Categories
ZAB

ZAB 71

Addu’ar Tsoho

1 A gare ka, ya Ubangiji, lafiya lau nake,

Faufau kada ka bari a yi nasara da ni!

2 Sabili da kai adali ne ka taimake ni, ka cece ni.

Ka kasa kunne gare ni, ka cece ni!

3 Ka zama mini lafiyayyiyar mafaka,

Da kagara mai ƙarfi, domin ka tsare ni,

Kai ne mafakata da kāriyata.

4 Ya Allahna, ka cece ni daga mugaye,

Daga ikon mugga, wato mugayen mutane.

5 Ya Ubangiji, a gare ka nake sa zuciya,

Tun ina yaro, nake dogara gare ka.

6 A duk kwanakina a gare ka nake dogara,

Kana kiyaye ni tun da aka haife ni,

Kullayaumi zan yabe ka!

7 Raina abin damuwa ne ga mutane da yawa,

Amma kai ne kāriyata mai ƙarfi.

8 Ina yabonka dukan yini,

Ina shelar darajarka.

9 Yanzu da na tsufa, kada ka yashe ni,

Yanzu da ƙarfina ya ƙare kuma, kada ka rabu da ni!

10 Maƙiyana, waɗanda suke so su kashe ni,

Suna magana, suna ƙulle-ƙulle gāba da ni.

11 Suna cewa, “Ai, Allah ya rabu da shi,

Gama ba wanda zai cece shi!”

12 Kada ka yi nisa da ni haka, ya Allah,

Ka yi hanzari ka taimake ni, ya Allahna!

13 Ka sa a kori waɗanda suka tasar mini,

A hallaka su!

Ka sa a kunyata waɗanda suke ƙoƙari su cuce ni,

A wulakanta su sarai!

14 A koyaushe zan sa zuciya gare ka,

Zan yi ta yabonka.

15 Zan ba da labarin adalcinka,

Zan yi magana a kan cetonka duk yini,

Ko da yake ya fi ƙarfin in san shi duka.

16 Zan tafi in yi yabon ikonka, ya Ubangiji Allah,

Zan yi shelar adalcinka,

Naka, kai kaɗai.

17 Kai ne ka koya mini, ya Allah, tun lokacin da nake yaro,

Har wa yau kuwa ina ba da labarin ayyukanka masu banmamaki.

18 Yanzu da na tsufa, na kuma yi furfura,

Kada ka rabu da ni, ya Allah!

Ka kasance tare da ni sa’ad da nake shelar ikonka da ƙarfinka ga mutanen dukan zamanai masu zuwa.

19 Adalcinka, ya Allah, ya kai har sammai.

Ka aikata manyan ayyuka,

Ba waninka!

20 Ka aiko mini da wahala da azaba,

Amma za ka mayar mini da ƙarfina,

Za ka tashe ni daga kabari.

21 Za ka girmama ni har abada,

Za ka sāke ta’azantar da ni.

22 Hakika zan yabe ka da garaya,

Zan yabi amincinka, ya Allahna.

Da garayata zan yi maka waƙoƙi,

Ya Mai Tsarki na Isra’ila.

23 Zan ta da muryar farin ciki

Sa’ad da nake raira maka waƙar yabbai,

Zan raira waƙa da zuciya ɗaya,

Gama dā ka fanshe ni.

24 Zan yi magana a kan adalcinka dukan yini,

Saboda an yi nasara da waɗanda suke ƙoƙari su cuce ni, sun ruɗe.

Categories
ZAB

ZAB 72

Mulkin Sarki Mai Adalci

1 Ka koya wa sarki ya yi shari’a

Da adalcinka, ya Allah,

Ka kuma ba shi shari’arka,

2 Don ya yi mulkin jama’arka bisa kan shari’a,

Ya kuma bi da mulki da adalci.

3 Ka sa ƙasar ta mori wadatarta,

Ka sa al’ummar ta san adalci.

4 Ka sa sarki ya yi wa talakawa shari’ar gaskiya,

Ya taimaki waɗanda suke da bukata,

Ya kuma hukunta azzalumai!

5 Ka sa su girmama ka

Muddin rana tana haskakawa,

Muddin wata yana ba da haske dukan lokaci.

