Categories
W. YAH

W. YAH 17

Hukunta Babbar Karuwar

1 Sai ɗaya daga cikin mala’ikun nan bakwai masu tasoshin nan bakwai, ya zo ya yi mini magana, ya ce, “Zo in nuna maka hukuncin da za a yi wa babbar karuwar nan, wadda take zaune a bisa ruwa mai yawa,

2 wadda sarakunan duniya suka yi fasikanci da ita, wadda kuma mazaunan duniya suka jarabtu da yin fasikanci da ita.”

3 Sai ya ɗauke ni ya tafi da ni zuwa jeji, Ruhu yana iza ni, sai na ga wata mace a kan wata dabba ja wur, duk jikin dabbar sunayen saɓo ne, tana kuma da kawuna bakwai, da ƙaho goma.

4 Matar kuwa tana saye da tufafi masu ruwan jar garura, da kuma ja wur, ta ci ado da kayan zinariya, da duwatsun alfarma, da lu’ulu’u, tana a riƙe da ƙoƙon zinariya a hannunta, cike da abubuwan ƙyama, da ƙazantar fasikancinta.

5 A goshinta kuma an rubuta wani sunan asiri, “Babila mai girma, uwar karuwai, uwar abubuwa masu banƙyama na duniya.”

6 Sai na ga matar ta bugu da jinin tsarkaka, da kuma jinin mashaidan Yesu.

Da na gan ta, sai na yi mamaki ƙwarai da gaske.

7 Amma mala’ikan ya ce mini, “Don me kake mamaki? Zan buɗa maka asirin matar nan, da kuma na dabbar nan mai kawuna bakwai, da ƙaho goma, da take ɗauke da ita.

8 Dabbar nan da ka gani, wadda dā take nan, a yanzu kuwa ba ta, za ta hawo ne daga ramin mahallaka, ta je ta hallaka, mazaunan duniya kuma waɗanda tun a farkon duniya, ba a rubuta sunayensu a Littafin Rai ba, za su yi mamakin ganin dabbar, don dā tana nan, a yanzu ba ta, za ta kuma dawo.

9 Fahimtar wannan abu kuwa, sai a game da hikima. Wato, kawuna bakwai ɗin nan tuddai ne guda bakwai, waɗanda matar take a zaune a kai.

10 Har wa yau kuma, sarakuna ne guda bakwai, waɗanda biyar daga cikinsu aka tuɓe, ɗaya yana nan, ɗayan bai zo ba tukuna, sa’ad da ya zo kuwa, lalle zamaninsa na lokaci kaɗan ne kawai.

11 Dabbar da take nan dā, a yanzu kuwa ba ta, ita ce ta takwas, daga cikin bakwai ɗin nan kuma ta fito, za ta kuwa hallaka.

12 Ƙahonin nan goma kuwa da ka gani, sarakuna goma ne, waɗanda ba a naɗa ba tukuna, amma sa’a ɗaya tak, za a ba su ikon yin mulki tare da dabbar.

13 Waɗannan ra’ayinsu ɗaya ne, za su kuma bai wa dabbar nan ikonsu da sarautarsu.

14 Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, Ɗan Ragon kuwa zai cinye su, shi da waɗanda suke tare da shi, kirayayyu, zaɓaɓɓu, amintattu, domin shi ne Ubangijin iyayengiji.”

15 Sai mala’ikan nan ya ce mini, “Ruwan nan da ka gani, a inda karuwar nan take a zaune, jama’a ce iri iri, da taro masu yawa, da al’ummai, da harsuna.

16 Ƙahonin nan goma kuma da ka gani, wato, su da dabbar nan za su ƙi karuwar, su washe ta, su tsiraita ta, su ci namanta, su ƙone ta,

17 domin Allah ya nufe su da zartar da nufinsa, su zama masu ra’ayi ɗaya, su bai wa dabbar nan, mulkinsu, har a cika Maganar Allah.

