Categories
YUSH

YUSH 11

Ƙaunar Allah zuwa ga Mutanensa Masu Tayarwa

1 “A lokacin da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi,

Daga cikin Masar na kirawo ɗana.

2 Yawan kiransu, yawan tayarwar da suke yi mini,

Sai ƙara miƙa wa Ba’al sadaka suke yi,

Suna ƙona turare ga gumaka.

3 Ko da yake ni ne na koya wa Ifraimu tafiya.

Na ɗauke su a hannuna,

Amma ba su sani ni ne na lura da su ba.

4 Na bishe su da linzamin alheri da ragamar ƙauna,

Na zama musu kamar wanda yake ɗauke musu karkiya daga muƙamuƙansu.

Na sunkuya, na ciyar da su.

5 “Ba su koma ƙasar Masar ba,

Amma Assuriya za ta zama sarkinsu

Gama sun ƙi yarda su koma wurina.

6 Takobi zai ragargaje biranensu,

Zai lalatar da sandunan ƙarafan ƙofofinsu,

Zai cinye su domin muguwar shawararsu.

7 Mutanena sun himmantu su rabu da ni,

Ko da yake an kira su ga Ubangiji,

Ba wanda ya girmama shi.

8 “Ƙaƙa zan iya rabuwa da ke, ya Ifraimu?

Ƙaƙa zan miƙa ki, ya Isra’ila?

Ƙaƙa zan maishe ki kamar Adma?

Ƙaƙa zan yi da ke kamar Zeboyim?

Zuciyata tana motsawa a cikina,

Juyayina ya huru.

9 Ba zan aikata fushina mai zafi ba,

Ba zan ƙara hallaka Ifraimu ba,

Gama ni Allah ne, ba mutum ba,

Maitsarki wanda yake tsakiyarku,

Ba zan zo wurinku da hasala ba.

10 “Za su bi Ubangiji,

Zai yi ruri kamar zaki, hakika zai yi ruri

‘Ya’yansa za su zo da rawar jiki da yamma.

11 Da sauri za su zo kamar tsuntsaye daga Masar,

Kamar kurciyoyi daga ƙasar Assuriya,

Zan komar da su gidajensu, ni Ubangiji na faɗa.”

An Tsauta wa Ifraimu domin Ƙarya da Zalunci

12 Ubangiji ya ce, “Ifraimu ta kewaye ni da ƙarairayi,

Jama’ar Isra’ila kuwa ta kewaye ni da munafuncinta,

Yahuza kuma ta tayar wa Allah,

Wato tana gāba da Mai Tsarki, mai aminci.

Categories
YUSH

YUSH 12

1 Ifraimu tana kiwon iska,

Tana ta bin iskar gabas dukan yini.

Tana riɓaɓɓanya ƙarya da kamakarya.

Tana ƙulla yarjejeniya da Assuriya,

Tana kai mai a Masar.”

2 Ubangiji yana da magana game da mutanen Yahuza,

Zai hukunta Isra’ila saboda hanyoyinta,

Zai sāka mata gwargwadon ayyukanta.

3 A cikin mahaifa kakansu Yakubu ya kama diddigen ɗan’uwansa,

Sa’ad da ya zama baligi ya yi kokawa da Allah.

4 Ya yi kokawa da mala’ika ya yi rinjaye.

Ya yi kuka, ya roƙi albarka.

Ya sadu da Allah a Betel,

A can Allah ya yi magana da shi.

5 Ubangiji Allah Mai Runduna,

Sunansa Ubangiji,

6 Sai ku koma wurin Allahnku,

Ku yi alheri, ku yi adalci,

Ku saurari Allahnku kullayaumin.

7 Ubangiji ya ce, “Ɗan kasuwa wanda yake da ma’aunin algus a hannunsa.

Yana jin daɗin yin zalunci.

8 Mutanen Ifraimu sun ce, ‘Hakika, mun zama attajirai,

Mun samar wa kanmu dukiya.

A cikin harkokinmu ba za a sami wata mugunta ba.’

9 Ni ne Ubangiji Allahnku tun daga ƙasar Masar,

Zan kuma sa ku zauna cikin alfarwai,

Kamar lokatan ƙayyadaddun idodi.

10 “Na yi magana da annabawa,

Ni ne na ba da wahayi da yawa,

Da misalai kuma ta wurin annabawa.

11 Idan akwai laifi a Gileyad,

Hakika za su zama wofi.

A Gilgal ana sadaka da bijimai,

Bagadansu za su zama kamar tsibin duwatsu

A gyaffan kunyoyin gona.”

12 Kakanmu Yakubu ya gudu zuwa ƙasar Aram,

A can Isra’ila ya yi barantaka saboda mace,

Saboda mace ya yi kiwon tumaki.

13 Ta wurin annabi Ubangiji ya fito da mutanen Isra’ila daga Masar,

Ta wurin annabi kuma ya kiyaye su.

14 Mutanen Ifraimu sun yi muguwar tsokana mai ta da fushi,

Domin haka Ubangiji zai ɗora musu hakkin jini a kansu,

Zai saka musu cin mutuncin da suka yi.

