Categories
W. YAH

W. YAH 11

Shaidu Biyu Ɗin

1 Sa’an nan aka ba ni wata gora kamar sanda, aka kuma ce mini, “Tashi ka auna Haikalin Allah, da bagadin hadaya, da kuma masu sujada a ciki,

2 amma kada ka auna harabar Haikalin, ka ƙyale ta, domin an ba da ita ga al’ummai, za su tattake tsattsarkan birnin nan har wata arba’in da biyu.

3 Zan kuma bai wa mashaidana biyu iko su yi annabci kwana dubu da metan da sittin, suna a saye da tsummoki.”

4 Waɗannan su ne itatuwan zaitun ɗin nan guda biyu, da fitilun nan biyu da suke a tsaye a gaban Ubangijin duniya.

5 In kuwa wani yana da niyyar cutarsu, sai wuta ta huro daga bakinsu, ta lashe maƙiyansu, duk mai niyyar cutarsu kuwa, ta haka ne lalle za a kashe shi.

6 Suna da ikon hana ruwan sama, don kada a yi ruwa a duk kwanakin da suke yin annabci, suna kuma da iko a kan ruwa, su mai da shi jini, su kuma ɗora wa duniya kowane irin bala’i, a duk lokacin da suke so.

7 Bayan da suka ƙare shaidarsu, sai wata dabba mai fitowa daga mahallaka tă yaƙe su, ta cinye su, ta kashe su,

8 a kuma bar gawawwakinsu a kan hanyar babban birnin nan da ake kira Saduma da Masar ga ma’ana ta ruhu, a inda aka gicciye Ubangijinsu.

9 Mutanen dukkan jama’a, da kabila, da harshe, da al’umma za su riƙa kallon gawawwakinsu, har kwana uku da rabi, su kuwa ƙi yarda a binne su.

10 Mazaunan duniya kuma, sai su yi ta alwashi a kansu, suna ta shagali, suna a’aika wa juna da kyauta, domin annabawan nan biyu dā sun azabtar da mazaunan duniya.

11 Amma bayan kwana uku da rabin nan, sai numfashin rai daga wurin Allah ya shiga a cikinsu, suka tashi a tsaye, matsanancin tsoro kuwa ya rufe waɗanda suka gan su.

12 Sai suka ji wata murya mai ƙara daga sama tana ce musu, “Ku hawo nan!” Sai suka tafi sama a cikin gajimare, maƙiyansu suna gani.

13 A nan tāke sai aka yi wata babbar rawar ƙasa, sai ushirin garin ya zube, mutum dubu bakwai aka kashe a rawar ƙasar, sauran kuwa suka tsorata, suka ɗaukaka Allah Mai Sama.

14 Bala’i na biyu ya wuce, ga kuma bala’i na uku yana zuwa nan da nan.

Ƙaho na Bakwai

15 Sa’an nan mala’ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji waɗansu muryoyi masu ƙara a Sama, suna cewa, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Almasihunsa, shi kuma zai yi mulki har abada abadin.”

16 Sai dattawan nan ashirin da huɗu da suke a zaune a kan kursiyansu a gaban Allah suka fādi suka yi wa Allah sujada,

17 Suna cewa,

“Mun gode maka, ya Ubangiji Allah, Maɗaukaki,

Wanda yake a yanzu, shi ne kuma a dā,

Saboda ka ɗauki ikonka mai girma, kana mulki.

18 Al’ummai sun husata, fushinka kuwa ya auko,

Lokaci ya yi da za a yi wa matuttu shari’a,

A kuma yi wa bayinka, annabawa da tsarkaka sakamako,

Da masu jin tsoron sunanka, yaro da babba,

A kuma hallaka masu hallaka duniya.”

19 Sa’an nan aka buɗe Haikalin nan na Allah da yake a Sama, aka kuma ga akwatin alkawarinsa a Haikalinsa. Sai aka yi ta walƙiya da kururuwa, da aradu, da rawar ƙasa, da ƙanƙara manya manya.

Categories
W. YAH

W. YAH 12

Wata Mace da Macijin

1 Aka kuma ga wata babbar alama a sama, wata mace tana a lulluɓe da rana, tana a tsaye a kan wata, da kuma kambi mai taurari goma sha biyu a kanta.

2 Tana da ciki, sai kuma ta yi ta ƙara ta ƙagauta domin ta haihu, saboda azabar naƙuda.

3 Sai kuma aka ga wata alama a sama, ga wani ƙaton jan maciji mai kawuna bakwai, da ƙahoni goma, da kambi bakwai a kawunansa.

4 Wutsiyarsa ta sharo sulusin taurari, ta zuba su a ƙasa. Sai macijin ya tsaya a gaban matar nan mai naƙuda, don ya lanƙwame ɗan nata in ta haife shi.

5 Ta kuwa haifi ɗa namiji, wanda zai mallaki dukkan al’ummai da sandar ƙarfe, amma aka fyauce ɗan nata, aka kai shi zuwa wurin Allah da kursiyinsa.