18 Matar nan da ka gani kuwa, ita ce babban birnin da yake mulkin sarakunan duniya.”

Categories
W. YAH

W. YAH 18

Faɗuwar Babila Mai Girma

1 Bayan haka, na ga wani mala’ika yana saukowa daga Sama, mai iko da yawa, sai aka haskaka duniya da ɗaukakarsa.

2 Sai ya yi kira da murya mai ƙarfi, ya ce,

“Ta fāɗi! Babila mai girma ta fāɗi!

Ta zama mazaunin aljannu,

Matattarar kowane baƙin aljani,

Da kowane irin ƙazamin tsuntsu, abin ƙyama.

3 Dukkan al’ummai sun yi tsananin jarabar yin fasikanci da ita,

Sarakunan duniya kuma sun yi fasikanci da ita,

Attajiran duniya kuma sun arzuta da almubazzarancinta.”

4 Sai na ji wata murya daga Sama, tana cewa,

“Ku fito daga cikinta, ya ku jama’ata,

Kada zunubanta su shafe ku,

Kada bala’inta ya taɓa ku.

5 Domin zunubanta sun yi tsororuwa, sun kai har Sama,

Allah kuwa ya tuna da laifofinta.

6 Ku saka mata daidai da yadda ta yi,

Ku biya ta ninkin ayyukanta,

Ku dama mata biyun abin da ta dama muku.

7 Yadda ta ɗaukaka kanta, ta yi almubazzaranci,

Haka ku ma ku saka mata da azaba, da baƙin ciki gwargwadon haka.

Tun da yake a birnin zuciyarta ta ce, ‘Ni sarauniya ce, a zaune nake,

Ni ba gwauruwa ba ce,

Ba ni da baƙin ciki kuma har abada!’

8 Saboda haka, bala’inta zai aukar mata rana ɗaya,

Mutuwa, da baƙin ciki, da yunwa.

Za a kuma ƙone ta,

Domin Ubangiji Allah da yake hukunta ta Mai Ƙarfi ne.”

9 Sarakunan duniya kuma da suka yi fasikanci da zaman almubazzaranci da ita, za su yi mata kuka da kururuwa, in sun ga hayaƙin ƙunarta,

10 za su tsaya a can nesa, don tsoron azabarta, su ce,

“Kaitonka! Kaitonka, ya kai babban birni!

Ya kai birni mai ƙarfi, Babila!

A sa’a ɗaya hukuncinka ya auko.”

11 Attajiran duniya kuma suna yi mata kuka suna baƙin ciki, tun da yake, ba mai ƙara sayen kayansu,

12 wato, zinariya, da azurfa, da duwatsun alfarma, da lu’ulu’u, da lallausan lilin, da hajja mai ruwan jar garura, da siliki, da jan alharini, da itacen ƙanshi iri iri, da kayan hauren giwa iri iri, da kayan da aka sassaƙa da itace mai tsada, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na dutse mai sheƙi,

13 da kirfa, da kayan yaji, da turaren wuta, da mur, da lubban, da ruwan inabi, da mai, da garin alkama, da alkama, da shanu, da tumaki, da dawaki, da kekunan doki, da kuma bayi, wato, rayukan ‘yan adam.

14 “Amfanin da kika ƙwallafa rai a kai, har ya kuɓuce miki,

Kayan annashuwarki da na adonki sun ɓace miki, ba kuwa za a ƙara samunsu ba har abada!”

15 Attajiran waɗannan hajjoji da suka arzuta a game da ita, za su tsaya a can nesa don tsoron azabarta, suna kuka, suna baƙin ciki, suna cewa,

16 “Kaito! Kaiton babban birnin nan!

Wanda dā ya sa lallausan lilin, da tufafi masu ruwan jar garura, da kuma jan alharini,

Wanda ya ci ado da kayan zinariya, da duwatsun alfarma, da lu’ulu’u!