6 Ka sa sarki ya zama kamar ruwan sama a gonaki,

Ya zama kamar yayyafi a bisa ƙasa.

7 Ka sa adalci ya bunƙasa a zamaninsa,

Wadata ta dawwama muddin wata na haskakawa.

8 Mulkinsa ya kai daga teku zuwa teku,

Daga Kogin Yufiretis, har zuwa iyakar duniya.

9 Kabilan hamada za su durƙusa a gabansa,

Abokan gābansa za su kwanta warwar a cikin ƙura.

10 Sarakunan Esbanya da na tsibirai,

Za su ba shi kyautai,

Sarakunan Arabiya da na Habasha

Za su kawo masa kyautai.

11 Dukan sarakuna za su durƙusa a gabansa,

Dukan sauran al’umma za su bauta masa!

12 Yakan ceci matalauta waɗanda suka yi kira gare shi,

Da waɗanda suke da bukata,

Da waɗanda ba a kula da su.

13 Yakan ji tausayin gajiyayyu da matalauta,

Yakan ceci rayukan waɗanda suke da bukata.

14 Yakan cece su daga zalunci da kama-karya,

Rayukansu suna da daraja a gare shi.

15 Ran sarki yă daɗe!

Da ma a ba shi zinariya daga Arabiya,

Da ma a yi masa addu’a dukan lokaci,

Allah ya sa masa albarka kullum!

16 Da ma a sami hatsi mai yawa a ƙasar,

Da ma amfanin gona yă cika tuddan,

Yă yi yawa kamar itatuwan al’ul na Lebanon,

Da ma birane su cika da mutane,

Kamar ciyayin da suke girma a sauruka.

17 Da ma a yi ta tunawa da sunansa har abada,

Da ma shahararsa ta ɗore muddin rana tana haskakawa.

Da ma dukan sauran al’umma su yabi sarkin,

Dukan jama’a su roƙi Allah yă sa musu albarka,

Kamar yadda ya sa wa sarki albarka.

18 Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila,

Wanda shi kaɗai ne yake aikata al’amuran nan masu banmamaki!

19 Ku yabi sunansa mai daraja har abada,

Allah ya sa ɗaukakarsa ta cika dukan duniya!

Amin! Amin!

20 Ƙarshen addu’o’in Dawuda, ɗan Yesse ke nan.

Categories
ZAB

ZAB 73

Ƙarshen Mugaye

1 Hakika, Allah yana yi wa Isra’ila alheri,

Da waɗanda suke da tsarkin zuciya!

2 Amma ina gab da fāɗuwa,

Ƙafafuna sun kusa zamewa,

3 Saboda na ji kishin masu girmankai,

Sa’ad da na ga mugaye suna arziki.

4 Ba su jin zafin ciwo,

Su ƙarfafa ne, lafiyayyu.

5 Ba su shan wahala yadda sauran mutane suke sha,

Ba su da wahala kamar sauran mutane,

6 Don haka suka ɗaura girmankai kamar dutsen wuya,

Suka sa hargitsi kuma kamar riga.

7 Zuciyarsu, cike take da mugunta,

Tunaninsu kuma cike suke da mugayen ƙulle-ƙulle.

8 Sukan yi wa waɗansu ba’a,

Suna faɗar mugayen abubuwa,

Masu girmankai ne su, suna shawara

A kan yadda za su zalunci waɗansu.

9 Sukan faɗi baƙar magana a kan Allah na Sama,

Su ba da umarnai na girmankai ga mutane a duniya,

10 Har jama’ar Allah ma sukan koma wurinsu,

Suna ɗokin gaskata dukan abin da suke faɗa musu.

11 Sukan ce, “Ai, Allah ba zai sani ba,

Maɗaukaki ba zai bincika ba!”

12 Haka mugaye suke.

Suna da dukiya da yawa, amma sai ƙaruwa suke ta yi.

13 Ashe, a banza nake kiyaye kaina da tsarki,

Hannuwana kuma a tsabtace daga zunubi?

14 Ya Allah, ka sa ina shan wahala dukan yini,

Kana horona kowace safiya!

15 Da na faɗi waɗannan abubuwa,

Da na zama marar gaskiya ga jama’arka.

