Categories
ZAB

ZAB 61

Dogara ga Kiyayewar Allah

1 Ya Allah, ka ji kukana,

Ka ji addu’ata!

2 Sa’ad da nake nesa da gida, zuciyata ta karai,

Zan yi kira gare ka!

Ka kai ni lafiyayyiyar mafaka.

3 Kai ne kāriyata mai ƙarfi

Da take kiyaye ni daga maƙiyana.

4 Ka yarda in zauna a alfarwarka dukan kwanakin raina,

Ka yarda in sami zaman lafiya a ƙarƙashin fikafikanka.

5 Ya Allah, kā ji alkawaraina,

Kā kuwa ba ni abin da ya dace,

Tare da waɗanda suke ɗaukaka ka.

6 Ka ƙara wa sarki tsawon rai,

Ka sa ya rayu dukan lokaci!

7 Ka sa ya yi mulki har abada a gabanka, ya Allah,

Ka tsare shi da madawwamiyar ƙaunarka, da amincinka.

8 Don haka zan yi ta raira waƙar yabonka kullayaumin,

A sa’ad da nake miƙa maka abin da na alkawarta.

Categories
ZAB

ZAB 62

Allah ne kaɗai Mafaka

1 Ga Allah kaɗai na dogara,

Cetona daga gare shi yake fitowa.

2 Shi kaɗai ne mai kiyaye ni, Mai Cetona,

Shi ne kariyata,

Ba kuwa za a yi nasara da ni ba sam.

3 Har yaushe dukanku za ku fāɗa wa wani don ku yi nasara da shi,

Kamar rusasshen garu,

Ko kuma dangar da ta fāɗi?

4 Ba abin da kuke so, sai ku ƙasƙantar da shi daga maƙaminsa na daraja,

Kuna jin daɗin yin ƙarairayi.

Kuna sa masa albarka,

Amma a zuciyarku la’antarwa kuke yi.

5 Ga Allah kaɗai na dogara,

A gare shi na sa zuciyata.

6 Shi kaɗai ne mai kiyaye ni, Mai Cetona,

Shi ne kariyata,

Ba kuwa za a yi nasara da ni ba sam.

7 Cetona da darajata daga Allah ne,

Shi ne ƙaƙƙarfan makiyayina,

Shi ne mafakata.

8 Ya jama’ata, ku dogara ya Allah a kowane lokaci!

Ku faɗa masa dukan wahalarku,

Gama shi ne mafakarmu.

9 Talakawa kamar shaƙar numfashi suke,

Manyan mutane, su ma haka suke marasa amfani.

Ko an auna su a ma’auni, sam ba su da nauyin kome,

Sun fi numfashi shakaf.

10 Kada ku dogara da aikin kama-karya.

Kada ku sa zuciya za ku ci ribar kome ta wurin fashi.

In kuwa dukiyarku ta ƙaru,

Kada ku dogara gare ta.

11 Sau ɗaya Allah ya faɗa,

Sau biyu na ji, cewa Allah yake da iko.

12 Madawwamiyar ƙauna, ta Ubangiji ce.

Kai kanka, ya Ubangiji, kake sāka wa

Kowane mutum bisa ga ayyukansa.

Categories
ZAB

ZAB 63

Sa Zuciya ga Allah

1 Ya Allah, kai ne Allahna,

Ina sa zuciya gare ka.

Duk niyyata ta nemanka ce,

Raina yana ƙishinka,

Kamar bussasshiyar ƙasa,

Wadda ta zozaye, ba ta da ruwa.

2 Bari in gan ka a tsattsarkan wurinka,

In dubi ɗaukakarka da darajarka.

3 Madawwamiyar ƙaunarka ta fi rai kansa,

Saboda wannan zan yabe ka.

4 Muddin raina, zan yi maka godiya,

Zan ta da hannuwana sama, in yi addu’a gare ka.

5 Raina zai yi liyafa, yă ƙoshi sosai,

Ni kuwa zan raira waƙoƙin murna na yabo a gare ka.

