Categories
YOW

YOW 1

Ɓarnar Fāra

1 Maganar Ubangiji zuwa ga Yowel, ɗan Fetuwel.

2 Ku dattawa, ku kasa kunne,

Bari kowa da kowa da yake cikin

Yahuza, ya kasa kunne.

Wani abu mai kamar wannan ya taɓa

faruwa a lokacinku,

Ko a lokacin kakanninku?

3 Ku faɗa wa ‘ya’yanku labarinsa,

‘Ya’yanku kuma su faɗa wa

‘ya’yansu,

‘Ya’yansu kuma su faɗa wa tsara

mai zuwa.

4 Abin da ɗango ya bari fara ta ci,

Abin da fara ta bari burduduwa ta

ci.

5 Ku farka, ku yi ta kuka, ku

bugaggu,

Ku yi kuka, ku mashayan ruwan

inabi,

An lalatar da ‘ya’yan inabin

Da ake yin sabon ruwan inabi da su.

6 Rundunar ta aukar wa ƙasarmu,

Tana da ƙarfi, ba ta kuma

ƙidayuwa,

Haƙoranta suna da kaifi kamar na

zaki.

7 Ta lalatar da kurangar inabinmu,

Ta cinye itatuwan ɓaurenmu.

Ta gaigaye ɓawo duka,

Saboda haka rassan sun zama fari

fat.

8 Ya jama’a, ku yi kuka

Kamar yarinyar da take makokin

rasuwar saurayinta.

9 Ba hatsi ko ruwan inabin

Da za a yi hadaya da su cikin

Haikalin.

Firistoci masu miƙa wa Ubangiji

hadaya suna makoki.

10 Ba kome a gonaki,

Ƙasa tana makoki,

Domin an lalatar da hatsin,

‘Ya’yan inabi sun bushe,

Itatuwan zaitun kuma sun yi yaushi.

11 Ya ku manoma, ku yi baƙin ciki,

Ku yi kuka, ku da kuke lura da

gonakin inabi,

Gama alkama, da sha’ir,

Da dukan amfanin gonaki sun

lalace.

12 Kurangar inabi ta bushe,

Itatuwan ɓaure kuma sun yi yaushi,

Rumman, da dabino, da gawasa,

Da dukan itatuwan gonaki sun

bushe.

Murna ta ƙare a wurin mutane.

13 Ya ku firistoci masu miƙa hadayu a

bagaden Ubangiji,

Ku sa tufafin makoki, ku yi kuka!

Ku shiga Haikali, ku kwana,

Kuna saye da tufafin makoki,

Gama ba hatsi ko ruwan inabi da za

a yi hadaya da su,

A cikin Haikalin Allahnku.

14 Ku sa a yi azumi,

Ku kira muhimmin taro.

Ku tara dattawa da dukan mutanen

ƙasar

A Haikalin Ubangiji Allahnku,

Ku yi kuka ga Ubangiji.

15 Taku ta ƙare a wannan rana!

Gama ranar Ubangiji ta kusa,

Halaka daga wurin Maɗaukaki ta zo.

16 An lalatar da amfanin gonaki a kan

idonmu,

Ba murna a Haikalin Allahnmu.

17 Itatuwa sun mutu a busasshiyar

ƙasa,

Ba hatsin da za a adana a rumbu,

Rumbuna sun lalace domin ba hatsi.

18 Dabbobi suna nishi!

Garkunan shanu sun ruɗe

Domin ba su da makiyaya.

Garkunan tumaki da awaki kuma

suna shan azaba.

19 Ina kuka a gare ka, ya Ubangiji,

Domin ciyayi da itatuwa sun bushe,

Sai ka ce wuta ce ta ƙone su.

20 Har ma namomin jeji suna kuka a

gare ka,

Domin rafuffuka sun bushe,

Ciyayi kuma sun bushe,

Sai ka ce wuta ce ta ƙone su.

Categories
YOW

YOW 2

Fāra ta Zama Musu Alamar Ranar Ubangiji

1 Ku busa ƙaho, ku yi gangami,

A cikin Sihiyona, tsattsarkan

dutsen Allah!

Duk mutanen ƙasar za su yi rawar

jiki,

Domin ranar Ubangiji tana zuwa, ta

yi kusa.

2 Za ta zama rana ce mai duhu

dulum,

Ranar gizagizai ce baƙi ƙirin.

Runduna mai ƙarfi tana tasowa,

Kamar ketowar hasken safiya bisa

tsaunuka.

Faufau ba a taɓa ganin irinta ba,

Ba kuwa za a sāke ganin irinta ba.

3 Tana cinye shuke-shuke kamar wuta,

Ƙasa kamar gonar Adnin take kafin

ta zo,

Amma a bayanta ta zama hamada,

Ba abin da ya tsere mata.

4 Kamar doki take,

Tana gudu kamar dokin yaƙi.

5 Motsin tsallenta a kan duwatsu

kamar Motsin karusa ne.

Kamar kuma amon wutar da take cin

tattaka.

