Categories
ZAB

ZAB 141

Addu’ar Maraice ta Neman Keɓewa daga Mugunta

1 Ina kira gare ka, ya Ubangiji,

Ka taimake ni yanzu!

Ka saurare ni sa’ad da na kira gare ka.

2 Ka karɓi addu’ata kamar turaren ƙonawa,

Ka karɓi ɗaga hannuwa sama da na yi kamar hadayar maraice.

3 Ya Ubangiji, ka sa a yi tsaron bakina,

Ka sa mai tsaro a leɓunana.

4 Ka tsare ni daga son yin mugunta,

Ko kuma in haɗa kai da mugaye cikin muguntarsu,

Ka sa kada in taɓa yin tarayya da su a bukukuwansu!

5 Nagarin mutum ya iya hukunta ni, ya tsauta mini da alheri,

Zai zamar mini kamar an shafe kaina da mai,

Domin kullayaumi ina addu’a gāba da mugayen ayyuka.

6 Mutane za su yarda, cewa maganata gaskiya ce,

Sa’ad da aka jefo da masu mulkinsu ƙasa, daga ƙwanƙolin dutse,

7 Kamar itacen da aka faskare, aka daddatse,

Haka aka watsar da ƙasusuwansu a gefen kabari.

8 Amma ni, ya Ubangiji Allah, da nake dogara a gare ka,

Ina neman kiyayewarka,

Kada ka bar ni in halaka!

9 Ka kiyaye ni daga tarkunan da suka kafa mini,

Daga ashiftar masu aikata mugunta.

10 Ka sa mugaye su fāɗa cikin tarkunansu,

Ni kuwa in zo in wuce lafiya.

Categories
ZAB

ZAB 142

Addu’ar Neman Taimako

1 Ina kira ga Ubangiji don neman taimako,

Ina roƙonsa.

2 Na kawo masa dukan koke-kokena,

Na faɗa masa dukan wahalaina.

3 Sa’ad da na yi niyyar fid da zuciya,

Ya san abin da zan yi.

A kan hanyar da zan bi

Maƙiyana sun kafa mini tarko a ɓoye.

4 Na duba kewaye da ni, sai na ga ba ni da wanda zai taimake ni,

Ba wanda zai kiyaye ni,

Ba kuwa wanda ya kula da ni.

5 Ya Ubangiji, na kawo kuka gare ka na neman taimako,

Ya Ubangiji, kai ne mai kiyaye ni,

Kai kaɗai nake so a rayuwata duka.

6 Ka kasa kunne ga kukana na neman taimako,

Gama na nutsa cikin fid da zuciya.

Ka cece ni daga maƙiyana

Waɗanda suka fi ƙarfina.

7 Ka cece ni daga cikin wahalata,

Sa’an nan zan yabe ka cikin taron jama’arka,

Domin ka yi mini alheri.

Categories
ZAB

ZAB 143

Addu’ar Neman Ceto da Kiyayewa

1 Ya Ubangiji ka ji addu’ata,

Ka kasa kunne ga roƙona!

Kai adali ne mai aminci,

Don haka ka amsa mini!

2 Ni bawanka, kada ka gabatar da ni a gaban shari’a,

Gama ba wanda ba shi da laifi a gare ka.

3 Maƙiyina ya tsananta mini,

Ya kore ni fata-fata.

Ya sa ni a kurkuku mai duhu,

Ina kama da waɗanda suka daɗe da mutuwa,

4 Don haka ina niyya in fid da zuciya,

Ina cikin damuwa mai zurfi.

5 Na tuna kwanakin baya,

Na tuna da dukan abin da ka yi,

Na tuna da dukan ayyukanka.

6 Na ɗaga hannuwana sama, ina addu’a gare ka,

Kamar busasshiyar ƙasa, raina yana jin ƙishinka.

7 Yanzu ka amsa mini, ya Ubangiji!

Na fid da zuciya duka!

Kada ka ɓuya mini,

Don kada in zama cikin waɗanda suke gangarawa zuwa lahira.

8 A gare ka nake dogara,

Da safe ka tuna mini da madawwamiyar ƙaunarka.

Addu’ata ta hau zuwa gare ka,

Ka nuna mini hanyar da zan bi.

9 Na tafi wurinka don ka kiyaye ni, ya Ubangiji,

Ka cece ni daga maƙiyana.

10 Kai ne Allahna,

Ka koya mini in aikata nufinka.