6 Sa’ad da nake kwance a gadona na tuna da kai,

Dare farai ina ta tunawa da kai,

7 Domin kai kake taimakona kullayaumin.

Da murna, nake raira waƙa,

A inuwar fikafikanka,

8 Raina yana manne maka,

Ikonka yana riƙe da ni.

9 Waɗanda suke ƙoƙari su kashe ni,

Za su gangara zuwa lahira,

10 Za a kashe su cikin yaƙi,

Kyarketai kuwa za su cinye gawawwakinsu.

11 Sarki zai yi farin ciki ga Allah,

Duk waɗanda suka yi alkawarai da sunan Allah

Za su yi murna,

Amma za a rufe bakunan maƙaryata.

Categories
ZAB

ZAB 64

Addu’ar Neman Tsari

1 Ina shan wahala, ya Allah, ka ji addu’ata!

Ina jin tsoro, ka cece ni daga maƙiyana!

2 Ka kiyaye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye,

Da iskancin mugayen mutane.

3 Sukan wasa harsunansu kamar takuba,

Sukan kai bāra da mugayen maganganu kamar kibau.

4 Sukan yi kwanto su harbi mutanen kirki da kibau,

Nan da nan sukan yi harbi, ba su kuwa jin tsoro.

5 Suna ƙarfafa junansu cikin yin mugayen ƙulle-ƙullensu,

Sukan yi ta taɗi a kan inda za su kafa tarkunansu.

“Ba wanda zai gan mu,” in ji su.

6 Sukan shirya maƙarƙashiya, su ce,

“Ai, mun gama shirin aikata laifi sarai.”

Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa!

7 Amma Allah zai harbe su da kibansa,

Za a yi musu rauni nan da nan.

8 Zai hallaka su saboda maganganunsu,

Duk wanda ya gan su zai kaɗa kansa.

9 Dukansu za su ji tsoro,

Za su faɗi abin da Allah ya aikata,

Su yi tunani a kan ayyukansa.

10 Dukan masu adalci za su yi murna,

Saboda abin da Ubangiji ya aikata.

Za su sami mafaka a gare shi,

Dukan mutanen kirki za su yabe shi.

Categories
ZAB

ZAB 65

Yabo da Miƙa Hadaya ta Godiya

1 Ya Allah, dole mutane su yabe ka a Sihiyona,

Tilas su ba ka abin da suka alkawarta.

2 Saboda kakan amsa addu’o’i,

Dukan mutane za su zo wurinka.

3 Zunubanmu sun kāshe mu,

Amma za ka gafarta zunubanmu.

4 Masu farin ciki ne waɗanda ka zaɓe su

Su zauna a tsattsarkan wurinka!

Za mu ƙoshi da kyawawan abubuwa da suke wurin zamanka,

Da albarkun tsattsarkan Haikalinka!

5 Ka amsa mana, ya Allah Mai Cetonmu,

Ka kuma cece mu ta wurin aikata al’amuran banmamaki.

Mutane daga ko’ina a duniya,

Har da waɗanda suke can nesa a hayin tekuna,

Sun dogara gare ka.

6 Ka kakkafa duwatsu ta wurin ikonka,

Ka bayyana ƙarfin ikonka.

7 Kakan kwantar da rurin tekuna,

Kakan kwantar da rurin igiyar ruwa,

Kakan kwantar da tarzomar jama’a.

8 Dukan duniya ta tsorata,

Saboda manyan ayyuka da ka aikata.

Ayyukanka sukan kawo sowa ta farin ciki

Daga wannan iyakar duniya zuwa wancan.

9 Kakan nuna kana kulawa da ƙasar,

Ta wurin aiko mata da ruwa.

Ka arzuta ta, ta zama dausayi.

Rafuffukan da ka bayar ba su taɓa ƙafewa ba,

Sun sa ƙasar ta ba da amfanin gonaki,

Abubuwan da ka aikata ke nan.

10 Ka kwarara ruwa mai yawa a gonakin da aka nome,

Ka jiƙe su da ruwa,

Ka tausasa ƙasar da yayyafi,

Ka sa ƙananan tsire-tsire su yi girma.

11 Saboda alherinka, ya Allah, an sami kaka mai albarka!

Inda ka tafi duka akwai wadata!