6 Matar kuwa, sai ta gudu ta shiga jeji, a inda Allah ya shirya mata wurin da za a cishe ta har kwana dubu da metan da sittin.

7 Sai yaƙi ya tashi a sama, Mika’ilu da mala’ikunsa suna yaƙi da macijin nan, macijin kuma da mala’ikunsa suka yi ta yaƙi,

8 amma aka cinye su, har suka rasa wuri a sama sam.

9 Sai aka jefa ƙaton macijin nan a ƙasa, wato macijin nan na tun dā dā, wanda ake kira Ibilis da Shaiɗan, mayaudarin dukkan duniya, aka jefa shi a duniya, mala’ikunsa ma aka jefa su tare da shi.

10 Sai na ji wata murya mai ƙara a Sama tana cewa, “A yanzu fa, ceto, da ƙarfi, da mulki na Allahnmu, da kuma ikon Almasihunsa sun bayyana, don an jefa mai ƙarar ‘yan’uwanmu a ƙasa, shi da yake ƙararsu dare da rana a gun Allahnmu.

11 Sun kuwa yi nasara da shi albarkacin jinin Ɗan Ragon nan, da kuma albarkacin maganar da suka shaida, domin ba su yi tattalin ransu ba, har abin ya kai su ga kisa.

12 Saboda haka, sai ku yi farin ciki, ya ku sammai, da ku mazauna a ciki. Amma kaitonku, ke ƙasa, da kai teku, don Ibilis ya sauko gare ku da matsanancin fushi, don ya san lokacinsa ya ƙure.”

13 Da macijin nan ya ga an jefa shi a ƙasa, ya fafari matar nan da ta haifi ɗa namiji, da tsanani.

14 Amma aka ba matar fikafikan nan biyu na babban juhurman nan, don ta tashi ta guje wa macijin nan, ta shiga jeji, ta je wurin da za a cishe ta a lokaci ɗaya, da lokatai, da rabin lokaci.

15 Sai macijin ya kwarara ruwa daga bakinsa kamar kogi daga bayan matar, don ya share ta da ambaliya.

16 Amma ƙasa ta taimaki matar, ita ƙasar ta buɗe bakinta ta shanye kogin da macijin nan ya kwararo daga bakinsa.

17 Macijin kuwa ya yi fushi da matar, ya tafi ya ɗaura yaƙi da sauran zuriyarta, wato, waɗanda suke kiyaye umarnin Allah, suke kuma shaidar Yesu. Sai ya tsaya a kan yashin teku.

Categories
W. YAH

W. YAH 13

Dabbobi Biyu Ɗin

1 Na kuma ga wata dabba tana fitowa daga cikin teku, mai ƙaho goma, da kawuna bakwai, da kambi goma a kan ƙahoninta, da kuma wani suna na saɓo a kawunanta.

2 Dabbar da na gani kuwa kamar damisa take, ƙafafunta kamar na beyar, bakinta kuma kamar na zaki. Macijin kuwa ya ba ta ƙarfinsa, da kursiyinsa, da ikonsa mai girma.

3 Ɗaya daga cikin kawunanta, an yi masa rauni kamar na ajali, amma rauninsa mai kamar na ajalin nan ya warke. Sai dabbar ta ɗauke wa duk duniya hankali, suna mamaki,

4 har suka yi wa macijin nan sujada, don shi ne ya bai wa dabbar ikonsa, suka kuma yi wa dabbar sujada, suna cewa, “Wa ya yi kama da dabbar nan? Wa kuma zai iya yaƙi da ita?”

5 An kuwa ba dabbar nan baki, tana fariya da maganganun saɓo, aka kuma yardar mata ta zartar da iko, har wata arba’in da biyu.

6 Sai ta buɗe bakinta don ta saɓi Allah, ta yi ta saɓon sunansa, da wurin zamansa, da waɗanda suke a zaune a Sama.

7 Aka kuma yardar mata ta yaƙi tsarkaka, ta cinye su. Aka kuma ba ta iko a kan kowace kabila, da jama’a, da harshe, da al’umma.

8 Duk mazaunan duniya kuma, za su yi mata sujada, wato, duk wanda, tun farkon duniya, ba a rubuta sunansa a Littafin Rai na Ɗan Ragon nan da yake Yankakke ba.

9 Duk mai kunnen ji, yă ji.

10 Kowa aka ƙaddara wa bauta, sai ya je aikin bautar.

Kowa kuwa ya yi kisa da takobi, to, kuwa da takobi za a kashe shi lalle.

Wannan yana nuna jimiri da bangaskiya na tsarkaka.

11 Sa’an nan na ga wata dabba na fitowa daga cikin ƙasa. Tana da ƙaho biyu kamar na ɗan rago, maganarta kuwa kamar ta macijin nan.

12 Tana zartar da duk ikon dabbar nan ta farko, a kan idonta, tana kuma sa duniya da duk mazauna a cikinta, su yi wa dabbar nan ta farko sujada, wadda aka warkar mata da rauninta mai kamar na ajali.

