Categories
ZAB

ZAB 81

Waƙar Idi

1 Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah Mai Cetonmu,

Ku raira yabbai ga Allah na Yakubu!

2 A fara waƙa, ku buga bandiri,

Ku yi waƙoƙi masu daɗi da molaye, da garayu.

3 Ku busa ƙaho domin idin,

A amaryar wata,

Da a tsakiyar farin wata.

4 Wannan doka ce a Isra’ila,

Umarni ne kuma daga Allah na Yakubu.

5 Ya ba da wannan umarni ga jama’ar Isra’ila,

A lokacin da ya fita gāba da ƙasar Masar.

Na ji wata murya da ban saba ji ba tana cewa,

6 “Na ɗauke muku kayayyaki masu nauyi da kuke ɗauke da su a kā,

Na sa kuka ajiye kwandunan aikinku.

7 Sa’ad da kuke shan wahala

Kuka yi kira a gare ni, na kuwa cece ku.

Daga maɓuyata cikin hadiri, na amsa muku,

Na jarraba ku a maɓuɓɓugan Meriba.

8 “Ya kuma jama’ata Isra’ila ku kasa kunne,

Ina kuwa so ku saurara gare ni.

9 Faufau kada ku bauta wa gumaka,

Ko ku yi sujada ga wanina.

10 Ni ne Ubangiji Allahnku,

Wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar.

Ku buɗe bakinku, zan ciyar da ku.

11 “Amma jama’ata ba su kasa kunne gare ni ba.

Isra’ila ta ƙi yi mini biyayya.

12 Saboda haka na bar su su yi ta kangarewarsu,

Su aikata duk irin abin da suka ga dama.

13 Ina kuwa so jama’ata su kasa kunne gare ni,

Su kuwa yi mini biyayya!

14 Da sai in kori abokan gābansu nan da nan,

In yi nasara da dukan maƙiyansu.

15 Maƙiyana, za su sunkuya a gabana saboda tsoro,

Hukuncinsu na har abada ne.

16 Zan ciyar da ku da kyakkyawar alkama,

In ƙosar da ku da zuma.”

Categories
ZAB

ZAB 82

Tsautawa a kan Muguwar Shari’a

1 Allah yana matsayinsa a taron jama’arsa,

Yakan zartar da nufinsa a taron alloli.

2 Tilas ku daina yin rashin gaskiya a shari’a,

Ku daina goyon bayan mugaye!

3 Ku kāre hakkin talakawa da na marayu,

Ku yi adalci ga matalauta,

Da waɗanda ba su da mataimaki.

4 Ku kuɓutar da talakawa da matalauta,

Ku cece su daga ikon mugaye!

5 “Waɗanne irin jahilai ne ku, wawaye!

Kuna zaune cikin duhu,

Ga shi, ba adalci a duniya sam!

6 Na faɗa muku, ku alloli ne,

Cewa dukanku ‘ya’ya ne na Maɗaukaki.

7 Amma za ku mutu kamar kowane mutum,

Ku fāɗi kamar kowane basarauce.”

8 Ya Allah, ka zo, ka mallaki duniya,

Dukan al’ummai naka ne.

Categories
ZAB

ZAB 83

Addu’a don A Hallaka Abokan Gāban Isra’ila

1 Ya Allah, kada ka yi shiru,

Kada ka tsaya cik,

Ya Allah, kada kuma ka yi tsit!

2 Duba, abokan gābanka suna tawaye,

Maƙiyanka sun tayar.

3 Suna ta ƙulle-ƙulle a asirce gaba da jama’arka,

Suna shirya maƙarƙashiya gāba da waɗanda kake tsaronsu.

4 Suna cewa, “Ku zo, mu hallakar da al’ummarsu,

Don a manta da Isra’ila har abada!”

5 Suka yarda a kan abin da suka shirya,

Suka haɗa kai gāba da kai.

6 Su ne mutanen Edom, da Isma’ilawa,

Da mutanen Mowab, da Hagarawa,

7 Da mutanen Gebal, da na Ammon, da na Amalek,

Da na Filistiya, da na Taya.