16 Don haka na yi iyakar ƙoƙari in fahimci wannan,

Ko da yake ya cika wuya,

17 Sai sa’ad da na shiga Haikalinka,

Sa’an nan na fahimci abin da zai sami mugaye.

18 Hakika ka sa su a wurare masu santsi,

Ka sa su su fāɗi su hallaka sarai!

19 Cikin ƙyaftawar ido aka hallaka su,

Suka yi mummunan ƙarshe!

20 Ya Ubangiji, kamar mafarki suke

Wanda akan manta da shi da safe,

Sa’ad da mutum ya farka yakan manta da kamanninsa.

21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci,

Hankalina ya tashi,

22 Sai na zama wawa, ban fahimta ba,

Na nuna halin dabba a gabanka.

23 Duk da haka ina tare da kai kullayaumin,

Kana riƙe da hannuna.

24 Shawararka, tana bi da ni,

Daga ƙarshe kuma za ka karɓe ni da daraja.

25 In banda kai, wa nake da shi a Sama?

Tun da yake ina da kai, me kuwa nake bukata a duniya?

26 Kwanyata da jikina za su raunana,

Amma Allah ne ƙarfina,

Shi nake so har abada!

27 Hakika waɗanda za su rabu da kai za su mutu,

Za ka hallakar da marasa aminci gare ka.

28 Amma a gare ni, ya fi mini kyau, in kasance kusa da Allah!

Na sami mafaka a wurin Ubangiji Allah,

Da zan yi shelar dukan abin da ya aikata.

Categories
ZAB

ZAB 74

Addu’ar Neman Ceton Al’ummar Allah

1 Don me ka yashe mu haka, ya Allah?

Za ka yi ta fushi da jama’arka har abada ne?

2 Ka tuna da jama’arka waɗanda ka zaɓa su zama naka tuntuni,

Ka tuna da jama’arka waɗanda ka fansa,

Don su zama kabilarka.

Ka tuna da Dutsen Sihiyona, inda zatinka yake!

3 Ka zo, ka yi yawo a wannan kufai,

Abokan gābanmu sun lalatar da kome na cikin Haikali!

4 Abokan gābanka suka yi sowa ta nasara

A inda akan sadu da kai,

Sun ƙwace Haikalin.

5 Suna kama da masu saran itace,

Suna saran itatuwa da gaturansu.

6 Da gaturansu da gudumarsu,

Sun ragargaje ƙyamaren da aka yi da katako.

7 Sun sa wa Haikalinka wuta,

Sun ƙazantar da wurin da akan yi maka sujada,

Sun farfashe shi duk.

8 Sun yi niyya su murƙushe mu sarai,

Sun ƙone kowane tsattsarkan wuri na ƙasar.

9 Ba sauran tsarkakan alamu,

Ba sauran annabawan da suka ragu,

Ba kuwa wanda ya san ƙarewar wannan.

10 Ya Allah, har yaushe abokan gābanmu za su yi ta yi mana ba’a?

Za su yi ta zargin sunanka har abada ne?

11 Me ya sa ka ƙi taimakonmu?

Ka tasar musu ka hallaka su!

12 Amma ya Allah, kai ne Sarkinmu tun daga farko,

Ka yi nasara da duniya.

13 Da ƙarfin ikonka ka raba teku,

Ka farfashe kawunan dodannin ruwa,

14 Ka ragargaje kawunan kadduna,

Ka kuwa ba mutanen hamada su ci.

15 Ka sa ruwan maɓuɓɓugai ya yi gudu,

Ka sa manyan koguna su ƙafe.

16 Ka halicci yini da dare,

Ka sa rana da wata a wurarensu.

17 Ka yi wa duniya kan iyaka,

Ka kuwa yi lokatan damuna da na rani.

18 Amma ka tuna fa, ya Ubangiji, abokan gābanka suna yi maka ba’a,

Su wawaye ne waɗanda suke raina ka.

19 Kada ka ba da jama’arka marasa taimako

A hannun mugayen maƙiyansu,

Kada ka manta da jama’arka waɗanda ake tsananta musu!

20 Ka tuna da alkawarin da ka yi mana,

Akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar!