Categories
YUSH

YUSH 13

Za A Hallaka Ifraimu

1 Sa’ad da Ifraimu ta yi magana, mutane suka yi rawar jiki. An ɗaukaka ta cikin Isra’ila,

Amma ta yi laifi ta wurin bauta gunkin nan Ba’al,

Ta kuwa mutu.

2 Har yanzu suna ta ƙara yin zunubi,

Suna yi wa kansu gumaka na zubi,

Da gwaninta sukan yi gumaka da azurfarsu,

Dukansu aikin hannu ne.

Sukan ce, “Ku miƙa wa waɗannan hadayu!”

Mutane sukan sumbaci siffofin maruƙa.

3 Don haka za su zama kamar ƙāsashin da akan yi da safe,

Ko kuwa kamar raɓa mai kakkaɓewa da wuri.

Za su zama kamar ƙaiƙayi wanda ake shiƙarsa cikin iska a masussuka,

Ko kuwa kamar hayaƙin da yake fita ta bututu.

4 Ubangiji ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku

Tun daga ƙasar Masar.

Banda ni ba ku san wani Allah ba,

Banda ni kuma ba wani mai ceto.

5 Ni ne wanda ya san ku a cikin jeji,

A ƙasar da take da ƙarancin ruwan sama.

6 Sa’ad da suka sami wurin kiwo, suka ƙoshi,

Sai suka yi girmankai,

Suka manta da ni.

7 Zan zama musu kamar zaki,

Kamar damisa zan yi kwanto a gefen hanya.

8 Zan auka musu kamar beyar,

Wadda aka ƙwace mata ‘ya’ya.

Zan yage ƙirjinsu, in cinye su kamar zaki,

Kamar mugun naman jeji zan yayyage su.

9 “Zan hallaka ku, ya mutanen Isra’ila!

Wane ne zai taimake ku?

10 Yanzu ina sarkinku da zai cece ku?

Ina kuma dukan shugabanninku da za su kāre ku?

Su waɗanda kuka roƙa, kun ce, ‘Ku naɗa mana sarki da shugabanni.’

11 Da fushina na naɗa muku sarki,

Da hasalata kuma na tuɓe shi.

12 “An ƙunshe muguntar Ifraimu,

Zunubinsa kuwa an ajiye shi a rumbu.

13 Naƙudar haihuwarsa ta zo,

Amma shi wawan yaro ne,

Bai fito daga mahaifar ba.

14 Zan fanshe su daga ikon lahira.

Zan fanshe su daga mutuwa.

Ya mutuwa, ina annobanki?

Ya kabari, ina halakarka?

Kan kawar da juyayi daga wurina.

15 Ko da yake Isra’ila tana bunƙasa kamar ciyayi,

Iskar gabas, wato iskar da za ta zo daga jeji,

Za ta busar da maɓuɓɓugarsu da idon ruwansu,

Za ta lalatar da abubuwa masu amfani da yake cikin taskarsu.

16 Samariya za ta ɗauki hakkin zunubinta,

Gama ta tayar wa Allahnta.

Za a kashe mutanenta da takobi.

Za a fyaɗa jariranta a ƙasa,

A kuma tsage matanta masu ciki.”

Categories
YUSH

YUSH 14

Ana Roƙon Isra’ila Ta Komo wurin Ubangiji

1 Ya mutanen Isra’ila, ku komo wurin Ubangiji Allahnku,

Gama zunubinku ya sa kun yi tuntuɓe.

2 Ku komo wurin Ubangiji, ku roƙe shi,

Ku ce, “Ka gafarta mana zunubanmu,

Ka karɓe mu saboda alherinka,

Mu kuwa za mu yabe ka da bakinmu.

3 Assuriya ba za ta cece mu ba,

Ba kuwa za mu hau dawakai ba.

Ba za mu kuma ƙara ce da aikin hannuwanmu,

‘Kai ne Allahnmu,’ ba.

A wurinka ne maraya yakan sami jinƙai.”

Ubangiji Ya Yi wa Isra’ila Alkawarin Sabon Rai

4 Ubangiji ya ce, “Zan warkar musu da riddarsu.

Zan kuma ƙaunace su sosai,

Gama fushina zai huce.

5 Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila,

Isra’ila za ta yi fure kamar lili,

Saiwarta za ta shiga kamar itacen al’ul.

6 Tohonta zai buɗo,

Kyanta zai zama kamar itacen zaitun,

Ƙashinta kuwa kamar itacen al’ul na Lebanon.

7 Waɗanda za su komo, za su zauna a inuwarta,

Za su yi noman hatsi da yawa.

Za su yi fure kamar kurangar inabi.

Ƙanshinsu zai zama kamar ruwan inabi na Lebanon.

8 Ya mutanen Ifraimu, me zan yi da gumaka?

Ni ne wanda yake amsa muku, mai lura da ku kuma.

Ni kamar itacen fir ne mai ganyaye kore shar.

Daga gare ni, kuke samun ‘ya’ya.”

9 Duk wanda yake da hikima, bari ya fahimci abubuwan nan.

Duk wanda yake da ganewa, bari ya san abubuwan nan,

Gama hanyoyin Ubangiji masu gaskiya ne,

Masu adalci kuwa za su yi tafiya a cikinsu,

Amma masu zunubi za su yi tuntuɓe a kansu.