8 Assuriya ma ta haɗa kai da su,

Haɗa kai ke nan mai ƙarfi da zuriyar Lutu.

9 Ka yi musu yadda ka yi wa Madayanawa,

Ka yi musu yadda ka yi wa Sisera

Da Yabin a Kogin Kishon,

10 Waɗanda aka kora a Endor,

Gawawwakinsu kuwa suka ruɓe a ƙasa.

11 Ka yi wa shugabannin yaƙinsu yadda ka yi wa Oreb da Ziyib,

Ka kori dukan masu mulkinsu yadda ka kori Zeba da Zalmunna,

12 Waɗanda suka ce, “Za mu ƙwace ƙasar da take ta Allah, ta zama tamu.”

13 Ya Allahna, ka warwatsa su kamar ƙura,

Ka warwatsa su kamar ciyayin da iska take hurawa.

14 Kamar yadda wuta take cin jeji,

Kamar yadda harshen wuta yake ƙone tuddai,

15 Ka runtume su da hadirinka,

Ka razanar da su da iskarka mai ƙarfi.

16 Ya Ubangiji, ka sa kunya ta rufe su,

Don su so su bauta maka.

17 Ka sa a kore su, a razanar da su har abada,

Ka sa su mutu, mutuwar ƙasƙanci!

18 Ka sa su sani kai kaɗai ne Ubangiji,

Kai kaɗai ne mamallakin dukan duniya!

Categories
ZAB

ZAB 84

Sa Zuciya ga Haikali

1 Ina ƙaunar Haikalinka ƙwarai,

Ya Allah Mai Iko Dukka!

2 A can nake so in kasance!

Ina marmarin farfajiyar Haikalin Ubangiji.

Da farin ciki mai yawa zan raira waƙa ga Allah Mai Rai.

3 Har ba’u ma sukan yi sheƙa,

Tsattsewa suna da sheƙunansu,

A kusa da bagadanka suke kiwon ‘ya’yansu.

Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina, Allahna.

4 Masu murna ne waɗanda suke zaune a Haikalinka,

Kullum suna raira yabonka!

5 Masu murna ne waɗanda suka sami ƙarfinsu daga gare ka,

Su waɗanda suka ƙosa su kai ziyara a Dutsen Sihiyona.

6 Sa’ad da suke ratsa busasshen kwari,

Sai ya zama maɓuɓɓugar ruwa,

Ruwan sama na farko yakan rufe wurin da tafkuna.

7 Sukan yi ta ƙara jin ƙarfi a cikin tafiyarsu,

Za su kuwa ga Allahn alloli a Sihiyona!

8 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Mai Runduna,

Ka ji ni, ya Allah na Yakubu!

9 Duba, ya Allah, kai ne garkuwarmu,

Ka dubi fuskar Sarkinmu, zaɓaɓɓenka.

10 Kwana guda da za a yi a Haikalinka,

Ya fi kwana dubu da za a yi a wani wuri dabam.

Na gwammace in tsaya a ƙofar Haikalin Allahna,

Da in zauna a gidajen mugaye.

11 Ubangiji shi ne makiyayinmu, sarkinmu mai daraja,

Yakan sa mana albarka, da alheri, da daraja,

Ba ya hana kowane abu mai kyau ga waɗanda suke aikata abin da yake daidai.

12 Masu farin ciki ne waɗanda suka dogara gare ka,

Ya Allah Mai Runduna!

Categories
ZAB

ZAB 85

Addu’a don Lafiyar Al’ummar

1 Ya Ubangiji, ka yi wa ƙasarka alheri,

Ka sāke arzuta Isra’ila kuma.

2 Ka gafarta wa jama’arka zunubansu,

Ka kuwa gafarta musu dukan kuskurensu,

3 Ka daina yin fushi da su,

Ka kuwa kawar da zafin fushinka.

4 Ka komo da mu, ya Allah Mai Cetonmu,

Ka daina jin haushinmu!

5 Za ka yi fushi da mu har abada?

Ba za ka taɓa hucewa ba?

6 Ka daɗa mana ƙarfi, ka yarda ka sabunta ƙarfinmu,

Mu kuwa, jama’arka, za mu yabe ka.