21 Kada ka bari a kori waɗanda ake zalunta,

Amma bari matalauta da masu mayata su yabe ka.

22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre kanka!

Ka tuna fa, marasa tsoronka suna ta yi maka ba’a dukan yini!

23 Kada ka manta da hargowar maƙiyanka,

Kada ka manta da hayaniyar da magabtanka suke ta yi.

Categories
ZAB

ZAB 75

Allah Ya Ƙasƙantar da Mugaye, Ya Ɗaukaka Adalai

1 Muna yabonka, ya Allah, muna yabonka!

Muna shelar sunanka mai girma,

Muna kuwa faɗa abubuwan banmamaki da ka aikata!

2 “Na ƙayyade lokacin yin shari’a,” in ji Ubangiji Allah,

“Zan kuwa yi shari’ar gaskiya.

3 Ko da duniya da dukan waɗanda yake zaune cikinta za su ɓace,

Zan ƙarfafa harsashin gininta.

4 Na faɗa wa masu girmankai kada su yi taƙama,

Na kuma faɗa wa mugaye kada su yi fāriya,

5 Na dai faɗa musu su daina yanga,

Su daina yin taƙama.”

6 Hukunci ba daga gabas, ko yamma,

Ko daga kudu, ko arewa yake zuwa ba.

7 Allah yake yin shari’a,

Yana ƙasƙantar da waɗansu, ya kuma ɗaukaka waɗansu.

8 Ubangiji yana riƙe da ƙoƙo,

Cike da sabon ruwan inabi mai ƙarfi,

Yana zuba shi, dukan mugaye kuwa suna ta sha,

Suka shanye shi ƙaƙaf.

9 Amma har abada ba zan daina yin magana a kan Allah na Yakubu ba,

Ko in daina raira yabbai gare shi.

10 Shi zai karya ikon mugaye,

Amma za a ƙara wa masu adalci ƙarfi.

Categories
ZAB

ZAB 76

Allah Mai Nasara Mai Hukunci

1 Allah sananne ne a Yahuza,

Mashahuri ne kuma a Isra’ila.

2 Wurin zamansa yana Urushalima,

A dutsen Sihiyona zatinsa yake.

3 A can yake kakkarya kiban abokan gāba,

Da garkuwoyinsu, da takubansu, i, har da dukan makamansu.

4 Ina misalin darajarka, ya Allah!

Ina misalin ɗaukakarka a sa’ad da ka komo daga kan duwatsu,

Daga korar abokan gābanka!

5 An kwashe ganimar sojojinsu masu ƙarfin hali,

Yanzu suna barci, barcin matattu,

Ba waninsu da ya ragu,

Da zai yi amfani da makamansa.

6 Sa’ad da ka fafare su, ya Allah na Yakubu,

Dawakansu da mahayansu suka fāɗi matattu.

7 Amma mutane suna jin tsoronka!

Wa zai iya tsayawa a gabanka

Sa’ad da ka yi fushi?

8 Daga Sama ka sanar da shari’arka,

Duniya ta tsorata, ta yi tsit,

9 Sa’ad da ka tashi domin ka yanke hukunci,

Domin ka ceci waɗanda ake zalunta a duniya.

10 Hasalar mutane ba ta ƙara kome, sai dai ta ƙara maka yabo.

Waɗanda suka tsira daga yaƙe-yaƙe za su kiyaye idodinka.

11 Ku ba Ubangiji Allahnku abin da kuka alkawarta masa,

Dukanku sauran al’umma da kuke kusa, ku kawo masa kyautai.

Allah yakan sa mutane su ji tsoronsa,

12 Yakan ƙasƙantar da shugabanni masu girmankai,

Ya tsoratar da manyan sarakuna.

Categories
ZAB

ZAB 77

Ta’aziyya a Lokacin Damuwa

1 Na ta da murya, na yi kuka ga Allah,

Na ta da murya, na yi kuka, ya kuwa ji ni.

2 A lokacin wahala, nakan yi addu’a ga Ubangiji,

Dukan dare nakan ɗaga hannuwana sama in yi addu’a,

Amma ban sami ta’aziyya ba.

3 Lokacin da na tuna da Allah na yi ajiyar zuciya.

Sa’ad da nake tunani,

Nakan ji kamar in fid da zuciya.