12 Makiyaya suna cike da tumaki masu ƙiba,

Tuddai kuma suna cike da farin ciki.

13 Sauruka suna cike da tumaki,

Kwaruruka suna cike da alkama,

Suna sowa suna raira waƙa ta farin ciki!

Categories
ZAB

ZAB 66

Waƙar Yabo da Miƙa Hadaya ta Godiya

1 Ku yabi Allah da babbar murya ta farin ciki,

Ya jama’a duka!

2 Ku raira waƙar darajar sunansa,

Ku yabe shi da ɗaukaka!

3 Ku faɗa wa Allah cewa, “Al’amuran da kake aikatawa

Suna da banmamaki ƙwarai!

Ikonka yana da girma ƙwarai,

Har maƙiyanka sukan durƙusa a gabanka don tsoro.

4 Duk wanda yake a duniya, yana yi maka sujada,

Yana raira maka waƙar yabbai,

Yana raira yabbai ga sunanka.”

5 Zo, ka ga abin da Allah ya yi,

Ayyukansa masu ban al’ajabi

Waɗanda ya aikata ga mutane.

6 Ya sa teku ta zama busasshiyar ƙasa,

Kakanninmu suka haye kogi da ƙafa.

A can muka yi farin ciki saboda abin da ya yi.

7 Har abada yana mulki ta wurin ƙarfinsa,

Yana duban al’ummai,

Don kada ‘yan tawaye su tayar masa!

8 Ku yabi Allahnmu, ya ku dukan al’ummai,

Bari a ji yabon da kuke yi masa.

9 Shi ne yake rayar da mu,

Bai kuwa yarda mu fāɗi ba.

10 Ka jarraba mu, ya Allah,

Kamar yadda ake tace azurfa da wuta,

Haka nan ka jarraba mu.

11 Ka bar mu muka fāɗa a tarko,

Ka ɗora mana kaya masu nauyi.

12 Ka bar maƙiyanmu suka tattaka mu,

Mun ratsa ta cikin wuta da rigyawa,

Amma yanzu ka kawo mu a lafiyayyen wuri.

13 Zan kawo hadayun ƙonawa a ɗakinka,

Zan miƙa maka abin da na alkawarta.

14 Zan ba ka abin da na ce zan bayar,

A lokacin da nake shan wahala.

15 Zan miƙa tumaki don a ƙona a kan bagade,

Nan za a ji ƙanshi mai daɗi na ƙonannun awaki,

Zan miƙa hadayu na bijimai da na awaki.

16 Ku zo ku ji, dukanku, ku da kuke girmama Allah,

Ni kuwa zan faɗa muku abin da ya yi mini.

17 Na yi kira gare shi neman taimako,

A shirye nake in yabe shi da waƙoƙi.

18 Da ban watsar da zunubaina ba,

Da Ubangiji bai ji ni ba.

19 Amma hakika Allah ya ji ni,

Ya saurari addu’ata.

20 Ina yabon Allah,

Domin bai ƙi addu’ata ba,

Bai kuwa hana mini madawwamiyar ƙaunarsa ba.

Categories
ZAB

ZAB 67

Waƙar Miƙa Hadaya ta Godiya

1 Ka yi mana jinƙai, ya Allah, ka sa mana albarka,

Ka dube mu da idon rahama,

2 Domin dukan duniya ta san nufinka,

Dukan sauran al’umma kuma su san cetonka.

3 Da ma dukan mutane su yabe ka, ya Allah,

Da ma dukan mutane su yabe ka!

4 Da ma sauran al’umma su yi murna, su raira waƙa ta farin ciki,

Domin kana yi wa jama’a shari’a ta adalci,

Kana kuma bi da dukan sauran al’umma.

5 Da ma dukan mutane su yabe ka, ya Allah,

Da ma dukan mutane su yabe ka!

6 Ƙasa ta ba da amfaninta,

Allah, wanda yake Allahnmu ne, ya sa mana albarka.

7 Allah ya sa mana albarka,

Da ma dukan jama’a ko’ina su girmama shi.

