ƙaƙa fa? Allah da yake yana so ya nuna fushinsa, ya kuma bayyana ikonsa, sai ya haƙura matuƙar haƙuri da waɗanda suka cancanci fushinsa, suka kuma isa hallaka,

23 Nufinsa ne yă bayyana yalwar ɗaukakarsa ga waɗanda ya yi wa jinƙai, wato, waɗanda dā ma ya yi wa tanadin ɗaukaka?

24 Wato, mu ke nan da ya kira, ba kuwa daga cikin Yahudawa kaɗai ba, har ma daga cikin al’ummai.

25 Kamar dai yadda ya faɗa a Littafin Yusha’u cewa,

“Waɗanda dā ba jama’ata ba,

Zan ce da su ‘jama’ata,’

Wadda dā ba abar ƙaunata ba kuma,

Zan ce da ita ‘abar ƙaunata.’ ”

26 “A daidai wurin da aka ce da su, ‘Ku ba jama’ata ba ne,’

A nan ne za a kira su ‘’ya’yan Allah Rayayye,’ ”

27 A game da Isra’ila Ishaya ma ya ɗaga murya ya ce, “Ko da yake yawan Isra’ilawa ya kai kamar yashin teku, duk da haka kaɗan ne za su sami ceto.

28 Domin Ubangiji zai zartar da hukuncinsa a duniya, ya gama shi tashi ɗaya.”

29 Kamar yadda Ishaya ya yi faɗa cewa,

“Da ba domin Ubangijin Runduna ya bar mana zuriya ba,

Da mun zama kamar Saduma,

An kuma maishe mu kamar Gwamrata.”

Isra’ila da Bishara

30 To, me kuma za mu ce? Ga shi, al’ummai da ba su nace da neman adalcin Allah ba, sun samu, wato, sun sami adalcin da yake daga bangaskiya.

31 Isra’ila kuwa da suka nace da neman hanyar adalcin Allah, suka kasa samunta.

32 Me ya sa? Don ba su neme ta ta hanyar bangaskiya ba, sai dai ta hanyar aikata aikin lada. Sai suka yi tuntuɓe da dutsen tuntuɓe,

33 kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Ga shi, na sa dutsen sa tuntuɓe a Sihiyona,

Da fā na sa faɗuwa.

Duk mai gaskatawa da shi, ba zai kunyata ba.”

Categories
ROM

ROM 10

1 Ya ‘yan’uwa, muradin zuciyata da kuma roƙona ga Allah saboda su, shi ne su sami ceto.

2 Na dai shaida su a kan suna da himmar bauta wa Allah, amma ba da cikakken sani ba.

3 Don saboda rashin fahimtar hanyar samun adalci, wadda Allah ya tanadar, da kuma neman kafa tāsu hanya, sai suka ƙi bin ita wannan hanya ta samun adalci wadda Allah ya tanadar.

4 Domin Almasihu shi ne cikamakin Shari’a, domin kowane mai ba da gaskiya yă sami adalcin Allah.

5 Gama Musa ya rubuta zancen adalcin da yake samuwa ta wurin bin Shari’a, cewa mai iya aikata ta zai rayu ta wurinta.

6 Amma, a game da samun adalcin Allah wanda yake ta wurin bangaskiya ya ce, Kada ka ce a ranka, “Wa zai hau zuwa sama?” Wato, yă sauko da Almasihu.

7 Ko kuwa, “Wa zai gangara can ƙasa?” Wato yă ta da Almasihu daga matattu.

8 Amma me Nassi ya ce? “Maganar, ai, tana kusa da kai, tana ma a bakinka, da kuma a cikin zuciyarka.” Ita ce maganar bangaskiya da muke wa’azi.

9 Wato, in kai da bakinka ka bayyana yarda, cewa Yesu Ubangiji ne, ka kuma gaskata a zuciyarka Allah ya tashe shi daga matattu, za ka sami ceto.

10 Domin da zuci mutum yake gaskatawa yă sami adalcin Allah, da baki yake shaidawa yă sami ceto.

11 Gama Nassi ya ce, “Duk mai gaskatawa da shi ba zai kunyata ba.”

12 Ai, ba wani bambanci a tsakanin Bayahude da Ba’al’umme. Ubangijin nan ɗaya shi ne Ubangijin kowa, mayalwacin baiwa ne kuma ga dukkan masu addu’a a gare shi.

13 “Duk wanda kuwa ya yi addu’a da sunan Ubangiji zai sami ceto.”

14 Amma ta ƙaƙa za su yi addu’a ga wanda ba su gaskata da shi ba? Ta ƙaƙa kuma za su gaskata da wanda ba su taɓa ji ba? Ta ƙaƙa kuma za su ji, in ba mai wa’azi?

15 Ta ƙaƙa kuma za su yi wa’azi, in ba aikarsu aka yi ba? Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yaya zai kasance a isowar masu kawo bishara!”

16 Amma ba duka ne suka yi na’am da bisharar ba. Ishaya ma ya ce, “Ya Ubangiji, wa ya gaskata jawabinmu?”

17 Ashe, bangaskiya ta wurin jawabin da ake ji take samuwa, jawabin da ake ji kuma ta Maganar Almasihu yake.

18 Amma ina tambaya. Ba su ji jawabin ba ne? Hakika sun ji.

“Muryarsu ta gama duniya duka,

Maganarsu kuma ta kai har bangon duniya.”

19 Har wa yau, ina tambaya. Shin, Isra’ila kam, ba su fahimta ba ne? Da farko dai Musa ya ce,

“Zan sa ku kishin waɗanda ba al’umma ba ne,

Zan kuma sa ku fushi da wata al’ummar marar fahimta.”

20 Ishayan kuma ya fito gabagaɗi ƙwarai ya ce,

“Waɗanda ba su neme ni ba, su suka same ni.

Na bayyana kuma ga waɗanda ba su taɓa neman sanina ba.”

21 Amma a game da isra’ila, sai ya ce, “Yini zubur ina miƙa hannuwana ga jama’a marasa biyayya, masu tsayayya.”