7 Ka ƙaunace mu da madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji,

Ka taimake mu da cetonka.

8 Ina kasa kunne ga abin da Ubangiji Allah yake cewa,

Mu da muke mutanensa, ya alkawarta mana salama,

Idan ba mu koma kan al’amuranmu na wauta ba.

9 Hakika a shirye yake yă ceci waɗanda suke girmama shi,

Kasancewarsa a ƙasar, ceto ne ga ƙasar.

10 Ƙauna da aminci za su sadu wuri ɗaya,

Adalci da salama za su gamu.

11 Amincin mutum zai yunƙura daga duniya, yă nufi sama.

Adalcin Allah kuwa zai dubo daga Sama.

12 Ubangiji zai arzuta mu,

Ƙasarmu kuwa za ta ba da amfanin gona mai yawa.

13 Adalci zai yi tafiya a gaban Ubangiji,

Yă shirya masa tafarki.

Categories
ZAB

ZAB 86

Addu’ar Neman Jinƙan Allah

1 Ka kasa kunne gare ni, ya Ubangiji, ka amsa mini,

Gama ba ni da ƙarfi, ba ni kuwa da mataimaki.

2 Ka cece ni daga mutuwa, saboda ni mai aminci ne a gare ka,

Ka cece ni saboda ni bawanka ne, ina kuwa dogara gare ka.

3 Kai ne Allahna, saboda haka ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji,

Ina yin addu’a a gare ka dukan yini.

4 Ka sa bawanka yă yi murna, ya Ubangiji,

Saboda addu’o’ina sun hau zuwa gare ka.

5 Ya Ubangiji, kai managarci ne, mai yin gafara,

Cike kake da madawwamiyar ƙauna ga dukan waɗanda suke yin addu’a gare ka.

6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji,

Ka ji kukana na neman taimako!

7 Nakan kira gare ka a lokacin wahala,

Saboda kakan amsa addu’ata.

8 Ba wani allah kamarka, ya Ubangiji,

Ba ko ɗaya, ba wanda zai iya aikata abin da kake aikatawa.

9 Dukan sauran al’umma da ka halitta

Za su zo su rusuna har ƙasa a gabanka.

Za su yabi girmanka,

10 Gama kai kaɗai ne Maɗaukaki, ya Allah,

Kai kaɗai ne ka aikata abubuwa na banmamaki.

11 Ya Ubangiji, ka koya mini abin da kake so in yi,

Ni kuwa zan yi maka biyayya da aminci.

Ka koya mini in bauta maka da zuciya ɗaya.

12 Zan yabe ka da zuciya ɗaya, ya Ubangiji Allahna,

Zan riƙa shelar girmanka har abada.

13 Wane irin girma madawwamiyar ƙaunarka take da shi a gare ni!

Gama ka cece ni daga zurfin kabari.

14 Masu girmankai sun tasar mini, ya Allah,

Ƙungiyar mugaye tana ƙoƙari ta kashe ni,

Mutanen da ba su kula da kai ba.

15 Ya Ubangiji, kai Allah ne mai jinƙai, mai ƙauna,

Mai jinkirin fushi, kullum kai mai alheri ne, mai aminci.

16 Ka juyo gare ni, ka yi mini jinƙai,

Ka ƙarfafa ni, ka cece ni,

Gama ina bauta maka, kamar yadda mahaifiyata ta yi.

17 Ka nuna mini alherinka, ya Ubangiji,

Sa’an nan su waɗanda suke ƙina za su sha kunya,

Sa’ad da suka ga ka ta’azantar da ni,

Ka kuma taimake ni.

Categories
ZAB

ZAB 87

Fa’idar Zama a Urushalima

1 Allah ya gina birninsa a bisa tsarkakan tuddai,

2 Yana ƙaunar birnin Urushalima fiye da kowane wuri a Isra’ila.

3 Ya birnin Allah, ka kasa kunne,

Ga abubuwan banmamaki da ya faɗa a kanka.