Categories
ZAB

ZAB 68

Waƙar Nasara ta Al’ummar Ƙasar

1 Da ma Allah ya tashi ya warwatsa maƙiyansa!

Da ma su waɗanda suke ƙinsa su gudu!

2 Kamar yadda iska take korar hayaƙi,

Haka nan zai kore su,

Kamar yadda kākin zuma yakan narke a gaban wuta,

Haka nan mugaye za su hallaka a gaban Allah.

3 Amma adalai za su yi murna,

Su kuma yi farin ciki a gaban Allah,

Za su yi murna ƙwarai da gaske.

4 Ku raira waƙa ga Allah,

Ku raira waƙar yabo ga sunansa,

Ku yi hanya ga wanda yake ratsa gizagizai.

Sunansa kuwa Ubangiji ne, ku yi murna a gabansa!

5 Allah, wanda yake zaune a tsattsarkan Haikalinsa,

Yana lura da marayu, yana kuwa kiyaye gwauraye,

Wato matan da mazansu suka mutu.

6 Yakan ba waɗanda suke da kewa gida, su zauna a ciki,

Yakan fitar da ‘yan sarƙa ya kai su ‘yanci mai daɗi,

Amma ‘yan tawaye za su zauna a ƙasar da ba kowa a ciki.

7 Sa’ad da ka bi da jama’arka, ya Allah,

Sa’ad da ka yi tafiya a hamada,

8 Duniya ta girgiza, sararin sama ya kwararo ruwa,

Saboda bayyanar Allah, har Dutsen Sinai ya girgiza,

Saboda bayyanar Allah na Isra’ila.

9 Ka sa aka yi ruwan sama mai yawa, ya Allah,

Ka rayar da ƙasarka wadda ta zozaye.

10 Jama’arka suka gina gidajensu a can,

Ta wurin alherinka ka yi wa matalauta tanadi.

11 Ubangiji ya ba da umarni,

Sai mata masu yawa suka baza labari cewa,

12 “Sarakuna da rundunan sojojinsu suna gudu!

Matan da suke a gida suka rarraba ganima.”

13 Suna kamar kurciyoyin da aka dalaye da azurfa,

Waɗanda fikafikansu suna ƙyalli kamar kyakkyawar zinariya.

(Me ya sa waɗansunku suke zaune cikin shingen tumaki?)

14 Sa’ad da Allah Mai Iko Dukka

Ya warwatsar da sarakuna a dutsen Zalmon,

Sai ya sa dusar ƙanƙara ta sauka a wurin.

15 Wane irin babban dutse ne wannan dutsen Bashan?

Tulluwarka nawa, dutsen Bashan?

16 Me ya sa, daga manyan kawunanka

Kake yi wa dutsen da Allah ya zaɓa

Ya zauna a kai, duban raini?

A nan Ubangiji zai zauna har abada!

17 Daga Sinai da dubban manyan karusansa,

Ubangiji ya zo tsattsarkan Haikalinsa.

18 Ya hau kan tsaunuka

Tare da ɗumbun waɗanda ya kamo daga yaƙi,

Yana karɓar kyautai daga wurin mutane,

Daga wurin ‘yan tawaye kuma.

Ubangiji Allah zai zauna a can.

19 Ku yabi Ubangiji,

Wanda yake ɗaukar nawayarmu ta yau da kullum,

Shi ne Allah wanda ya cece mu.

20 Allahnmu, Allah Mai Ceto ne,

Shi ne Ubangiji, Ubangijinmu,

Wanda yake cetonmu daga mutuwa.

21 Hakika Allah zai farfashe kawunan abokan gābansa,

Da na waɗanda suka nace bin hanyoyinsu na zunubi.

22 Ubangiji ya ce, “Zan komo da su daga Bashan,

Zan komo da su daga zurfin teku,

23 Don ku wanke sawayenku a cikin jinin maƙiyanku,

Karnukanku kuwa za su lashe iyakar abin da suke so.”

24 Ya Allah, jama’a duka sun ga irin tafiyarka ta nasara,

Irin tafiyar Allah, Sarkina, zuwa tsattsarkan wurinsa.