4 Ba ya barina in yi barci,

Na damu har na kāsa magana.

5 Na yi tunanin kwanakin da suka wuce,

Nakan kuma tuna da shekarun da suka wuce da daɗewa.

6 Dare farai ina ta tunani mai zurfi,

A cikin tunani nakan yi wa kaina tambaya.

7 A kullum ne Ubangiji zai yashe ni?

Ba kuma zai ƙara yin murna da ni ba?

8 Ya daina ƙaunata ke nan?

Alkawarinsa ba shi da wani amfani?

9 Allah ya manta da yin jinƙai ne?

Fushinsa ya maye matsayin juyayinsa ne?

10 Sa’an nan sai na ce, “Abin da ya fi mini zafi duka,

Shi ne ikon Maɗaukaki ya ragu.”

11 Zan tuna da manyan ayyukanka, ya Ubangiji,

Zan tuna da al’amura masu banmamaki da ka aikata a dā.

12 Zan tuna da dukan abubuwan da ka yi,

Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka.

13 Dukan abin da kake yi mai tsarki ne, ya Allah!

Ba wani allah mai girma kamarka!

14 Kai ne Allah wanda kake aikata al’ajabai,

Ka nuna ikonka cikin sauran al’umma.

15 Ta wurin ikonka ka fanshi jama’arka,

Zuriyar Yakubu da ta Yusufu.

16 Ya Allah, sa’ad da ruwaye suka gan ka, sai su tsorata,

Zurfafan teku kuma suka yi rawar jiki.

17 Gizagizai suka zubo da ruwa,

Aka buga tsawa daga sama,

Aka kuwa yi walƙiya ko’ina.

18 Bugawar tsawarka ta gama ko’ina,

Hasken walƙiya ya haskaka dukan duniya,

Duniya ta yi rawa, ta girgiza, ta kaɗu.

19 Ka yi tafiya a teku,

Ka haye teku mai zurfi,

Amma ba a ga shaida inda ka taka ba.

20 Ka bi da jama’arka yadda makiyayi yake yi,

Musa da Haruna suke lura da su.

Categories
ZAB

ZAB 78

Amincin Allah ga Jama’arsa

1 Ku kasa kunne ga koyarwata, ya ku jama’ata,

Ku kula da abin da nake faɗa.

2 Zan yi magana da ku,

In faɗa muku asirai na dā,

3 Abubuwan da muka ji muka kuwa sani,

Waɗanda kakanninmu suka faɗa mana.

4 Ba za mu ɓoye waɗannan abubuwa daga ‘ya’yanmu ba,

Amma za mu faɗa wa tsara mai zuwa

Labarin ikon Ubangiji, da manya manyan ayyukansa,

Da abubuwan banmamaki waɗanda ya aikata.

5 Ya ba da dokoki ga jama’ar Isra’ila,

Da umarnai ga zuriyar Yakubu.

Ya ba kakanninmu ka’idodi,

Don su koya wa ‘ya’yansu dokokinsa,

6 Saboda tsara mai zuwa ta koye su,

Su kuma su koya wa ‘ya’yansu.

7 Ta haka su ma za su dogara ga Allah,

Ba za su manta da abin da ya yi ba,

Amma a kullum za su riƙa biyayya da umarnansa.

8 Kada su zama kamar kakanninsu,

Jama’ar ‘yan tawaye marasa biyayya.

Ba su taɓa dogara ga Ubangiji da zuciya ɗaya ba,

Ba su kuwa yi masa aminci ba.

9 Ifraimawa waɗanda suka yi yaƙi da bakkuna da kibau

Suka gudu a ranar yaƙi.

10 Ba su kiyaye alkawarinsu da Allah ba,

Sun ƙi biyayya da dokokinsa.

11 Sun manta da abin da ya aikata,

Da mu’ujizan nan da ya nuna musu.

12 Kakanninsu na kallo sa’ad da Allah ya aikata wata mu’ujiza

A filin Zowan a ƙasar Masar.

13 Ya raba teku, ya ratsa da su ta cikinta,

Ya sa ruwa ya tsaya kamar bango.

14 Da rana sai ya bi da su da girgije,

Da dare kuwa ya bi da su da hasken wuta.