17 Domin a sa’a ɗaya duk ɗumbun dukiyar nan ta hallaka.”

Sai duk masu jiragen ruwa, da masu shiga, da masu tuƙi, da duk waɗanda cinikinsu ya gamu da bahar, suka tsaya a can nesa,

18 suna kururuwa da suka ga hayaƙin ƙunarsa, suna cewa,

“Wane birni ne ya yi kama da babban birnin nan?”

19 Har suka tula wa kansu ƙasa suna ta kuka, suna baƙin ciki, suna kururuwa, suna cewa,

“Kaito! Kaiton babban birnin nan!

Wanda duk masu jiragen ruwa a bahar suka arzuta da ɗumbun dukiyarsa,

A sa’a ɗaya ya hallaka.

20 Ki yi farin ciki saboda an yi masa haka, ya sama!

Ku yi farin ciki, ku tsarkaka da manzanni da annabawa, domin Allah ya rama muku abin da ya yi muku!”

21 Sai wani ƙaƙƙarfan mala’ika ya ɗauki wani dutse kamar babban dutsen niƙa, ya jefa a teku, ya ce,

“Haka za a fyaɗa Babila babban birni, da ƙarfi, ba kuwa za a ƙara ganinta ba.

22 Ba za a ƙara jin kiɗan masu molo, da mawaƙa, da masu sarewa, da masu bushe-bushe a cikinki ba,

Ba kuma za a ƙara ganin mai kowace irin sana’a a cikinki ba,

Ba kuma za a ƙara jin niƙa a cikinki ba,

23 Fitila ba za ta ƙara haskakawa a cikinki ba,

Ba kuma za a ƙara jin muryar ango da amarya a cikinki ba,

Don attajiranki, dā su ne ƙusoshin duniya,

An kuma yaudari dukkan al’ummai da sihirinki.

24 Har an tarar hakkin jinin annabawa da na tsarkaka suna a wuyanta, da kuma na duk waɗanda aka kashe a duniya.”

Categories
W. YAH

W. YAH 19

1 Bayan wannan na ji kamar wata sowa mai ƙarfi ta ƙasaitaccen taro a Sama, suna cewa,

“Halleluya! Yin ceto, da ɗaukaka, da iko, sun tabbata ga Allahnmu,

2 Don hukuncinsa daidai yake, na adalci ne,

Ya hukunta babbar karuwar nan wadda ta ɓata duniya da fasikancinta,

Ya kuma ɗauki fansar jinin bayinsa a kanta.”

3 Sai suka sāke yin sowa, suna cewa,

“Halleluya! Hayaƙinta yana tashi har abada abadin.”

4 Sai dattawan nan ashirin da huɗu, da rayayyun halittan nan huɗu, suka fāɗi suka yi wa Allah sujada, shi da yake zaune a kan kursiyin, suna cewa, “Amin. Halleluya!”

5 Sai aka ji wata murya daga kursiyin, tana cewa,

“Ku yabi Allahnmu, ya ku bayinsa,

Ku da kuke jin tsoronsa, yaro da babba.”

Bikin Auren Ɗan Rago

6 Sai na ji kamar wata sowar ƙasaitaccen taro, kamar ƙugin ruwa mai gudu, kamar aradu mai ƙara, suna cewa,

“Halleluya! Gama Ubangiji Allahnmu

Maɗaukaki shi ne yake mulki.

7 Mu yi ta murna da farin ciki matuƙa,

Mu kuma ɗaukaka shi,

Domin bikin Ɗan Ragon nan ya zo,

Amaryarsa kuma ta kintsa.

8 An yardar mata ta sa tufafin lallausan lilin

mai ɗaukar ido, mai tsabta.”

Lallausan lilin ɗin nan, shi ne aikin adalci na tsarkaka.

9 Sai mala’ikan ya ce mini, “Rubuta wannan, ‘Albarka tā tabbata ga waɗanda aka gayyata, zuwa cin abincin bikin Ɗan Ragon nan.’ ” Ya kuma ce mini, “Wannan ita ce Maganar Allah ta gaskiya.”