13 Tana yin manyan abubuwan al’ajabi, har ma tana sa wuta ta zuba a ƙasa daga sama, a gaban idon mutane.

14 Tana kuma yaudarar mazaunan duniya, da abubuwan al’ajabin nan da aka yardar mata ta yi a gaban dabbar nan, tana umartarsu, su yi wata siffa saboda dabbar nan wadda aka yi wa rauni da takobi, ta kuwa rayu.

15 An kuma yardar mata ta busa wa siffar dabbar nan rai, har siffar dabbar nan ma ta iya yin magana, ta kuma sa a kashe waɗanda suka ƙi yi wa siffar dabbar nan sujada.

16 Har wa yau, sai ta sa a yi wa kowa alama a hannun dama, ko a goshi, manya da yara duka, mawadata da matalauta, ɗa da bawa,

17 har ba mai iya saye ko sayarwa sai ko yana da alamar nan, wato, sunan dabbar nan, ko kuwa lambar sunanta.

18 Wannan abu sai a game da hikima. Duk mai basira ya ƙididdige lambar dabbar nan, don lamba ce ta wani mutum, lambar kuwa ɗari shida ce da sittin da shida.

Categories
W. YAH

W. YAH 14

Waƙar 144,000 Ɗin

1 Sa’an nan na duba, sai ga Ɗan Ragon nan a tsaye a kan Dutsen Sihiyona, akwai kuma mutum dubu ɗari da dubu arba’in da huɗu tare da shi, waɗanda aka rubuta sunansa, da sunan Ubansa, a goshinsu.

2 Sai na ji wata murya daga Sama kamar ƙugin ruwa mai gudu, kamar aradu mai ƙara, muryar da na ji kuwa, kamar ta masu molo ce na kiɗan molo.

3 Suna raira wata sabuwar waƙa a gaban kursiyin, a gaban rayayyun halittan nan huɗu, da kuma a gaban dattawan nan. Ba mai iya koyon waƙar nan, sai mutum dubu ɗari da dubu arba’in da huɗu ɗin nan, waɗanda aka fanso daga duniya.

4 Waɗannan su ne waɗanda ba su taɓa ƙazantuwa da fasikanci ba, domin su tsarkaka ne. Su ne kuma suke bin Ɗan Ragon a duk inda ya je. Su ne kuma aka fanso daga cikin mutane a kan su ne nunan fari na Allah, da na Ɗan Ragon nan kuma,

5 ba wata ƙarya a bakinsu, domin su marasa aibu ne.

Sanarwar Mala’iku Uku Ɗin

6 Sa’an nan na ga wani mala’ika yana kaɗawa a tsakiyar sararin sama, yana tafe da madawwamiyar bishara, domin ya sanar da ita ga mazaunan duniya, wato, ga kowace al’umma, da kabila, da harshe, da jama’a.

7 Sai ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Ku ji tsoron Allah, ku ɗaukaka shi, domin lokacinsa na yin hukunci ya yi. Ku yi masa sujada, shi da ya halicci sama, da ƙasa, da teku, da kuma maɓuɓɓugan ruwa.”

8 Sai kuma mala’ika na biyu ya biyo, yana cewa, “Ta fāɗi! Babila mai girma ta fāɗi! Ita da ta zuga dukkan al’ummai su yi tsananin jarabar yin fasikanci da ita.”

9 Sai kuma mala’ika na uku ya biyo, yana ɗaga murya da ƙarfi, yana cewa, “Duk mai yi wa dabbar nan da siffarta sujada, wanda kuma ya yarda a yi masa alama a goshinsa, ko a hannunsa,

10 zai ci karo da azabar Allah tsantsa ta tsananin fushinsa, za a kuwa azabta shi da wuta, da duwatsun wuta, a gaban mala’iku tsarkaka, da kuma Ɗan Ragon.

11 Hayaƙin azabar nan tasu ya dinga tashi har abada abadin, ba su da wani rangwame dare da rana, wato, waɗannan masu yi wa dabbar nan da siffarta sujada, da kuma duk wanda ya yarda aka yi masa alamar sunanta.”

12 Wannan yana nuna jimirin tsarkaka, masu kiyaye umarnin Allah da kuma bangaskiya ga Yesu.

13 Sai kuma na ji wata murya daga Sama tana cewa, “Rubuta wannan. Albarka tā tabbata ga matattu, wato, waɗanda za su mutu a nan gaba a kan su na Ubangiji ne.” Ruhu ya ce, “Hakika, masu albarka ne, domin su huta daga wahalarsu, gama aikinsu yana a biye da su!”

Girbe Duniya

14 Sa’an nan na duba, sai ga wani farin gajimare, da wani kamar Ɗan Mutum a zaune a kan gajimaren, da kambin zinariya a kansa, da kakkaifan lauje a hannunsa.

15 Sai mala’ika ya fito daga Haikalin, yana magana da murya mai ƙarfi da wanda yake a zaune a kan gajimaren, yana cewa, “Ka sa laujenka ka yanke, don lokacin yanka ya yi, amfanin duniya ya nuna sarai.”

