Categories
ZAB

ZAB 121

Ubangiji Ne Yake Kiyaye Ku

1 Na duba wajen duwatsu,

Daga ina taimakona zai zo?

2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji,

Wanda ya yi sama da ƙasa.

3 Ba zai bar ka ka fāɗi ba,

Makiyayinka, ba zai yi barci ba!

4 Makiyayin Isra’ila,

Ba ya gyangyaɗi ko barci!

5 Ubangiji zai lura da kai,

Yana kusa da kai domin ya kiyaye ka.

6 Ba za ka sha rana ba,

Ko farin wata da dare.

7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan hatsari,

Zai sa ka zauna lafiya.

8 Zai kiyaye shigarka da fitarka,

Tun daga yanzu har abada.

Categories
ZAB

ZAB 122

Yabon Urushalima

1 Na yi murna sa’ad da suka ce mini,

“Tashi mu tafi Haikalin Ubangiji!”

2 Ga shi kuwa, mun iso,

Muna tsaye a ƙofofin Urushalima!

3 Urushalima birni ce wadda aka maido ta yadda take dā,

Da kyakkyawan tsari, a shirye!

4 A nan kabilai sukan zo,

Kabilan Isra’ila,

Domin su yi godiya ga Ubangiji,

Kamar yadda ya umarce su.

5 A nan majalisu suke,

Wurin da sarki yake yi wa jama’arsa shari’a.

6 Ku yi wa Urushalima addu’ar salama!

“Allah ya sa masu ƙaunarki su arzuta!

7 Salama ta samu a garukanki,

Da zaman lafiya kuma a fādodinki.”

8 Saboda abokaina da aminaina,

Na ce wa Urushalima, “Salama a gare ki!”

9 Saboda Haikalin Ubangiji, Allahnmu,

Ina addu’a domin ki arzuta.

Categories
ZAB

ZAB 123

Addu’ar Neman Jinƙai

1 Ya Ubangiji, ina zuba ido gare ka,

A Sama inda kake mulki.

2 Kamar yadda bara yake dogara ga maigidansa,

Baranya kuma ga uwargijiyarta,

Haka nan muke zuba ido gare ka, ya Ubangiji Allahnmu,

Har mu sami jinƙanka.

3 Ka yi mana jinƙai, ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai,

An gwada mana wulakanci matuƙa!

4 Attajirai sun daɗe suna ta yi mana ba’a,

Azzalumai masu girmankai sun raina mu!

Categories
ZAB

ZAB 124

Allah Ne Mai Ceton Jama’arsa

1 Da a ce Ubangiji ba ya tare da mu,

Da me zai faru?

Ba da amsa, ya Isra’ila!

2 “Da a ce Ubangiji ba ya tare da mu,

A lokacin da abokan gābanmu suka auka mana,

3 Da sun haɗiye mu da rai a lokacin nan,

Saboda zafin fushi da suke yi da mu,

4 Da rigyawa ta kwashe mu,

Da ruwa yi ci mu,

5 Kwararowar ruwa ya nutsar da mu.”

6 Sai mu gode wa Ubangiji,

Da bai bar abokan gābanmu su hallaka mu ba.

7 Mun kuɓuta kamar tsuntsu daga tarkon mai farauta,

Tarkon ya tsinke, mun ‘yantu!

8 Taimakonmu daga wurin Ubangiji yake zuwa,

Shi wanda ya yi sama da duniya.

Categories
ZAB

ZAB 125

Zaman Lafiyar Jama’ar Allah

1 Waɗanda suke dogara ga Ubangiji,

Suna kama da Dutsen Sihiyona,

Wanda ba zai jijjigu ba, faufau.

Faufau kuma ba za a kawar da shi ba.

2 Kamar yadda duwatsu suka kewaye Urushalima,

Haka nan Ubangiji zai kewaye jama’arsa,

Daga yanzu har abada.

3 Ba a koyaushe mugaye za su yi mulki a ƙasar jama’ar Allah ba,

Idan kuwa suka yi, to, ya yiwu jama’ar Allah su yi laifi.

4 Ya Ubangiji, ka yi wa mutanen kirki alheri,

Su waɗanda suke biyayya da umarnanka!

5 Amma ka hukunta waɗanda suke bin mugayen al’amuransu,

Sa’ad da kake hukunta wa masu aikata mugunta!

Salama ta kasance tare da Isra’ila!

Categories
ZAB

ZAB 126

Godiyar Samun Ceto

1 Sa’ad da Ubangiji ya komar da mu cikin Sihiyona,

Sai abin ya zama kamar mafarki!