10 Sai na fāɗi a gabansa, don in yi masa sujada, amma, sai ya ce mini, “Ko kusa kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da ‘yan’uwanka, waɗanda suke shaidar Yesu. Allah za ka yi wa sujada.” Domin gaskiyar da Yesu ya bayyana ita ce ta ba da ikon yin annabci.

Mahayin Farin Doki

11 Sai na ga sama ta dāre, sai ga wani farin doki! Mahayinsa kuwa ana ce da shi Amintacce, Mai Gaskiya, yana hukunci da adalci, yana kuma yaƙi.

12 Idanunsa kamar harshen wuta suke, kansa da kambi da yawa, yana kuma da wani suna a rubuce, wanda ba wanda ya sani sai shi.

13 Yana saye da riga wadda aka tsoma a jini, sunan da ake kiransa da shi kuma, shi ne Kalman Allah.

14 Rundunonin Sama, saye da lallausan lilin fari mai tsabta, suna a biye da shi a kan fararen dawakai.

15 Daga cikin bakinsa wani kakkaifan takobi yake fitowa, wanda zai sare al’ummai da shi, zai kuwa mallake su da tsanani ƙwarai, zai tattake mamatsar inabi, ta tsananin fushin Allah Maɗaukaki.

16 Da wani suna a rubuce a jikin rigarsa, har daidai cinyarsa, wato Sarkin sarakuna, Ubangijin iyayengiji.

17 Sa’an nan na ga wani mala’ika tsaye a jikin rana. Sai kuma ya kira dukkan tsuntsaye da suke tashi a sararin sama, da murya mai ƙarfi, ya ce, “Ku zo, ku taru wurin babban bikin nan na Allah,

18 ku ci naman sarakuna, da naman sarakunan yaƙi, da naman ƙarfafa, da naman dawakai, da na mahayansu, da naman kowa da kowa, wato, na ɗa da na bawa, na yaro da na babba.”

19 Sai na ga dabbar nan, da sarakunan duniya, da rundunoninsu, sun taru, don su yaƙi wanda yake kan dokin, da kuma rundunarsa.

20 Sai aka kama dabbar, da kuma annabin nan na ƙarya tare da ita, wanda ya yi al’ajabai a gabanta, waɗanda da su ne ya yaudari waɗanda suka yarda a yi musu alamar dabbar nan, da kuma waɗanda suka yi wa siffarta sujada. Waɗannan biyu kuwa aka jefa su da ransu a cikin tafkin wuta da ƙibiritu.

21 Sauran kuwa aka sare su da takobin wanda yake a kan doki, wato, da takobin nan da yake fitowa daga cikin bakinsa. Dukan tsuntsaye kuwa suka ci namansu har suka yi gamba.

Categories
W. YAH

W. YAH 20

Shekara Dubu

1 Sa’an nan na ga wani mala’ika yana saukowa daga Sama, yana a riƙe da mabuɗin mahallaka, da kuma wata babbar sarƙa a hannunsa.

2 Sai ya kama macijin nan, wato, macijin nan na tun dā dā, wanda yake shi ne Ibilis, shi ne kuma Shaiɗan, ya ɗaure shi har shekara dubu,

3 ya jefa shi mahallakar, ya rufe, ya kuma yimƙe ta da hatimi, don kada ya ƙara yaudarar al’ummai, har dai shekarun nan dubu su ƙare. Bayan wannan lalle ne a sake shi zuwa ɗan lokaci kaɗan.

4 Sa’an nan na ga kursiyai, da waɗanda aka bai wa ikon hukunci, zaune a kai. Har wa yau, kuma na ga rayukan waɗanda aka fille wa kai saboda shaidar da suka yi wa Yesu, da kuma Maganar Allah, ba su kuwa yi wa dabbar nan da siffarta sujada ba, ba su kuma yarda a yi musu alamarta a goshinsu ko a hannunsu ba, sun sāke rayuwa, sun yi mulki tare da Almasihu har shekara dubu.