25 Mawaƙa suna kan gaba, mabusa suna biye,

A tsakiya kuwa ‘yan mata suna kaɗa bandiri.

26 “Ku jama’ar Allah, ku yabe shi cikin taronku,

Ku yabi Ubangiji, dukanku, ku zuriyar Isra’ila!”

27 Ga Biliyaminu mafi ƙanƙanta

Cikin kabilai, a kan gaba,

Sa’an nan shugabannin Yahuza da ƙungiyarsu,

Daga nan sai shugabannin Zabaluna da na Naftali suna biye da su.

28 Ka nuna ikonka, ya Allah,

Ikon nan da ka nuna saboda mu.

29 Daga Haikalinka a Urushalima,

Sarakuna sukan kawo maka kyautai.

30 Ka tsauta wa Masar, naman jejin nan

Mai zafin hali da yake cikin iwa,

Ka tsauta wa sauran al’umma, taron bijiman nan da ‘yan maruƙansu,

Har dukansu su durƙusa, su miƙa maka azurfarsu.

Ka warwatsar da jama’ar nan

Masu son yin yaƙi!

31 Wakilai za su zo daga Masar,

Habashawa za su miƙa hannuwansu sama,

Su yi addu’a ga Allah.

32 Ku raira waƙa ga Allah, ku mulkokin duniya,

Ku raira waƙar yabo ga Ubangiji,

33 Shi wanda ya hau cikin sararin sama,

Daɗaɗɗen sararin sama!

Ku kasa kunne ga muryarsa mai ƙarfi!

34 Ku yi shelar ikon Allah,

Ɗaukakarsa tana bisa kan Isra’ila,

Ikonsa yana cikin sararin sama.

35 Allah al’ajabi ne a tsattsarkan wurinsa,

Allah na Isra’ila!

Yana ba da ƙarfi da iko ga jama’arsa.

Ku yabi Allah!

Categories
ZAB

ZAB 69

Kukan Neman Taimako

1 Ka cece ni, ya Allah!

Ruwa ya sha kaina.

2 Ina nutsewa cikin laka mai zurfi,

Ba kuwa ƙasa mai ƙarfi,

Na tsunduma cikin ruwa mai zurfi,

Raƙuman ruwa kuwa sun kusa kashe ni.

3 Na gaji da kira, ina neman taimako,

Maƙogwarona yana yi mini ciwo,

Idanuna duka sun gaji,

Saboda ina zuba ido ga taimakonka.

4 Waɗanda suke ƙina ba dalili

Sun fi gashin kaina yawa,

Waɗanda suke baza ƙarya suke ƙina,

Suna da ƙarfi, suna kuwa so su kashe ni.

Suka tilasta ni in mayar da abubuwan da ba satarsu na yi ba.

5 Zunubaina ba a ɓoye suke a gare ka ba ya Allah,

Ka san irin wawancin da na yi!

6 Kada ka bar ni in jawo kunya ga waɗanda suka dogara gare ka,

Ya Ubangiji Allah Mai Iko Dukka!

Kada ka bar ni in jawo abin kunya

Ga waɗanda suke maka sujada, ya Allah na Isra’ila!

7 Sabili da kai ne aka ci mutuncina,

Kunya ta rufe ni.

8 Kamar baƙo nake ga ‘yan’uwana,

Haka ma ga iyalina, kamar baƙo nake.

9 Ƙaunar da nake da ita ta yin ibada a Haikalinka

Tana iza ni a ciki kamar wuta,

Zargin da suke yi a kanka, ya fāɗa a kaina.

10 Na ƙasƙantar da kaina ta wurin yin azumi,

Jama’a kuwa suka ci mutuncina.

11 Na sa tufafin makoki,

Sai suka maishe ni abin dariya.

12 A tituna suna ta magana a kaina,

Bugaggu da giya kuwa suna raira waƙa a kaina.

13 Amma ni, zan yi addu’a gare ka, ya Ubangiji,

Ka amsa mini, ya Allah, a lokacin da ka zaɓa,

Sabili da muhimmiyar ƙaunarka,

Saboda kana cika alkawarinka na yin ceto.