4 “Sa’ad da na lasafta sauran al’umma da suke yi mini biyayya,

Zan sa Masar da Babila a cikinsu,

Zan ce da Filistiya, da Taya, da Habasha,

Su ma na Urushalima ne.”

5 A kan Sihiyona kuwa za a ce,

“Dukan sauran al’umma nata ne.”

Maɗaukaki kuwa zai ƙarfafa ta.

6 Ubangiji zai rubuta lissafin jama’o’i,

Ya sa su duka cikin jimilla ta Urushalima.

7 Duk mazauna a wurin za su raira waƙa, su yi rawa,

Su ce, “Dukan maɓuɓɓugaina suna cikinka.”

Categories
ZAB

ZAB 88

Kukan Neman Taimako

1 Ya Ubangiji Allah, Mai Cetona,

Duk yini ina ta kuka,

Da dare kuma na zo gare ka.

2 Ka ji addu’ata,

Ka kasa kunne ga kukana na neman taimako!

3 Wahala mai yawa ta auko mini,

Har ina gab da mutuwa.

4 Ina daidai da sauran mutanen da suke gab da mutuwa,

Dukan ƙarfina ya ƙare.

5 An yashe ni a cikin matattu,

Kamar waɗanda aka karkashe,

Suna kuma kwance cikin kaburburansu,

Waɗanda ka manta da su ɗungum,

Waɗanda taimakonka ya yi musu nisa.

6 Ka jefar da ni cikin zurfin kabari,

Da cikin rami mafi zurfi, mafi duhu.

7 Fushinka yana da nauyi a kaina,

An turmushe ni a cikin tuƙuƙinka.

8 Ka sa abokaina su yashe ni,

Ka sa sun ware ni.

An kange ni, ba yadda zan kuɓuta.

9 Idanuna sun raunana saboda wahala.

Ya Ubangiji, kowace rana ina kira gare ka,

Ina ta da hannuwana zuwa gare ka da addu’a!

10 Kakan yi wa matattu mu’ujizai ne?

Sukan tashi su yabe ka?

11 Akan yi maganar madawwamiyar ƙaunarka a kabari?

Ko amincinka a inda ake hallaka?

12 Za a iya ganin mu’ujizanka a cikin duhu?

Ko kuwa alherinka a lahira?

13 Ya Ubangiji, ina kira gare ka, neman taimako,

Kowace safiya nakan yi addu’a gare ka.

14 Me ya sa ka yashe ni, ya Ubangiji?

Me ya sa ka ɓoye kanka daga gare ni?

15 Tun ina ƙarami nake shan wahala,

Har ma na kusa mutuwa,

Na tafke saboda nauyin hukuncinka.

16 Hasalarka ta bi ta kaina,

Tasar mini da kake ta yi, ta hallaka ni.

17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa,

Ta kowace fuska, sun rufe ni.

18 Ka sa har abokaina na kusa sun yashe ni,

Duhu ne kaɗai abokin zamana.

Categories
ZAB

ZAB 89

Alkawarin Allah da Dawuda

1 Ya Ubangiji zan raira waƙar

Madawwamiyar ƙaunarka koyaushe,

Zan yi shelar amincinka a dukan lokaci.

2 Na sani ƙaunarka za ta dawwama har abada,

Amincinka kuma tabbatacce ne kamar sararin sama.

3 Ka ce, “Na yi alkawari da mutumin da na zaɓa,

Na yi wa bawana Dawuda alkawari cewa,

4 ‘Daga zuriyarka kullum za a sami sarki,

Zan kiyaye mulkinka har abada.’ ”

5 Talikan da suke Sama suna raira waƙa a kan

Abubuwan banmamakin da kake yi,

Suna raira waƙa kan amincinka, ya Ubangiji.

6 Ba wani kamarka a Sama, ya Ubangiji,

Ba wani daga su cikin talikai da yake daidai da kai.

7 Ana girmama ka a cikin majalisar talikai,

Duk waɗanda suke kewaye da kai suna yin tsoronka ƙwarai.

8 Ya Ubangiji Allah, Mai Runduna,

Ba wani mai iko kamarka,

Kai mai aminci ne a kowane abu.