5 Sauran matattu kuwa, ba su sāke rayuwa ba, sai bayan da shekaran nan dubu suka cika. Wannan fa shi ne tashin matattu na farko.

6 Duk wanda yake da rabo a tashin nan na farko, mai albarka ne, tsattsarka ne. Mutuwa ta biyu ba ta da iko a kan irin waɗannan, amma za su zama firistocin Allah da na Almasihu, su kuma yi mulki tare da shi har shekara dubu.

7 Bayan shekaran nan dubu sun ƙare, sai a saki Shaiɗan daga ɗaurinsa,

8 ya kuma fito ya yaudari al’ummai waɗanda suke kusurwoyin nan huɗu na duniya, wato, Gog da Magog, ya tattara su saboda yaƙi, yawansu kamar yashin teku.

9 Sai kuma su bazu, su mamaye duk duniya, su yi wa sansanin tsarkaka da ƙaunataccen birni ƙawanya, sai wuta ta zubo daga sama ta lashe su.

10 Shi kuwa Ibilis mayaudarinsu, sai da aka jefa shi a tafkin wuta da ƙibiritu, a inda dabbar nan da annabin nan na ƙarya suke, za a kuma gwada musu azaba dare da rana har abada abadin.

Ranar Shari’a a Gaban Babban Farin Kursiyi

11 Sa’an nan na ga wani babban kursiyi fari, da wanda yake a zaune a kai, sai sama da ƙasa suka guje wa Zatinsa, suka ɓace.

12 Sai na ga matattu manya da yara, a tsaitsaye a gaban kursiyin, aka kuma buɗe littattafai. Sai kuma aka buɗe wani littafi, wanda yake shi ne Littafin Rai. Aka kuwa yi wa matattu shari’a bisa ga abin da yake a rubuce a cikin littattafan, gwargwadon aikin da suka yi.

13 Sai teku ta ba da matattun da suke a cikinta, mutuwa da Hades kuma sun ba da matattun da suke a gare su, aka kuwa yi wa kowa shari’a gwargwadon aikin da ya yi.

14 Sa’an nan aka jefa mutuwa da Hades a tafkin nan na wuta. Wannan ita ce mutuwa ta biyu, wato, tafkin wuta.

15 Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce a Littafin Rai ba, sai a jefa shi a tafkin nan na wuta.

Categories
W. YAH

W. YAH 21

Sabuwar Sama da Sabuwar Ƙasa

1 Sa’an nan na ga sabuwar sama da sabuwar ƙasa, don sama ta farko da ƙasa ta farko sun shuɗe, ba kuma sauran teku.

2 Sai na ga tsattsarkan birni kuma, Sabuwar Urushalima, tana saukowa daga Sama daga wurin Allah, shiryayyiya kamar amaryar da ta yi ado saboda mijinta.

3 Na kuma ji wata murya mai ƙara daga kursiyin, tana cewa, “Kun ga, mazaunin Allah na tare da mutane. Zai zauna tare da su, za su zama jama’arsa, Allah kuma shi kansa zai kasance tare da su,

4 zai share musu dukkan hawaye. Ba kuma sauran mutuwa, ko baƙin ciki, ko kuka, ko azaba, don abubuwan dā sun wuce.”

5 Sai na zaune a kan kursiyin ya ce, “Kun ga, ina yin kome sabo.” Ya kuma ce, “Rubuta wannan, domin maganar nan tabbatacciya ce, gaskiya ce kuma.”

6 Sai ya ce mini, “An gama! Ni ne Alfa, Ni ne Omega, Ni ne na Farko, Ni ne kuma na Ƙarshe. Duk mai jin ƙishirwa zan ba shi ruwa daga maɓuɓɓugar ruwan rai kyauta.