Ka sa in sami alherin Ruhunka.

Ka bi da ni a hanyar lafiya.

11 Ka cece ni, ya Ubangiji, kamar yadda ka alkawarta.

Saboda alherinka ka tsamo ni daga wahalaina!

12 Saboda ƙaunar da kake yi mini,

Ka kashe maƙiyana.

Ka hallakar da dukan waɗanda suke zaluntata.

Gama ni bawanka ne.

Categories
ZAB

ZAB 144

Addu’ar Neman Ceto da Wadata

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, mai kiyaye ni,

Ya hore ni don yaƙi,

Ya kuwa shirya ni don yaƙi.

2 Shi yake kiyaye ni,

Shi yake kāre ni,

Shi ne mafakata da Mai Cetona,

Wanda nake dogara gare shi

Don samun zaman lafiya.

Shi ne ya ɗora ni a kan al’ummai.

3 Ya Ubangiji wane ne mutum, har da kake lura da shi?

Wane ne ɗan adam kurum, har da kake kulawa da shi?

4 Shi kamar hucin iska yake,

Kwanakinsa kuwa kamar inuwa mai wucewa ne.

5 Ya Ubangiji, ka kware sararin sama, ka sauko,

Ka taɓa duwatsu, don su tuƙaƙo da hayaƙi.

6 Ka aiko da walƙiyar tsawa ta warwatsa maƙiyanka,

Ka harba kibanka, ka sa su sheƙa a guje!

7 Ka sunkuyo daga Sama,

Ka tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi, ka cece ni,

Ka cece ni daga ikon baƙi,

8 Waɗanda ba su taɓa faɗar gaskiya ba,

Sukan yi rantsuwar ƙarya.

9 Zan raira maka sabuwar waƙa, ya Allah,

Zan kaɗa garaya in raira maka waƙa.

10 Ka ba sarakuna nasara,

Ka kuma ceci bawanka Dawuda.

11 Ka cece ni daga mugayen abokan gābana,

Ka ƙwato ni daga ikon baƙi,

Waɗanda ba su taɓa faɗar gaskiya ba,

Sukan yi rantsuwar ƙarya.

12 Ka sa ‘ya’yanmu maza waɗanda suke cikin samartaka,

Su zama kamar itatuwan da yake girma da ƙarfi.

Ka sa ‘ya’yanmu mata

Su zama kamar al’amudai,

Waɗanda suke adanta kusurwoyin fāda.

13 Ka sa rumbunanmu su cika

Da kowane irin amfanin gona.

Ka sa tumakin da suke cikin saurukanmu

Su hayayyafa dubu dubu har sau goma,

14 Ka sa shanunmu su hayayyafa,

Kada su yi ɓari ko su ɓace.

Ka sa kada a ji kukan damuwa a kan titunanmu!

15 Mai farin ciki ce al’ummar

Da abin nan da aka faɗa ya zama gaskiya a gare ta.

Masu farin ciki ne jama’ar da Allahnsu shi ne Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 145

Waƙar Yabon Allah domin Alherinsa da Ikonsa

1 Zan yi shelar girmanka, ya Allahna, Sarkina,

Zan yi maka godiya har abada abadin.

2 Kowace rana zan yi maka godiya,

Zan yabe ka har abada abadin.

3 Ubangiji mai girma ne, dole ne a fifita yabonsa,

Girmansa ya fi ƙarfin ganewa.

4 Za a yabi abin da ka aikata daga tsara zuwa tsara,

Za su yi shelar manya manyan ayyukanka.

5 Mutane za su yi magana a kan darajarka da ɗaukakarka,

Ni kuwa zan yi ta tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.

6 Mutane za su yi magana a kan manya manyan ayyukanka,

Ni kuwa zan yi shelar girmanka.

7 Za su ba da labarin girmanka duka,

Su kuma raira waƙa a kan alherinka.

8 Ubangiji mai ƙauna ne, mai jinƙai, mai jinkirin fushi,

Cike da madawwamiyar ƙauna.

9 Shi mai alheri ne ga kowa,

Yana juyayin dukan abin da ya halitta.

10 Ya Ubangiji, talikanka duka za su yabe ka,

Jama’arka kuma za su yi maka godiya!

11 Za su yi maganar darajar mulkinka,

Su ba da labarin ikonka,

12 Domin haka dukan mutane za su san manyan ayyukanka,

Da kuma darajar ɗaukakar mulkinka.