9 Kai kake mulkin haukan teku,

Kakan kwantar da haukan raƙuman ruwa.

10 Ka ragargaza dodon nan Rahab, ka kashe shi,

Da ƙarfin ikonka ka cinye maƙiyanka.

11 Duniya taka ce, haka ma samaniya taka ce,

Kai ne ka halicci duniya da dukan abin da yake cikinta.

12 Kai ne ka yi kudu da arewa,

Dutsen Tabor da Dutsen Harmon

Suna raira waƙa gare ka don farin ciki.

13 Kai kake da iko!

Kai kake da ƙarfi!

14 A gaskiya da adalci aka kafa mulkinka,

Akwai ƙauna da aminci a dukan abin da kake yi.

15 Masu farin ciki ne jama’ar da suke yi maka sujada, suna raira waƙoƙi,

Waɗanda suke zaune a hasken alherinka.

16 Suna murna dukan yini saboda da kai,

Suna kuwa yabonka saboda alherinka.

17 Kana sa mu ci babbar nasara,

Da alherinka kakan sa mu yi rinjaye,

18 Sabili da ka zaɓar mana mai kāre mu,

Kai, Mai Tsarki na Isra’ila,

Kai ne ka ba mu sarkinmu.

19 Ka faɗa wa amintattun bayinka a wahayin da ka nuna musu tun da daɗewa, ka ce,

“Na sa kambin sarauta a kan shahararren soja,

Na ba da gadon sarauta ga wanda aka zaɓa daga cikin jama’a.

20 Na zaɓi bawana Dawuda,

Na naɗa shi sarkinku.

21 Ƙarfina zai kasance tare da shi,

Ikona kuma zai ƙarfafa shi.

22 Abokan gābansa ba za su taɓa cin nasara a kansa ba,

Mugaye ba za su kore shi ba.

23 Zan ragargaza magabtansa,

In karkashe duk waɗanda suke ƙinsa.

24 Zan ƙaunace shi kullum, in amince da shi,

Zan sa ya yi nasara kullayaumin.

25 Zan faɗaɗa mulkinsa tun daga Bahar Rum,

Har zuwa Kogin Yufiretis.

26 Zai ce mini, ‘Kai ubana ne da Allahna,

Kai ne kake kiyaye ni, kai ne Mai Cetona.’

27 Zan maishe shi ɗan farina,

Mafi girma daga cikin dukan sarakuna.

28 Zan riƙa ƙaunarsa har abada,

Alkawarin da na yi da shi kuma zai tabbata har abada.

29 A kullayaumin daga cikin zuriyarsa ne za a naɗa sarki,

Mulkinsa zai dawwama kamar sararin sama.

30 “Amma idan zuriyarsa sun ƙi yin biyayya da shari’ata,

Ba su kuwa zauna cikin ka’idodina ba,

31 In sun ƙyale koyarwata,

Ba su kiyaye umarnaina ba,

32 To, sai in hukunta su saboda zunubansu,

Zan bulale su saboda laifofinsu.

33 Amma fa, ba zan daina ƙaunar Dawuda ba,

Ba kuwa zan rasa cika alkawarin da na yi masa ba.

34 Ba zan keta alkawarin da na yi masa ba,

Ba zan soke ko ɗaya daga cikin alkawaran da na yi masa ba.

35 “Da sunana mai tsarki na yi alkawari sau ɗaya tak,

Ba zan yi wa Dawuda ƙarya ba!

36 Zuriyarsa za ta kasance kullum,

Zan lura da mulkinsa muddin rana tana haskakawa.

37 Zai dawwama kamar wata,

Kamar amintaccen mashaidin nan da yake a sararin sama.”

38 Amma kana fushi da zaɓaɓɓen sarkinka,

Ka rabu da shi, ka yashe shi.

39 Ka soke alkawarinka wanda ka yi wa bawanka,

Ka jefar da kambinsa a cikin ƙazanta.

40 Ka rurrushe garun birninsa,

Ka mai da sansaninsa mai kagara kufai.

41 Dukan waɗanda suke wucewa za su sace masa kayansa,

Maƙwabtansa duka suna yi masa ba’a.