15 Ya tsaga duwatsu, suka buɗe a hamada,

Ya ba su ruwa daga cikin zurfafa.

16 Ya sa rafi ya fito daga cikin dutse,

Ya sa ruwan ya yi gudu kamar a kogi.

17 Amma sun ci gaba da yi wa Allah zunubi,

A hamada suka yi wa Maɗaukaki tawaye.

18 Da gangan suka jarraba Allah,

Da suka ce ya ba su irin abincin da suke so.

19 Suka yi magana gāba da Allah, suka ce,

“Ko Allah yana da iko ya ba mu abinci a hamada?

20 Gaskiya ce, ya bugi dutse,

Ruwa kuwa ya fito a yalwace,

Amma ko yana da iko ya ba da abinci da nama ga jama’arsa?”

21 Saboda haka Allah ya yi fushi sa’ad da ya ji su,

Ya aukar wa jama’arsa da wuta,

Fushinsa ya haɓaka a kansu,

22 Saboda ba su amince da shi ba,

Ba su kuma gaskata yana da ikon cetonsu ba.

23 Amma ya yi magana da sararin sama,

Ya umarci ƙofofinsa su buɗe,

24 Ya ba su tsaba daga sama,

Da ya sauko musu da manna, su ci.

25 Ta haka suka ci abincin mala’iku.

Allah ya ba su iyakar abin da za su iya ci.

26 Sa’an nan sai ya sa iskar gabas ta hura,

Da ikonsa kuma ya sa iskar kudu ta tashi.

27 Ya aika da tsuntsaye bisansu kamar ƙura,

Yawansu kamar yashi a gaɓa,

28 Sai suka fāɗo a zango,

Kewaye da alfarwai ko’ina.

29 Sai mutane suka ci suka ƙoshi,

Allah ya ba su iyakar abin da suke bukata.

30 Amma sa’ad da suke cikin ci,

Tun ba su ƙoshi ba,

31 Sai Allah ya yi fushi da su.

Ya karkashe ƙarfafan mutane,

Da samarin Isra’ila na gaske!

32 Ko da yake ya aikata mu’ujizai da yawa,

Duk da haka jama’a suka ci gaba da yin zunubi,

Ba su kuwa gaskata shi ba.

33 Ta haka ya ƙare kwanakinsu kamar fitar numfashi,

Bala’i ya aukar wa rayukansu farat ɗaya.

34 Amma sa’ad da ya kashe waɗansunsu,

Sai sauran suka juyo gare shi suka tuba,

Suka yi addu’a sosai a gare shi.

35 Sun tuna, ashe, Allah ne mai kiyaye su,

Sun tuna Maɗaukaki shi ne Mai Fansarsu.

36 Amma maganganunsu duka ƙarya ne,

Dukan abin da suka faɗa kuwa daɗin baki ne kawai.

37 Ba su yi masa biyayya ba,

Ba su yi aminci game da alkawarin da suka yi da shi ba.

38 Amma Allah ya yi wa jama’arsa jinƙai,

Ya gafarta zunubansu,

Bai hallaka su ba.

Sau da yawa yakan kanne fushinsa,

Ya dakatar da hasalarsa.

39 Yakan tuna su mutane ne kawai,

Kamar iskar da take hurawa ta wuce .

40 Sau da yawa suka tayar masa a hamada.

Sau da yawa suka sa shi yin ɓacin rai!

41 Suka yi ta jarraba Allah a kai a kai,

Suka kuwa sa Mai Tsarki na Isra’ila yin fushi.

42 Suka manta da ikonsa mai girma.

Suka manta da lokacin da ya cece su daga abokan gābansu,

43 Lokacin da ya aikata manyan ayyuka da mu’ujizai

A filin Zowan, ta ƙasar Masar.

44 Ya mai da koguna su zama jini,

Masarawa kuwa suka kasa sha daga rafuffukansu.

45 Ya aiko da ƙudaje gare su, suka wahalshe su,

Kwaɗi suka lalata filayensu.

46 Ya aiko da gamzari don su ci amfanin gonakinsu,

Ya aiko da ɗango su lalata gonakinsu.