7 Duk wanda ya ci nasara, zai ci wannan gādo, wato, in zama Allahnsa, shi kuma ya zama ɗa a gare ni.

8 Amma matsorata, da marasa riƙon amana, da masu aikin ƙyama, da masu kisankai, da fasikai, da masu sihiri, da masu bautar gumaka, da kuma duk maƙaryata, duk rabonsu tafkin nan ne mai cin wuta da kibiritu, wanda yake shi ne mutuwa ta biyu.”

Sabuwar Urushalima

9 Sai kuma ɗaya daga cikin mala’ikun nan bakwai, masu tasoshin nan bakwai, cike da bala’i bakwai na ƙarshe, ya zo ya yi mini magana, ya ce, “Zo in nuna maka amarya, matar Ɗan Ragon.”

10 Sai ya ɗauke ni, Ruhu yana iza ni, ya kai ni wani babban dutse mai tsawo, ya nuna mini tsattsarkan birnin Urushalima yana saukowa daga Sama daga wurin Allah,

11 yana tare da ɗaukakar Allah. Hasken birnin yana ƙyalƙyali kamar wani irin nadirin dutse mai daraja, kamar yasfa, garau kamar ƙarau.

12 Yana da babban garu mai tsawo, da ƙofar gari goma sha biyu, a ƙofofi ɗin da akwai mala’iku goma sha biyu. A jikin ƙofofin kuma an rubuta sunayen kabilan nan goma sha biyu na Isra’ila,

13 a gabas, ƙofa uku, a yamma ƙofa uku, a kudu ƙofa uku, a arewa kuma ƙofa uku.

14 Garun birnin kuwa, tana da dutsen harsashi goma sha biyu, a jikinsu kuma an rubuta sunayen manzannin nan goma sha biyu na Ɗan Ragon.

15 Shi wanda ya yi mini magana kuwa yana da sandar awo ta zinariya, domin ya auna birnin, da ƙofofinsa, da garunsa.

16 Birnin murabba’i ne, tsawonsa da fāɗinsa duka ɗaya ne. Sai ya auna birnin da sandarsa, mil dubu da ɗari biyar, tsawonsa, da fāɗinsa da zacinsa, duka ɗaya suke.

17 Ya kuma auna garunsa, kamu ɗari da arba’in da huɗu ne na mutum, wato, na mala’ika ke nan.

18 Garun kuwa da yasfa aka gina shi, birnin kuma da zinariya zalla, garau kamar ƙarau.

19 An kuma ƙawata harsasan garun birnin da kowane irin dutse mai daraja. Yasfa shi ne na farko, na biyu saffir, na uku agat, na huɗu zumurrudu,

20 na biyar onis, na shida yaƙutu, na bakwai kirisolat, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofaras, na sha ɗaya yakinta, na sha biyu kuma ametis.

21 Ƙofofin gari goma sha biyun nan kuwa lu’ulu’u ne goma sha biyun, kowace ƙofa da lu’ulu’u guda aka yi ta, hanyar birnin kuwa zinariya ce zalla garau kamar ƙarau.

22 Ban kuwa ga wani Haikali a birnin ba, domin Haikalinsa Ubangiji Allah Maɗaukaki ne, da kuma Ɗan Ragon.

23 Birnin kuwa ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi, domin ɗaukakar Allah ita ce haskensa, Ɗan Ragon kuma fitilarsa.

24 Da haskensa al’ummai za su yi tafiya. Sarakunan duniya za su kawo darajarsu a gare shi.

25 Ƙofofinsa kuwa ba za a rufe su da rana ba har abada, ba kuwa za a yi dare a can ba.

26 Za a kuma kawo darajar al’ummai da girmansu a gare shi.

27 Amma ko kaɗan ba wani abu marar tsarki da zai shiga cikinsa, ko wani mai aikata abin ƙyama ko ƙarya, sai dai waɗanda aka rubuta sunayensu a Littafin Rai na Ɗan Ragon kaɗai.