42 Ka ba maƙiyansa nasara,

Ka sa dukansu su yi murna.

43 Ka sa makamansa su zama marasa amfani,

Ka bari a ci shi da yaƙi.

44 Ka ƙwace masa sandan sarautarsa,

Ka buge gadon sarautarsa ƙasa.

45 Ka sa shi ya tsofe kafin lokacinsa,

Ka rufe shi da kunya.

46 Har yaushe za ka ɓoye kanka, ya Ubangiji?

Har abada ne?

Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?

47 Ka tuna kwanakin mutum kaɗan ne, ya Ubangiji,

Ka tuna yadda ka halicci mutane duka masu mutuwa ne!

48 Wa zai rayu har abada, ba zai mutu ba?

Ƙaƙa mutum zai hana kansa shiga kabari?

49 Ya Ubangiji, ina ƙaunarka ta dā?

Ina alkawaran nan waɗanda ka yi wa Dawuda?

50 Kada ka manta da yadda aka ci mutuncina, ni da nake bawanka,

Da yadda na daure da dukan cin mutuncin da arna suka yi mini.

51 Ya Ubangiji, kada ka manta da yadda maƙiyanka

suka ci mutuncin zaɓaɓɓen sarki da ka naɗa!

Suka yi ta cin mutuncinsa duk inda ya tafi.

52 Mu yabi Ubangiji har abada! Amin! Amin!

Categories
ZAB

ZAB 90

Allah Madawwami, Mutum mai Shuɗewa

1 Ya Ubangiji, a koyaushe kai ne wurin zamanmu.

2 Kafin a kafa tuddai,

Kafin kuma ka sa duniya ta kasance,

Kai Allah ne, Madawwami.

Ba ka da farko, ba ka da ƙarshe.

3 Kakan sa mutane su koma yadda suke,

Su zama ƙura.

4 A gare ka shekara dubu, kamar kwana ɗaya ne,

Kamar jiya ce wadda ta shige,

Gajeruwa ce kamar sa’a guda ta dare.

5 Kakan kwashe mutane kamar yadda ambaliyar ruwa take yi,

Kamar mafarki suke, ba su daɗewa.

Kamar tsire-tsire suke waɗanda suke tsirowa da safe,

6 Su yi girma har su yi huda,

Sa’an nan su yi yaushi su bushe da yamma.

7 Mun halaka ta wurin fushinka,

Mun razana saboda hasalarka.

8 Ka jera zunubanmu a gabanka,

Zunubanmu na ɓoye kuwa,

Ka sa su a inda za ka gan su.

9 Fushinka ya gajerta tsawon ranmu,

Ranmu ya ƙare kamar ajiyar zuciya.

10 Tsawon kwanakin ranmu duka a ƙalla shekara ce saba’in,

In kuwa muna da ƙarfi, shekara tamanin ne.

Duk da haka iyakar abin da waɗannan shekaru

Suke kawo mana, damuwa ce da wahala,

Nan da nan sukan wuce,

Tamu da ƙare.

11 Wa ya san iyakar ikon fushinka?

Wa ya san irin tsoron da hasalarka za ta kawo?

12 Ka koya mana mu sani ranmu na ɗan lokaci ne,

Domin mu zama masu hikima.

13 Ya Ubangiji, sai yaushe za ka ji tausayinmu?

Ka ji tausayin bayinka!

14 Ka cika mu da madawwamiyar ƙaunarka a kowace safiya,

Don mu raira waƙoƙin murna dukan kwanakin ranmu.

15 Yanzu sai ka sa mu yi farin ciki mai yawa,

Kamar yadda ka sa muka yi baƙin ciki

A dukan shekarun nan, da muka sha wahala.

16 Ka yarda mana, mu bayinka, mu ga ayyukanka masu girma,

Ka yardar wa zuriyarmu su ga ikonka mai girma.

17 Ka yarda, albarkarka ta kasance tare da mu, ya Ubangiji Allahnmu.

Ka sa mu yi nasara game da dukan abin da za mu yi!

I, ka ba mu nasara a dukan abin da muke yi!