2 Muka kece da dariya, muka raira waƙa don farin ciki,

Sa’an nan sai sauran al’umma suka ambace mu, suka ce,

“Ubangiji ya yi manyan al’amura masu girma, sabili da su!”

3 Hakika ya aikata manyan al’amura sabili da mu,

Mun kuwa yi farin ciki ƙwarai!

4 Ya Ubangiji, ka komar da mu ƙasarmu

Kamar yadda ruwan da kake yi yakan koma cikin busassun koguna,

5 Ka sa waɗanda suke kuka a lokacin da suke dashe,

Su tattara albarkar kaka da farin ciki!

6 Su waɗanda suka yi kuka a sa’ad da suka fita suna ɗauke da iri,

Za su komo ɗauke da albarkar kaka,

Suna raira waƙa don farin ciki!

Categories
ZAB

ZAB 127

Yabon Alherin Ubangiji

1 Idan ba Ubangiji ne ya gina gidan ba,

Aikin magina banza ne.

Idan ba Ubangiji ne ya tsare birnin ba,

Ba wani amfani a sa matsara su yi tsaro.

2 Ba wani amfani a sha wahalar aiki saboda abinci,

A yi asubancin tashi, a yi makarar kwanciya,

Gama Ubangiji yakan hutar da waɗanda yake ƙauna.

3 ‘Ya’ya kyauta ne daga wurin Ubangiji,

Albarka ce ta musamman.

4 ‘Ya’ya maza da mutum ya haifa a lokacin ƙuruciyarsa

Kamar kibau suke a hannun mayaƙi.

5 Mai farin ciki ne mutumin da yake da irin waɗannan kibau da yawa!

Faufau ba za a ci nasara a kansa ba,

Sa’ad da ya kara da maƙiyansa a wurin shari’a.

Categories
ZAB

ZAB 128

Albarkar Mai Tsoron Ubangiji

1 Mai farin ciki ne wanda yake tsoron Ubangiji,

Wanda yake zamansa bisa ga umarnansa!

2 Za ka sami isasshen abin biyan bukatarka,

Za ka yi farin ciki ka arzuta.

3 Matarka za ta zama kamar kurangar inabi

Mai ‘ya’ya a gidanka,

‘Ya’yanka maza kuma kamar dashen zaitun

Suna kewaye da teburinka.

4 Mutumin da yake yi wa Ubangiji biyayya,

Hakika za a sa masa albarka kamar haka.

5 Ubangiji ya sa maka albarka daga Sihiyona!

Ya sa ka ga Urushalima ta arzuta

Dukan kwanakinka!

6 Ya kuma sa ka ka ga jikokinka!

Salama ta kasance ga Isra’ila!

Categories
ZAB

ZAB 129

Addu’a a kan Maƙiyan Isra’ila

1 Isra’ila, sai ka faɗi irin muguntar

Da maƙiyanka suka tsananta maka da ita,

Tun kana ƙarami!

2 “Maƙiyana suka tsananta mini da mugunta,

Tun ina ƙarami,

Amma ba su yi nasara da ni ba.

3 Suka sa mini raunuka masu zurfi a bayana,

Suka mai da shi kamar gonar da aka nome.

4 Amma Ubangiji mai adalci,

Ya ‘yantar da ni daga bauta.”

5 Allah ya sa duk waɗanda suke ƙin Sihiyona,

A yi nasara da su a kuma kore su!

6 Allah ya sa su zama kamar ciyawar da take girma a kan soraye,

Ta kuwa bushe kafin ta isa yanka.

7 Ba wanda zai tattara ta,

Ya ɗaure ta dami dami.

8 Duk waɗanda suke wucewa a hanya ba za su ce,

“Ubangiji ya sa maka albarka!” ba,

Ko su ce, “Muna sa maka albarka da sunan Ubangiji!”

Categories
ZAB

ZAB 130

Sa Zuciya ga Ceton Allah

1 A cikin fid da zuciyata,

Na yi kira gare ka, ya Ubangiji.

2 Ka ji kukana, ya Ubangiji,

Ka kasa kunne ga kiran da nake yi na neman taimako!

3 Idan kana yin lissafin zunubanmu,

Wa zai kuɓuta daga hukunci?

4 Amma kakan gafarta mana,

Domin mu zama masu tsoronka.

5 Na zaƙu, ina jiran taimako daga Ubangiji,

Ga maganarsa na dogara.

6 Ina jiran Ubangiji,

Na zaƙu ƙwarai, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir,

I, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir.

7 Ya Isra’ila, ki dogara ga Ubangiji,

Saboda ƙaunarsa madawwamiya ce,

A koyaushe yana da nufin yin gafara.

8 Zai fanshi jama’arsa Isra’ila

Daga dukan zunubansu.