13 Mulkinka, madawwamin mulki ne,

Sarki ne kai har abada.

14 Ubangiji, yakan taimaki dukan waɗanda yake shan wahala,

Yakan ta da waɗanda aka wulakanta.

15 Dukan masu rai suna sa zuciya gare shi,

Yana ba su abinci a lokacin da suke bukata,

16 Yana kuwa ba su isasshe,

Yakan biya bukatarsu duka.

17 Ubangiji mai adalci ne a abin da yake yi duka,

Mai jinƙai ne a ayyukansa duka.

18 Yana kusa da dukan waɗanda suke kira gare shi,

Waɗanda suke kiransa da zuciya ɗaya.

19 Yakan biya bukatar dukan waɗanda suke tsoronsa,

Yakan ji kukansu, ya cece su.

20 Yakan kiyaye dukan waɗanda suke ƙaunarsa,

Amma zai hallaka mugaye duka.

21 A kullum zan yabi Ubangiji,

Bari talikai duka su yabi sunansa mai tsarki har abada!

Categories
ZAB

ZAB 146

Yabon Allah Mai Ceto

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Ka yabi Ubanigji, ya raina!

2 Zan yabe shi muddin raina.

Zan raira waƙa ga Allahna dukan kwanakina.

3 Kada ka dogara ga shugabanni,

Ko kowane mutum da ba zai iya cetonka ba.

4 Sa’ad da suka mutu sai su koma turɓaya,

A wannan rana dukan shirye-shiryensu sun ƙare.

5 Mai farin ciki ne mutumin da Allah na Yakubu ne yake taimakonsa,

Yana kuma dogara ga Ubangiji Allahnsa,

6 Wanda ya halicci sama, da duniya, da teku,

Da dukan abin da yake cikinsu.

Kullum yakan cika alkawaransa.

7 A yanke shari’arsa yakan ba wanda aka zalunta gaskiya.

Yana ba da abinci ga mayunwata.

Ubangiji yakan kuɓutar da ɗaurarru.

8 Yakan ba makafi ganin gari.

Yakan ɗaukaka waɗanda aka wulakanta.

Yana ƙaunar jama’arsa, adalai.

9 Yakan kiyaye baƙi waɗanda suke zaune a ƙasar.

Yakan taimaki gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu.

Yakan lalatar da dabarun mugaye.

10 Ubangiji Sarki ne har abada!

Ya Sihiyona, Allahnki zai yi mulki har dukan zamanai!

Yabo Ya tabbata ga Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 147

Yabon Alherin Allah a kan Urushalima

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Abu mai kyau ne mu yabi Allahnmu,

Abu mai daɗi ne, daidai ne kuma, a yabe shi.

2 Ubangiji yana rayar da Urushalima,

Yana komo da waɗanda aka kai su baƙunci a wata ƙasa.

3 Yakan warkar da masu karyayyiyar zuciya,

Yakan ɗaure raunukansu.

4 Ya ƙididdige yawan taurari,

Yakan kira kowanne da sunansa.

5 Ubangijinmu mai girma ne, Mai Iko Dukka,

Saninsa ya fi gaban aunawa.

6 Yakan ɗaukaka masu tawali’u,

Amma yakan ragargaza mugaye har ƙasa.

7 Ku raira waƙar yabo ga Ubangiji,

Ku yabi Allah da garaya.

8 Ya shimfiɗa gajimare a sararin al’arshi.

Ya tanada wa duniya ruwan sama,

Ya sa ciyayi su tsiro a kan tuddai.

9 Yakan ba dabbobi abincinsu,

Yakan ciyar da ‘ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kuka gare shi.

10 Ba ya jin daɗin ƙarfafan dawakai,

Ba ya murna da jarumawan mayaƙa.

11 Amma yana jin daɗin waɗanda suke tsoronsa,

Yana jin daɗin waɗanda suke dogara da madawwamiyar ƙaunarsa.

12 Ya Urushalima, ki yabi Ubangiji,

Ya Sihiyona, ki yabi Allahnki.

13 Shi yake riƙe da ƙofofinki da ƙarfi,

Yakan sa wa jama’arki albarka.

14 Yakan kiyaye kan iyakar ƙasarki lafiya,

Yakan kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.

15 Yakan ba da umarni,

Nan da nan umarnin yakan iso duniya.

16 Yakan aiko da dusar ƙanƙara mai kauri kamar ulu,

Ya watsa jaura kamar ƙura.