16 Sai wanda yake a zaune a kan gajimaren ya wurga laujensa zuwa duniya, aka girbe amfanin duniya.

17 Wani mala’ika kuma ya fito daga Haikali a Sama, shi ma kuwa yana da kakkaifan lauje.

18 Sai kuma wani mala’ika ya fito daga bagadin ƙona turare, wato, mala’ikan da yake da iko da wutar, ya yi magana da murya mai ƙarfi da wannan mai kakkaifan lauje, ya ce, “Ka sa laujenka ka yanke nonnan inabin zuwa duniya, don inabin ya nuna.”

19 Sai mala’ikan ya wurga laujensa duniya, ya tattara inabin duniya, ya zuba a cikin babbar mamatsar inabi ta fushin Allah.

20 Aka tattake mamatsar inabin a bayan gari, jini kuma ya yi ta gudana daga mamatsar inabin, ya kai kamar tsawon linzami a bakin doki, har mil metan.

Categories
W. YAH

W. YAH 15

Mala’iku Masu Bala’i Bakwai

1 Na kuma ga wata alama a Sama, mai girma, mai banmamaki, mala’iku bakwai masu bala’i bakwai, waɗanda suke bala’in ƙarshe, don su ne iyakacin fushin Allah.

2 Sai na ga wani abu kamar bahar na gilas, gauraye da wuta, na kuma ga waɗanda suka yi nasara da dabbar nan, da siffarta, da kuma lambar sunanta, a tsaitsaye a bakin bahar na gilas, da molayen yabon Allah a hannunsu.

3 Suna raira waƙar da Musa bawan Allah ya yi, da kuma wadda ake yi wa Ɗan Ragon nan, suna cewa,

“Ayyukanka manya ne, masu banmamaki,

Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki!

Hanyoyinka na adalci ne, na gaskiya ne kuma,

Ya Sarkin al’ummai.

4 Wane ne ba zai ji tsoronka ba, ya Ubangiji,

Ya kuma ɗaukaka sunanka?

Domin kai kaɗai ne Mai Tsarki.

Dukkan al’ummai za su zo su yi maka sujada,

Don ayyukanka na adalci sun bayyana.”

5 Bayan wannan na duba, ga Wuri Mafi Tsarki a buɗe a Haikali a Sama.

6 Sai mala’ika bakwai ɗin nan masu bala’i bakwai suka fito daga Haikalin, saye da tufafin lilin mai tsabta, mai ɗaukar iko, da ɗamarar zinariya a ƙirjinsu.

7 Sai ɗaya daga cikin rayayyun halittan nan guda huɗu, ta ba mala’ikun nan bakwai tasoshi bakwai na zinariya, a cike da fushin Allah, shi da yake a raye har abada abadin.

8 Sai Haikalin ya cika da hayaƙi mai fitowa daga ɗaukakar Allah da ikonsa. Ba mai iya shiga Haikalin nan, sai bayan bala’i bakwai na mala’ikun nan bakwai sun ƙare.

Categories
W. YAH

W. YAH 16

Tasoshin Azaba

1 Sai na ji wata murya mai ƙara daga Haikalin, tana ce wa mala’ikun nan bakwai, “Ku je ku juye tasoshin nan bakwai na fushin Allah a kan duniya.”

2 Daga nan mala’ikan farko ya je ya juye abin da yake a tasarsa a kan duniya, sai kuwa waɗansu mugayen miyaku masu azabtarwa suka fito a jikin mutanen da suke da alamar dabbar nan, suke kuma yi wa siffarta sujada.

3 Mala’ika na biyu ya juye abin da yake a tasarsa a teku, ya zama kamar jinin mataccen mutum, kowane abu mai rai na cikin teku kuma ya mutu.

4 Mala’ika na uku ya juye abin da yake a tasarsa a koguna da maɓuɓɓugan ruwa, sai suka zama jini.

5 Na kuwa ji mala’ikan ruwa yana cewa,

“Kai mai adalci ne a hukuncin nan naka,

Ya kai Mai Tsarki, wanda kake a yanzu, kake kuma a dā.

6 Don mutane sun zub da jinin tsarkaka da na annabawa,

Ga shi kuwa, ka ba su jini su sha.

Sakamakonsu ke nan!”

7 Sai na ji wata murya a bagadin ƙona turare, tana cewa,

“Hakika, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki,

Hukuncinka daidai yake, na adalci ne kuma!”

8 Sai mala’ika na huɗu ya juye abin da yake a tasarsa a rana, sai aka yardar mata ta ƙona mutane da wuta.

9 Sai matsanancin zafi ya ƙona mutane, har suka zagi sunan Allah, shi da yake da ikon waɗannan bala’i, ba su kuwa tuba sun ɗaukaka shi ba.

10 Mala’ika na biyar ya juye abin da yake a tasarsa a kursiyin dabbar nan, sai mulkinta ya zama duhu, har mutane suka ciji leɓunansu don azaba,

11 suka zagi Allah Mai Sama saboda azabarsu da miyakunsu, ba su kuma tuba da ayyukansu ba.