Kamar runduna mai ƙarfi wadda ta

ja dāgar yaƙi.

6 Da zuwanta mutane sukan firgita,

Dukan fuskoki sukan ɓaci.

7 Takan auka kamar mayaƙa,

Takan hau garu kamar sojoji,

Takan yi tafiya,

Kowa ta miƙe sosai inda ta sa

gaba,

Ba ta kaucewa.

8 Ba ta hawan hanyar juna,

Kowa tana bin hanyarta.

Takan kutsa cikin abokan gāba, ba a

iya tsai da ita.

9 Takan ruga cikin birni,

Takan hau garu a guje,

Takan hau gidaje,

Takan shiga ta tagogi kamar ɓarawo.

10 Duniya takan girgiza saboda ita,

Sammai sukan yi rawar jiki.

Rana da wata sukan duhunta,

Taurari kuwa sukan daina

haskakawa.

11 Ubangiji yakan umarci rundunarsa,

Rundunarsa mai cika umarninsa

babba ce, mai ƙarfi,

Gama ranar Ubangiji babba ce mai

banrazana.

Wa zai iya daurewa da ita?

Jinƙan Ubangiji

12 “Koyanzu,” in ji Ubangiji,

“Ku juyo wurina da zuciya ɗaya,

Da azumi, da kuka, da makoki,

13 Ku kyakkece zuciyarku, ba tufafinku

kaɗai ba.”

Ku komo wurin Ubangiji Allahnku.

Gama shi mai alheri ne, mai jinƙai,

Mai jinkirin fushi ne, mai yawan

ƙauna,

Yakan tsai da hukunci.

14 Wa ya sani ko Ubangiji Allahnmu zai

sāke nufinsa,

Ya sa mana albarka,

Har mu miƙa masa hadaya ta gari da

ta sha?

15 Ku busa ƙaho a Sihiyona,

Ku sa a yi azumi,

Ku kira muhimmin taro.

16 Ku tattara jama’a wuri ɗaya,

Ku tsarkake taron jama’a,

Ku tattara dattawa da yara,

Har da jarirai masu shan mama.

Ku sa ango ya fito daga cikin

turakarsa,

Amarya kuma ta fito daga cikin

ɗakinta.

17 Sai firistoci masu hidimar Ubangiji,

Su yi kuka a tsakanin shirayi da

bagade,

Su ce, “Ya Ubangiji, ka ceci

jama’arka,

Kada ka bar gādonka ya zama abin

zargi

Da abin ba’a a tsakiyar al’ummai.

Don kada al’ummai su ce,

‘Ina Allahnsu?’ ”

18 Sai Ubangiji ya ji kishin ƙasarsa,

Ya kuma ji ƙan mutanensa.

19 Sa’an nan ya ce musu,

“Ga shi, zan ba ku hatsi da ruwan

inabi, da mai,

Za ku ƙoshi.

Ba zan sa ku ƙara zama abin zargi ga

al’ummai ba.

20 Zan kawar muku da waɗanda suka

zo daga arewa,

Zan kori waɗansunsu zuwa cikin

hamada.

Zan kori sahunsu na gaba zuwa cikin

Tekun Gishiri,

Zan kori sahunsu na baya, zuwa

cikin Bahar Rum.

Gawawwakinsu za su yi ɗoyi.

Zan yi musu haka saboda dukan abin

da suka yi muku.”

21 Kada ki ji tsoro, ya ƙasa,

Ki yi farin ciki, ki yi murna,

Gama Ubangiji ne ya yi waɗannan

manyan al’amura.

22 Kada ku ji tsoro, ku dabbobin

saura,

Gama wuraren kiwo a jeji sun yi kore

shar.

Itatuwa suna ta yin ‘ya’ya,

Itacen ɓaure da kurangar inabi suna

ta yin ‘ya’ya sosai.

23 Ya ku mutanen Sihiyona, ku yi

murna,

Ku yi farin ciki da Ubangiji

Allahnku,

Gama ya ba ku ruwan farko

Domin shaidar gafarar da ya yi

muku,

Ya kwararo muku da ruwan farko da

na ƙarshe da yawa kamar dā.

24 Masussukai za su cika da hatsi,

Wuraren matse ruwan inabi za su

malala da ruwan inabi.

25 “Zan mayar muku da abin da kuka

yi hasararsa

A shekarun da fara ta cinye

amfaninku,

Wato ɗango da fara mai gaigayewa,

da mai cinyewa,

Su ne babbar rundunata wadda na

aiko muku.

26 Yanzu za ku ci abinci a wadace ku

ƙoshi,

Za ku yabi sunan Ubangiji

Allahnku,

Wanda ya yi muku abubuwa masu

banmamaki,

Ba kuma za a ƙara kunyatar da

mutanena ba.

27 Ku mutanen Isra’ila, za ku sani ina

cikinku,

Ni ne kuwa Ubangiji Allahnku, ba

wani kuma,

Ba kuma za a ƙara kunyatar da

mutanena ba.”