17 Yakan aiko da ƙanƙara kamar duwatsu,

Ba wanda yake iya jurewa da sanyin da yakan aiko!

18 Sa’an nan yakan ba da umarni,

Ƙanƙara kuwa ta narke,

Yakan aiko da iska, ruwa kuwa yakan gudu.

19 Yana ba Yakubu saƙonsa,

Koyarwarsa da dokokinsa kuma ga Isra’ila.

20 Bai yi wa sauran al’umma wannan ba,

Domin ba su san dokokinsa ba.

Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 148

Bari dukan Halittar Allah su yi Yabonsa

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Ku yabi Ubangiji daga sama,

Ku da kuke zaune a tuddan sama.

2 Ku yabe shi dukanku mala’ikunsa,

Ku yabe shi, ku dukan rundunansa na sama!

3 Ku yabe shi, ku rana da wata,

Ku yabe shi, ku taurari masu haskakawa!

4 Ku yabe shi, ku sammai mafi tsayi duka!

Ku yabe shi, ku ruwayen da kuke bisa sararin sama!

5 Bari su duka su yabi sunan Ubangiji!

Ya umarta, sai suka kasance.

6 Ta wurin umarninsa aka kafa su

A wurarensu har abada,

Ba su kuwa da ikon ƙi.

7 Ku yabi Ubangiji daga duniya,

Ku yabi Ubangiji, ku dodanin ruwa da dukan zurfafan teku.

8 Ku yabe shi, ku walƙiya, da ƙanƙara, da dusar ƙanƙara,

Da gizagizai, da ƙarfafan iska waɗanda suke biyayya da umarnansa!

9 Ku yabe shi, ku tuddai da duwatsu,

Da itatuwa ‘ya’ya da kurama.

10 Ku yabe shi dukanku dabbobi, na gida da na jeji,

Masu rarrafe da tsuntsaye!

11 Ku yabe shi, ku sarakuna da dukan kabilai,

Ku yabe shi, ku shugabanni da dukan hukumomi.

12 Ku yabe shi ku samari da ‘yan mata!

Ku yabe shi, ku tsoffafi da yara!

13 Bari dukansu su yabi sunan Ubangiji,

Sunansa ya fi dukan sauran sunaye girma,

Ɗaukakarsa kuwa tana bisa duniya da samaniya!

14 Ya sa al’ummarsa ta yi ƙarfi,

Domin dukan jama’arsa su yabe shi

Jama’arsa Isra’ila, wadda yake ƙauna ƙwarai!

Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 149

Bari Isra’ilawa su Yabi Ubangiji

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Ku raira sabuwar waƙa ga Ubangiji

Ku yabe shi cikin taron jama’arsa masu aminci!

2 Ki yi murna, ke Isra’ila, sabili da Mahaliccinki,

Ku yi farin ciki, ku jama’ar Sihiyona, sabili da Sarkinku!

3 Ku yabi sunansa, kuna taka rawa,

Ku kaɗa bandiri da garayu, kuna yabonsa.

4 Ubangiji yana jin daɗin jama’arsa,

Yakan girmama mai tawali’u ya sa ya ci nasara.

5 Bari jama’ar Allah su yi farin ciki saboda cin nasararsu,

Su raira waƙa don farin ciki.

6 Bari su yi sowa da ƙarfi

Sa’ad da suke yabon Allah, da takubansu masu kaifi.

7 Don su ci nasara bisa al’ummai,

Su kuma hukunta wa jama’a,

8 Su ɗaure sarakunansu da sarƙoƙi,

Su ɗaure shugabanninsu da sarƙoƙin baƙin ƙarfe,

9 Su hukunta wa al’ummai, kamar yadda Allah ya umarta.

Wannan shi ne cin nasarar jama’ar Allah!

Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 150

Ku Yabi Ubangiji

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Ku yabi Allah a cikin Haikalinsa!

Ku yabi ƙarfinsa a sama!

2 Ku yabe shi saboda manyan abubuwa

Waɗanda ya aikata!

Ku yabi mafificin girmansa!

3 Ku yabe shi da kakaki!

Ku yabe shi da garayu da molaye!

4 Ku yabe shi da bandiri kuna taka rawa!

Ku yabe shi da garayu da sarewa!

5 Ku yabe shi da kuge!

Ku yabe shi da kuge masu amo!

6 Ku yabi Ubangiji dukanku rayayyun talikai.

Yabo ya tabbata ga Ubangiji!