12 Mala’ika na shida ya juye abin da yake a tasarsa a babban kogin nan Yufiretis, sai ruwansa ya ƙafe, don a shirya wa sarakuna daga gabas tafarki.

13 Na kuma ga baƙaƙen aljannu masu kama da kwaɗi gudu uku, suna fitowa daga bakin macijin nan, da bakin dabbar nan, da kuma bakin annabin nan na ƙarya,

14 su iskoki ne, aljannu masu yin abubuwan al’ajabi, masu zuwa wurin sarakunan duniya duka, don su tara su saboda yaƙi a babbar ranar nan ta Allah Maɗaukaki.

15 (“Ga ni nan a tafe kamar ɓarawo! Albarka tā tabbata ga wanda yake a zaune a faɗake, yana saye da tufafinsa, don kada ya tafi tsirara, a ga tsiraicinsa.”)

16 Sai suka tattara su a wurin da ake kira Armageddon da Yahudanci.

17 Mala’ika na bakwai ya juye abin da yake a tasarsa a sararin sama, sai aka ji wata murya mai ƙara daga Haikali, wato, daga kursiyin, ta ce, “An gama!”

18 Sai aka yi ta walƙiya, da ƙararraki masu tsanani, da aradu, da wata babbar rawar ƙasa irin wadda ba a taɓa yi ba, tun da ɗan adam yake a duniya, gawurtacciyar rawar ƙasa ƙwarai da gaske.

19 Babban birnin nan kuwa ya rabu gida uku, biranen al’ummai kuma suka fāɗi. Sai Allah ya tuna da Babila mai girma, don ya sa ta, ta sha fushinsa mai tsananin gaske.

20 Kowane tsibiri ya ɓace, manyan duwatsu ma ba a ƙara ganinsu ba.

21 Waɗansu manyan ƙanƙara kuma kamar kayan jaki suka faɗo a kan mutane daga sama, har mutane suka zagi Allah, saboda bala’in ƙanƙarar. Bala’in nan da matuƙar bantsoro yake!

Categories
W. YAH

W. YAH 17

Hukunta Babbar Karuwar

1 Sai ɗaya daga cikin mala’ikun nan bakwai masu tasoshin nan bakwai, ya zo ya yi mini magana, ya ce, “Zo in nuna maka hukuncin da za a yi wa babbar karuwar nan, wadda take zaune a bisa ruwa mai yawa,

2 wadda sarakunan duniya suka yi fasikanci da ita, wadda kuma mazaunan duniya suka jarabtu da yin fasikanci da ita.”

3 Sai ya ɗauke ni ya tafi da ni zuwa jeji, Ruhu yana iza ni, sai na ga wata mace a kan wata dabba ja wur, duk jikin dabbar sunayen saɓo ne, tana kuma da kawuna bakwai, da ƙaho goma.

4 Matar kuwa tana saye da tufafi masu ruwan jar garura, da kuma ja wur, ta ci ado da kayan zinariya, da duwatsun alfarma, da lu’ulu’u, tana a riƙe da ƙoƙon zinariya a hannunta, cike da abubuwan ƙyama, da ƙazantar fasikancinta.

5 A goshinta kuma an rubuta wani sunan asiri, “Babila mai girma, uwar karuwai, uwar abubuwa masu banƙyama na duniya.”

6 Sai na ga matar ta bugu da jinin tsarkaka, da kuma jinin mashaidan Yesu.

Da na gan ta, sai na yi mamaki ƙwarai da gaske.

7 Amma mala’ikan ya ce mini, “Don me kake mamaki? Zan buɗa maka asirin matar nan, da kuma na dabbar nan mai kawuna bakwai, da ƙaho goma, da take ɗauke da ita.

8 Dabbar nan da ka gani, wadda dā take nan, a yanzu kuwa ba ta, za ta hawo ne daga ramin mahallaka, ta je ta hallaka, mazaunan duniya kuma waɗanda tun a farkon duniya, ba a rubuta sunayensu a Littafin Rai ba, za su yi mamakin ganin dabbar, don dā tana nan, a yanzu ba ta, za ta kuma dawo.

9 Fahimtar wannan abu kuwa, sai a game da hikima. Wato, kawuna bakwai ɗin nan tuddai ne guda bakwai, waɗanda matar take a zaune a kai.

10 Har wa yau kuma, sarakuna ne guda bakwai, waɗanda biyar daga cikinsu aka tuɓe, ɗaya yana nan, ɗayan bai zo ba tukuna, sa’ad da ya zo kuwa, lalle zamaninsa na lokaci kaɗan ne kawai.

11 Dabbar da take nan dā, a yanzu kuwa ba ta, ita ce ta takwas, daga cikin bakwai ɗin nan kuma ta fito, za ta kuwa hallaka.

12 Ƙahonin nan goma kuwa da ka gani, sarakuna goma ne, waɗanda ba a naɗa ba tukuna, amma sa’a ɗaya tak, za a ba su ikon yin mulki tare da dabbar.