Za a Ba da Ruhun Allah

28 “Bayan wannan zan zubo Ruhuna a

kan jama’a duka,

‘Ya’yanku mata da maza za su iyar

da saƙona,

Tsofaffinku kuwa za su yi mafarkai,

Samarinku za su ga wahayi da yawa.

29 A lokacin zan zubo Ruhuna,

Har a kan barori mata da maza.

30 “Zan yi faɗakarwa a kan wannan

rana

A sararin sama da a duniya.

Za a ga jini, da wuta, da murtukewar

hayaƙi,

31 Rana za ta duhunta,

Wata zai zama ja wur kamar jini,

Kafin isowar babbar ranan nan mai

bantsoro ta Ubangiji.

32 Amma dukan waɗanda suka nemi

Ubangiji za su tsira.

Kamar yadda Ubangiji ya ce,

Akwai waɗanda suke a Dutsen

Sihiyona da Urushalima

Da za su tsira,

Waɗannan da Ubangiji ya zaɓa za su

tsira.”

Categories
YOW

YOW 3

Shari’ar Al’ummai

1 “A wannan lokaci zan mayar wa

Yahuza da Urushalima da

wadatarsu.

2 Zan tattara dukan al’ummai,

In kai su kwarin Yehoshafat.

A can zan yi musu shari’a

A kan dukan abin da suka yi wa

jama’ata.

Sun warwatsa Isra’ilawa a sauran

ƙasashe,

Suka rarraba ƙasata.

3 Sun jefa kuri’a a kan mutanena,

Sun sayar da yara, mata da maza,

zuwa bauta

Don su biya karuwai da ruwan

inabi.

4 “Taya da Sidon, da dukan Filistiya, me kuke so ku yi mini? Kuna ƙoƙari ku rama mini saboda wani abu? Idan haka ne, zan rama muku da gaggawa.

5 Kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe taskata, kun kai cikin haikalinku.

6 Kun kwashe mutanen Yahuza da Urushalima, kun kai su nesa da ƙasarsu, sa’an nan kun sayar da su ga Helenawa.

7 Yanzu zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, zan yi muku abin da kuka yi musu.

8 Zan sa a sayar wa mutanen Yahuza ‘ya’yanku mata da maza, su kuma za su sayar da su ga Sabiyawa, can nesa. Ni Ubangiji na faɗa.”

9 Ku sanar wa al’ummai da wannan,

Su yi shirin yaƙi,

Su kira mayaƙa!

Su tattaro sojoji, su zo!

10 Su bubbuge allunan garmunansu,

Su yi takuba da su.

Su ƙera māsu da wuƙaƙen da ake

yi wa itatuwa aski.

Sai marar ƙarfi ya ce, “Ni jarumi

ne!”

11 Su gaggauta, su zo su al’ummai da

suke kewaye,

Su tattaru a kwarin.

“Ya Ubangiji, ka saukar da

rundunarka mai ƙarfi.”

12 “Sai al’ummai su yi shiri,

Su zo kwarin Yehoshafat,

Gama a can zan zauna in shara’anta

al’umman da suke kewaye,

13 Su sa lauje gama hatsin ya isa girbi.

Su shiga su tattaka,

Gama wurin matsewar ruwan inabi

ya cika.

Manyan randuna sun cika suna

tumbatsa,

Gama muguntarsu da yawa take.”

14 Dubun dubbai suna cikin kwarin da

za a yanke shari’a!

Gama ranar Ubangiji ta kusa zuwa a

kwarin yanke shari’a.

15 Rana da wata sun yi duhu,

Taurari kuma ba su haskakawa.

Ceton Yahuza

16 Ubangiji yana magana da ƙarfi daga

Sihiyona,

Yana tsawa daga Urushalima,

Sammai da duniya sun girgiza.

Amma Ubangiji shi ne mafakar

jama’arsa, Shi ne kagarar mutanen Isra’ila.

17 “Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji

Allahnku,

Wanda yake zaune a Sihiyona, tuduna

tsattsarka.

Urushalima kuma za ta tsarkaka,

Sojojin abokan gāba ba za su ƙara

ratsawa ta cikinta ba.

18 “A wannan lokaci tsaunuka za su rufu

da kurangar inabi,

Tuddai za su cika da shanu,

Dukan rafuffukan Yahuza za su

gudano da ruwa,

Maɓuɓɓuga za ta gudano daga

Haikalin Ubangiji,

Ta shayar da kwarin Shittim.

19 “Masar za ta zama hamada,

Edom kuma za ta zama kufai,

Saboda kama-karya da suka yi wa

mutanen Yahuza,

Saboda sun zubar da jinin marasa

laifi a ƙasarsu,

20 Za a zauna a Yahuza da Urushalima

dukan tsararraki har abada.

21 Zan sāka alhakin jininsu,

Ba zan kuɓutar da mai laifi ba,

Gama Ubangiji yana zaune a Sihiyona.”

Sihiyona.”