14 Ka cece ni daga nutsewa cikin wannan laka,

Ka kiyaye ni daga maƙiyana,

Daga kuma wannan ruwa mai zurfi.

15 Kada ka bar ambaliyar ruwa ta rufe ni.

Kada ka bar ni in mutu cikin zurfafa,

Ko in nutse a cikin kabari.

16 Sabili da madawwamiyar ƙaunarka, ka amsa mini, ya Ubangiji,

Ka juyo wurina, saboda juyayinka mai girma!

17 Kada ka ɓoye kanka daga bawanka,

Ina shan babbar wahala, ka yi hanzari ka amsa mini!

18 Ka zo ka fanshe ni,

Ka kuɓutar da ni daga abokan gābana.

19 Ka san yadda ake cin mutuncina,

Da yadda ake kunyata ni, ake ƙasƙantar da ni,

Kana ganin dukan abokan gābana.

20 Zuciyata ta karai saboda cin mutuncin da ake ci mini,

Ni kuwa ba ni da mataimaki,

Na sa zuciya za a kula da ni,

Amma babu.

Na sa zuciya zan sami ta’aziyya,

Amma ban samu ba.

21 Sa’ad da na ji yunwa, sai suka ba ni dafi,

Sa’ad da na ji ƙishi, sai suka ba ni ruwan tsami.

22 Allah ya sa bukukuwansu su zama lalacewarsu,

Shagulgulansu kuma su zama sanadin fāɗuwarsu!

23 Ka makantar da su, har da ba za su iya gani ba,

Kullum ka sa bayansu ya ƙage!

24 Ka kwarara musu fushinka,

Bari zafin fushinka ya ci musu!

25 Allah ya sa su gudu su bar sansaninsu,

Kada wani ya ragu da rai cikin alfarwansu!

26 Sun tsananta wa waɗanda ka hukunta,

Suna taɗin shan wuyar waɗanda ka aukar wa cutar.

27 Ka riɓaɓɓanya zunubansu,

Kada ka bar su su sami rabon kome daga cikin cetonka.

28 Ka sa a goge sunansu daga cikin littafin rai,

Kada a sa su a lissafin jama’arka.

29 Amma ni mai bukata ne, ina shan wahala,

Ka tsame ni, ya Allah, ka cece ni!

30 Zan raira waƙar yabo ga Allah,

Zan yi shelar girmansa ta wurin yi masa godiya,

31 Wannan zai daɗaɗa wa Ubangiji rai

Fiye da hadayar bijimi,

Fiye da a ba shi bijimi bana bakwai.

32 Sa’ad da masu bukata suka ga wannan za su yi murna,

Waɗanda suke yi wa Allah sujada kuwa za a ƙarfafa su.

33 Ubangiji yana kasa kunne ga masu bukata,

Bai manta da jama’arsa da suke a kurkuku ba.

34 Ku yabi Allah, ku al’arshi da duniya, ku yabi Allah,

Tekuna da dukan talikan da suke cikinsu!

35 Gama zai ceci Sihiyona,

Ya sāke gina garuruwan Yahuza,

Jama’arsa za su zauna a wurin, su mallaki ƙasar.

36 Zuriyar bayinsa za su gāje ta,

Masu ƙaunarsa za su zauna a wurin.

Categories
ZAB

ZAB 70

Addu’ar Neman Kuɓuta

1 Ka cece ni, ya Allah!

Ya Ubangiji, ka yi hanzari ka taimake ni!

2 Ka sa masu so su kashe ni,

A ci nasara a kansu, su ruɗe!

Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalaina, su koma baya, su sha kunya!

3 Ka sa waɗanda suke mini ba’a

Su razana sabili da fāɗuwarsu!

4 Ka sa dukan waɗanda suke zuwa gare ka

Su yi murna, su yi farin ciki!

Ka sa waɗanda suke ƙaunar cetonka

Kullayaumi su ce, “Allah da girma yake!”

5 Ba ni da ƙarfi, ba mataimaki,

Ya Allah, ka zo wurina da hanzari.

Kai ne mataimakina da Mai Cetona,

Kada ka yi jinkiri, ya Ubangiji!