13 Waɗannan ra’ayinsu ɗaya ne, za su kuma bai wa dabbar nan ikonsu da sarautarsu.

14 Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, Ɗan Ragon kuwa zai cinye su, shi da waɗanda suke tare da shi, kirayayyu, zaɓaɓɓu, amintattu, domin shi ne Ubangijin iyayengiji.”

15 Sai mala’ikan nan ya ce mini, “Ruwan nan da ka gani, a inda karuwar nan take a zaune, jama’a ce iri iri, da taro masu yawa, da al’ummai, da harsuna.

16 Ƙahonin nan goma kuma da ka gani, wato, su da dabbar nan za su ƙi karuwar, su washe ta, su tsiraita ta, su ci namanta, su ƙone ta,

17 domin Allah ya nufe su da zartar da nufinsa, su zama masu ra’ayi ɗaya, su bai wa dabbar nan, mulkinsu, har a cika Maganar Allah.

18 Matar nan da ka gani kuwa, ita ce babban birnin da yake mulkin sarakunan duniya.”

Categories
W. YAH

W. YAH 18

Faɗuwar Babila Mai Girma

1 Bayan haka, na ga wani mala’ika yana saukowa daga Sama, mai iko da yawa, sai aka haskaka duniya da ɗaukakarsa.

2 Sai ya yi kira da murya mai ƙarfi, ya ce,

“Ta fāɗi! Babila mai girma ta fāɗi!

Ta zama mazaunin aljannu,

Matattarar kowane baƙin aljani,

Da kowane irin ƙazamin tsuntsu, abin ƙyama.

3 Dukkan al’ummai sun yi tsananin jarabar yin fasikanci da ita,

Sarakunan duniya kuma sun yi fasikanci da ita,

Attajiran duniya kuma sun arzuta da almubazzarancinta.”

4 Sai na ji wata murya daga Sama, tana cewa,

“Ku fito daga cikinta, ya ku jama’ata,

Kada zunubanta su shafe ku,

Kada bala’inta ya taɓa ku.

5 Domin zunubanta sun yi tsororuwa, sun kai har Sama,

Allah kuwa ya tuna da laifofinta.

6 Ku saka mata daidai da yadda ta yi,

Ku biya ta ninkin ayyukanta,

Ku dama mata biyun abin da ta dama muku.

7 Yadda ta ɗaukaka kanta, ta yi almubazzaranci,

Haka ku ma ku saka mata da azaba, da baƙin ciki gwargwadon haka.

Tun da yake a birnin zuciyarta ta ce, ‘Ni sarauniya ce, a zaune nake,

Ni ba gwauruwa ba ce,

Ba ni da baƙin ciki kuma har abada!’

8 Saboda haka, bala’inta zai aukar mata rana ɗaya,

Mutuwa, da baƙin ciki, da yunwa.

Za a kuma ƙone ta,

Domin Ubangiji Allah da yake hukunta ta Mai Ƙarfi ne.”

9 Sarakunan duniya kuma da suka yi fasikanci da zaman almubazzaranci da ita, za su yi mata kuka da kururuwa, in sun ga hayaƙin ƙunarta,

10 za su tsaya a can nesa, don tsoron azabarta, su ce,

“Kaitonka! Kaitonka, ya kai babban birni!

Ya kai birni mai ƙarfi, Babila!

A sa’a ɗaya hukuncinka ya auko.”

11 Attajiran duniya kuma suna yi mata kuka suna baƙin ciki, tun da yake, ba mai ƙara sayen kayansu,

12 wato, zinariya, da azurfa, da duwatsun alfarma, da lu’ulu’u, da lallausan lilin, da hajja mai ruwan jar garura, da siliki, da jan alharini, da itacen ƙanshi iri iri, da kayan hauren giwa iri iri, da kayan da aka sassaƙa da itace mai tsada, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na dutse mai sheƙi,

13 da kirfa, da kayan yaji, da turaren wuta, da mur, da lubban, da ruwan inabi, da mai, da garin alkama, da alkama, da shanu, da tumaki, da dawaki, da kekunan doki, da kuma bayi, wato, rayukan ‘yan adam.

14 “Amfanin da kika ƙwallafa rai a kai, har ya kuɓuce miki,

Kayan annashuwarki da na adonki sun ɓace miki, ba kuwa za a ƙara samunsu ba har abada!”

15 Attajiran waɗannan hajjoji da suka arzuta a game da ita, za su tsaya a can nesa don tsoron azabarta, suna kuka, suna baƙin ciki, suna cewa,

16 “Kaito! Kaiton babban birnin nan!

Wanda dā ya sa lallausan lilin, da tufafi masu ruwan jar garura, da kuma jan alharini,

Wanda ya ci ado da kayan zinariya, da duwatsun alfarma, da lu’ulu’u!

17 Domin a sa’a ɗaya duk ɗumbun dukiyar nan ta hallaka.”

Sai duk masu jiragen ruwa, da masu shiga, da masu tuƙi, da duk waɗanda cinikinsu ya gamu da bahar, suka tsaya a can nesa,

18 suna kururuwa da suka ga hayaƙin ƙunarsa, suna cewa,

“Wane birni ne ya yi kama da babban birnin nan?”