47 Ya kashe kurangar inabinsu da ƙanƙara,

Ya kuma kashe itatuwan ɓaurensu da jaura.

48 Ya karkashe shanunsu da ƙanƙara,

Ya kuma karkashe garkunan tumakinsu da na awakinsu da tsawa.

49 Ya buge su da fushinsa mai zafi, da hasalarsa,

Ya sa su damuwa ƙwarai,

Da ya aiko da mala’iku masu hallakarwa.

50 Bai kanne fushinsa ba,

Bai bar su da rai ba,

Amma ya karkashe su da annoba.

51 Ya karkashe ‘yan fari maza

Na dukan iyalan da suke Masar.

52 Sa’an nan ya bi da jama’arsa

Kamar makiyayi, ya fito da su,

Ya yi musu jagora cikin hamada.

53 Ya bi da su lafiya, ba su kuwa ji tsoro ba,

Amma teku ta cinye abokan gābansu.

54 Ya kawo su tsattsarkar ƙasarsa,

Ya kawo su a duwatsun da shi kansa ya ci da yaƙi.

55 Ya kori mazaunan wurin sa’ad da jama’arsa suka dirkako,

Ya rarraba ƙasar ga kabilan Isra’ila,

A nan ya ba su izini su zauna a wurin, a cikin alfarwansu.

56 Amma sai suka yi wa Allah Mai Iko Dukka tawaye,

Suka jarraba shi.

Ba su kiyaye dokokinsa ba,

57 Amma suka yi tawaye da rashin aminci

Kamar kakanninsu,

Kamar kiban da aka harba da tanƙwararren baka,

Waɗanda ba su da tabbas.

58 Suka sa shi ya yi fushi saboda

Masujadansu na arnanci.

Suka sa ya ji kishi saboda gumakansu.

59 Allah ya yi fushi sa’ad da ya ga haka,

Don haka ya rabu da jama’arsa ɗungum.

60 Ya bar alfarwarsa da take a Shilo,

Wato wurin da yake zaune a dā, a tsakiyar mutane.

61 Ya yardar wa abokan gāba su ƙwace akwatin alkawari,

Inda aka ga ikonsa da darajarsa,

62 Ya ji fushi da jama’arsa,

Ya bar abokan gābansu su karkashe su.

63 Aka karkashe samari a cikin yaƙi,

‘Yan mata kuma suka rasa ma’aura.

64 Aka karkashe firistoci da takuba,

Matansu ba su yi makoki dominsu ba.

65 Daga bisani sai Ubangiji ya tashi

Kamar wanda ya farka daga barci,

Kamar jarumi wanda ya bugu da ruwan inabi.

66 Ya tura abokan gābansa baya,

Da mummunar kora mai bankunya

Da ba za su sāke tashi ba.

67 Ubangiji ya rabu da zuriyar Yusufu,

Bai kuma zaɓi kabilar Ifraimu ba.

68 A maimakonsu sai ya zaɓi kabilar Yahuza.

Ya zaɓi Dutsen Sihiyona, wanda yake ƙauna ƙwarai.

69 A can ya gina Haikalinsa,

Kamar wurin zamansa a Sama.

Ya kafa shi da ƙarfi kamar duniya,

Tabbatacce a kowane lokaci.

70 Ya zaɓi bawansa Dawuda,

Ya ɗauko shi daga wurin kiwon tumaki,

71 Ya ɗauko shi daga inda yake lura da ‘yan raguna.

Ya naɗa shi Sarkin Isra’ila,

Ya naɗa shi makiyayin jama’ar Allah.

72 Dawuda kuwa ya lura da su da zuciya ɗaya,

Da gwaninta kuma ya bi da su.

Categories
ZAB

ZAB 79

Makoki saboda An Lalatar da Urushalima

1 Ya Allah, arna sun fāɗa wa ƙasar jama’arka!

Sun ƙazantar da Haikalinka tsattsarka,

Sun bar Urushalima kufai.

2 Suka bar wa tsuntsaye gawawwakin jama’arka su ci,

Suka bar wa namomin jeji gawawwakin bayinka.

3 Suka zubar da jinin jama’arka kamar ruwa,

Jini ya yi ta gudu kamar ruwa

Ko’ina a Urushalima,

Ba ma wanda ya ragu don yă binne gawawwaki.