Categories
W. YAH

W. YAH 22

1 Sa’an nan, sai ya nuna mini kogin ruwan rai, yana ƙyalli kamar ƙarau, yana gudana daga kursiyin Allah, shi da Ɗan Rago,

2 ta tsakiyar hanyar birnin kuma, ta kowane gefen kogin, akwai itatuwan rai masu haihuwar ‘ya’ya iri goma sha biyu, kowane wata suna haihuwa, ganyen itatuwan kuwa saboda lafiyar al’ummai ne.

3 Ba sauran wani abin la’antarwa, amma kursiyin Allah, shi da Ɗan Rago, zai kasance a cikinsa. Bayinsa za su bauta masa,

4 za su kuma ga fuskarsa, sunansa kuwa zai kasance a goshinsu.

5 Ba za a ƙara yin dare ba, ba za su bukaci hasken fitila, ko na rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su, za su kuma sha ni’imar Mulki har abada abadin.

Yesu Yana Zuwa da Wuri

6 Sai ya ce mini, “Wannan magana tabbatacciya ce, ta gaskiya ce kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa ya aiko mala’ikansa, ya nuna wa bayinsa abin da lalle ne zai auku ba da daɗewa ba.”

7 “Ga shi kuwa, ina zuwa da wuri. Albarka tā tabbata ga wanda yake kiyaye maganar annabcin littafin nan.”

8 Ni Yahaya, ni ne na ji, na kuma ga waɗannan abubuwa. Sa’ad da kuwa na ji su, na kuma gan su, sai na fāɗi a gaban mala’ikan da ya nuna mini su, domin in yi masa sujada.

9 Amma, sai ya ce mini, “Ko kusa kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da ‘yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye maganar littafin nan. Allah za ka yi wa sujada.”

10 Ya kuma ce mini, “Kada ka rufe maganar annabcin littafin nan, domin lokaci ya kusa.

11 Marar gaskiya yă yi ta rashin gaskiyarsa, fajiri kuwa yă yi ta fajircinsa, adali kuwa yă yi ta aikata adalcinsa, wanda yake tsattsarka kuwa ya yi ta zamansa na tsarki.”

12 “Ga shi, ina zuwa da wuri, tare da sakamakon da zan yi wa kowa gwargwadon abin da ya yi.

13 Ni ne Alfa, Ni ne Omega, Ni ne na Farko, Ni ne na Ƙarshe.”

14 Albarka tā tabbata ga masu wanke rigunansu, domin su sami izinin ɗiba daga itacen rai, su kuma shiga birnin ta ƙofa.

15 Waɗanda aka hana shiga birnin kuwa, su ne fajirai, da masu sihiri, da fasikai, da masu kisankai, da masu bautar gumaka, da kuma duk wanda yake son ƙarya, yake kuma yinta.

16 “Ni Yesu, na aiko mala’ikana a gare ka, da wannan shaida saboda ikilisiyoyi. Ni ne tsatson Dawuda, da zuriyarsa, Gamzaki mai haske.”

17 Ruhu da amarya suna cewa, “Zo.” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo.” Duk mai jin ƙishirwa ya zo, duk mai bukata, yă ɗibi ruwan rai kyauta.

18 Ina yi wa duk mai jin maganar annabcin littafin nan kashedi, in wani ya yi wani ƙari a kanta, Allah zai ƙara masa bala’in da aka rubuta a littafin nan.

19 In kuma wani ya yi ragi a maganar littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai, da na tsattsarkan birnin, waɗanda aka rubuta a littafin nan.

20 Shi wanda ya shaida abubuwan nan ya ce, “Hakika, ina zuwa da wuri.” Amin! Zo, ya Ubangiji Yesu.

21 Alherin Ubangiji Yesu yă tabbata ga dukkan tsarkaka. Amin!