19 Har suka tula wa kansu ƙasa suna ta kuka, suna baƙin ciki, suna kururuwa, suna cewa,

“Kaito! Kaiton babban birnin nan!

Wanda duk masu jiragen ruwa a bahar suka arzuta da ɗumbun dukiyarsa,

A sa’a ɗaya ya hallaka.

20 Ki yi farin ciki saboda an yi masa haka, ya sama!

Ku yi farin ciki, ku tsarkaka da manzanni da annabawa, domin Allah ya rama muku abin da ya yi muku!”

21 Sai wani ƙaƙƙarfan mala’ika ya ɗauki wani dutse kamar babban dutsen niƙa, ya jefa a teku, ya ce,

“Haka za a fyaɗa Babila babban birni, da ƙarfi, ba kuwa za a ƙara ganinta ba.

22 Ba za a ƙara jin kiɗan masu molo, da mawaƙa, da masu sarewa, da masu bushe-bushe a cikinki ba,

Ba kuma za a ƙara ganin mai kowace irin sana’a a cikinki ba,

Ba kuma za a ƙara jin niƙa a cikinki ba,

23 Fitila ba za ta ƙara haskakawa a cikinki ba,

Ba kuma za a ƙara jin muryar ango da amarya a cikinki ba,

Don attajiranki, dā su ne ƙusoshin duniya,

An kuma yaudari dukkan al’ummai da sihirinki.

24 Har an tarar hakkin jinin annabawa da na tsarkaka suna a wuyanta, da kuma na duk waɗanda aka kashe a duniya.”

Categories
W. YAH

W. YAH 19

1 Bayan wannan na ji kamar wata sowa mai ƙarfi ta ƙasaitaccen taro a Sama, suna cewa,

“Halleluya! Yin ceto, da ɗaukaka, da iko, sun tabbata ga Allahnmu,

2 Don hukuncinsa daidai yake, na adalci ne,

Ya hukunta babbar karuwar nan wadda ta ɓata duniya da fasikancinta,

Ya kuma ɗauki fansar jinin bayinsa a kanta.”

3 Sai suka sāke yin sowa, suna cewa,

“Halleluya! Hayaƙinta yana tashi har abada abadin.”

4 Sai dattawan nan ashirin da huɗu, da rayayyun halittan nan huɗu, suka fāɗi suka yi wa Allah sujada, shi da yake zaune a kan kursiyin, suna cewa, “Amin. Halleluya!”

5 Sai aka ji wata murya daga kursiyin, tana cewa,

“Ku yabi Allahnmu, ya ku bayinsa,

Ku da kuke jin tsoronsa, yaro da babba.”

Bikin Auren Ɗan Rago

6 Sai na ji kamar wata sowar ƙasaitaccen taro, kamar ƙugin ruwa mai gudu, kamar aradu mai ƙara, suna cewa,

“Halleluya! Gama Ubangiji Allahnmu

Maɗaukaki shi ne yake mulki.

7 Mu yi ta murna da farin ciki matuƙa,

Mu kuma ɗaukaka shi,

Domin bikin Ɗan Ragon nan ya zo,

Amaryarsa kuma ta kintsa.

8 An yardar mata ta sa tufafin lallausan lilin

mai ɗaukar ido, mai tsabta.”

Lallausan lilin ɗin nan, shi ne aikin adalci na tsarkaka.

9 Sai mala’ikan ya ce mini, “Rubuta wannan, ‘Albarka tā tabbata ga waɗanda aka gayyata, zuwa cin abincin bikin Ɗan Ragon nan.’ ” Ya kuma ce mini, “Wannan ita ce Maganar Allah ta gaskiya.”

10 Sai na fāɗi a gabansa, don in yi masa sujada, amma, sai ya ce mini, “Ko kusa kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da ‘yan’uwanka, waɗanda suke shaidar Yesu. Allah za ka yi wa sujada.” Domin gaskiyar da Yesu ya bayyana ita ce ta ba da ikon yin annabci.

Mahayin Farin Doki

11 Sai na ga sama ta dāre, sai ga wani farin doki! Mahayinsa kuwa ana ce da shi Amintacce, Mai Gaskiya, yana hukunci da adalci, yana kuma yaƙi.

12 Idanunsa kamar harshen wuta suke, kansa da kambi da yawa, yana kuma da wani suna a rubuce, wanda ba wanda ya sani sai shi.

13 Yana saye da riga wadda aka tsoma a jini, sunan da ake kiransa da shi kuma, shi ne Kalman Allah.

14 Rundunonin Sama, saye da lallausan lilin fari mai tsabta, suna a biye da shi a kan fararen dawakai.

15 Daga cikin bakinsa wani kakkaifan takobi yake fitowa, wanda zai sare al’ummai da shi, zai kuwa mallake su da tsanani ƙwarai, zai tattake mamatsar inabi, ta tsananin fushin Allah Maɗaukaki.