4 Sauran al’ummar da take kewaye da mu,

Suka maishe mu abin ba’a, suka yi mana dariya,

Suka yi mana ba’a.

5 Har yaushe za ka yi ta fushi da mu, ya Ubangiji?

Har abada ne?

Kullum ne fushinka zai yi ta ci kamar wuta?

6 Ka yi fushi da al’umman da ba su yi maka sujada,

Ka yi fushi da jama’ar da suka ƙi ka!

7 Sun karkashe mutanenmu,

Sun kuwa lalatar da ƙasarmu.

8 Kada ka hukunta mu saboda zunuban kakanninmu,

Amma ka yi mana jinƙai yanzu,

Gama mun fid da zuciya sarai.

9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu,

Saboda girmanka.

Ka cece mu, ka gafarta mana zunubanmu,

Don mutane su yabe ka.

10 Don me al’ummai za su tambaye mu cewa,

“Ina Allahnku?”

Bari mu ga ka hukunta al’ummai

Saboda sun zubar da jinin bayinka!

11 Ka kasa kunne ga nishin ‘yan sarƙa,

Ka kuɓutar da waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa,

Ta wurin ikonka mai girma.

12 Ya Ubangiji, ka rama wa al’umman nan har sau bakwai,

Saboda tsiwace-tsiwacen da suka yi maka.

13 Mu waɗanda muke jama’arka, tumakin garkenka,

Za mu gode maka, mu yabe ka har abada.

Categories
ZAB

ZAB 80

Addu’ar Komo da Al’umma

1 Ka kasa kunne gare mu, ya Makiyayin Isra’ila,

Ka ji mu, kai da kake shugaban garkenka,

Da kake zaune a kan kursiyinka, a bisa kerubobi.

2 Ka bayyana ƙaunarka ga kabilar Ifraimu,

Da ta Biliyaminu, da ta Manassa!

Ka nuna mana ikonka,

Ka zo ka cece mu!

3 Ka komo da mu, ya Allah!

Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!

4 Har yaushe ke nan ya Ubangiji Allah Mai Runduna,

Za ka yi ta fushi da addu’o’in jama’arka?

5 Ka ciyar da mu da hawaye,

Ka shayar da mu da babban ƙoƙo na hawaye.

6 Ka bar al’umman da take makwabtaka da mu

Su yi ta faɗa a kan ƙasarmu,

Abokan gābanmu kuma suna yi mana ba’a.

7 Ka komo da mu, ya Allah Mai Runduna!

Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!

8 Ka fito da kurangar inabi daga cikin Masar,

Ka kori sauran al’umma,

Ka dasa kurangar a ƙasarsu.

9 Ka gyara mata wuri don ta yi girma,

Saiwoyinta suka shiga ƙasa sosai,

Ta yaɗu, ta rufe dukan ƙasar.

10 Ta rufe tuddai da inuwarta,

Ta rufe manya manyan itatuwan al’ul da rassanta.

11 Rassanta sun miƙe har Bahar Rum,

Har zuwa Kogin Yufiretis.

12 Me ya sa ka rushe shingen da yake kewaye da ita?

Ga shi yanzu, duk mai wucewa yana iya satar ‘ya’yanta.

13 Aladen jeji kuma za su tattake ta,

Namomin jeji duka za su cinye ta.

14 Ka juyo wurinmu, ya Allah Mai Runduna!

Daga Sama, ka dube mu,

Ka zo ka ceci kurangar inabinka!

15 Ka zo ka ceci kurangar inabin nan

Wadda kai da kanka ka dasa,

Wannan ƙaramar kuranga,

Ka sa ta yi girma, ta yi ƙarfi sosai!

16 Abokan gābanmu sun sa mata wuta, sun sare ta,

Ka yi fushi da su, ka hallaka su!

17 Ka kiyaye jama’arka wadda ka zaɓa,

Ka keɓe ta.

Al’umman nan wadda ka sa ta yi girma, ta yi ƙarfi sosai!

18 Ba za mu ƙara rabuwa da kai ba,

Ka rayar da mu, mu kuwa za mu yabe ka.

19 Ka komo da mu, ya Ubangiji Allah Mai Runduna!

Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!