16 Da wani suna a rubuce a jikin rigarsa, har daidai cinyarsa, wato Sarkin sarakuna, Ubangijin iyayengiji.

17 Sa’an nan na ga wani mala’ika tsaye a jikin rana. Sai kuma ya kira dukkan tsuntsaye da suke tashi a sararin sama, da murya mai ƙarfi, ya ce, “Ku zo, ku taru wurin babban bikin nan na Allah,

18 ku ci naman sarakuna, da naman sarakunan yaƙi, da naman ƙarfafa, da naman dawakai, da na mahayansu, da naman kowa da kowa, wato, na ɗa da na bawa, na yaro da na babba.”

19 Sai na ga dabbar nan, da sarakunan duniya, da rundunoninsu, sun taru, don su yaƙi wanda yake kan dokin, da kuma rundunarsa.

20 Sai aka kama dabbar, da kuma annabin nan na ƙarya tare da ita, wanda ya yi al’ajabai a gabanta, waɗanda da su ne ya yaudari waɗanda suka yarda a yi musu alamar dabbar nan, da kuma waɗanda suka yi wa siffarta sujada. Waɗannan biyu kuwa aka jefa su da ransu a cikin tafkin wuta da ƙibiritu.

21 Sauran kuwa aka sare su da takobin wanda yake a kan doki, wato, da takobin nan da yake fitowa daga cikin bakinsa. Dukan tsuntsaye kuwa suka ci namansu har suka yi gamba.

Categories
W. YAH

W. YAH 20

Shekara Dubu

1 Sa’an nan na ga wani mala’ika yana saukowa daga Sama, yana a riƙe da mabuɗin mahallaka, da kuma wata babbar sarƙa a hannunsa.

2 Sai ya kama macijin nan, wato, macijin nan na tun dā dā, wanda yake shi ne Ibilis, shi ne kuma Shaiɗan, ya ɗaure shi har shekara dubu,

3 ya jefa shi mahallakar, ya rufe, ya kuma yimƙe ta da hatimi, don kada ya ƙara yaudarar al’ummai, har dai shekarun nan dubu su ƙare. Bayan wannan lalle ne a sake shi zuwa ɗan lokaci kaɗan.

4 Sa’an nan na ga kursiyai, da waɗanda aka bai wa ikon hukunci, zaune a kai. Har wa yau, kuma na ga rayukan waɗanda aka fille wa kai saboda shaidar da suka yi wa Yesu, da kuma Maganar Allah, ba su kuwa yi wa dabbar nan da siffarta sujada ba, ba su kuma yarda a yi musu alamarta a goshinsu ko a hannunsu ba, sun sāke rayuwa, sun yi mulki tare da Almasihu har shekara dubu.

5 Sauran matattu kuwa, ba su sāke rayuwa ba, sai bayan da shekaran nan dubu suka cika. Wannan fa shi ne tashin matattu na farko.

6 Duk wanda yake da rabo a tashin nan na farko, mai albarka ne, tsattsarka ne. Mutuwa ta biyu ba ta da iko a kan irin waɗannan, amma za su zama firistocin Allah da na Almasihu, su kuma yi mulki tare da shi har shekara dubu.

7 Bayan shekaran nan dubu sun ƙare, sai a saki Shaiɗan daga ɗaurinsa,

8 ya kuma fito ya yaudari al’ummai waɗanda suke kusurwoyin nan huɗu na duniya, wato, Gog da Magog, ya tattara su saboda yaƙi, yawansu kamar yashin teku.

9 Sai kuma su bazu, su mamaye duk duniya, su yi wa sansanin tsarkaka da ƙaunataccen birni ƙawanya, sai wuta ta zubo daga sama ta lashe su.

10 Shi kuwa Ibilis mayaudarinsu, sai da aka jefa shi a tafkin wuta da ƙibiritu, a inda dabbar nan da annabin nan na ƙarya suke, za a kuma gwada musu azaba dare da rana har abada abadin.

Ranar Shari’a a Gaban Babban Farin Kursiyi

11 Sa’an nan na ga wani babban kursiyi fari, da wanda yake a zaune a kai, sai sama da ƙasa suka guje wa Zatinsa, suka ɓace.

12 Sai na ga matattu manya da yara, a tsaitsaye a gaban kursiyin, aka kuma buɗe littattafai. Sai kuma aka buɗe wani littafi, wanda yake shi ne Littafin Rai. Aka kuwa yi wa matattu shari’a bisa ga abin da yake a rubuce a cikin littattafan, gwargwadon aikin da suka yi.

13 Sai teku ta ba da matattun da suke a cikinta, mutuwa da Hades kuma sun ba da matattun da suke a gare su, aka kuwa yi wa kowa shari’a gwargwadon aikin da ya yi.

14 Sa’an nan aka jefa mutuwa da Hades a tafkin nan na wuta. Wannan ita ce mutuwa ta biyu, wato, tafkin wuta.

15 Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce a Littafin Rai ba, sai a jefa shi a tafkin nan na wuta.